yayi idanunsa na sake kaɗawa suna sake komawa jajur fiye da yanda muka fito gida. Bayanin duk yanda yanda al'amarin ya faru ta shiga yimasa kamar yanda tayima su Sir Ahmad ma. Kasa cewa komai yay, sai jikinsa dake wani irin rawar bala'i, ƙwanjinsa da jijiyoyin kansa na sake buɗewa, yanda ƙirjinsa ke sama da ƙasa kawai zai tabbatar maka zuciyarsa na gudu maiban tsoro dake neman fin ƙarfin gangangar jikin nasa. ya saki hannunta ya nufi inda su oga A
liyu suke. Matsawa nai na rungumeta muna hawayen tare, sai dai ni saɓanin ita ina ƙarfafa zuciyata yau ina lallashinta, sai da naga ta tsagaita da kukan sannan na ɗagota na share mata hawayen. “Ki kwantar da hankalinki aunty Batool, insha ALLAHU zasu dawo, kosu wanene ALLAH bazai basu dama akan ƙudirinsu ba”. “ALLAH yasa haka mami” ta faɗa wasu hawayen na sake jiraro mata. kiran da oga Jabeer yaymin ne yasa na taimaka mata ta zauna a cikin motar.
Tun a yanda Jawaad ɗin ya taka birki sanda suka iso gidan su Sir Ahmad sukasan ransa a matuƙar ɓace yake fiyema da yanda sukai hasashen ganinsa. ganin Batool ta nufesa sai duk suka dakata daga yunƙurin zuwa inda yaken, bayan yabar wajen ya nufesu ne, Sir Ahmad yay saurin tararsa cikin zafin nama yana riƙe hannunsa “Jay! Ka kwantar da hankalinka, insha ALLAHU zamu gano inda suke, koma su wanene suka aikata hakan basuyi nisa damuba a halin yanzu tabbas, yanzu haka har su Jabeer sun fara ƙoƙarin gano inda suke. Ka nutsu banason ka fusata kanka da yawa, domin nutsuwarka ce abar buƙatarmu fiye da komai a yanzu. shin akwai wani da kake zargi ne?”.
Jawaad dake tsaye kawai yana kallon yanda su Aliyu da sauran ƴan sandan keta kai kawo akan al'amarin ya lumshe idanunsa yana busar da zazzafan numfashi, “Sir! Kowama zan iya zarga a halin yanzun, sai dai hakan bazai saka na kasa fidda ɗaya a cikin dubu ba”. “Nasani gwarzona”. Sir Ahmad ya faɗa yana ɗan bubbuga kafaɗar Jay ɗin cike dajin ƙarin alfahari da ƙwazon yaron.
Jabeer ne ya ƙaraso wajen riƙe da tab.. A hannu, yay salute ɗin Sir Ahmad sannan ya kalli Jay dake kallonsa shima. “Boss ƴan iskan mutanen nan basu bar wani alama ko kaɗan da za'a iya bibiyarsu ba, bayanan dake hannunmu ma a yanzu haka ko motar da sukazo a cikinta babu Number ma, abinda bayanan mutanen anguwa suke faɗa mana kawai motar baƙa ce, suma mutanen kuma baƙaƙen kayane a jikinsu, fuskokinsu a rufe”. Shiru yay yana kallon Jabeer cike da nazarin maganganunsa, kafin kuma ya kallesa yana ɗan cije lip ɗinsa na ƙasa, “Dama bana tunanin zasu bar wata alama ta zahiri, sai dai dolene za'a samu ta baɗini Jabeer. Zamanmu anan gidan baida wani amfani, inaga mu wuce office kawai”.
Jabeer yace, “Okay nima nayi wannan tunanin, dama isowarka muke jira muji ta bakinka, dan yanzu haka dai Number shi Alhaji Babba muketa ƙoƙarin bibiya saboda Batool tace tana zaton da ita ya tafi a jikinsa batare da suma maharan sun sani ba. a yanzu haka dai wayar na nuna tana titin gambari gab da babban titin ƴan robobi na gabashiya. Jami'anmu suma suna gab da isa wajen harda Aliyu”. Amsar Tab ɗin Jay yayi daga hannun Jabeer da sauri....
Hakan yay dai-dai da isowar Bilkisu da wani tunani yazo mata a zuciya inda suke. Sai da tai Salute ɗin Sir Ahmad itama sannan taɗan matsa kusa da Jay da hankalinsa kega Tab... ɗin da ya amsa a hannun Jabeer, amma yasan da zuwanta, dan ƙamshin turarenta ma ya ishesa shaidar tana wajen. “Sir anya kuwa wannan aiken ba daga gidancan bane?”. Da sauri Jay ya ɗago yana kallonta, “Wanne a ciki?” ya faɗa cike da ƙaguwa. “Inda na dawo daga farauta shekaran jiya”. Kafeta yay da ido dan maganarta na tafiya bisa ƙamshin gaskiya. Ta ƙara risinar da kanta cikin girmamawa a garesu, cigaba tai da faɗin, “Bazai yuwu ace dama ya barmu ba, dolene zai bibiyemu kodan maigadinsa, sai dai bamu da tabbas, hasashene kawai nayi Sir”. Jawaad yay wani ɗan murmushi yana maida duka hannayensa biyu ya goya a bayansa, taku ɗaya biyu yay sai kuma ya sake juyowa, hannunsa ɗaya ya sauke daga bayan ya tura cikin aljihu, ɗayan dake riƙe da tab... Kuma ya ɗagosa yana goga tab... Ɗin akan hancinsa. Daga Jabeer har Sir Ahmad da bilyn duk kallonsa sukeyi. Wani murmushin ya sakeyi da tsayawa cak, bily ya nuna da tab... ɗin hannunsa yana faɗin, “Maganarki akwai ƙamshin gaskiya, dolene a cikin biyu a samu ɗaya, idan kuma nai wani nazari zan iya ɗaurasu a mizani guda ya zama aikin haɗaka ne”. Ya ƙare maganar yana maida dubansa ga sir Ahmad da ke binsu da kallo kawai. Kafin yace wani abu Hafiz ma ya iso riƙe da waya alamar magana ya gamayi. “Mutanen nanfa inaga sun farga da
wayar jikin Alhaji babba, sam yanzu bama ganinsu alamar an kashe wayar”. Kallonsa duk sukayi, Sir Ahmad yace, “Dai-dai ina kuka daina samunsu?”. “Sir a Roundabout ɗin titin General hospital”. “General hospital?”. Jay ya faɗa cikin sigar tambaya. “Ƙwarai kuwa boss, ka duba ma zaka gani anan”. Tab... Ɗin Jay ya sake buɗewa, dai-dai inda Hafiz ya faɗa shima nan ya nuna masa, ya miƙama Jabeer tab... ɗin yana faɗin, “Yanzunan inason a bincikamin inda Alhaji Kokino yake, a kuma bincikamin inda Alhaji Ali da Qaseem suke, sai Mr Gebrail shima”. Yana maganarne yana daddana wayarsa daya ciro a aljihun wandonsa. Da mamaki na kallesa jin ya sako Dad da Yah Qaseem ciki, sai dai yanda yay kicin-kicin da fuska yasa na gaza cewa komai, sannan ma bani da wannan damar dan a fagen aiki muke matsayinsa na ogana ba miji ba. Da to muka amsa masa kawai, muna barin wajen.
Sir Ahmad dake kallon Jay yace, “Miyasa ka lissafo waɗanan mutanen? Kana zarginsu da aikata hakanne?”. “Sosaima kuwa Sir”. Jay ya faɗa yana ɗaura wayar a kunnensa jin an ɗaga. “Munkaila kana ina?”. Bansan amsar da aka bashiba daga can, ya gyara tsaiwarsa idonsa a sashen da su Bilkisu ke magana ita dasu Jabeer yace, “Ka ajiye wannan aikin, yanzun nan kaje gidan Alhaji Ali a ɗakkomin maigadin gidansa da kuku”. Kansa ya gyaɗa da sauke wayar.
“Jay ka sake sakani a duhu, wai ba kana magana bane akan Alhaji Ali dana sani baban Qaseem? Da shi Qassem ɗin kansa?”. Fuskar Jay cike da murmushin takaici ya jinjina ma Sir Ahmad kai, “Shi nake nufi Sir”. “To amma miya haɗashi da Alhaji kokino da har kake tunanin zasuyi aiki tare?”. “Hasashene kawai Sir”. Ya bama sir Ahmad ɗin amsa a taƙaice. Badan bai yarda da shi bane, yanason tabbatarwa kasafin ya buɗe aikin kowa ya sani........
__________________
BABA ƘAURA
______________
Tun a safiyar yau baba ƙaura ya sa ake nemar masa Number Jay sai dai ba'a samu ba, iya ƙoƙari sojan dake taimakama baba ƙaura idan zaiyi waya da Jay yayi amma wayoyin Jawaad ɗin duk sun ƙi shiga, sai kusan goma na safe da ƙyar ɗaya ta shiga, sai dai kuma anƙi ɗagawa kusan kira goma.
Ganin lokaci na sake ƙwacewa baba ƙaura yace sojan idan yasan inda gidan Jay yake ya kwatanta masa. Sojan shima bai saniba, dan haka yacema baba ƙaura bara yaje ya bincika ko za'a dace. Tunda sojan ya fita baba ƙaura ya kasa zaune ya kasa tsaye, ba komai ya kawo hakanba sai abinda ya jiyo a daren jiya, ga lokaci yanata sake tafiya kuma.
A jiya gaba ɗaya zaman ya gunduresa, jiyay yana sha'awar zagaya jeji, dan haka tun bayan sallar la'asar ya sulale yabar Barrack batare da sanin kowaba sai sojan nan da General ya ɗaura alhakin kula da shi akansa, yanda yaron ke masane ya sakashi ƙaunarsa harma yake masa wasu abubuwa na taimako, sannan baya ɓoye masa wasu abubuwan da suka shafesa, hakan yasa a fitarsa ta jiya ma ya sanar masa. Yayi ninƙaya cikin jejin sosai jiya bisa al'adarsa ta farauta da sanin sirrin jajejin da ALLAH ya bashi badan zaiyi farautar ba, dan ko karnuka babuma a tare da shi. Tun daga farkon dare har kusan ƙarshensa bai fitoba yana a dajin. sai da ya gama jin sirri mai girma daga shaiɗanun da suka maida wani yankin jejin nasu sannan ya fito, gab da asubahi ya shigo cikin gari, ana shiga salla masallaci yana isowa Barrack. A gaggauce yay alwala ya shiga masallacin shima. bayan an idar da salla ya saka sojan nan ya nemo masa Number Jawaad zaiyi magana da shi, sai dai sam an gaza samunsa, da aka samesan kuma ma sai bai ɗaukaba.....
Dawowar sojan tasakashi tsayawa cak daga kai kawon da yake faman yi da tunanin daren jiya, cikin ɗoki ya sanar masa an gano family house ɗin su Jawaad ɗin, kuma yana ƙyautata zaton a ciki jay yake zaune da iyalinsa. Baba ƙaura yayi murna, sojan nan yay masa rakkiya har bakin hanya ya sakashi a napep da faɗama mai napep ɗin inda zai kai baba ƙaura. Kasancewar gidan su Jay sanan nan gidane sai akaci sa'a mai napep ya sani.
Da ƙyar suka samu maigadin ya sauraresu, danshi tsoron baba ƙaura ne ya kamashi ganinsa sanye cikin fatun namin jeji, gashi babu hannu guda. Sai da baba ƙaura yayta m
asa magiya sannan ya sanar masa cewar Jawaad ba nan yake zauneba yanzu, yana gidansa da ke a A.Y street. Nanma sunsha daga kafin ya basu address ɗin, mai napep ɗin da yake yanada kirki shine ya sake ɗaukar baba ƙaura zuwa A.Y. sai dai suna shiga layin, motar Jay na fita. A gidan Jay ɗinma sunsha daga da maigadi kafin ya sanar musu Jawaad ɗin baya gida ya fita babu jimawa, suka roƙesa koya san inda ya nufa yace shi bai saniba. Sosai hankalin baba ƙaura ya sake tashi, burinsa kawai yaga Jawaad, harsun baro gidan ya roƙi mai napep ɗin suka sake komawa. Tambayar maigadi yayi ko ina drivern Jawaad ɗin?. Maigadi ya amsawa baba ƙaura a daƙile cewar yau Sadiq baizai zo aikiba yana gidansa. “Dan ALLAH ka faɗa mana inda gidan nashi yake zamuje mu samesa?”. baba ƙaura ya faɗa yana kallon mai gadin. A fusace mai gadi yace, “Kai malam kafa isheni, taya zan faɗa maka bayan bansan kaiɗin wanene ba? Nama sani ko cutar da waninsu zakayi, indai ma ogane yafi ƙarfinka dan shima wlhy aljanin kansane da kake ganinsa nan”. Murmushi baba ƙaura yayi, yace, “Yaro nafika sanin hakan ai, ka daure dai ka faɗa mana kokuma ka kira mana shi direban a waya idan ya gammu shi yasan manufarmu”. Kamar maigadi bazaiyi ba, sai kuma miya tuna oho masa ya ɗauka waya yay kiran Sadiq.
Babu jimawa saiga Sadiq mai napep shima ya kasowa, yana ganin baba ƙaura ya rikice, dan baiyi zaton shiɗin bane da gaske. Haƙuri yayta bashi akan abinda maigadi yay masa, baba ƙaura yace babu damuwa, so yake yanzunan ya kaisa inda Jawaad yake shidai. Maigadi dai jikinsa yayi sanyi ganin yanda Sadiq ya bama baba ƙaura muhimmanci, a take ya shiga bashi haƙuri. Baba ƙaura yay murmushi kawai yace karya damu........
___________________________
Anbar ƴan sanda zagaye da gidan Alhaji babba, su Jay kuma suka kwasa zuwa station dan aikin zaifi yuwuwa acan cikin sauri.
Bilkisu dai duk ta kasa sukuni akan sako Qaseem da Dad da Jay yayi a waɗanda yake zargi, zuwa yanzun kam tafara yarda da saƙe-saƙen zuciyaryarta, anya kuwa babu wani abu a rufe da bata saniba? Haka kawai mijinta da Dad bazasu ringa takun saƙa na kamar wasu maƙiya ba, a dafa surukinsa ne, sannan mijin yayar mahaifinsa ne. Ta tuna kallon kallo da suka dinga yima juna jiya duk da shi Dad yanata nuna babu komai.....
Da wannan tunanin a ranta suka isa station, babu mutane da yawa saboda weekend ne. Ni da su oga hafiz muka nufi office ɗin boss, shi kuma suka nufi na sir Ahmad..
Bamufi mintuna goma ba shima sai gashi ya shigo office ɗin ɗauke da takardu a hannu.
Kujerar zamansa ya nufa yana faɗin, “Miemaa taso kiyi wannan aikin”. Miƙewa nai daga inda nake zaune ni kaɗai na nufesa. Kujerar zamansa ya nunamin, babu musu na zauna shi kuma ya shiga ƙoƙarin dai-daita Computer ɗin.
Oga Jabeer da Hafiz dake can gaban Computers ɗin dake gefe guda biyu suka juyo suna kallonmu, Hafiz ne yace, “Boss babu watafa alamar waya data shiga tsakanin Alhaji kokino da Dadyn su Shahudah gaskiya, amma Dad yayi waya da Qaseem awa ɗaya da mintuna hamsin da uku da suka wuce. Barin inda nake yay ya nufesu, “Zamu iya samun maganar da sukayi?”. Jabeer da hankalinsa ke ga Computer gaba ɗaya yace, “Bazai yuwuba gaskiya, dan inhar mukai hakan zai gane, kasan wayar Qaseem tana da tsaro kamar yanda namu suke”. Jay yayi ɗan jimm na tunani. Numfashi ya furzar mai zafi yana dafe kansa dake sara masa, sai kuma ya zabura kamar wanda ya tuno wani abu. “Jabeer ina zuwa, bara na turo muku Numbers ɗin nan, dukansu inason mu tabbatar idan suna aiki a halin yanzun”. Yay maganar yana sake nufo inda nake, drawer ɗin jikin table ɗin ya jawo, flash ne da yawa a ciki, ya shiga ɗakkosu ɗaya bayan ɗaya yana duba rubutun da yay a jiki, cikin sa'a ya samo wanda yake nema, miƙamin yay yana faɗin, “Saka shi”. Yanda yake min magana babu wasa tattare da shi yasaka jikina har tsuma yake, sai da na gama dai-daita komai abubuwan dake cikin flash ɗin suka bayyana sannan ya ranƙwafo kaina, hannunsa ya ɗora bisa nawa dake a dafe da mouse muka ringa control ɗin Computer tare.
A haka Sir Ahmad da wasu jami'a
nmu manya biyu suka shigo suka samemu. Nan take aikin ya sake ɗaukar zafi, ni dai ta ɓangarena da taimakon boss nakeyi. Kusan minti goma sha biyar mun duƙufa, hankalin kowa nakan abinda ke gabansa akai knocking ƙofar office ɗin, batare da jiran izini ba oga Aliyu ya shigo da sallama. Inda muke ya nufo bayan yayi salute ɗin su Sir Ahmad. Bansan miya gwargwaɗa ma Boss a kunne ba, na gadai shima boss ɗin ya miƙe ya nufi Sir Ahmad cikin zafin nama. Sai kuma suka fice shi da Sir Ahmad ɗin daga office ɗin.........
_________________
BABA ƘAURA
_______________
Cikin mintuna ƙalilan suka iso station ɗin bisa taimakon Sadiq, sai dai kuma securitys sun hanasu shigowa musamman ganin yanayin baba ƙauran, sun musu roƙon duniya amma sun hanasu, Sadiq ya kira wayar Jay amma bai ɗagaba, hakan yasa suka koma gefe cike da damuwa, musamman ma baba ƙaura dake matuƙar matse da son ganin Jay.
Suna a wajen tsaye su biyu Sadiq na cigaba da kiran Number Jay sai ga motar su Aliyu, harma an buɗe musu gate zasu shige Aliyun ya hango baba ƙaura ta mirror. Sauke gilashin motar yay ya saka ɗaya daga cikin securitys ɗin yay masa magana da baba ƙaura. Ganin shi ɗinne dai kamar yanda yay hasashe sai ya bada umarnin barinsu su shigo. Bayan ya shige da motar ya samu waje yay fakin ya fito shi da waɗanda sukabi masu ƙwamushe Alhaji babba, gaisuwa kawai yay da baba ƙauran ya shiga ya sanarma Jay.
Duk da Aliyu ya sanar masa baba ƙaura ne hakan nbai hanashi yin mamakin ganinsa har station ɗinsu ba, ya ƙarasa fuskarsa babu walwala, dan duk yanda yaso aro fara'a ya azama fuskar tasa kamar yanda ya saba idan yaje wajen baba ƙaura hakan ya gagara. Cike da girmamawa suka gaishesa har Sir Ahmad.
Kallonsu baba ƙaura yay ya ɗauke kansa yana faɗin, “Kagani har a wajen aikinka ko?”.
Ɗan murmushi Jay yayi da cewa, “Babu komai baba, ai nasan zuwan naka mai muhimmanci ne”. “Hakane” baban ya faɗa yana sake maido hankalinsa garesu sosai. Yace, “Tun da safe na saka a nemomin kai amma hakan ya gagara, ba'a samunka da farko, daga baya kuma ta shiga ba'a ɗagawa”. Kai Jawaad ya dafe, “Dan ALLAH kayi haƙuri baba, wlhy na tsinci kainane a yanayin da komaima bazan iyaba”. “Gudun faruwar hakanne ya sakani yimaka neman gaggawa ai daman, tun bayan wucewarka na tafi jeji ne, acan ma na kwana, dan sai gabannin asubahi na shigo gari, sanda na iso nan har an shiga salla. Na saka a nema min kaine domin isar maka da saƙon abinda idona ya ganomin jiya a cikin jajin nan. Muhammad Jawaad lallai akwai matsala babba dake tunkaroku, da idona na gani, na kumaji da kunnena, gashi rashin samunka akan lokaci ya nunamin alamomin fara faruwar matsalar dana guda ma a yanzun”.
Hankalin Jawaad a tashe yace, “Baba hasashenka duk haka yake, yanzu haka zancen da nake maka anje har gida an ɗauke kakana, akan binciken inda zamu samesa muke”.
“Wannan shine shirinsu na farko dama. Na zauna nayi ƙyaƙyƙyawan nazari mutanen nan ba haka nan suke bibiyarka ba, akwai wani abu aƙasa wanda akwai jininka a ciki, ina nufin cikin zuri'arku akwai wanda ke tare da mutanen nan.....” cike da mamaki Sir Ahmad da Jay suke kallon baba ƙaura. Ya jinjina kansa yana cigaba da faɗin, “Kar kuyi mamaki, neman duniya babu wanda baya ɓatarwa, lallai kamar yanda na faɗa akwai wani abu a ƙasa, dan babu rami miya kawo rami? Bayan abubuwan dana sani ke a hannunku akwai wani abu da kuka ɗakko a wani gida ne?”. Sir Ahmad ya kalli Jay, shima ya kalleshi, sai kuma ya maida dubansa ga baban yana jinjina masa kai. “Akwai wani tukunya baba, wanda.........” ya labartama baba ƙaura da Sir Ahmad komai.
Baba ƙaura da keta faman
Showing 210001 words to 213000 words out of 249282 words
liyu suke. Matsawa nai na rungumeta muna hawayen tare, sai dai ni saɓanin ita ina ƙarfafa zuciyata yau ina lallashinta, sai da naga ta tsagaita da kukan sannan na ɗagota na share mata hawayen. “Ki kwantar da hankalinki aunty Batool, insha ALLAHU zasu dawo, kosu wanene ALLAH bazai basu dama akan ƙudirinsu ba”. “ALLAH yasa haka mami” ta faɗa wasu hawayen na sake jiraro mata. kiran da oga Jabeer yaymin ne yasa na taimaka mata ta zauna a cikin motar.
Tun a yanda Jawaad ɗin ya taka birki sanda suka iso gidan su Sir Ahmad sukasan ransa a matuƙar ɓace yake fiyema da yanda sukai hasashen ganinsa. ganin Batool ta nufesa sai duk suka dakata daga yunƙurin zuwa inda yaken, bayan yabar wajen ya nufesu ne, Sir Ahmad yay saurin tararsa cikin zafin nama yana riƙe hannunsa “Jay! Ka kwantar da hankalinka, insha ALLAHU zamu gano inda suke, koma su wanene suka aikata hakan basuyi nisa damuba a halin yanzu tabbas, yanzu haka har su Jabeer sun fara ƙoƙarin gano inda suke. Ka nutsu banason ka fusata kanka da yawa, domin nutsuwarka ce abar buƙatarmu fiye da komai a yanzu. shin akwai wani da kake zargi ne?”.
Jawaad dake tsaye kawai yana kallon yanda su Aliyu da sauran ƴan sandan keta kai kawo akan al'amarin ya lumshe idanunsa yana busar da zazzafan numfashi, “Sir! Kowama zan iya zarga a halin yanzun, sai dai hakan bazai saka na kasa fidda ɗaya a cikin dubu ba”. “Nasani gwarzona”. Sir Ahmad ya faɗa yana ɗan bubbuga kafaɗar Jay ɗin cike dajin ƙarin alfahari da ƙwazon yaron.
Jabeer ne ya ƙaraso wajen riƙe da tab.. A hannu, yay salute ɗin Sir Ahmad sannan ya kalli Jay dake kallonsa shima. “Boss ƴan iskan mutanen nan basu bar wani alama ko kaɗan da za'a iya bibiyarsu ba, bayanan dake hannunmu ma a yanzu haka ko motar da sukazo a cikinta babu Number ma, abinda bayanan mutanen anguwa suke faɗa mana kawai motar baƙa ce, suma mutanen kuma baƙaƙen kayane a jikinsu, fuskokinsu a rufe”. Shiru yay yana kallon Jabeer cike da nazarin maganganunsa, kafin kuma ya kallesa yana ɗan cije lip ɗinsa na ƙasa, “Dama bana tunanin zasu bar wata alama ta zahiri, sai dai dolene za'a samu ta baɗini Jabeer. Zamanmu anan gidan baida wani amfani, inaga mu wuce office kawai”.
Jabeer yace, “Okay nima nayi wannan tunanin, dama isowarka muke jira muji ta bakinka, dan yanzu haka dai Number shi Alhaji Babba muketa ƙoƙarin bibiya saboda Batool tace tana zaton da ita ya tafi a jikinsa batare da suma maharan sun sani ba. a yanzu haka dai wayar na nuna tana titin gambari gab da babban titin ƴan robobi na gabashiya. Jami'anmu suma suna gab da isa wajen harda Aliyu”. Amsar Tab ɗin Jay yayi daga hannun Jabeer da sauri....
Hakan yay dai-dai da isowar Bilkisu da wani tunani yazo mata a zuciya inda suke. Sai da tai Salute ɗin Sir Ahmad itama sannan taɗan matsa kusa da Jay da hankalinsa kega Tab... ɗin da ya amsa a hannun Jabeer, amma yasan da zuwanta, dan ƙamshin turarenta ma ya ishesa shaidar tana wajen. “Sir anya kuwa wannan aiken ba daga gidancan bane?”. Da sauri Jay ya ɗago yana kallonta, “Wanne a ciki?” ya faɗa cike da ƙaguwa. “Inda na dawo daga farauta shekaran jiya”. Kafeta yay da ido dan maganarta na tafiya bisa ƙamshin gaskiya. Ta ƙara risinar da kanta cikin girmamawa a garesu, cigaba tai da faɗin, “Bazai yuwu ace dama ya barmu ba, dolene zai bibiyemu kodan maigadinsa, sai dai bamu da tabbas, hasashene kawai nayi Sir”. Jawaad yay wani ɗan murmushi yana maida duka hannayensa biyu ya goya a bayansa, taku ɗaya biyu yay sai kuma ya sake juyowa, hannunsa ɗaya ya sauke daga bayan ya tura cikin aljihu, ɗayan dake riƙe da tab... Kuma ya ɗagosa yana goga tab... Ɗin akan hancinsa. Daga Jabeer har Sir Ahmad da bilyn duk kallonsa sukeyi. Wani murmushin ya sakeyi da tsayawa cak, bily ya nuna da tab... ɗin hannunsa yana faɗin, “Maganarki akwai ƙamshin gaskiya, dolene a cikin biyu a samu ɗaya, idan kuma nai wani nazari zan iya ɗaurasu a mizani guda ya zama aikin haɗaka ne”. Ya ƙare maganar yana maida dubansa ga sir Ahmad da ke binsu da kallo kawai. Kafin yace wani abu Hafiz ma ya iso riƙe da waya alamar magana ya gamayi. “Mutanen nanfa inaga sun farga da
wayar jikin Alhaji babba, sam yanzu bama ganinsu alamar an kashe wayar”. Kallonsa duk sukayi, Sir Ahmad yace, “Dai-dai ina kuka daina samunsu?”. “Sir a Roundabout ɗin titin General hospital”. “General hospital?”. Jay ya faɗa cikin sigar tambaya. “Ƙwarai kuwa boss, ka duba ma zaka gani anan”. Tab... Ɗin Jay ya sake buɗewa, dai-dai inda Hafiz ya faɗa shima nan ya nuna masa, ya miƙama Jabeer tab... ɗin yana faɗin, “Yanzunan inason a bincikamin inda Alhaji Kokino yake, a kuma bincikamin inda Alhaji Ali da Qaseem suke, sai Mr Gebrail shima”. Yana maganarne yana daddana wayarsa daya ciro a aljihun wandonsa. Da mamaki na kallesa jin ya sako Dad da Yah Qaseem ciki, sai dai yanda yay kicin-kicin da fuska yasa na gaza cewa komai, sannan ma bani da wannan damar dan a fagen aiki muke matsayinsa na ogana ba miji ba. Da to muka amsa masa kawai, muna barin wajen.
Sir Ahmad dake kallon Jay yace, “Miyasa ka lissafo waɗanan mutanen? Kana zarginsu da aikata hakanne?”. “Sosaima kuwa Sir”. Jay ya faɗa yana ɗaura wayar a kunnensa jin an ɗaga. “Munkaila kana ina?”. Bansan amsar da aka bashiba daga can, ya gyara tsaiwarsa idonsa a sashen da su Bilkisu ke magana ita dasu Jabeer yace, “Ka ajiye wannan aikin, yanzun nan kaje gidan Alhaji Ali a ɗakkomin maigadin gidansa da kuku”. Kansa ya gyaɗa da sauke wayar.
“Jay ka sake sakani a duhu, wai ba kana magana bane akan Alhaji Ali dana sani baban Qaseem? Da shi Qassem ɗin kansa?”. Fuskar Jay cike da murmushin takaici ya jinjina ma Sir Ahmad kai, “Shi nake nufi Sir”. “To amma miya haɗashi da Alhaji kokino da har kake tunanin zasuyi aiki tare?”. “Hasashene kawai Sir”. Ya bama sir Ahmad ɗin amsa a taƙaice. Badan bai yarda da shi bane, yanason tabbatarwa kasafin ya buɗe aikin kowa ya sani........
__________________
BABA ƘAURA
______________
Tun a safiyar yau baba ƙaura ya sa ake nemar masa Number Jay sai dai ba'a samu ba, iya ƙoƙari sojan dake taimakama baba ƙaura idan zaiyi waya da Jay yayi amma wayoyin Jawaad ɗin duk sun ƙi shiga, sai kusan goma na safe da ƙyar ɗaya ta shiga, sai dai kuma anƙi ɗagawa kusan kira goma.
Ganin lokaci na sake ƙwacewa baba ƙaura yace sojan idan yasan inda gidan Jay yake ya kwatanta masa. Sojan shima bai saniba, dan haka yacema baba ƙaura bara yaje ya bincika ko za'a dace. Tunda sojan ya fita baba ƙaura ya kasa zaune ya kasa tsaye, ba komai ya kawo hakanba sai abinda ya jiyo a daren jiya, ga lokaci yanata sake tafiya kuma.
A jiya gaba ɗaya zaman ya gunduresa, jiyay yana sha'awar zagaya jeji, dan haka tun bayan sallar la'asar ya sulale yabar Barrack batare da sanin kowaba sai sojan nan da General ya ɗaura alhakin kula da shi akansa, yanda yaron ke masane ya sakashi ƙaunarsa harma yake masa wasu abubuwa na taimako, sannan baya ɓoye masa wasu abubuwan da suka shafesa, hakan yasa a fitarsa ta jiya ma ya sanar masa. Yayi ninƙaya cikin jejin sosai jiya bisa al'adarsa ta farauta da sanin sirrin jajejin da ALLAH ya bashi badan zaiyi farautar ba, dan ko karnuka babuma a tare da shi. Tun daga farkon dare har kusan ƙarshensa bai fitoba yana a dajin. sai da ya gama jin sirri mai girma daga shaiɗanun da suka maida wani yankin jejin nasu sannan ya fito, gab da asubahi ya shigo cikin gari, ana shiga salla masallaci yana isowa Barrack. A gaggauce yay alwala ya shiga masallacin shima. bayan an idar da salla ya saka sojan nan ya nemo masa Number Jawaad zaiyi magana da shi, sai dai sam an gaza samunsa, da aka samesan kuma ma sai bai ɗaukaba.....
Dawowar sojan tasakashi tsayawa cak daga kai kawon da yake faman yi da tunanin daren jiya, cikin ɗoki ya sanar masa an gano family house ɗin su Jawaad ɗin, kuma yana ƙyautata zaton a ciki jay yake zaune da iyalinsa. Baba ƙaura yayi murna, sojan nan yay masa rakkiya har bakin hanya ya sakashi a napep da faɗama mai napep ɗin inda zai kai baba ƙaura. Kasancewar gidan su Jay sanan nan gidane sai akaci sa'a mai napep ya sani.
Da ƙyar suka samu maigadin ya sauraresu, danshi tsoron baba ƙaura ne ya kamashi ganinsa sanye cikin fatun namin jeji, gashi babu hannu guda. Sai da baba ƙaura yayta m
asa magiya sannan ya sanar masa cewar Jawaad ba nan yake zauneba yanzu, yana gidansa da ke a A.Y street. Nanma sunsha daga kafin ya basu address ɗin, mai napep ɗin da yake yanada kirki shine ya sake ɗaukar baba ƙaura zuwa A.Y. sai dai suna shiga layin, motar Jay na fita. A gidan Jay ɗinma sunsha daga da maigadi kafin ya sanar musu Jawaad ɗin baya gida ya fita babu jimawa, suka roƙesa koya san inda ya nufa yace shi bai saniba. Sosai hankalin baba ƙaura ya sake tashi, burinsa kawai yaga Jawaad, harsun baro gidan ya roƙi mai napep ɗin suka sake komawa. Tambayar maigadi yayi ko ina drivern Jawaad ɗin?. Maigadi ya amsawa baba ƙaura a daƙile cewar yau Sadiq baizai zo aikiba yana gidansa. “Dan ALLAH ka faɗa mana inda gidan nashi yake zamuje mu samesa?”. baba ƙaura ya faɗa yana kallon mai gadin. A fusace mai gadi yace, “Kai malam kafa isheni, taya zan faɗa maka bayan bansan kaiɗin wanene ba? Nama sani ko cutar da waninsu zakayi, indai ma ogane yafi ƙarfinka dan shima wlhy aljanin kansane da kake ganinsa nan”. Murmushi baba ƙaura yayi, yace, “Yaro nafika sanin hakan ai, ka daure dai ka faɗa mana kokuma ka kira mana shi direban a waya idan ya gammu shi yasan manufarmu”. Kamar maigadi bazaiyi ba, sai kuma miya tuna oho masa ya ɗauka waya yay kiran Sadiq.
Babu jimawa saiga Sadiq mai napep shima ya kasowa, yana ganin baba ƙaura ya rikice, dan baiyi zaton shiɗin bane da gaske. Haƙuri yayta bashi akan abinda maigadi yay masa, baba ƙaura yace babu damuwa, so yake yanzunan ya kaisa inda Jawaad yake shidai. Maigadi dai jikinsa yayi sanyi ganin yanda Sadiq ya bama baba ƙaura muhimmanci, a take ya shiga bashi haƙuri. Baba ƙaura yay murmushi kawai yace karya damu........
___________________________
Anbar ƴan sanda zagaye da gidan Alhaji babba, su Jay kuma suka kwasa zuwa station dan aikin zaifi yuwuwa acan cikin sauri.
Bilkisu dai duk ta kasa sukuni akan sako Qaseem da Dad da Jay yayi a waɗanda yake zargi, zuwa yanzun kam tafara yarda da saƙe-saƙen zuciyaryarta, anya kuwa babu wani abu a rufe da bata saniba? Haka kawai mijinta da Dad bazasu ringa takun saƙa na kamar wasu maƙiya ba, a dafa surukinsa ne, sannan mijin yayar mahaifinsa ne. Ta tuna kallon kallo da suka dinga yima juna jiya duk da shi Dad yanata nuna babu komai.....
Da wannan tunanin a ranta suka isa station, babu mutane da yawa saboda weekend ne. Ni da su oga hafiz muka nufi office ɗin boss, shi kuma suka nufi na sir Ahmad..
Bamufi mintuna goma ba shima sai gashi ya shigo office ɗin ɗauke da takardu a hannu.
Kujerar zamansa ya nufa yana faɗin, “Miemaa taso kiyi wannan aikin”. Miƙewa nai daga inda nake zaune ni kaɗai na nufesa. Kujerar zamansa ya nunamin, babu musu na zauna shi kuma ya shiga ƙoƙarin dai-daita Computer ɗin.
Oga Jabeer da Hafiz dake can gaban Computers ɗin dake gefe guda biyu suka juyo suna kallonmu, Hafiz ne yace, “Boss babu watafa alamar waya data shiga tsakanin Alhaji kokino da Dadyn su Shahudah gaskiya, amma Dad yayi waya da Qaseem awa ɗaya da mintuna hamsin da uku da suka wuce. Barin inda nake yay ya nufesu, “Zamu iya samun maganar da sukayi?”. Jabeer da hankalinsa ke ga Computer gaba ɗaya yace, “Bazai yuwuba gaskiya, dan inhar mukai hakan zai gane, kasan wayar Qaseem tana da tsaro kamar yanda namu suke”. Jay yayi ɗan jimm na tunani. Numfashi ya furzar mai zafi yana dafe kansa dake sara masa, sai kuma ya zabura kamar wanda ya tuno wani abu. “Jabeer ina zuwa, bara na turo muku Numbers ɗin nan, dukansu inason mu tabbatar idan suna aiki a halin yanzun”. Yay maganar yana sake nufo inda nake, drawer ɗin jikin table ɗin ya jawo, flash ne da yawa a ciki, ya shiga ɗakkosu ɗaya bayan ɗaya yana duba rubutun da yay a jiki, cikin sa'a ya samo wanda yake nema, miƙamin yay yana faɗin, “Saka shi”. Yanda yake min magana babu wasa tattare da shi yasaka jikina har tsuma yake, sai da na gama dai-daita komai abubuwan dake cikin flash ɗin suka bayyana sannan ya ranƙwafo kaina, hannunsa ya ɗora bisa nawa dake a dafe da mouse muka ringa control ɗin Computer tare.
A haka Sir Ahmad da wasu jami'a
nmu manya biyu suka shigo suka samemu. Nan take aikin ya sake ɗaukar zafi, ni dai ta ɓangarena da taimakon boss nakeyi. Kusan minti goma sha biyar mun duƙufa, hankalin kowa nakan abinda ke gabansa akai knocking ƙofar office ɗin, batare da jiran izini ba oga Aliyu ya shigo da sallama. Inda muke ya nufo bayan yayi salute ɗin su Sir Ahmad. Bansan miya gwargwaɗa ma Boss a kunne ba, na gadai shima boss ɗin ya miƙe ya nufi Sir Ahmad cikin zafin nama. Sai kuma suka fice shi da Sir Ahmad ɗin daga office ɗin.........
_________________
BABA ƘAURA
_______________
Cikin mintuna ƙalilan suka iso station ɗin bisa taimakon Sadiq, sai dai kuma securitys sun hanasu shigowa musamman ganin yanayin baba ƙauran, sun musu roƙon duniya amma sun hanasu, Sadiq ya kira wayar Jay amma bai ɗagaba, hakan yasa suka koma gefe cike da damuwa, musamman ma baba ƙaura dake matuƙar matse da son ganin Jay.
Suna a wajen tsaye su biyu Sadiq na cigaba da kiran Number Jay sai ga motar su Aliyu, harma an buɗe musu gate zasu shige Aliyun ya hango baba ƙaura ta mirror. Sauke gilashin motar yay ya saka ɗaya daga cikin securitys ɗin yay masa magana da baba ƙaura. Ganin shi ɗinne dai kamar yanda yay hasashe sai ya bada umarnin barinsu su shigo. Bayan ya shige da motar ya samu waje yay fakin ya fito shi da waɗanda sukabi masu ƙwamushe Alhaji babba, gaisuwa kawai yay da baba ƙauran ya shiga ya sanarma Jay.
Duk da Aliyu ya sanar masa baba ƙaura ne hakan nbai hanashi yin mamakin ganinsa har station ɗinsu ba, ya ƙarasa fuskarsa babu walwala, dan duk yanda yaso aro fara'a ya azama fuskar tasa kamar yanda ya saba idan yaje wajen baba ƙaura hakan ya gagara. Cike da girmamawa suka gaishesa har Sir Ahmad.
Kallonsu baba ƙaura yay ya ɗauke kansa yana faɗin, “Kagani har a wajen aikinka ko?”.
Ɗan murmushi Jay yayi da cewa, “Babu komai baba, ai nasan zuwan naka mai muhimmanci ne”. “Hakane” baban ya faɗa yana sake maido hankalinsa garesu sosai. Yace, “Tun da safe na saka a nemomin kai amma hakan ya gagara, ba'a samunka da farko, daga baya kuma ta shiga ba'a ɗagawa”. Kai Jawaad ya dafe, “Dan ALLAH kayi haƙuri baba, wlhy na tsinci kainane a yanayin da komaima bazan iyaba”. “Gudun faruwar hakanne ya sakani yimaka neman gaggawa ai daman, tun bayan wucewarka na tafi jeji ne, acan ma na kwana, dan sai gabannin asubahi na shigo gari, sanda na iso nan har an shiga salla. Na saka a nema min kaine domin isar maka da saƙon abinda idona ya ganomin jiya a cikin jajin nan. Muhammad Jawaad lallai akwai matsala babba dake tunkaroku, da idona na gani, na kumaji da kunnena, gashi rashin samunka akan lokaci ya nunamin alamomin fara faruwar matsalar dana guda ma a yanzun”.
Hankalin Jawaad a tashe yace, “Baba hasashenka duk haka yake, yanzu haka zancen da nake maka anje har gida an ɗauke kakana, akan binciken inda zamu samesa muke”.
“Wannan shine shirinsu na farko dama. Na zauna nayi ƙyaƙyƙyawan nazari mutanen nan ba haka nan suke bibiyarka ba, akwai wani abu aƙasa wanda akwai jininka a ciki, ina nufin cikin zuri'arku akwai wanda ke tare da mutanen nan.....” cike da mamaki Sir Ahmad da Jay suke kallon baba ƙaura. Ya jinjina kansa yana cigaba da faɗin, “Kar kuyi mamaki, neman duniya babu wanda baya ɓatarwa, lallai kamar yanda na faɗa akwai wani abu a ƙasa, dan babu rami miya kawo rami? Bayan abubuwan dana sani ke a hannunku akwai wani abu da kuka ɗakko a wani gida ne?”. Sir Ahmad ya kalli Jay, shima ya kalleshi, sai kuma ya maida dubansa ga baban yana jinjina masa kai. “Akwai wani tukunya baba, wanda.........” ya labartama baba ƙaura da Sir Ahmad komai.
Baba ƙaura da keta faman
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71 Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84