tare da kalmashesa a ƙirjina ya rufe ruf na ɗora a kafaɗa ƙasanshi suka sauka bayana, basai an faɗaminba, ni kaina nasan nayi ƙyau, hakan yasa naita kallon kaina a mirror ina murmushi, a gurguje na ƙarasa kimtsawa na fito sagale da ƴar jikkata a kafaɗa ina ƙamshi mai sanyi, sai takalma masu ɗan tudu kaɗan, na riga na faɗama Mom zan fita dama tun da daddare, hakan yasa yanzu nai ficewata kaina tsaye tunda babu wanda ya tashi har Yah Qaseem da baisan zan fitaba, dan banfaɗa masabama gudun matsala.
       Da ƙafa na taka har titi na tari napep na hau zuwa inda Oga Jabeer ya bani.

        Bayan fitar Bilkisu daga gidan Mom ta fito daga ɗakinta, tanason tayi magana da Shahudah ne, shiyyasa tun ɗazun taketa dakon fitar bily, tana tsoron halin da Shahudah zata iya shiga da har bily zata sani, dan a ganinta bily ita kaɗaice bare a cikinsu da bai kamata tasan sirrinsu ba. Sam jiya batai barciba akan bayanin da Shahudah tai musu na zuwa ɓangaren Jawaad da tayi, ta fahimci sunyi kuskuren ƙin sanarma Shahudah gaskiyar lamari akan sakinta da Jawaad yayi tun lokacin da wancan al'amarin ya faru, ba damuwarta abinda Shahudah ta aikataba, damuwarta kar Jawaad ya sake gudun Shahudah akan hakan, dan ita kanta inhar zata faɗi gaskiya bata taɓa kama Jawaad da abun rashin gaskiya ba dangane da fasiƙanci, dan ko lokacin da basa ƙasar ma idan yaje musu hutu duk jarabar Shahudah da naci akan yazo suje club baya zuwa, ita kanta ma faɗa yake mata, shiyyasa da yaje take kame kanta. To tasan akan hakan Jawaad zai iya sake bijire musu ne dangane da maida Shahudah.
     Tashin Shahudah kenan a barci tayo brush da alwala ta fito mom ta shigo, ƙarfe goma saura sai yanzune wai ake alwalar sallar asuba😭🤦🏻.
     “Mom lafiya?” Shahudah dake ƙoƙarin saka gyale ta faɗa tana kallon mom. Mom ta zauna bakin gado tana faɗin, “Magana nazo muyi”. Zama Shahudah tai ta fasa sallan, Mom tace ba salla zakiyiba ne?” “Eh salla zanyi, amma muyi magana sai nayi daga baya”. “Karki damu tashi kiyi sallar zan jiraki”. Shahudah batace komaiba ta miƙe ta kabbara salla, wadda ALLAH kaɗai yasan mima take karantawa, dan a mintuna ƙalilan ta idar da kayarta ta dawo wajen mom dake zaune tai tagumi da juya abinda zai iya biyo baya a ranta. Motsin Shahudah ne ya maidota hayyacinta ta gyara zama, tare da kamo hannayen Shahudah duka cikin nata ta kafeta da idanu, “Shahudah magana zanyi miki, inason ki nutsu ki fahimta, domin muma a yanzu haka hanyar gyara ɓarnar da kikayi muke, munada tabbacin samun nasara kuma, abinda yasa muka yanke hukunci sanar mikin a yanzu dukda mun ɓoye a baya saboda gudun halin da zaki shiga, yanzu kam saboda karki sake ƙara tafka irin kuskuren da kikayi ranar na zuwa wajen Jawaad”.
       “Mom ni dan ALLAH kimin magana kai tsaye, ki daina yimin wannan manya-manyan hausan naki da ba wani fahimtarsu nakeba, minene ya faru”. Yanda tai maganar da kumbura bakin shagwaɓa yasa mon yin ƴar dariya tana shafar kumatunta, “Nifa daɗina dake taɓara maman Dadynta, karki damu ai zan kaiki, kumani sonake ki iya hausar ai tunda yaren mamanki ce”. Shahudah batace komaiba sai ɓata fuska data sake yi. Mom ta ɗauka takardan data shigo dashi ta miƙama Shahudah. Babu musu Shahudah ta amsa tabuɗe takardan batare da tace komaiba.
      Kasancewar Jawaad da turanci ya rubutama Shahudah takardan saki sai ta fahimci komai dallah-dallah. Hannunta na rawa da bakinta ta ɗaga takardar, “Mom kina nufin BB ne ya aiko min da wanan dan naje wajensa?”.
     Kai Mom ta girgiza mata, “Badan kinje wajensa bane, wannan takardar shekararta biyar kenan a gidannan, mune dai bamu bakiba tun lokacin da akai rikicin zubar da cikin nan, munƙi bakine saboda gudun karki sake shiga wani hali akan wanda kika tsinci kanki a wancan lokacin, dan muna

ta ƙoƙarin duk bin hanyar data dace ki koma ɗakinki, sai dai zuwan da kikai wajensa ya ɗakko hanyar ɓata dukkanin shirin namu, shi bazai fahimci bakisan ya sakekiba, zai fassara abinne ta wata siga daban”.
        Matsanancin kuka shahudah ta fashe dashi, ta dafe kanta dake juya mata lokaci ɗaya, yanda tai baya zata faɗine yasa Mom azamar tarota tana kiran sunanta a razane, rungumeta shahudah tayi tana kuma kuka tamkar ranta zai fita, sai dai ƙarancin tunaninta na raya mata cewar tamkar sakin a banzane, dan Jawaad yayi ƙarya ya kwana da yunwa, aurensu baida maraba dana zobe, babu kishiya babu saki, ta daka tsalle ta dire a gaban Mom tare da wawaso rantsuwa ta sake direwa akan baima isaba. Yanda ta birkicema Mom tana kuka da rantsuwar Jawaad bai isabane ya jawo hankalin Aamilah data fito falon ƙasa neman abinci, sai Qaseem dake a d/table zaune yana karyawa shima, a guje Aamilah tay sama, Qaseem ma ya miƙe yabi bayanta. Yanda Shahudah ta rikice Mom na rirriƙeta sai abun ya basu mamaki suka shiga tambayar mom ko lafiya?. Basu samu amsa daga bakin mom ɗinba sai a takardar sakin da Shahudah ta jefar ƙasa, Qaseem yace, “K dalla malama nutsu mana anan” yanda yay maganar a tsawace yasa Shahudah nutsuwa sai dai ta maka masa harara tamkar zata makesa.
      Bai kulata ba ya maida dubansa ga Mom yana kaɗa takardar, “Ita wannan ɗin kuma daga ina Mom? Wata ya sake aikowa?” mom tace, “A'a waccance dai, kasan bata saniba, shinefa ranar Alhamis datasa muka barta can taje.........” Mom ta zayyanema Qaseem komai daya faru tsakanin Jay da Shahudah a daren juma'a wato ranar alhamis, wanda shine sanadin ciwonta. Jiyay tamkar ya make Shahudah dan takaici, Aamilah kam da yake Shahudah ta faɗa mata komai sai bataji abun a saboba, ya nuna ta da yatsa yana faɗin, “Kedai wlhy daƙiƙiyace, wai ubanmiye a jikin wannan wawan Jawaad ɗin da sauran maza suka rasa har kika nace masa?”. A fusace Shahudah tace, “Sai dai idan kaine daƙiƙin, kaiɗin ubanmiye a jikin yarinyarnan da sauran mata suka rasa ka nace mata (Bilkisu take nufi) (hakan ba sabon abu bane dan babu wani girmama juna a tsakaninsu). Duka yakai mata yana faɗin, “Idan kinajin iskancinki a gidannan kibar sakkoni, inba hakaba wlhy saina ɓallaki watan Shahudah. “Ka ɓallani ɗin tunda kai ɗin ubanane, saika gayamin banza na kasa maida maka amsa da wofi, uwarwa yama sakaka cikin maganar? Bansan shishshigi”. Dukan ya sake kaimata Mom ta tare. “Wai wane irin iskancine wannan!! Taya zaku sakani tsakkiya da shirme, ku barni naji da abinda ya dameni mana!!”. Duk dakatawa sukai kowa na huci kamar wasu ƴan dambe. Daga ƙarshe Qaseem ya juya zai fita Mom ta dakatar dashi ta hanyar kamo hannunsa, ƙin juyowa yay yadai tsaya, “Kayi haƙuri, ni banason wannan saurin fushin naka Qaseem, kasandai halin rashin kunyar Shahudah a gidanan, yakamata ka cigaba da haƙuri dasu a matsayinka na babba a cikinsu, kaji”. Ajiyar zuciya ya sauke, ya kaɗa kansa kawai. Tace, “To ku zauna muyi magana, Aamilah jeki kira Salman”.

BILKEESU

           Gurin ya haɗu matuƙa, bawani mugun ƙato baneba, madaidaici ne da akayisa domin masu hutawa kawai, yasha gyara da korayen ciyayi da flowers masu ƙamshi, nidai saima na zama baƙauya, dan duk zamana garin bansan da zamansa ba, koda yake inama nake zuwa, dama yawona dasu Ummie ne idan mun dawo hutu, to ƙafarmu bata taɓa zuwa nanba kuma, sai dai a zahiri na kame kaina ina tafiya cikin nutsuwa, ƙarƙashin ɗaya daga cikin ƙananun bukkokin da aka ƙawata wajen na nufa, naja kujera ɗaya cikin huɗu dake a kowacce ruffa na zauna tare da ɗora jikkata akan tebir ɗin na buɗe na ciro waya. Motsi naji a kaina, dan haka na duba wanda yazo wajen, ɗaya daga ma'aikatansu ne, ya gaisheni yana mai dire tiren hannunsa. Amsa masa nai tare da jeho masa tambaya akan kuɗin abinda ya kawo, duk da bani nace ya kawoba, tunanina tsarinsu kenan. “Karki damu Madam, an rigada an biya” ya faɗa yana barin wajen. Binsa kawai nai da kallo harya shigema ganina, mamakina shine ‘waye ya biya?’. bani da mai bani amsa, hakan yasani kauda abin a raina na duba abinda ya ajiye ɗin. Popcorn ne sai robar ice-creem da Malt ɗaya da ruwa, n

a ɗauke idona inajan guntun tsaki tare maida hankalina ga wayata na fara tafama Oga Jabeer saƙo. Bayan na tura masa naga ya wuce sai kawai na shiga yin Game batare dana kula abinda aka ajiye min ɗinba dan a ƙoshe nake.
       “Hy Babie!” aka faɗa dai-dai kunnena, a tsorace na ɗago idanuna dan a bazata abin yazomin, banji motsin kowaba. Ƙyaƙyƙyawan saurayi fari tas kuma ɗan gaye ya sakarmin murmushi da ɗage gira ɗaya sama, “Sorry na tsorataki ko?”.
          Janye idanuna nayi daga kansa batare dana tanka masaba ko magana. “Kin cancanta” ya faɗa yana zama kujerar dake facing ɗina. Nanma dai ƙin kulashi nayi, yaja ɗan kwalin da Popcorn ɗin ke ciki ya fara ɗiba yana afawa a bakinsa tare da lumshe ido alamar dai akwai daɗi. Janye idanuna nai daga satar kallonsa na tura wayata a jikka na miƙe zan bar masa wajen. Da sauri shima ya miƙe yazo gabana ya tsaya, baya naja kaɗan ina ɓata fuska. Yace, “ALLAH bazaki tafiba sai kin kulani”. Na dafe kaina ina lumshe idanuna irin na ka kaini bango ɗin nan......
     “Please babie kice wani abu mana”.
Nabuɗe baki zanyi magana kawai naji baƙon ƙamshin turare a wajen tare da motsi, waigawa nai saboda yanda, nakejin bugun zuciyata na sauya salo. Wanda nai tunanin kuwa shine na gani. ‘Boss!’ na ambata a cikin zuciyata, duk da ya rufe fuskarsa sosai da facing cap baƙa datai masa masifar ƙyau hakan bazaisa naƙi ganesa ba, ƙamshinsa ma kawai amsatace dan bana manta ƙamshin turarensa sam, dana jisa nake shaida yazo waje. sake ja baya daga gaban gayen da shima shi yake kallo nayi.
          Jawaad kam yayi tamkarma bai gansu ba, sai ƙoƙarin buɗe gwangwanin Malt.. Ɗin da aka kawoma Bily kawai yake hankalinsa kwance, sai dai fuskarsa a matuƙar ɗaure take babu alamun sassauci, ya zaro wayarsa da ga aljihu tare da gyara zamansa, ya kwantar da bayansa jikin kujerar sosai ƙafa ɗaya kan ɗaya, sai kace wani saraki, yana sanye cikin ƙananun kaya da sukai masa masifar ƙyau da fidda cikar haibarsa, sai hula hana salla inji hausawa😂, a samanta an rubuta favourite da ruwan gwal mai ƙyalƙyali, idanunsa toshe da baƙin glasess, hakan yasa babu mai fahimtar ina idanunsa suke kallo kai tsaye. A zuciyata nace, ‘glass nama Boss ƙyau matuƙa idan ya saka, bansaniba koni kaɗai ke iya ganin hakan banda sauran mutane, amm.....
         “Babie!” saurayin ya ambata da ɗan ƙarfi ganin hankalin Bily baya tare da shi. Kallona na maido kansa, nace, “Ba sunana Babie ba” yay murmushi mai ƙayatarwa, “To a faɗamin sunan mana uhum”. “Bana doguwar magana da wanda bai iya sallama ba”. kansa ya dafe alamar ya fahimci kuskurensa, yace, “Sorry Assalamu alaiki”. “Wa'alaikassalam”. Na amsa masa.
       Murmushi ya sake yi, yace, “Na gode da kika tunatar dani abinda na manta, hakan na sake tabbatarmin na samu abokiyar rayuwa ta gari, irin wadda ta cancanci zama uwar ƴaƴana. Sunana Kamaludden shehu Manya, matar tawa fa?”. ni dariyama yaso bani wlhy, wai matarsa, daga ganin sarkin fawa sai miya tai daɗi. kaina na girgiza masa kawai na juya zan bar wajen, amma sai yay azamar sake shan gabana, “Haba babie, naga na gyara kuskuren da yasa aka ƙi kulani tun a farko ai, koda bazaki kulani a nanba ki bani Number mana. Sonake ya barni, shiyyasa na miƙa masa hannu alamar ya bani wayarsa na saka masa. Cike da ɗoki ya ciro wayarsa a aljihu ya miƙomin, sai dai kafin na kai hannu na amsa wani hannun ya amshe wayar..............✍




ALLAH ka gafartama iyayrnmu😭🙏🏻
  
   
[12/31/2020, 9:31 PM] Abubakar Saleh Kurami: Bilyn Abdull 📚:
Page 16

...............Napep na samu na tare nai tafiyata gidan Inna zainabu. Can nai zamana mukasha hira da Lawusa da a yanzu muke ɗasawa har bayan sallar isha'i sannan na nufo gida.

★★★★★

           Bayan an buɗe taro da addu'a Uncle Nasir ya fara jawabi kamar haka. “Kamar yanda kowa ya sani mun fara tattaunawa akan maganar zaman Jawaad babu aure a kwanakin baya, har takai mukai masa tayin cikin yaran gidannan ko akwai wadda ya keso, sai dai ya nuna a lokacin zaiyi tunani, tun daga wancan lokacin ban sakeji daga gareshiba, to magana ta gaskiya mun gaji da ganinsa yana yawo a gari haka ana zaginmu, shi kansa bama girmansa bane, ƙannen-ƙannen bayansa ma gasunan duk da iyalansu har da ƴaƴa, yakamata Jawaad kaima kanka faɗa, dan lokaci bawai zai zauna jiranka baneba, kai kaɗai Abdul-aziz ya haifa, zamuso ganin ƴaƴanka a duniya kamar yanda mukasan da yanada rai zai ɗokantu da haka shima. A wannan karon ba shawara muke bakaba, umarnine, shiyyasama mukazo da Alhaji Baba domin ya zama shaida, tare da iyayenka, dolene a wannan karon kayi aure, ka zaɓi mace ɗaya a cikin ƴaƴan gidannan koma fiye da ɗayar mukuma zamu aura maka”.
     Jawaad da kansa ke ƙasa yay guntun murmushi domin son ɓoye ɓacin ransa, batare da ya ɗagoba yace, “Uncle ku gafarceni, bazan jaku da nisaba, duk cikin yaran gidannan bazan iya auren kowaba, dan kallon ƙannena nake musu tamkar ciki ɗaya...” da sauri Uncle Uwaisu yace, “Ai tamkar kace, bawai hakan bane, tunda babu ta inda ALLAH ya haramta maka, Jawaad bamason shirme, garama ka zaɓa komu mu zaɓa maka, kokuma ka ɗauki zaɓi na biyu, wato ka maida matarka ɗakinta kuje kuyi haƙuru da juna tunda yarinyarnan ta horu kuma tana sonka”. Yanzu kam kasa daurewa yay saida ya ɗago kansa ya kalli Uncle Uwaisu, kamar zaiyi magana sai kuma yay shiru saboda gargaɗi da Alhaji Baba yay masa da ido, kansa ya maida ƙasa yana sauke ajiyar zuciya.
      Uncle Sulaiman yace, “Son!” ɗago kai Jawaad yay ya kalli Uncle ɗin nasa da yake matuƙar so saboda ƙyawun halinsa, yace, “Na'am Uncle”. “Ko Kanada wadda kake sone?”. Ƙasa Jay ya maida kansa yana motsa laɓɓansa, sai dai babu maijin mi yake cewa, Uncle Taheer ya katsesa da faɗin, “Kai muke saurare Jawaad”. Batare daya ɗagoba ya girgiza musu kai alamar a'a. Shiru falon ya ɗauka kowa ya zuba masa idonu, shi kuma yaƙi kallonsu. Mama Zuhurah da bata da yawan magana tace, “To Jawaad ya kakeso ayi kenan? Yanzu kai kafijin daɗin kullum aita zaman meeting akanka akan maganar kaƙi aure, ka rufa mana asiri ka fidda kanka damu iyayenka daga zargi da zunɗen al'umma kaji, ƴar uwarka na sonka, tayi nadamar kuskuren datai a baya, kayi haƙuri a maida aurenku kaji”.
          Ɗagowa yay zaiyi magana fitowar Shahudah ta katse masa hanzari, gabansa taje ta durƙusa tamkar yanda Mama Atika da Mom suka kitsa mata, ta fashe da kuka tare da kama ƙafafunsa, cikin gurɓatacciyar hausarta da harshen turancin da tafi ƙwarewa ya cinye tace, “Bb dan ALLAH ka gafarceni, wlhy nayi nadamar abinda na aikata, nakumayi alƙawrin bazan sakeba, na yarda zan haihu maka yara komai yawan da kake buƙata yanzun, idan ka barni mutuwa zanyi wlhy, dan ALLAH ka ceci rayuwata Bb...” hannunta ya ture daga saman ƙafarsa yana hararta, “Kima daina ɓata lokacinki, indai haihuwace bana buƙata daga gareki Hudah, karki damu kije kicigaba da cin moriyar ƙuruciyarki kinji, indai nine kima saka a ranki baki taɓa sanin mai kama daniba dan mun rabu kenan”. Fashewa tai da matsanancin kuka yanzunkam fiye da da, dan har ƙasan ranta kalamansa sun masifar sosa mata zuciya, ta dafe kanta dake juya mata, babu zato sai kawai ganinta ƙasa sukai ta yanke jiki ta faɗi. Gaba ɗaya ƴan falon da suka zuba musu ido suka miƙe, shi kansa Jawaad ɗin kallonta yake, dan ya zata salon iskancinta ne, sai daga baya da aketa jijjigata babu alamar rai tattare da itane ya fuskanci babu wasa a lamarinta, gaba ɗaya falon ya rikice, dan iya ƙoƙari anyi Shahudah taƙi farfaɗowa, Mom sai kuka take da sambatu.
       Dole aka kwashi Shahudah zuwa asibiti da gaggawa kuwa, dan wasunsu harsu fidda ran da gaske ta mutu.

★★★★★★★

          Tun a gate baba maigadi yake sanarmi

n ai babu kowa a gidan duk suna asibiti aunty Shahudah babu lafiya, hankalina ya tashi sosai, dan haka nai azamar tsayar da mai napep ɗin dake shirin juyawa dan harma ya fara tafiya, shiga nayi na sanar masa asibitin da baba magadi ya sanarmin an kaita. Asibitine mai ƙyau dan na kuɗine, kasancewar bansan ina zan nufaba sai nai kiran aunty Aamilah, saidai bata amsa ba, na sake kira nanma babu amsa, maida kiran nai kan Yah Qaseem, sai da ta kusan tsinkewa sannan ya ɗaga, faɗa masa nai gani a asibitin a ina suke?. Muryarsa a sanyaye yace na jirasa yazo ya shiga dani.
        A yanda na gansa kawai na tabbatar akwai babbar damuwa dangane da aunty Shahudah, kasa daurewa nai na shiga jera masa tambayoyi. Amsa ɗaya na samu daga garesa, shine ta farfaɗo, sai dai sun mata allurar barci, sun kuma hana kowa ganinta sai banzan Jawaad ɗin da taketa sambatun kira. Ta bani tausayi matuƙa, dan na sake fahimtar tsananin son da takema Boss.
           Duk sai da na gaida waɗanda na tarar a wajen, sannan na tambayesu ya mai jiki, sai dai babu Boss babu dalilinsa a wajen, zama nai kamar yanda suke zaune jigum-jigum, kusan mintuna biyar sai naji ƙamshin turarensa. Ɗago kai nai dan tabbatarwa, karaf kuwa muka haɗa ido dashi, ya dalla mani harara sannan ya ɗauke kansa tamkar baiyiba.  Nima janye nawa nai, dan nasan laifina dai bai wuce tafiya bada izininsa ba. Cikin nutsatstsiyar muryarsa dake tattare da alamun gajiya naji yana faɗima Uncles nasa da matansu ya kamata su tafi gida su huta, tunda dai Doctor yace bazasu bari a gantaba har sai zuwa safiya.
     
Showing 45001 words to 48000 words out of 249282 words