Labarin Hasiya ne boyayye ga Ahalinsa kuma yanzu ba bu ita acikin Rayuwarsa.
Shiyasa kawai ya fad'a mata iya abunda ya sani game da Sadiq sannan ya tabbatar mata da cewa ko shi bai gayamasa ya koma karatu zariya ba.
Tahir ya Boye maganar Hasiya saboda akwai Amana Tsakaninsa da Sadiq bazai iya fallasa sirrinsaba, in dai ba shi ya nemi hakan ba.
Sun rabu akan zai bincika mata achan Zariya in da Sadiq ya ke zaune yanzu da kuma Halin da ya ke ciki domin tace ita fa bata yarda ba akwai abunda ya ke d'aukan Hankalin Sadiq a zariyan nan, sannan ta fad'a ta kara Fad'a Hallayar sadiq ta fara sauyawa.
Tahir suna gama waya da Anty Surayya ya kira Sadiq bai Dauka ba sai da ya kara kira ne sannan ya Dauka yana fad'a masa yana aji ne in ya fito zai kirasa.
Sai Tahir ya kara Tabbatarea duk da yasan Daman Anty Surayya bazata gayamasa karya ba
Haka ya yi ta dakon kiran Sadiq ammh har Dare bai kirasa ba, sannan shi din daya damu su yi mgana ya kirasa sai sharrin Network yasa bai same shi ba, Tahir yaji kamar ya zama Tsutsu ya gansa a Zariya.
Har wani Shamsu ya kira cikin yan makaranta da suka zauna tare da su yana Tambayansa ko Sadiq ya Dawo nan dakin ne again? Nan take shamsu ya tabbatar masa da cewa tafiyarsu ba Dadewa wasu yan makarantar suka kama Dakin nasu sai anan ya kara Tabbatarma da kansa cewa Sadiq ya Sauya Muhalli wannan karon.
Shi ko Sadiq sam ya manta da Tahir suna gama Lectures ya tafi wajen aikinsa sai Gabda mangariba ya koma gida.
Ya iske Hasiya ta gama girki ta share daki ya na tashin kamshi sannan itama ta ci gayunta kamar yadda ta fara sabama kanta acikin yan kwanakin da suke tare.
Babban abun da ke sakashi cikin Farinciki ya fita da Safe ya dawo ya iske Hasiya na jiransa cikin Farinciki nan take sai yaji komai na Duniya ya gama samu in dai ga shi ga Hasiya ne.
Baisan wani iri abu ne mai karfi haka yake ji a kanta ba abu d'aya ya sani Allah ya had'a zuciyarsa da ta Hasiya waje d'aya.
Tun dawowarsa ya zaunar da ita ya fad'amata cewa yanzu tare zasu zauna Ya samu gurbin cigaba da karatu sannan kamfanin da ya yi musu hidimar kasa sun Daukesa a aiki a matsayin ma'aikacin su cikakke, Hasiya ta yi murna da Farincikin jin wannan Labarin barin ma da ya ce tare zasu zauna tare yanzu.
Sai ya kasance sun fara shimfid'a wata Sabuwar Rayuwar da dukkansu ba su Shiryamata ba.
In ya na da Shiga cikin makaranta da Safe ya kan fara shiga kafin ya wuce wajen aiki daman kuma sun riga sun san ya na masters dinsa kuma sun amince da hakan.
In bazai shiga makarantar ba sai ya wuce wajen aikinsa in kuma ya Dawo gida suna manne da juna shi da Hasiya.
Girki ma tare suke yi ya na taimakamata da Dauko wannan suna yi suna Hira, Dibar ruwa shi ya ke mata wanki ma damam ya saba tare suke yi, abinci ma yanzu a kwano daya suke ci, in kuma baya Bukata sai su fita waje su ci abinci, da Daddare kafin su kwanta za su yi kallo ko kuma ya kunna musu game a babbar wayarsa su yi, ko kuma ya yi ta mata Hira kala kala na Duniya duk domin ya sakata Farinciki.
Yana waya da duka yan'uwanta da shi har da Amma, hankalinsu ya kwanta a zaton su da kyakyawan yakininsu Hasiya ta samu sukuni da zaman lafiya a gidan auranta.
Amma ta fi kowa jin dadin haka In Sadiq yace za su zo su gaisheta sai tace ba yanzu ba, tafi bukatar su natsu su samu kwanciyar Hankali da zaman lafiya.
Har gidan Adda Rukayya sun je tare ba dai su jima ba ne a gidan duk da ya Fahimci kamar ba su cika shakuwa kamar Adda Fati ba, bai matsa sai yaji wani abun ba, gidan ramatu kuwa sun je bai san iyaka ba har gidan Inna Talatu ta kaisa ya gaisheta ya yi mata alheri.
Kwata kwata Sadiq ya sauya Rayuwarsa gabadaya kamar ba shi ba, abu daya me bai sauya ba kwanan da suke yi Dabam Dabam, har gobe ita ta na cikin Daki shi kuma ya na Falo ne.
Wannan matakin kam Sadiq ya kasa Jarumtar ketare sa tukunnah.
*****
Yau ma bayan mun gama cin Tsiren da ya fita ya siyo mana da kayan Fruit muka zauna saman kujera muna kallo a karamar Computers dinsa.
Tun ba na Fahimtar fina finan har yanzu na Fara Fahimta nima.
Sanye ya ke da Riga da wando ammh wando 3quater rigar kuma mai gajerun Hannu.
Ni kuma na sanya wata Rigar barci na Doguwa mai kauri wanda Ramatu ne ta bani kyautar ta acikin kayan auranta Lokacin bikinta da ya ke a gida ban cika sakata ba, shiyasa bata ji wani jiki ba.
Ina zaune kusa da shi sai na yi matashi da kafad'arsa kamar yadda ya sabamin, bamu jima da gama jera kayansa acikin Wardrope dina ba da ya karbo daga wajen guga har da nawa, Da ba su da yawa sosai.
Na tuna muna cikin jeran kayan ya kalleni ya na fadin"Iya kayan sawan ki kenan ko kin bar wasu a gida?
Batare da Tunanin komai ba nace"Su kenan fa, don ma Adda Fati tamin Dinki Lokacin bikin mu."
Kai Tsaye ya kalleni ya na fadin"Daman an yi mana Biki ne?
Cikin ido ya kalleni nima ina kallonsa nace"Na manta Lokacin Tariyan mu zan ce."
Sai ya jinjina kai kafin yace"Kinga kuma nima akwai hakkin yi miki kaya a kaina fa."
Kai Tsaye nace"Ni na yafe maka Assadiq"
Da Sauri yace"Ni ban yafe ma kaina ba zan siya miki kaya masu yawa In sha Allahu."
A lokacin da zan kara mgana sai ya had'e rai yace baya son gaddama shiyasa na yi gum da bakina.
Ni yanzu bani da wata matsala sai wacce Ba'a rasa ba na yi kiba na kara Fari kamar bani bace wannan Hasiyar da ke Danwake a dogon gida da ke Samaru ba.
Ina yawan Tuna yan gidanmu in naga su Ummi na min wani abu sai na girgiza kai kawai, ni wani irin nau'in makirci da Ukuban gidan Haya ne ban sani ba ko nace ban gani ba ai sai dai na ba wasu Labari.
Sun gama yada min Habaici da karad'e anguwa da Sirrina shiyasa ba mai kulani ballatana ya shiga Sabgata.
Nima sai na kama kaina in ba Dalili mai karfi ba ko fitowa waje ba na yi.
Ni dai ina musu sallama da gaisuwa in muka had'u saboda Nasihan Assadiq da yace kada na Biye musu mu yi gaba da Juna mu sani Tunda Zama ya had'a mu waje daya ko da bazamu yi Huld'a da juna ba to ya zama Dole mu zama ma su yad'a sallama a tsakaninmu.
Shi ya kara nuna min cewa kada na Damu da mganar mutane a kaina abu daya zan yi yakini acikin raina shine Babu wani mai yi face Ubangijin sammai da kassai.
Zama da Assadiq na kara sani wasu abubuwan mutun ne mai Addini da Sanin ya kamata, ni kaina a gabansa gabadaya raina ilimi na ke yi, ya faramin karatun Qur'ani da asuba bayan ya dawo daga masallaci Domin ya Lura ina da Rauni ta bangaran sanin addinin ma gabadaya.
Sannan ya yi min fadan in na idar da sallah ba na tsayawa na yi azkar ballatana na yi addu'a ni kaina nasan gaakiya ya fad'a kwata kwata bani da Dakewa kan ibada da addu'a.
Ammh yanzu na fara Sauyawa ya sanar dani muhimmanci Addu'a da rike Allah Saboda duk bala'in da Mutum zai shiga in ka kad'aita Allah to shi zai sama ma mutum mafita.
K'aruwan da na samu sanadin zamana da Assadiq k'aruwa ce mai yawan da bazan iya kirga su duka ba.
Ni kaina nasan Assadiq ya shiga zuciyata da Duniyata gabadaya batare da na sani ba.
Idanuwana na wajen kallon ammh sam Hankalina ya tafi wani wajen sai da naji wayarsa na Vibration Gir! Gir alamun ana kiransa kenan, na yi mamakin ganin ana kira wayarsa sanin da na yi cewa in dai muna tare bai cika barin wayarsa a kunne ba.
Da Sauri ya Daukota daga gefe ya duba ganin Tahir ke kiransa yasa ya saci kallona ni kuma sanin baya barina ina sanin wasu abubuwan da suka Dangancesa batare da ya fad'amin ba yasa na kauda kaina kamar bansa ma ana kiransa ba.
Taba Fuskata ya yi Lokaci daya ya na fad'in"Kin fara barci ne?
Cikin kankance idanuwana nace"Eh na fara barci."
Kai Tsaye ya kashe kallon ya Dauke na'urar daga saman jikinsa ya ijiye a saman kujera ya saka duka Hannuwansa ya Dagoni.
Sumbatar goshina ya yi kafin ya dan Rumgumeni Lokaci daya ya na Fadin"To je ki kwanta ko?
Sai na gyada masa kai ya na rike da Hannuna har cikin Daki.
Ya gyaramin in da zan kwanta ni kuma na shiga tiolet na kama Ruwa ko da na fito ya na Tsaye yana jirana.
Na hau gadon ya lulluba min zani a saman kafata ya na fadin"Ki yi addu'a kafin barci ya Dauke ki "
Nan ma sai na kara Daga masa kaina har zai fita sai kuma ya Dawo da Dauri daidai fuskata ya Duko ya sumbaci labbana sannan ya juya ya fita daga dakin ya na fadin"Sai da Safe."
Ina jin ana ta kiran wayarsa bai Dauka ba, sai dai ya na fita ya jawomin kofar dakin ruf ya Rufeni.
Tunanina ya fara kai kawon abunda Assadiq ke boyemin wanda ban sani ba, Sai dai na bi mganar Amma da tace kada mutum ya matsa da sai ya san abunda ba'a so ya sani ba.
Gwara mutum ya yi shuru ya jira Lokacin da aka so ya san wani abun
Addu'an barcin nayi sannan na gyara kwanciya ba Dadewa sai barci.
Shi ko ba a falon ya tsaya ba, sannan ba'a a tsakar gidan ba sai da ya Bude gidan ya fita waje sannan ya Kira Tahir da ya ke ta Uban kiransa.
Tahir da ya gama Fusata ya na Daukan kiran da ya fara fad'in"Kai ammh dai dan wulakanci ne Sadiq."
Sadiq yace"Da na yi me kuma Dahiru?
Tahir ya kasa mgana Saboda Haushi Cikin Kufuluwa yace"Bansani ba. Nace bansani ba, ka manta kace zaka kira dazu? Yanzu ma kira nawa na yi maka baka Dauka ba?
Sadiq yace"Ina wani abun ne sanda ka kirani yanzu, dazu kuma ai na fadamaka uziri na ko?
Tahir yace"Ah Lalle Sadiq me ka koma yi a zariya?
Sadiq ya yi shuru kafin yace"Me kuwa? Karatu da aiki mana."
Domin daman Tunda ya rika ganin Kiran Tahir a kai akai a ransa yasan yaji Labarin dawowarsa zariya.
Cikin son sanin wani abu Tahir yace"Ammh shine baka gayamin ba Sadiq?
Sadiq yace"Ga shi yanzu ina fadamaka."
Tahir ya sauke Numfashi kafin yace"Anty Surayya ce ta kirani. Nan ya shiga gayamasa duk suka yi da ita.
Ya karishe da fad'in"Sadiq ka tabbata ba domin Hasiya ka dawo zariya ba?
Sadiq yace"Wata Hasiyar kuma? Akwai wani abu tsakanina da ita ne yanzu?
Tahir yace"Babu, ammh kuma dawowarka garin shima baya cikin Tsarin da muka yi mgana dakai."
Sadiq ya yi shuru kafin yace"Tahir aiki na samu, kuma tunda na samu wannan damar sai na kara wata damar na Cigaba da karatuna"
Tahir yace"Shikenan ammh ka kula Anty Surayya tace ka sauya hali sannan ta Umarceni da na saka ido a kanka.".
Sadiq cikin Halin ko in kula yace"To ka yi mata abunda ta saka baka da matsala da ni."
Tahir na Dariya yace"Har da Labarin wannan Zabiyar na bata?
Sadiq yace"Duk ka yi daidai ne."
Tahir yace"Kace eh mana in ba Tsoro ba."
Sadiq yace"Ni cikakken Namiji ne kuma Tsoro ba shi da Gurbi a wajen Cikakun maza Tahir.".
Tahir ya sheke da dariya Lokaci d'aya ya na fadin"Namiji Maza!
Sadiq ya yi mirmishi kafin yace"Tahir. Tahir mu kwana lafiya."
Tahir ya yi saurin tare shi da fadin"To a ina ka ke zaune yanzu?
Sadiq yace"Uhm nan kusa da kamfani mu na samu wajen zama saboda yafi kusa."
Duk yadda Tahir yaso ya gano wani abu Sai da Sadiq yasan yadda ya yi suka Rabu Lafiya batare da ya gane wani abu ba.
Sadaf sadaf kamar mara gaskiya ya koma Daki ya Rufe kofa, Hasiya ya fara lekawa yaga ta samu barci karisa shiga dakin ya yi ya shiga makewayi ya kama ruwa sannan ya fito ya sauya kaya zuwa jallabiya ya koma Falo bayan ya kara gyarama Hasiya kwanciya saura kiris ta fado kasa.
Akan doguwar kujeran da ya saba kwana ya kwanta ya fad'a Tunani bayan ya yi matashi da Hannayensa.
Tunanin makomar wannan Boyayyiyar Rayuwarsa nasa ya ke yi, ya na da tabbacin yadda Big sis ta fara zarginsa bazata yi kasa a gwiwa ba sai ta Binciko komai kuma Faruwan haka daidai ya ke da Tsarwatsewan komai batare da ya Shirya ba.
Ya zama Dole ya yi wani abu saboda Dauke musu hankali daga kara munana zargin da suke a kansa.
SULTANA ce ta fad'o masa a rai sai kuma yaga tabbas itace makaminsa a daidai wannan Lokacin.
Da ita zai yi amfani ya nuna musu cewa bai sauya ba, bayan Rayuwar da suka san shi da ita bai yin wata Rayuwar da suke zarginsa a kai.
Ya tuna tunda ya bar garin sau daya ya Kirata a waya, shima zai yi mgana da Umma me ya kira wayarta a kashe sai ya kira Sultanan yace ta kai mata.
Tun daga kuma ranar bai kara Kiranta ba ammh yana ganin sakonta a kai akai duk da yasan duk sakata aka yi ta rika yi masa wad'anan sakunan iskancin.
Sannan yaga maganarta a WhatsApp duk da shi sai ya yi sati bai bude data ba, shi kafafen sada zumunta ba su cika Damunsa ba Tahir ya yi har ya gaji da ya Fahimci baya Ra'ayi.
Da wannan Tunanin ya ta shi, yau wajen aiki zai je tunda bai da shiga makaranta.
Shiyasa da wuri ya fita Tea kawai ya sha ya fita ya bar Flat din da ya Rage agidan ana tarewa aciki.
Sai da yaje wajen aikinsa ya natsu sannan ya kira Sultana bayan ya Duba Lokaci yaga sun isa dawowa daga makaranta.
Sai ga shi Sadiq ya Daddage ya na yi ma Sultana Hira wanda ya ke da yakinin yan saka ido duk za su ji Labari kamar ya sani kowacce na yawan kiranta suna tambayanta kuna waya da Sadiq? Ranar sun samu Labari mai dadi ta sanar da su ya kirata sun sha fira.
Daga ranar kullum sai ya kirata in ya na wajen aiki duk da dai hiran ta su ta karatu da Tambayan gida ne ammah tabbas Hasashensa ya yi tasiri.
Surayya da kanta ta kirashi ta na yi mishi Tsiyan wai ya shiga hannu sai yadda suka ga Dama da shi.
Dariya ya rika yi a ransa ya na fad'in na shiga hannu ko kun shiga Hannu.
Har su Umma suna samun Labari kowa sai yaji dadi jin Sadiq yanzu ya nuna da Gaske ya na son Sultana.
Sai kuma mganar komawarsa Zariya ta bar Tunanin kowa.
Suka koma Binsu da Fatan alheri tare da kara koyama Sultana wasu Dubarun zamantakewar.
Sadiq ya na waya da Abba sosai tare da Mutanen shinkafi ammh sai in baya tare da Hasiya saboda gudun Tautsayi ma kashe wayarsa ya ke da Zarar ya dawo gidan nan.
Ana cikin Hakane Abba ya kirasa da Mganar Salima da d'an abokin kasuwancinsa Alhaji Jibril.
Tunda Had'in da yaso na Sadiq bai samu ba ya ba ma Mubarak izini ya zo ya nemi d'aya daga cikin ya'yansa.
Sadiq ya yi supporting mganar Sosai.
Acikin kuma Satin Mubarak yazo ganin Salima bayan Abba ya Kira Umma da Mama ya sanar da su komai.
Ba'a samu matsala ta bangaren kowa ba sai Salima ta fara compain din cewa ita karatu zata cigaba Tunda suna Zana jarabawar Fita ne daga Secondary, mama ta kira sauran ya'yan yan Dakin su, su Sa'ima suka shige da ita suna mata fad'an ta shiga Hankalinta ga Sultana nan kanwar bayanta zata yi aure ammh ita ta Samu tana wani iskanci.
Duk yadda ta nuna bata so sai da suka Tursasata ta amshi mganar Mubarak.
Har sakeena na fadin bata da Tunani ne? Ba gwara ta yi ta Riga sultanan aure ba ta na dai ji ta na kuma gani Sadiq din baya son auran Sultana ammh Uwarsa da yan'uwansa sun kafe sai an yi saboda sun san amfanin su kuma da ba sa son Sadiq din ya auri wata Daga waje.
Kananun manganganu suna ta tashi, Duk da ga junansu ba sa nuna yan Ubanci ammh akwai wannan kishin Tsakanin ya'yan da suka Had'a Uba d'aya a tsakaninsu.
Salima ba ta da mafita illah na Amince ma Mubarak sannan da yazo suka samu Lokaci suka gana sai taga zata yi auransa domin shima 80% ya yi daidai da Ra'ayinta kamar yadda shima ta yi masa daidai Dari bisa Dari.
Hajiya Murjanatu ba ta so wannan had'in ba saboda a cewarta ba Tsaran juna ba ne shi da Alhaji Sulaimanu kuma ta na da Tabbacin ba domin Allah zai had'a wannan auran ba
Da nuna raahin amincewarta Har ikirarin sakinta ya yi, kuma shima Mubarak din ya nuna mata ya na so, sannan da shawaran yaranta da na yan'uwanta sai ta koma ta yi shuru kawai Tunda ba ta da ta cewa.
Da kansa ya shirya yaje zariya wajen yan'uwansa ya fad'a musu cewa zai kira su in Lokacin neman auran ya taso.
Hajiya Murjanatu ta na mamakin irin zumunci na gidan mijinta da babu ruwansa kowa da kowa, ita kanta ta jima Rabonta da garin zariya da sunan wani sha'ani.
Suma ba sa zuwa ballatana matansu da ya'yansu hana rantsuwa ta san iyalan Alhaji Tanko da iyalansa, sai Goggo Saratu ita gwara ita ta na biyo dan'uwan nata.
Hajiya Halima ta garin ikko kuwa ba su had'u ya kai sau biyar ba.
Ita fa tun wani rasuwar kanin Babansu Zahra da akayi ta yawo da Cewar Dalilin yar da ya Haifa mai Farar kafa ce ta yi sanadiyar karayan arzikinsa da Mutuwarsa bata kara ganin Hajiya Halimar ba.
Su kansu yaran na su ba su san kowa ba domin da wayan su bai wuce sau d'aya suka taba zuwa garin da wayaun su ba.
In ta yi masa magana sai yace shi ya ji da aiki yara kuma suna karatu in tace ita ya barta ta rika zuwa sai yace a'a, rabonta da Zariya tun auran Diyar Kaninsa Saminu wajen Shekaru hud'u kenan.
Ita ta na ma so ta yi masa mganar
Showing 66001 words to 69000 words out of 98628 words
Shiyasa kawai ya fad'a mata iya abunda ya sani game da Sadiq sannan ya tabbatar mata da cewa ko shi bai gayamasa ya koma karatu zariya ba.
Tahir ya Boye maganar Hasiya saboda akwai Amana Tsakaninsa da Sadiq bazai iya fallasa sirrinsaba, in dai ba shi ya nemi hakan ba.
Sun rabu akan zai bincika mata achan Zariya in da Sadiq ya ke zaune yanzu da kuma Halin da ya ke ciki domin tace ita fa bata yarda ba akwai abunda ya ke d'aukan Hankalin Sadiq a zariyan nan, sannan ta fad'a ta kara Fad'a Hallayar sadiq ta fara sauyawa.
Tahir suna gama waya da Anty Surayya ya kira Sadiq bai Dauka ba sai da ya kara kira ne sannan ya Dauka yana fad'a masa yana aji ne in ya fito zai kirasa.
Sai Tahir ya kara Tabbatarea duk da yasan Daman Anty Surayya bazata gayamasa karya ba
Haka ya yi ta dakon kiran Sadiq ammh har Dare bai kirasa ba, sannan shi din daya damu su yi mgana ya kirasa sai sharrin Network yasa bai same shi ba, Tahir yaji kamar ya zama Tsutsu ya gansa a Zariya.
Har wani Shamsu ya kira cikin yan makaranta da suka zauna tare da su yana Tambayansa ko Sadiq ya Dawo nan dakin ne again? Nan take shamsu ya tabbatar masa da cewa tafiyarsu ba Dadewa wasu yan makarantar suka kama Dakin nasu sai anan ya kara Tabbatarma da kansa cewa Sadiq ya Sauya Muhalli wannan karon.
Shi ko Sadiq sam ya manta da Tahir suna gama Lectures ya tafi wajen aikinsa sai Gabda mangariba ya koma gida.
Ya iske Hasiya ta gama girki ta share daki ya na tashin kamshi sannan itama ta ci gayunta kamar yadda ta fara sabama kanta acikin yan kwanakin da suke tare.
Babban abun da ke sakashi cikin Farinciki ya fita da Safe ya dawo ya iske Hasiya na jiransa cikin Farinciki nan take sai yaji komai na Duniya ya gama samu in dai ga shi ga Hasiya ne.
Baisan wani iri abu ne mai karfi haka yake ji a kanta ba abu d'aya ya sani Allah ya had'a zuciyarsa da ta Hasiya waje d'aya.
Tun dawowarsa ya zaunar da ita ya fad'amata cewa yanzu tare zasu zauna Ya samu gurbin cigaba da karatu sannan kamfanin da ya yi musu hidimar kasa sun Daukesa a aiki a matsayin ma'aikacin su cikakke, Hasiya ta yi murna da Farincikin jin wannan Labarin barin ma da ya ce tare zasu zauna tare yanzu.
Sai ya kasance sun fara shimfid'a wata Sabuwar Rayuwar da dukkansu ba su Shiryamata ba.
In ya na da Shiga cikin makaranta da Safe ya kan fara shiga kafin ya wuce wajen aiki daman kuma sun riga sun san ya na masters dinsa kuma sun amince da hakan.
In bazai shiga makarantar ba sai ya wuce wajen aikinsa in kuma ya Dawo gida suna manne da juna shi da Hasiya.
Girki ma tare suke yi ya na taimakamata da Dauko wannan suna yi suna Hira, Dibar ruwa shi ya ke mata wanki ma damam ya saba tare suke yi, abinci ma yanzu a kwano daya suke ci, in kuma baya Bukata sai su fita waje su ci abinci, da Daddare kafin su kwanta za su yi kallo ko kuma ya kunna musu game a babbar wayarsa su yi, ko kuma ya yi ta mata Hira kala kala na Duniya duk domin ya sakata Farinciki.
Yana waya da duka yan'uwanta da shi har da Amma, hankalinsu ya kwanta a zaton su da kyakyawan yakininsu Hasiya ta samu sukuni da zaman lafiya a gidan auranta.
Amma ta fi kowa jin dadin haka In Sadiq yace za su zo su gaisheta sai tace ba yanzu ba, tafi bukatar su natsu su samu kwanciyar Hankali da zaman lafiya.
Har gidan Adda Rukayya sun je tare ba dai su jima ba ne a gidan duk da ya Fahimci kamar ba su cika shakuwa kamar Adda Fati ba, bai matsa sai yaji wani abun ba, gidan ramatu kuwa sun je bai san iyaka ba har gidan Inna Talatu ta kaisa ya gaisheta ya yi mata alheri.
Kwata kwata Sadiq ya sauya Rayuwarsa gabadaya kamar ba shi ba, abu daya me bai sauya ba kwanan da suke yi Dabam Dabam, har gobe ita ta na cikin Daki shi kuma ya na Falo ne.
Wannan matakin kam Sadiq ya kasa Jarumtar ketare sa tukunnah.
*****
Yau ma bayan mun gama cin Tsiren da ya fita ya siyo mana da kayan Fruit muka zauna saman kujera muna kallo a karamar Computers dinsa.
Tun ba na Fahimtar fina finan har yanzu na Fara Fahimta nima.
Sanye ya ke da Riga da wando ammh wando 3quater rigar kuma mai gajerun Hannu.
Ni kuma na sanya wata Rigar barci na Doguwa mai kauri wanda Ramatu ne ta bani kyautar ta acikin kayan auranta Lokacin bikinta da ya ke a gida ban cika sakata ba, shiyasa bata ji wani jiki ba.
Ina zaune kusa da shi sai na yi matashi da kafad'arsa kamar yadda ya sabamin, bamu jima da gama jera kayansa acikin Wardrope dina ba da ya karbo daga wajen guga har da nawa, Da ba su da yawa sosai.
Na tuna muna cikin jeran kayan ya kalleni ya na fadin"Iya kayan sawan ki kenan ko kin bar wasu a gida?
Batare da Tunanin komai ba nace"Su kenan fa, don ma Adda Fati tamin Dinki Lokacin bikin mu."
Kai Tsaye ya kalleni ya na fadin"Daman an yi mana Biki ne?
Cikin ido ya kalleni nima ina kallonsa nace"Na manta Lokacin Tariyan mu zan ce."
Sai ya jinjina kai kafin yace"Kinga kuma nima akwai hakkin yi miki kaya a kaina fa."
Kai Tsaye nace"Ni na yafe maka Assadiq"
Da Sauri yace"Ni ban yafe ma kaina ba zan siya miki kaya masu yawa In sha Allahu."
A lokacin da zan kara mgana sai ya had'e rai yace baya son gaddama shiyasa na yi gum da bakina.
Ni yanzu bani da wata matsala sai wacce Ba'a rasa ba na yi kiba na kara Fari kamar bani bace wannan Hasiyar da ke Danwake a dogon gida da ke Samaru ba.
Ina yawan Tuna yan gidanmu in naga su Ummi na min wani abu sai na girgiza kai kawai, ni wani irin nau'in makirci da Ukuban gidan Haya ne ban sani ba ko nace ban gani ba ai sai dai na ba wasu Labari.
Sun gama yada min Habaici da karad'e anguwa da Sirrina shiyasa ba mai kulani ballatana ya shiga Sabgata.
Nima sai na kama kaina in ba Dalili mai karfi ba ko fitowa waje ba na yi.
Ni dai ina musu sallama da gaisuwa in muka had'u saboda Nasihan Assadiq da yace kada na Biye musu mu yi gaba da Juna mu sani Tunda Zama ya had'a mu waje daya ko da bazamu yi Huld'a da juna ba to ya zama Dole mu zama ma su yad'a sallama a tsakaninmu.
Shi ya kara nuna min cewa kada na Damu da mganar mutane a kaina abu daya zan yi yakini acikin raina shine Babu wani mai yi face Ubangijin sammai da kassai.
Zama da Assadiq na kara sani wasu abubuwan mutun ne mai Addini da Sanin ya kamata, ni kaina a gabansa gabadaya raina ilimi na ke yi, ya faramin karatun Qur'ani da asuba bayan ya dawo daga masallaci Domin ya Lura ina da Rauni ta bangaran sanin addinin ma gabadaya.
Sannan ya yi min fadan in na idar da sallah ba na tsayawa na yi azkar ballatana na yi addu'a ni kaina nasan gaakiya ya fad'a kwata kwata bani da Dakewa kan ibada da addu'a.
Ammh yanzu na fara Sauyawa ya sanar dani muhimmanci Addu'a da rike Allah Saboda duk bala'in da Mutum zai shiga in ka kad'aita Allah to shi zai sama ma mutum mafita.
K'aruwan da na samu sanadin zamana da Assadiq k'aruwa ce mai yawan da bazan iya kirga su duka ba.
Ni kaina nasan Assadiq ya shiga zuciyata da Duniyata gabadaya batare da na sani ba.
Idanuwana na wajen kallon ammh sam Hankalina ya tafi wani wajen sai da naji wayarsa na Vibration Gir! Gir alamun ana kiransa kenan, na yi mamakin ganin ana kira wayarsa sanin da na yi cewa in dai muna tare bai cika barin wayarsa a kunne ba.
Da Sauri ya Daukota daga gefe ya duba ganin Tahir ke kiransa yasa ya saci kallona ni kuma sanin baya barina ina sanin wasu abubuwan da suka Dangancesa batare da ya fad'amin ba yasa na kauda kaina kamar bansa ma ana kiransa ba.
Taba Fuskata ya yi Lokaci daya ya na fad'in"Kin fara barci ne?
Cikin kankance idanuwana nace"Eh na fara barci."
Kai Tsaye ya kashe kallon ya Dauke na'urar daga saman jikinsa ya ijiye a saman kujera ya saka duka Hannuwansa ya Dagoni.
Sumbatar goshina ya yi kafin ya dan Rumgumeni Lokaci daya ya na Fadin"To je ki kwanta ko?
Sai na gyada masa kai ya na rike da Hannuna har cikin Daki.
Ya gyaramin in da zan kwanta ni kuma na shiga tiolet na kama Ruwa ko da na fito ya na Tsaye yana jirana.
Na hau gadon ya lulluba min zani a saman kafata ya na fadin"Ki yi addu'a kafin barci ya Dauke ki "
Nan ma sai na kara Daga masa kaina har zai fita sai kuma ya Dawo da Dauri daidai fuskata ya Duko ya sumbaci labbana sannan ya juya ya fita daga dakin ya na fadin"Sai da Safe."
Ina jin ana ta kiran wayarsa bai Dauka ba, sai dai ya na fita ya jawomin kofar dakin ruf ya Rufeni.
Tunanina ya fara kai kawon abunda Assadiq ke boyemin wanda ban sani ba, Sai dai na bi mganar Amma da tace kada mutum ya matsa da sai ya san abunda ba'a so ya sani ba.
Gwara mutum ya yi shuru ya jira Lokacin da aka so ya san wani abun
Addu'an barcin nayi sannan na gyara kwanciya ba Dadewa sai barci.
Shi ko ba a falon ya tsaya ba, sannan ba'a a tsakar gidan ba sai da ya Bude gidan ya fita waje sannan ya Kira Tahir da ya ke ta Uban kiransa.
Tahir da ya gama Fusata ya na Daukan kiran da ya fara fad'in"Kai ammh dai dan wulakanci ne Sadiq."
Sadiq yace"Da na yi me kuma Dahiru?
Tahir ya kasa mgana Saboda Haushi Cikin Kufuluwa yace"Bansani ba. Nace bansani ba, ka manta kace zaka kira dazu? Yanzu ma kira nawa na yi maka baka Dauka ba?
Sadiq yace"Ina wani abun ne sanda ka kirani yanzu, dazu kuma ai na fadamaka uziri na ko?
Tahir yace"Ah Lalle Sadiq me ka koma yi a zariya?
Sadiq ya yi shuru kafin yace"Me kuwa? Karatu da aiki mana."
Domin daman Tunda ya rika ganin Kiran Tahir a kai akai a ransa yasan yaji Labarin dawowarsa zariya.
Cikin son sanin wani abu Tahir yace"Ammh shine baka gayamin ba Sadiq?
Sadiq yace"Ga shi yanzu ina fadamaka."
Tahir ya sauke Numfashi kafin yace"Anty Surayya ce ta kirani. Nan ya shiga gayamasa duk suka yi da ita.
Ya karishe da fad'in"Sadiq ka tabbata ba domin Hasiya ka dawo zariya ba?
Sadiq yace"Wata Hasiyar kuma? Akwai wani abu tsakanina da ita ne yanzu?
Tahir yace"Babu, ammh kuma dawowarka garin shima baya cikin Tsarin da muka yi mgana dakai."
Sadiq ya yi shuru kafin yace"Tahir aiki na samu, kuma tunda na samu wannan damar sai na kara wata damar na Cigaba da karatuna"
Tahir yace"Shikenan ammh ka kula Anty Surayya tace ka sauya hali sannan ta Umarceni da na saka ido a kanka.".
Sadiq cikin Halin ko in kula yace"To ka yi mata abunda ta saka baka da matsala da ni."
Tahir na Dariya yace"Har da Labarin wannan Zabiyar na bata?
Sadiq yace"Duk ka yi daidai ne."
Tahir yace"Kace eh mana in ba Tsoro ba."
Sadiq yace"Ni cikakken Namiji ne kuma Tsoro ba shi da Gurbi a wajen Cikakun maza Tahir.".
Tahir ya sheke da dariya Lokaci d'aya ya na fadin"Namiji Maza!
Sadiq ya yi mirmishi kafin yace"Tahir. Tahir mu kwana lafiya."
Tahir ya yi saurin tare shi da fadin"To a ina ka ke zaune yanzu?
Sadiq yace"Uhm nan kusa da kamfani mu na samu wajen zama saboda yafi kusa."
Duk yadda Tahir yaso ya gano wani abu Sai da Sadiq yasan yadda ya yi suka Rabu Lafiya batare da ya gane wani abu ba.
Sadaf sadaf kamar mara gaskiya ya koma Daki ya Rufe kofa, Hasiya ya fara lekawa yaga ta samu barci karisa shiga dakin ya yi ya shiga makewayi ya kama ruwa sannan ya fito ya sauya kaya zuwa jallabiya ya koma Falo bayan ya kara gyarama Hasiya kwanciya saura kiris ta fado kasa.
Akan doguwar kujeran da ya saba kwana ya kwanta ya fad'a Tunani bayan ya yi matashi da Hannayensa.
Tunanin makomar wannan Boyayyiyar Rayuwarsa nasa ya ke yi, ya na da tabbacin yadda Big sis ta fara zarginsa bazata yi kasa a gwiwa ba sai ta Binciko komai kuma Faruwan haka daidai ya ke da Tsarwatsewan komai batare da ya Shirya ba.
Ya zama Dole ya yi wani abu saboda Dauke musu hankali daga kara munana zargin da suke a kansa.
SULTANA ce ta fad'o masa a rai sai kuma yaga tabbas itace makaminsa a daidai wannan Lokacin.
Da ita zai yi amfani ya nuna musu cewa bai sauya ba, bayan Rayuwar da suka san shi da ita bai yin wata Rayuwar da suke zarginsa a kai.
Ya tuna tunda ya bar garin sau daya ya Kirata a waya, shima zai yi mgana da Umma me ya kira wayarta a kashe sai ya kira Sultanan yace ta kai mata.
Tun daga kuma ranar bai kara Kiranta ba ammh yana ganin sakonta a kai akai duk da yasan duk sakata aka yi ta rika yi masa wad'anan sakunan iskancin.
Sannan yaga maganarta a WhatsApp duk da shi sai ya yi sati bai bude data ba, shi kafafen sada zumunta ba su cika Damunsa ba Tahir ya yi har ya gaji da ya Fahimci baya Ra'ayi.
Da wannan Tunanin ya ta shi, yau wajen aiki zai je tunda bai da shiga makaranta.
Shiyasa da wuri ya fita Tea kawai ya sha ya fita ya bar Flat din da ya Rage agidan ana tarewa aciki.
Sai da yaje wajen aikinsa ya natsu sannan ya kira Sultana bayan ya Duba Lokaci yaga sun isa dawowa daga makaranta.
Sai ga shi Sadiq ya Daddage ya na yi ma Sultana Hira wanda ya ke da yakinin yan saka ido duk za su ji Labari kamar ya sani kowacce na yawan kiranta suna tambayanta kuna waya da Sadiq? Ranar sun samu Labari mai dadi ta sanar da su ya kirata sun sha fira.
Daga ranar kullum sai ya kirata in ya na wajen aiki duk da dai hiran ta su ta karatu da Tambayan gida ne ammah tabbas Hasashensa ya yi tasiri.
Surayya da kanta ta kirashi ta na yi mishi Tsiyan wai ya shiga hannu sai yadda suka ga Dama da shi.
Dariya ya rika yi a ransa ya na fad'in na shiga hannu ko kun shiga Hannu.
Har su Umma suna samun Labari kowa sai yaji dadi jin Sadiq yanzu ya nuna da Gaske ya na son Sultana.
Sai kuma mganar komawarsa Zariya ta bar Tunanin kowa.
Suka koma Binsu da Fatan alheri tare da kara koyama Sultana wasu Dubarun zamantakewar.
Sadiq ya na waya da Abba sosai tare da Mutanen shinkafi ammh sai in baya tare da Hasiya saboda gudun Tautsayi ma kashe wayarsa ya ke da Zarar ya dawo gidan nan.
Ana cikin Hakane Abba ya kirasa da Mganar Salima da d'an abokin kasuwancinsa Alhaji Jibril.
Tunda Had'in da yaso na Sadiq bai samu ba ya ba ma Mubarak izini ya zo ya nemi d'aya daga cikin ya'yansa.
Sadiq ya yi supporting mganar Sosai.
Acikin kuma Satin Mubarak yazo ganin Salima bayan Abba ya Kira Umma da Mama ya sanar da su komai.
Ba'a samu matsala ta bangaren kowa ba sai Salima ta fara compain din cewa ita karatu zata cigaba Tunda suna Zana jarabawar Fita ne daga Secondary, mama ta kira sauran ya'yan yan Dakin su, su Sa'ima suka shige da ita suna mata fad'an ta shiga Hankalinta ga Sultana nan kanwar bayanta zata yi aure ammh ita ta Samu tana wani iskanci.
Duk yadda ta nuna bata so sai da suka Tursasata ta amshi mganar Mubarak.
Har sakeena na fadin bata da Tunani ne? Ba gwara ta yi ta Riga sultanan aure ba ta na dai ji ta na kuma gani Sadiq din baya son auran Sultana ammh Uwarsa da yan'uwansa sun kafe sai an yi saboda sun san amfanin su kuma da ba sa son Sadiq din ya auri wata Daga waje.
Kananun manganganu suna ta tashi, Duk da ga junansu ba sa nuna yan Ubanci ammh akwai wannan kishin Tsakanin ya'yan da suka Had'a Uba d'aya a tsakaninsu.
Salima ba ta da mafita illah na Amince ma Mubarak sannan da yazo suka samu Lokaci suka gana sai taga zata yi auransa domin shima 80% ya yi daidai da Ra'ayinta kamar yadda shima ta yi masa daidai Dari bisa Dari.
Hajiya Murjanatu ba ta so wannan had'in ba saboda a cewarta ba Tsaran juna ba ne shi da Alhaji Sulaimanu kuma ta na da Tabbacin ba domin Allah zai had'a wannan auran ba
Da nuna raahin amincewarta Har ikirarin sakinta ya yi, kuma shima Mubarak din ya nuna mata ya na so, sannan da shawaran yaranta da na yan'uwanta sai ta koma ta yi shuru kawai Tunda ba ta da ta cewa.
Da kansa ya shirya yaje zariya wajen yan'uwansa ya fad'a musu cewa zai kira su in Lokacin neman auran ya taso.
Hajiya Murjanatu ta na mamakin irin zumunci na gidan mijinta da babu ruwansa kowa da kowa, ita kanta ta jima Rabonta da garin zariya da sunan wani sha'ani.
Suma ba sa zuwa ballatana matansu da ya'yansu hana rantsuwa ta san iyalan Alhaji Tanko da iyalansa, sai Goggo Saratu ita gwara ita ta na biyo dan'uwan nata.
Hajiya Halima ta garin ikko kuwa ba su had'u ya kai sau biyar ba.
Ita fa tun wani rasuwar kanin Babansu Zahra da akayi ta yawo da Cewar Dalilin yar da ya Haifa mai Farar kafa ce ta yi sanadiyar karayan arzikinsa da Mutuwarsa bata kara ganin Hajiya Halimar ba.
Su kansu yaran na su ba su san kowa ba domin da wayan su bai wuce sau d'aya suka taba zuwa garin da wayaun su ba.
In ta yi masa magana sai yace shi ya ji da aiki yara kuma suna karatu in tace ita ya barta ta rika zuwa sai yace a'a, rabonta da Zariya tun auran Diyar Kaninsa Saminu wajen Shekaru hud'u kenan.
Ita ta na ma so ta yi masa mganar
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23 Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33