murmushi da hawaye tace, “N: Kaifa anta Jay-p na”. Idanu ya lumshe a hankali yana haɗiye nauyin da ƙirjinsa yay masa da sake damƙe hannunta cikin nashi kamar mai gudun a ƙwace masa ita yace, “Ana bikhairin Ummuna”. Ta shafa kansa tana murmushi da faɗin, “Alhamdulillahi ala kulli halin Noorul Ayn”. Ɗagowa yay idanu jazur ya kalleta da sake sumbar hannunta ya ɗaura kansa saman kafadanrta yana sake lumshe idanu. “Ummuna nayi kewarki”. “Nima haka Muhammad Jawaad”. Ta faɗa tana sumbatar goshinsa.
Cikin nutsuwa motocin suka fice daga airport ɗin, ta Jay ce gaba shi da Umm-Anum, sai kuma wadda su Anuwar ke ciki shi da Anum, sai ɗaya da babu kowa a ciki, ta ƙarshe kuma dogaraine.
___________________
Daga kukan da ya barni inayi sai barci ya kwasheni, cikin barci naji ana knocking ƙofar, na buɗe ido a hankali da tashi zaune dan nasan bazai wuci Nabeelah bace, bayi na fara shiga na wanko fuskata da hawaye suka bushe, sannan na fita. Nabeelah tai saurin riƙo hannuna tana faɗin, “Baƙinfa sun iso inaga, dan naji ƙarar buɗe gate”. Bata jira amsata ba taja hannuna muka fito babban falo. Kiciɓis mukai da Anum data fara shigowa. Ta daka wani uban tsalle ta ɗareni, tuni naji duk wani ɓacin ran da Boss ya barni da shi ya gudu, na rungumeta nima cike da tsantsar farin ciki.
Anuwar ne na biyun shigowa, ya fara sauke idanunsa akan Nabeelah da ke tsaye tana kallon su bily da dariya, kafin ya maida ga su Bilkisun yana ɗan ɓata fuska. “Lallaima Aunty, ni baki ganniba sai wannan yarinyar”. “Tuba nake Yah Anuwar ” na faɗa ina sakin Anum.
A waje kam Jay ya taimakama Umm-Anum ta fito daga motar, ƙafafunta duk sunyi fushi saboda zaman jirgi, ga kuma dama ƙafarta na mata ciwo. Wani irin kallo take bin gidan da shi dan bazata taɓa mantawa da shi ba koda a magagin mutuwa take, gidan da yazama tushen komai na maida mijinta wane, gidan da yazama harsashin ginin ɗaukaka ga abin sonta, gidan da zata iya a
mbatonsa da komai a ɓangaren farin cikin rayuwar aurensu da akasinsa, gidan data haifi gudan jininta bayan shafe shekaru tana kuka da fatan samu. kallon Jay tayi hawaye cike da idanunta. A hankali ya kaɗa mata nasa kan yana ɗan murmushi. Ta sake damƙe hannunsa cikin nashi tana haɗiye abubuwa masu yawan gaske dake yunƙuro mata tun daga ƙasan zuciya har saman harshe. A hankali ya fara takawa da ita suka nufi ƙofar da zata sadasu da cikin gidan, suna gab da isa ƙofar falon Bilkisu ta fito cikin matsanancin hanzari.
Nai saurin ƙarasawa garesu batare dana tuna da wani matsayinta na surukata ba, ni kallon uwa nake mata, uwa ɗinma mai muhimmancin gaske ga ɗa. sakin Jawaad Umm-Anum tai itama da sauri ta buɗema bily hannayenta, aiko tazo ta shige jikinta. A take hawayen da Umm-Anum ke maƙalewa suka gangaro mata saman kumatu. Kauda kai Jay yayi daga kallonsu saboda ƙwallan da suka cika masa idanu, sai ya tura duka hannayensa cikin aljihun farin wandonsa ya ɗaga kansa sama ya maida hawayen. Sai da ya tabbatar hawayen sun koma sannan ya sauke fuskarsa a kansu. Yanzu kam Bilkisu ta ɗago daga jikin Umm-Anum, sai dai su duka hawaye suke tana jeramata sannu da zuwa. Umm-Anum ta shafa fuskar bilyn tana ƙare mata kallo sosai, wani sassanyan murmushi ta sake saki da jawota jikinta ta sake rungumeta, dan ita kaɗai tasan mita gano.
“Ummuna kumuje ciki, sai ku cigaba da murnan”. Jay ya faɗa a hankali kamar bashine yay maganarba. Kallonsa tai shima ta riƙo hannunsa suka sakata tsakkiya shi da Bilkisu, a haka suka shiga falon inda Nabeelah da Anum ke zaune surutu ya kaure tsakaninsu, Anuwar kuma ya tasasu a gaba yana kallon Nabeelah kamar ya samu wani majigi.
Cak Umm-Anum ta tsaya tana kallon Nabeelah da itama tai mutuwar tsaye tana kallon mai tsananin kama da Ummahn ta. Kallon Jawaad Umm-Anum tayi cikin wani yanayi na alamar tambaya. Hannunta ya kama ya zaunar da ita yana ɗan murmushi, sai da ya tabbar ta zauna sannan ya kalli Nabeelah da ke ƙoƙarin gaisheta. Hannun Nabeelah ta kamo ta matso da ita jikinta, da ƴar rawar murya Umm-Anum tace, “Da ace mutum baya ƙara shekaru da girma ni dai da nace wannan Mariya ta ce Jawaad, kamar yanda nake kallon takwarata da kamannin Rahma”. duk da ba yaune karan farko da akace Bilkisu na kama da aunty Mah-mah ba a gabansa sai da ya kalli Bilkisun da tasha jinin jikinta, sai kuma ya ɗauke kansa yana zama kusa da Umm-Anum. “Ummuna ki kwantar da hankalinki kinji, dukkan abinda kike buƙatar ji zaki samu fiyema da hakan har sai kin gaji, yanzu dai kitashi a kaiki inda zakiyi wanka, kuci abinci ki kwanta ki huta, sai komai ya biyo bayan hakan kinji”.
Kansa ta shafa da ja masa hanci tana faɗin, “Rigimammen Mama har yanzu dai ana taɓawa kenan”. Dariya duk su Anuwar sukayi, shi kuma ya zuba musu harara da kama hannun Umm-Anum ɗin ya miƙar da ita. Da kansa yay mata rakkiya har ɗakin bily, itama da tabi bayansu tai saurin shiga bayi domin haɗa mata ruwan wanka.
Nabeelah na ganin Jay da bily sun shige da Umm-Anum tai saurin ɗaukar wayarta ta turama Ummah babba saƙo.
Sai da suka tabbatar Umm-Anum ta shiga wanka sannan Jawaad ya fito, kayansu da Sadiq tuni ya gama shigo musu da su ya saka Anum ta ɗauka na Umm-Anum ta kai mata ɗakin Bilkisu, shi kuma ya kai Anuwar ɗakin baƙi inda zai zauna, Anum ma ɗakin baƙin dake cikin falon bily zata zauna. Bilkisu da Nabeelah da keta ALLAH, ALLAH su Ummah su iso sukai hidimar shirya abinci su kuma a tsakkiyar falon, dan yanda Umm-Anum ta gaji bai kamata a sakata zaman Dining ba.
Tana son tabi Jay ɗakinsa dan ta nuna masa farin cikin data shiga na bazatar da yay mata akan zuwan su Umm-Anum amma haushinsa da takeji ya hanata aikata hakan, sai kawai ta sharesa ta cigaba da harkokin gabanta, dan farin cikin ganin su Umm-Anum ya shafe mata duk wani damuwarta kuma.
A ɓangaren Jawaad shima tun shigowarsa ɗakin ya ke zuba idanu ya ga bilkisu ta biyosa amma sai yaji tsit, duk da farin cikin ganin mahaifiyarsa da ƙannensa ya shafe masa duk wani ɓacin ran da ya samo daga Qaseem da gidan Dad hakan bai hana ransa sosuwa ba da ƙ
in shigowar Bilkisun, sai huci yake da jera tsagwayen ƙwafa, ayyanawa yake a ransa sai yayi maganin miskilancin yarinyarnan a yau ɗin nan basai gobe ba, dan ya gama lura gadon barcinsa da ta gama ganine yasa take neman fara kawoma rayuwarsa raini (Ka manta wulaƙancin da kai mata kai ɗazun saraki🙄😜).
Tashi yay da ga kwancen da yake saboda jin an fara kiraye-kirayen sallar Magriba. Alwala yayi sannan ya fito, a babban balo suka haɗu da Anuwar da shima ya fito daga sashen baƙi da alamar shirin tafiya masallacin. Yayma abincin da aka shirya a tsakkiyar falon kallo ɗaya ya ɗauke kansa batare da yace komaiba suka fice shi da Anuwar dan falon babu kowa cikinsa.
Da taimakon Bilkisu Umm-Anum ta dawo falon bayan an idar da sallar Magriba, suna zama Ummah babba da Ummah ƙarama da Batool nayin sallama, cikin matsananciyar faɗuwar gaba Umm-Anum ta juya tana kallon ƙofar dan ko'a cikin magagin barci waɗannan muryoyin sunfi gaban mantuwa a gareta balle ma a zahiri.
Kasancewar akwai hasken Genretor da aka kunna tas suke ganin junansu, da ga Ummah ƙarama har Ummah babba jikinsu rawa yake da tsuma sosai, sun ƙurama Umm-Anum idanu tamkar yanda itama ɗin kallonsu take bata ko ƙyaftawa. Su dai su Bilkisu kallonsu kawai suke da son ganin yaya za'a kwashe. A haka Jawaad da Anuwar suka shigo suka samosu. Jay ya kalli su Ummah da mamaki sai kuma ya kalli Nabeelah da ya tabbatar itace da wannan aikin. Aiko sai tai ƙasa da kai gabanta na faɗuwa dan tsoro ta koma bayan bily ta maƙale.
Ɗauke kansa yay daga gareta, ya ƙarasa gaban su Ummah ya tsaya a tsakkiyarsu, hannayensu duka ya kama a cikin nasa, a take duk suka ɗago suna kallonsa hawaye na gangaro musu saman fuskokinsu. Yanda laɓɓansu ke rawa zai baka tabbacin magana suke son yi amma sun kasa saboda ruɗani. Jay yaɗan murmusa yana mai lumshe idanunsa ya buɗe alamar tabbatar musu da wadda suke hasashen ce ba mafarki bane ko gizago. Cikin ƙarfin hali Ummah Babba tace, “Yarona da gaske kake Yaya Bilkisu ce a gabanmu ba mafarkin da muka sabayi bane?”. Yanzunma kansa ya jinjina musu, ya kuma ja hannayensu har gaban Umm-Anum da alamu ya nuna suman zaune tayi. Hannayensu ya saka a cikin nata yana sake faɗaɗa fuskarsa da murmushi yaja jikinsa baya.
A gaban Umm-Anum Ummah ƙarama da Ummah babba suka zube suna fashewa da kuka mai tsuma rai da cin zukata. Umm-Anum ta kawo nannauyan numfashi lokacin da suka rungumeta su duka biyun a jikinsu.
Su Bilkisu dake kallonsu suma hawayen sukeyi, Jawaad kansa sai da ƙwalla ta cika masa idanu, amma jarumta ta saka shi haɗiye kayansa ya koma cikin kujera ya zauna yana jin wani irin matsanancin farin cikin da ƙirjinsa ma ke neman gaza ɗauka. Su Ummah sunkai kusan mintuna huɗu zuwa biyar a jikin Umm-Anum suna raira kuka kafin su saki juna, hannayenta ta ɗaura saman kumatunsu tana shafawa da murmushi saman fuskarta ga kuma hawaye, suma dai murmushin sukeyi hannayensu duka akan nata kumatun suna share mata nata hawayen. “Ashe Mariya ta da Wasila basu girmaba har yanzun? Ashe shagwaɓar nan da akema Yaya tana nan ba'a fasaba”. Dariya ta kwacema su Ummah lokaci guda da kuka, jikinta suka sake faɗawa ta rungumesu tana dariya. Su ma ƴaƴansu dariyar sukeyi da hawaye banda Jay da murmushi ne kawai a saman fuskar tasa.
Da sauri Umm-Anum ta sake ɗagosu tana faɗin, “Ina Rahmah take ita kuma? Ko ba'a nan take aure ba?”. Duk ƙasa sukai da kawunansu hawaye masu zafi sosai na sake rige-rigen fitowa daga idanunsu, Umm-Anum ta shiga girgiza kanta a hankali tana kallonsu a tsorace, “Karku cemin na rasa Rahmah Mariya, kar kucemin rabuwa ta har abada nayi da Rahmah dan ALLAH” “Sai dai haƙuri Yayah, Rahma ta jima da barinmu gaba ɗaya, ta tafi tafiya mai nisan zango da babu iyakar sake ganin juna sai idan ALLAH ya ƙaddara hakan a can wata rana”. Ummah babba ta faɗa zuciyarta na mata zogi tamkar a yaune Rahmah tabar duniya. Yanzun kam Umm-Anum ce ta fashe da kuka mai tsuma rai da cin zuciya, tana son Rahmah, tana ƙaunar Rahma sosai, dan tafi shaƙuwa da ita a kaf cikin ƴan uwanta.
Ganin kukan nasu yana neman yin yawa gashi ha
r ana kiran sallar isha'i sai Jay yay gyaran murya. ɗagowa sukai duk suka kallesa. Ya sakar musu murmushi da waro idanunsa waje kaɗan ya miƙa musu kwalin tissue da ya ɗauka saman centre table. Babu musu suka amsa. “Yauwa Momys ɗina ababen alfaharina, kukan ya isa haka nan kar ku ƙarar mana da hawayenku, lokacin kuka ya wuce yanzu farin ciki ake buƙata da godiyar ALLAH da ya kawo ranar da ba'a taɓa tunani ko tsamanin zuwanta ba, idan kuna kuka mu kuma mi zamuyi to?”. Cikin kaɗa kai Ummah babba tace, “Hakane Jawaad, ALLAH yay maka albarka kaida sauran ƴan uwanka kaji, a ina ka gano mana Zuciyarmu ne yaron albarka?”. “Ihhhmmm karku damu zan faɗa muku komai sweet Ummahs ɗina, amma ba yanzu ba sai tsohon can shima yana gefena”. Daƙƙuwa Ummah ƙarama tai masa tana faɗin, “Sai dai idan iyayenka ne tsoffi”. Dariya ce ta nema kufcema su Bilkisu, suka saka hannaye duk suka kare bakunansu banda Aunty Batool da tayi abunta sosai. Miƙewa yay ya dungurema Aunty Batool kai yay ficewarsa domin yin sallar isha'i.
Bayan sallar isha'i natsuwa da ga UBANGIJI ta kuma saukar musu a zukata, duk da su Ummah suna ƙage da sonjin wani abu daga yayar tasu, kamar yanda itama a ƙagen take sai Jay ya hana, a cewarsa sai sunci sun ƙoshi sannan hakan zata kasance. Babu yanda suka iya suka yarda da batunsa, dan suma sunsan ya cancanci Umm-Anum taci abin ma ta kwanta ta huta, sai dai zukatansu bazasu iya jure hakanba.
Ummah babba da kanta ta bama Anuwar da Anum abinci a baki cike da so da ƙauna, hakama Umm-Anum ta bama Aunty Batool da Nabeelah da Bilkisu, Jay kuma Ummah ƙarama ta bashi. Cikin wani irin farin ciki mai wahalar misaltuwa sukaci abincin suka ƙoshi, dan Umm-Anum har su Ummah ma sai da ta dinga basu a baki da kanta. Abin dolene ya sakaka kuka ya kuma birgeka. Sai da sukai nak da girki suka godema UBANGIJIN daya basu badan ƙarfinsu ba ba kuma dan sunfi kowa ba sannan su bily suka tattare wajen tas. Da taimakon aunty Batool da Nabeelah da Anum suka wanke komai tsaf. Yayinda a falo kuma Jawaad ke ta bama su Ummah labarin yanda komai ya kasance game da ganin Umm-Anum ɗin duk da dama tun a wancan lokacin ya labarta musu a sanadin Bilkisu ne. Wata iriyar ƙauna da soyayyar Bilkisu sai ta ƙara faɗaɗa da daɗuwa a cikin zukatansu. Duk yanda mai hasashe zaiyi tunaninta a zukatansu tafi gaban hakan ta wuce.
Sabon babin fira aka buɗe a cikin falon ba tare da sunma tuna darene ba ranaba, babu mai kallon lokaci babu mai tunawa ma da shi. Ba suba ko Jay da baisan yawan surutu yau sai yaji hakan bai gunduresa ba, wani wajen ayi kuka wani wajen ayi dariya, wani wajen ayi tausayi da al'ajabi. Haka kawai bilkisu ta tsinci kanta da yin matsanancin kuka akan labarin Aunty Mah-mah (Rahmah), haka kawai taji tana ƙwaɗayin ganinta koda kuwa a hotone. Hakama Umm-Anum ta shiga matsanancin mamaki da jin wai Bilkisu ba ɗiyar Rahmah bace ba. Yayinda shi kuma Jawaad al'amarin yay masa tsaye cak a zuciya baisan dalili ba, kawai yanaji a ransa kamar akwai wani abu dake a binne game da rayuwar bilkisun, musamman idan ya tuna da maganar baba ƙaura akan duhun dake biye da Bilkisun, da kuma furucin baba ƙauran a jiya da yaje wajensa saboda kiran da yay masa. ‘Kai anya kuwa babu wani abu........?’ ya faɗa a cikin ransa yana kafe Bilkisu da idanu harta tsargu ta ɗan ɗago suka haɗa ido.
Barci ma da kansa yasan inda yake zuwa yay sata, dan kuwa idanun waɗanan bayin ALLAH ko gyangyaɗi basaji balle ai maganar barci, suna zaune dingangan har agogo ya nuna ƙarfe uku saura na dare. Jay ne ya katse firar tasu da roƙonsu akan suje su kwanta haka da safe idan ALLAH ya kaimu saisu ɗora. Badan sunso hakan ba suka miƙe dan suma susan Umm-Anum na buƙatar ace ta huta kodan doguwar tafiyar da tayo wadda bata saba ba. Su mamaki ma abin ya basu dan basusan lokaci yaja haka ba, jima suke tamkar daren bai wuce ƙarfe goma ba. Dole dai yau su kwana gidan ɗansu.
Ummah babba Umm-Anum da Ummah ƙarama ɗakin bily aka kaisu su kwanta tare da ƴar uwarsu, duk da dai ba kwanciyar sukaiba wani babin sabuwar hirar suka sake buɗewa ma su. Batool da Anum da Nabeelah kuma ɗaki
n dake kusa dana Bilkisu, Anuwar yana a ɗakin baƙi. Jay ya nufi nasa ɗakin, Bilkisu na shirin shigewa wajensu Nabeelah Ummah ƙarama ta korata ɗakin Jawaad.
Sosai kunya ta lulluɓeni har inaji kamar ƙasa ta tsage na shige, to amma yaya na iya suɗin ba abin wasana bane balle nai tunanin musu gardama ma, haka na nufi sashen nasa kamar na nutse dan kunya. Ina jiyo su Nabeelah namin dariya harda Yah Anuwar. Sam banso hakanba, dan naso ace mun samu nisa da juna ni da shi koda na kwanaki biyu ne dan ya fahimci inajin zafin abinda ke faruwa tsakaninsa da ƴan uwana, ƙila ta hakan zan samu ya faɗamin abinda ke faruwar. Badan a ciwon kan da nake ji ba da falo zanyi zamana na ƙarasa daren, haka dai na daure fuska a ciskule na nufi bedroom ɗinsa, ciki ciki nai sallama na shiga, yana kwance a saman gado da ga shi sai noxer kawai, idanunsa a rufe suke amma na tabbata ba barci yake ba, na ɗauke kaina daga garesa na nufi bayi. Ban wani jimaba na fito dan fitsari kawai nayi da abinda baza'a rasaba. Yanda na barsa haka na fito na samesa, bani da kaya a ɗakin, sai naita tunanin mizan saka na kwanta dan bazan iya barci da kayan jikina ba. Ganin lokaci na sake ja ga zazzaɓi nama neman saukarmin yasa na nufi Wadrobe ɗinsa, cikin sa'a kuwa idanuna saka sauka akan t-shirt ɗinsa mara nauyi ruwan toka, nasan indai na saka zata sakkomin dan babbace kuma girman ba ɗaya ba.
Zagayawa nai ta ɗayan gefen na kwanta can ƙarshen gado na juya masa baya.....
“K har kin isa mu kwanta a gado ɗaya ki juyamin baya!”. Na tsinkayi saukar muryarsa da furucinsa a fusace cikin kunnuwana. Ɗan rintse idanu nayi ina haɗiyar yawu da ƙyar, zuciyata sai harbawa take da sauri-sauri na tsoro. A hankali na juyo ina tura baki da sake ɓata fuska sosai, abin mamaki har yanzu yana a yanda yake. A ƙasan ido naɗan hararesa naja bargo na rufe har fuskata ma.
Wani haushi ya sake kume zuciyar Jay, jiyake kamar yay mata filla-filla ɗin da saita ƙarasa daren da kuka, sai dai yanata ƙoƙarin danne fushinsa kawai.
Showing 204001 words to 207000 words out of 249282 words
Cikin nutsuwa motocin suka fice daga airport ɗin, ta Jay ce gaba shi da Umm-Anum, sai kuma wadda su Anuwar ke ciki shi da Anum, sai ɗaya da babu kowa a ciki, ta ƙarshe kuma dogaraine.
___________________
Daga kukan da ya barni inayi sai barci ya kwasheni, cikin barci naji ana knocking ƙofar, na buɗe ido a hankali da tashi zaune dan nasan bazai wuci Nabeelah bace, bayi na fara shiga na wanko fuskata da hawaye suka bushe, sannan na fita. Nabeelah tai saurin riƙo hannuna tana faɗin, “Baƙinfa sun iso inaga, dan naji ƙarar buɗe gate”. Bata jira amsata ba taja hannuna muka fito babban falo. Kiciɓis mukai da Anum data fara shigowa. Ta daka wani uban tsalle ta ɗareni, tuni naji duk wani ɓacin ran da Boss ya barni da shi ya gudu, na rungumeta nima cike da tsantsar farin ciki.
Anuwar ne na biyun shigowa, ya fara sauke idanunsa akan Nabeelah da ke tsaye tana kallon su bily da dariya, kafin ya maida ga su Bilkisun yana ɗan ɓata fuska. “Lallaima Aunty, ni baki ganniba sai wannan yarinyar”. “Tuba nake Yah Anuwar ” na faɗa ina sakin Anum.
A waje kam Jay ya taimakama Umm-Anum ta fito daga motar, ƙafafunta duk sunyi fushi saboda zaman jirgi, ga kuma dama ƙafarta na mata ciwo. Wani irin kallo take bin gidan da shi dan bazata taɓa mantawa da shi ba koda a magagin mutuwa take, gidan da yazama tushen komai na maida mijinta wane, gidan da yazama harsashin ginin ɗaukaka ga abin sonta, gidan da zata iya a
mbatonsa da komai a ɓangaren farin cikin rayuwar aurensu da akasinsa, gidan data haifi gudan jininta bayan shafe shekaru tana kuka da fatan samu. kallon Jay tayi hawaye cike da idanunta. A hankali ya kaɗa mata nasa kan yana ɗan murmushi. Ta sake damƙe hannunsa cikin nashi tana haɗiye abubuwa masu yawan gaske dake yunƙuro mata tun daga ƙasan zuciya har saman harshe. A hankali ya fara takawa da ita suka nufi ƙofar da zata sadasu da cikin gidan, suna gab da isa ƙofar falon Bilkisu ta fito cikin matsanancin hanzari.
Nai saurin ƙarasawa garesu batare dana tuna da wani matsayinta na surukata ba, ni kallon uwa nake mata, uwa ɗinma mai muhimmancin gaske ga ɗa. sakin Jawaad Umm-Anum tai itama da sauri ta buɗema bily hannayenta, aiko tazo ta shige jikinta. A take hawayen da Umm-Anum ke maƙalewa suka gangaro mata saman kumatu. Kauda kai Jay yayi daga kallonsu saboda ƙwallan da suka cika masa idanu, sai ya tura duka hannayensa cikin aljihun farin wandonsa ya ɗaga kansa sama ya maida hawayen. Sai da ya tabbatar hawayen sun koma sannan ya sauke fuskarsa a kansu. Yanzu kam Bilkisu ta ɗago daga jikin Umm-Anum, sai dai su duka hawaye suke tana jeramata sannu da zuwa. Umm-Anum ta shafa fuskar bilyn tana ƙare mata kallo sosai, wani sassanyan murmushi ta sake saki da jawota jikinta ta sake rungumeta, dan ita kaɗai tasan mita gano.
“Ummuna kumuje ciki, sai ku cigaba da murnan”. Jay ya faɗa a hankali kamar bashine yay maganarba. Kallonsa tai shima ta riƙo hannunsa suka sakata tsakkiya shi da Bilkisu, a haka suka shiga falon inda Nabeelah da Anum ke zaune surutu ya kaure tsakaninsu, Anuwar kuma ya tasasu a gaba yana kallon Nabeelah kamar ya samu wani majigi.
Cak Umm-Anum ta tsaya tana kallon Nabeelah da itama tai mutuwar tsaye tana kallon mai tsananin kama da Ummahn ta. Kallon Jawaad Umm-Anum tayi cikin wani yanayi na alamar tambaya. Hannunta ya kama ya zaunar da ita yana ɗan murmushi, sai da ya tabbar ta zauna sannan ya kalli Nabeelah da ke ƙoƙarin gaisheta. Hannun Nabeelah ta kamo ta matso da ita jikinta, da ƴar rawar murya Umm-Anum tace, “Da ace mutum baya ƙara shekaru da girma ni dai da nace wannan Mariya ta ce Jawaad, kamar yanda nake kallon takwarata da kamannin Rahma”. duk da ba yaune karan farko da akace Bilkisu na kama da aunty Mah-mah ba a gabansa sai da ya kalli Bilkisun da tasha jinin jikinta, sai kuma ya ɗauke kansa yana zama kusa da Umm-Anum. “Ummuna ki kwantar da hankalinki kinji, dukkan abinda kike buƙatar ji zaki samu fiyema da hakan har sai kin gaji, yanzu dai kitashi a kaiki inda zakiyi wanka, kuci abinci ki kwanta ki huta, sai komai ya biyo bayan hakan kinji”.
Kansa ta shafa da ja masa hanci tana faɗin, “Rigimammen Mama har yanzu dai ana taɓawa kenan”. Dariya duk su Anuwar sukayi, shi kuma ya zuba musu harara da kama hannun Umm-Anum ɗin ya miƙar da ita. Da kansa yay mata rakkiya har ɗakin bily, itama da tabi bayansu tai saurin shiga bayi domin haɗa mata ruwan wanka.
Nabeelah na ganin Jay da bily sun shige da Umm-Anum tai saurin ɗaukar wayarta ta turama Ummah babba saƙo.
Sai da suka tabbatar Umm-Anum ta shiga wanka sannan Jawaad ya fito, kayansu da Sadiq tuni ya gama shigo musu da su ya saka Anum ta ɗauka na Umm-Anum ta kai mata ɗakin Bilkisu, shi kuma ya kai Anuwar ɗakin baƙi inda zai zauna, Anum ma ɗakin baƙin dake cikin falon bily zata zauna. Bilkisu da Nabeelah da keta ALLAH, ALLAH su Ummah su iso sukai hidimar shirya abinci su kuma a tsakkiyar falon, dan yanda Umm-Anum ta gaji bai kamata a sakata zaman Dining ba.
Tana son tabi Jay ɗakinsa dan ta nuna masa farin cikin data shiga na bazatar da yay mata akan zuwan su Umm-Anum amma haushinsa da takeji ya hanata aikata hakan, sai kawai ta sharesa ta cigaba da harkokin gabanta, dan farin cikin ganin su Umm-Anum ya shafe mata duk wani damuwarta kuma.
A ɓangaren Jawaad shima tun shigowarsa ɗakin ya ke zuba idanu ya ga bilkisu ta biyosa amma sai yaji tsit, duk da farin cikin ganin mahaifiyarsa da ƙannensa ya shafe masa duk wani ɓacin ran da ya samo daga Qaseem da gidan Dad hakan bai hana ransa sosuwa ba da ƙ
in shigowar Bilkisun, sai huci yake da jera tsagwayen ƙwafa, ayyanawa yake a ransa sai yayi maganin miskilancin yarinyarnan a yau ɗin nan basai gobe ba, dan ya gama lura gadon barcinsa da ta gama ganine yasa take neman fara kawoma rayuwarsa raini (Ka manta wulaƙancin da kai mata kai ɗazun saraki🙄😜).
Tashi yay da ga kwancen da yake saboda jin an fara kiraye-kirayen sallar Magriba. Alwala yayi sannan ya fito, a babban balo suka haɗu da Anuwar da shima ya fito daga sashen baƙi da alamar shirin tafiya masallacin. Yayma abincin da aka shirya a tsakkiyar falon kallo ɗaya ya ɗauke kansa batare da yace komaiba suka fice shi da Anuwar dan falon babu kowa cikinsa.
Da taimakon Bilkisu Umm-Anum ta dawo falon bayan an idar da sallar Magriba, suna zama Ummah babba da Ummah ƙarama da Batool nayin sallama, cikin matsananciyar faɗuwar gaba Umm-Anum ta juya tana kallon ƙofar dan ko'a cikin magagin barci waɗannan muryoyin sunfi gaban mantuwa a gareta balle ma a zahiri.
Kasancewar akwai hasken Genretor da aka kunna tas suke ganin junansu, da ga Ummah ƙarama har Ummah babba jikinsu rawa yake da tsuma sosai, sun ƙurama Umm-Anum idanu tamkar yanda itama ɗin kallonsu take bata ko ƙyaftawa. Su dai su Bilkisu kallonsu kawai suke da son ganin yaya za'a kwashe. A haka Jawaad da Anuwar suka shigo suka samosu. Jay ya kalli su Ummah da mamaki sai kuma ya kalli Nabeelah da ya tabbatar itace da wannan aikin. Aiko sai tai ƙasa da kai gabanta na faɗuwa dan tsoro ta koma bayan bily ta maƙale.
Ɗauke kansa yay daga gareta, ya ƙarasa gaban su Ummah ya tsaya a tsakkiyarsu, hannayensu duka ya kama a cikin nasa, a take duk suka ɗago suna kallonsa hawaye na gangaro musu saman fuskokinsu. Yanda laɓɓansu ke rawa zai baka tabbacin magana suke son yi amma sun kasa saboda ruɗani. Jay yaɗan murmusa yana mai lumshe idanunsa ya buɗe alamar tabbatar musu da wadda suke hasashen ce ba mafarki bane ko gizago. Cikin ƙarfin hali Ummah Babba tace, “Yarona da gaske kake Yaya Bilkisu ce a gabanmu ba mafarkin da muka sabayi bane?”. Yanzunma kansa ya jinjina musu, ya kuma ja hannayensu har gaban Umm-Anum da alamu ya nuna suman zaune tayi. Hannayensu ya saka a cikin nata yana sake faɗaɗa fuskarsa da murmushi yaja jikinsa baya.
A gaban Umm-Anum Ummah ƙarama da Ummah babba suka zube suna fashewa da kuka mai tsuma rai da cin zukata. Umm-Anum ta kawo nannauyan numfashi lokacin da suka rungumeta su duka biyun a jikinsu.
Su Bilkisu dake kallonsu suma hawayen sukeyi, Jawaad kansa sai da ƙwalla ta cika masa idanu, amma jarumta ta saka shi haɗiye kayansa ya koma cikin kujera ya zauna yana jin wani irin matsanancin farin cikin da ƙirjinsa ma ke neman gaza ɗauka. Su Ummah sunkai kusan mintuna huɗu zuwa biyar a jikin Umm-Anum suna raira kuka kafin su saki juna, hannayenta ta ɗaura saman kumatunsu tana shafawa da murmushi saman fuskarta ga kuma hawaye, suma dai murmushin sukeyi hannayensu duka akan nata kumatun suna share mata nata hawayen. “Ashe Mariya ta da Wasila basu girmaba har yanzun? Ashe shagwaɓar nan da akema Yaya tana nan ba'a fasaba”. Dariya ta kwacema su Ummah lokaci guda da kuka, jikinta suka sake faɗawa ta rungumesu tana dariya. Su ma ƴaƴansu dariyar sukeyi da hawaye banda Jay da murmushi ne kawai a saman fuskar tasa.
Da sauri Umm-Anum ta sake ɗagosu tana faɗin, “Ina Rahmah take ita kuma? Ko ba'a nan take aure ba?”. Duk ƙasa sukai da kawunansu hawaye masu zafi sosai na sake rige-rigen fitowa daga idanunsu, Umm-Anum ta shiga girgiza kanta a hankali tana kallonsu a tsorace, “Karku cemin na rasa Rahmah Mariya, kar kucemin rabuwa ta har abada nayi da Rahmah dan ALLAH” “Sai dai haƙuri Yayah, Rahma ta jima da barinmu gaba ɗaya, ta tafi tafiya mai nisan zango da babu iyakar sake ganin juna sai idan ALLAH ya ƙaddara hakan a can wata rana”. Ummah babba ta faɗa zuciyarta na mata zogi tamkar a yaune Rahmah tabar duniya. Yanzun kam Umm-Anum ce ta fashe da kuka mai tsuma rai da cin zuciya, tana son Rahmah, tana ƙaunar Rahma sosai, dan tafi shaƙuwa da ita a kaf cikin ƴan uwanta.
Ganin kukan nasu yana neman yin yawa gashi ha
r ana kiran sallar isha'i sai Jay yay gyaran murya. ɗagowa sukai duk suka kallesa. Ya sakar musu murmushi da waro idanunsa waje kaɗan ya miƙa musu kwalin tissue da ya ɗauka saman centre table. Babu musu suka amsa. “Yauwa Momys ɗina ababen alfaharina, kukan ya isa haka nan kar ku ƙarar mana da hawayenku, lokacin kuka ya wuce yanzu farin ciki ake buƙata da godiyar ALLAH da ya kawo ranar da ba'a taɓa tunani ko tsamanin zuwanta ba, idan kuna kuka mu kuma mi zamuyi to?”. Cikin kaɗa kai Ummah babba tace, “Hakane Jawaad, ALLAH yay maka albarka kaida sauran ƴan uwanka kaji, a ina ka gano mana Zuciyarmu ne yaron albarka?”. “Ihhhmmm karku damu zan faɗa muku komai sweet Ummahs ɗina, amma ba yanzu ba sai tsohon can shima yana gefena”. Daƙƙuwa Ummah ƙarama tai masa tana faɗin, “Sai dai idan iyayenka ne tsoffi”. Dariya ce ta nema kufcema su Bilkisu, suka saka hannaye duk suka kare bakunansu banda Aunty Batool da tayi abunta sosai. Miƙewa yay ya dungurema Aunty Batool kai yay ficewarsa domin yin sallar isha'i.
Bayan sallar isha'i natsuwa da ga UBANGIJI ta kuma saukar musu a zukata, duk da su Ummah suna ƙage da sonjin wani abu daga yayar tasu, kamar yanda itama a ƙagen take sai Jay ya hana, a cewarsa sai sunci sun ƙoshi sannan hakan zata kasance. Babu yanda suka iya suka yarda da batunsa, dan suma sunsan ya cancanci Umm-Anum taci abin ma ta kwanta ta huta, sai dai zukatansu bazasu iya jure hakanba.
Ummah babba da kanta ta bama Anuwar da Anum abinci a baki cike da so da ƙauna, hakama Umm-Anum ta bama Aunty Batool da Nabeelah da Bilkisu, Jay kuma Ummah ƙarama ta bashi. Cikin wani irin farin ciki mai wahalar misaltuwa sukaci abincin suka ƙoshi, dan Umm-Anum har su Ummah ma sai da ta dinga basu a baki da kanta. Abin dolene ya sakaka kuka ya kuma birgeka. Sai da sukai nak da girki suka godema UBANGIJIN daya basu badan ƙarfinsu ba ba kuma dan sunfi kowa ba sannan su bily suka tattare wajen tas. Da taimakon aunty Batool da Nabeelah da Anum suka wanke komai tsaf. Yayinda a falo kuma Jawaad ke ta bama su Ummah labarin yanda komai ya kasance game da ganin Umm-Anum ɗin duk da dama tun a wancan lokacin ya labarta musu a sanadin Bilkisu ne. Wata iriyar ƙauna da soyayyar Bilkisu sai ta ƙara faɗaɗa da daɗuwa a cikin zukatansu. Duk yanda mai hasashe zaiyi tunaninta a zukatansu tafi gaban hakan ta wuce.
Sabon babin fira aka buɗe a cikin falon ba tare da sunma tuna darene ba ranaba, babu mai kallon lokaci babu mai tunawa ma da shi. Ba suba ko Jay da baisan yawan surutu yau sai yaji hakan bai gunduresa ba, wani wajen ayi kuka wani wajen ayi dariya, wani wajen ayi tausayi da al'ajabi. Haka kawai bilkisu ta tsinci kanta da yin matsanancin kuka akan labarin Aunty Mah-mah (Rahmah), haka kawai taji tana ƙwaɗayin ganinta koda kuwa a hotone. Hakama Umm-Anum ta shiga matsanancin mamaki da jin wai Bilkisu ba ɗiyar Rahmah bace ba. Yayinda shi kuma Jawaad al'amarin yay masa tsaye cak a zuciya baisan dalili ba, kawai yanaji a ransa kamar akwai wani abu dake a binne game da rayuwar bilkisun, musamman idan ya tuna da maganar baba ƙaura akan duhun dake biye da Bilkisun, da kuma furucin baba ƙauran a jiya da yaje wajensa saboda kiran da yay masa. ‘Kai anya kuwa babu wani abu........?’ ya faɗa a cikin ransa yana kafe Bilkisu da idanu harta tsargu ta ɗan ɗago suka haɗa ido.
Barci ma da kansa yasan inda yake zuwa yay sata, dan kuwa idanun waɗanan bayin ALLAH ko gyangyaɗi basaji balle ai maganar barci, suna zaune dingangan har agogo ya nuna ƙarfe uku saura na dare. Jay ne ya katse firar tasu da roƙonsu akan suje su kwanta haka da safe idan ALLAH ya kaimu saisu ɗora. Badan sunso hakan ba suka miƙe dan suma susan Umm-Anum na buƙatar ace ta huta kodan doguwar tafiyar da tayo wadda bata saba ba. Su mamaki ma abin ya basu dan basusan lokaci yaja haka ba, jima suke tamkar daren bai wuce ƙarfe goma ba. Dole dai yau su kwana gidan ɗansu.
Ummah babba Umm-Anum da Ummah ƙarama ɗakin bily aka kaisu su kwanta tare da ƴar uwarsu, duk da dai ba kwanciyar sukaiba wani babin sabuwar hirar suka sake buɗewa ma su. Batool da Anum da Nabeelah kuma ɗaki
n dake kusa dana Bilkisu, Anuwar yana a ɗakin baƙi. Jay ya nufi nasa ɗakin, Bilkisu na shirin shigewa wajensu Nabeelah Ummah ƙarama ta korata ɗakin Jawaad.
Sosai kunya ta lulluɓeni har inaji kamar ƙasa ta tsage na shige, to amma yaya na iya suɗin ba abin wasana bane balle nai tunanin musu gardama ma, haka na nufi sashen nasa kamar na nutse dan kunya. Ina jiyo su Nabeelah namin dariya harda Yah Anuwar. Sam banso hakanba, dan naso ace mun samu nisa da juna ni da shi koda na kwanaki biyu ne dan ya fahimci inajin zafin abinda ke faruwa tsakaninsa da ƴan uwana, ƙila ta hakan zan samu ya faɗamin abinda ke faruwar. Badan a ciwon kan da nake ji ba da falo zanyi zamana na ƙarasa daren, haka dai na daure fuska a ciskule na nufi bedroom ɗinsa, ciki ciki nai sallama na shiga, yana kwance a saman gado da ga shi sai noxer kawai, idanunsa a rufe suke amma na tabbata ba barci yake ba, na ɗauke kaina daga garesa na nufi bayi. Ban wani jimaba na fito dan fitsari kawai nayi da abinda baza'a rasaba. Yanda na barsa haka na fito na samesa, bani da kaya a ɗakin, sai naita tunanin mizan saka na kwanta dan bazan iya barci da kayan jikina ba. Ganin lokaci na sake ja ga zazzaɓi nama neman saukarmin yasa na nufi Wadrobe ɗinsa, cikin sa'a kuwa idanuna saka sauka akan t-shirt ɗinsa mara nauyi ruwan toka, nasan indai na saka zata sakkomin dan babbace kuma girman ba ɗaya ba.
Zagayawa nai ta ɗayan gefen na kwanta can ƙarshen gado na juya masa baya.....
“K har kin isa mu kwanta a gado ɗaya ki juyamin baya!”. Na tsinkayi saukar muryarsa da furucinsa a fusace cikin kunnuwana. Ɗan rintse idanu nayi ina haɗiyar yawu da ƙyar, zuciyata sai harbawa take da sauri-sauri na tsoro. A hankali na juyo ina tura baki da sake ɓata fuska sosai, abin mamaki har yanzu yana a yanda yake. A ƙasan ido naɗan hararesa naja bargo na rufe har fuskata ma.
Wani haushi ya sake kume zuciyar Jay, jiyake kamar yay mata filla-filla ɗin da saita ƙarasa daren da kuka, sai dai yanata ƙoƙarin danne fushinsa kawai.
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69 Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84