wani ya shigo, saida na cire komaina kafin na fara saka ƙafa cikin kwamin, ajiyar zuciya na sauke a hankali saboda ɗan ɗumi-ɗumin ruwan mai warware gajiyar jiki, na ida saka ɗayar ƙafar sannan na shige gaba ɗayana, sihirtaccen ƙamshin da ruwan keyine ya sakani lumshe idanu ina karanto addu'ar godiya ga ALLAH da ni'imominsa masu yalwata ta fuskoki da dama ga ɗan adam. Sai da nai kusan mintuna uku da zama sannan ta shigo da sallama, ta canja kayanta da wata doguwar riga mai kama da leda, hannayenta sanye da safar hannu ta leda itama, murmushi taimin ta tako inda nake. Ɗan kwalina daban cireba ta zame daga kaina, ta warware gashina da Alhmdllh yanzu ya cika sosai kuma yanada tsayi gwargwado saboda kulawar da naita bashi bisa koyarwar su Ummie tun muna boarding, wani ɗumi mai daɗi naji ya ratsa kan nawa, hakan yasani kallon madubin dake gabana da nake iya hango kaina da ita kanta.
 

        Tace, “A cikin ruwannan zaki kwana, babu abinda zai sameki insha ALLAH karkiji tsoro, ruwane mai ɗauke da sirrika kala-kala da duk macen da aka gyara dasu dolene mijinta yasan ta isa mace, sirrikane na ƙamshi masu daraja a jikin ƴa mace, ƙa'idar makarantarmu watanni ukune domin mace ta samu damar koyon abubuwa masu yawa, ba sirrin gyaran jiki bane kawai mace tafi buƙata a rayuwar aure ɗiyata, zakiga wata macen komai ta iya ta kuma ƙware, amma idan batasan yanda zataima miji maganaba kawai sai ya rusa mata komai, dan wani namijin shi abinda ke ƙololuwar birgesa ga mace shine iya magana, wani kuma a kallo kawai zaki gama dashi, wani tafiya, wani girki, wani ƙamshi, wani shagwaɓa, wani kwalliya, wani kwanciya. Karki sakama ranki cewa tarayya da miji a gado shine kawai farin cikin aure ko shikaɗaine auren, hakan kuskurene, wani namijin ƙanƙanin abun da kika raina shike sakashi farin ciki. Karkiyi tunanin gyara kanki yana nufin kin mallaki namiji ya zama naki ke kaɗaine, macen data isa mace bata shakkar zama da kishiya ɗiyata, dan wani lokacin zama da kishiya nasake bayyana darajar macene a wajen mijinta. Karkuma kiyi tunanin babu wata mace data isa raɓar mijinki dan yana sonki ko kin iya komai, wani namijin badan baya sonki yake miki kishiyaba ko yake budurwa, a'a halayyar san mace fiye da ɗaya a jinin maza yake, ko bazasu ƙara aureba saisun kalla. kizama mai gyara aurenki ta kowanne ɓangare, idan nace kowane ɓangare ina nufin kowanne fanni hatta da ƴan uwansa da duk abinda ya shafesa. Inason ki cire komai a cikin ranki ki nutsu ki bani dukkanin hankalinki a kwanakinan goma sha biyu da zamuyi tare, sonake komai na cikinsa ya zama tamkar rubutu bisa dutse a cikin ƙwaƙwalwarki, ki ɗaukeni tamkar mahaifiyarki, kuma ƙawarki aminiya wadda zaki iya magana kowacce iri da ita batare da kinji kunya ba, inhar kika riƙe duk abinda zaki koya a kwanakinan ina mai tabbatar miki bazaki taɓa goguwa a zuciyat mijinki ba koda zai auri mata uku ku zama huɗu bayan ke”.
         Idona a risine na ɗaga mata kai alamar to, inajiyo sautun murmushinta itama. Abu ta fara shafamin a fuska tana cigaba da min magana cikin nutsuwa, sosai kunya ta lulluɓeni, dan abubuwane masu matuƙar nauyi a gareni take faɗa a buɗe, ta haɗe fuska a yanzu babu wasa tattare da ita ko kaɗan. Saida ta gama tsaf sannan ta fita suka sake dawowa da wata mata. Matar ta nunamin da faɗin, “zata zauna dake anan, ni zan koma gida sai da safe idan ALLAH ya kaimu zan dawo”. Kaina na jinjina mata dan ta hanani magana tunda ta shafamin abin fuskarnan.

            Duk yanda zan baku labarin abinda ya gudana a kwanakinan da wahala ku iya fahimtata, abubuwan dana koya kam ba'a magana, sam Umm-Anum bata wasa dani idan akazo ɓangaren abinda zan iya jin kunyarta balle naga fuskar yin sakaci da abinda ake koyamin, tsaye take kaina ɗari bisa ɗari, komai buɗemin shi take babu hijjabi, aduk lokacin da takemin bayani aka abinda yafi ƙarfin kaina tamke fuska take tamau babu wasa, kai jama'a hatta da salon tafiya ba'a barniba sai da aka koyan, komai a tsare yake. Matar da take bari ta kwana dani kasa haƙuri tayi ranar dai take tambayata wai kodai ni ƴar uwar Umm-Anum ce? Dan ita yanda take ganin tanamin ya ninka yanda takema ɗalibanta fiye da zato. An kawoni ɗaki na musamman, sannan komai ba'a sakani cikin ɗalibai ni kaɗai ake koyamashi a nutse, daɗin daɗawa da kanta take min komai bata yadda kowa yayminba sai abubuwan da ba'a rasaba, dan takance kowa a rayuwa da irin basirar da ALLAH yay masa, abinda suma sauran malaman makarantar suke koyamin zai amfanar dani ta fannoni da dama. Murmushi nayi nidai bance komaiba, dan nikaɗai nasan mi nakeji game da matar nan, ita kanta lokuta da dama nakan kamata ta shagala da kallona, kallo maiban mamaki, kallo irin na shagala da zurfi ason tunano wani abu, idan tai irin wannan zurfin kuma zakaga daga ƙarshe ta dafe kanta tamkar zata fita cikin hayyacinta. Akwai randa naga kallon har yaso yimin yawa, sannan ni kaina yanda takemin ɗin nasan ba kamar yanda takema kowa baneba, tana sakin jiki dani fiye da hasashen mai hasashe. Akwai randa tazo tana koyamin

girki sai muke ɗan hira kaɗan-kaɗan, cikin dabara nake tambayarta ko zasuje ƙasarmu nan kusa?. Shiru tai bata bani amsaba, na kasa daurewa dai na sake mata tambayar cike da ladabi. Yanda ta juyo ta kalleni fuska a haɗe saida naso firgita. Kaina na duƙar ƙasa ina faɗin, “Kiyi haƙuri dan ALLAH Ummu, bansan tambayar zata ɓata ranki ba”. Sautin murmushinta na jiyo, hakan yasa na ɗan ɗago na kalleta, ta ajiye cokalin hannunta tazo ta kama hannayena, murya a sanyaye tace, “Ɗiyata ba laifi kikayiminba, ƙasar takuma ni ban taɓa zuwantaba ai, duk amintakar dakika gani tsakanina da ƙanwata Gimbiya Munaya ban taɓa ziyartarta ba, sai dai ita idan tazo nan mu haɗu, duk lokacin danai yunƙurin zuwa nakan tsinci kainane a wani mummunan hali da baida fassara”. Tana gama faɗa ta saki hannuna ta juyamin baya, aikin da mukeyi ta cigaba dayi batare da ta sake min maganarba.
     Ajiyar zuciya na ɗan sauke hawaye na ziraromin, haka kawai yanda tayi maganar sai naji abun daban, to amma ai Ummu ta sanarmin itaɗin ƴar ƙasarmu ce, sanadin neman magani ya kawota nan hartai aure, itakuma gashi yanzun tace bama ta taɓa zuwa canba, anya kuwa babu wani sirrin dake ɓoye?.......
        Ajiyar zuciya na sauke da saurin kallonta jin ta taɓanu, tace, “Kinama fahimtar abinda nakeyi kuwa?”. Da sauri na ɗaga mata kai alamar eh na tattara hankalina gareta baki ɗaya.


____________________________

           A ɓangaren Jawaad ma dai shirye-shirye sun kankama, an gama gyaran gida tsaf, ya canja kamanni gaba ɗaya tamkar bashiba, amarya kawai yake jira ta shigo cikinsa. Gaba ɗaya a tsakaninan a busy yake matuƙa, ga aiki ga shirye-shiryen biki dasu Jabeer ketayi naban mamaki, dan gayya suke ta gaske da gayya tamkar wannan shine auren farko da Jawaad ɗin zaiyi. Shidai ya zuba musu idone kawai yana kallon ikon ALLAH, dan dayay magana ca sukai babu ruwansa, kawai dai yama shirya dan bai isa cewa bazaije wajen abinda suke shiryawanba ehe. Bai sake musu maganarba kuwa ya cigaba da nasa harkokin, maganar kayan da za'a saka a gidan kuwa gimbiya Munaya tace Takawa yace zaiyi komai, kayan kicin kuwa itace zatayi. Da yay mata maganar lefe tace masa ya dakata, zasu nema Dady suyi magana, sai ana saura kwana biyu tarewar za'a kaisu can gidan Dad ɗin dan sune sukafi cancanta da amsar lefen, koyayane zasu bashi matsayinsa na uba kodan ɗawainiyar da yay da Bilkisun. Jawaad baice komaiba shi dai sai ALLAH ya kaimu.

       A yau tunda safe Su Amaturrahman suka shirya yima Mami (Munubiya) rakkiya gidan kamar yanda Gimbiya da Takawa suka buƙata, zataje su haɗu da kamfanin da zasu shirya gidan. bayan sun duba saisu zaɓa mata kalar data dace a tsara komai yanda ya dace..............✍


Bara dai na baku hakanan, inata ƙoƙarin typing ɗin bayan tafiyar baƙi amma kiraye-kirayen waya ya hanani nutsuwar yi da yawa, takaima harna daina ɗaga wayoyin mutane wlhy🤦🏻😑😓.
[1/11, 10:48 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: ƘWAI CIKIN KAYA!!
.
Book Two
.
Bilyn Abdull 📚:
Page 35

.................Rintse idanuna nai da azabar ƙarfi, a duk lokacin da jikinsa ya taɓa nawa nakanji tamkar na taɓa wuta, daga randa mukaje ɗakko gawar Gimba kuma sai na rage jin hakan, sai dai sam banason yace zai taɓani, amma a mamakina yau sai naji tamkar an azani bisa wutar. A take jikina ya fara karkarwa saboda azabar da nakeji, cikin gangarowar hawaye bisa idanuna nace, “Boss dan ALLAH ka matsa, wlhy jikinka tamkar wuta nake jinsa”.
      Yanda ta ƙare maganar da fashewa da kuka tana neman silalewa ƙasa yasaka Jay ja baya cikin ɓacin rai, dan shi kalamanta zafi sukai masa a zuciya, cikin kaushin murya yace, “Qaseem ne kawai idan ya taɓaki baƙyajin zafi tunda shi kikeso?”. Idanuna na shiga lumshewa ga zufa sai karyomin take a jiki saboda azabar da nakeji, na shiga girgiza masa kawai, “Kaimin addu'a, fatar jikina jinake tamkar ana ɗayemin itane”. Yanzu kam da mamaki yake kallonta, dan yanda jikinta ke wani irin karkarwa da zufar da takeyi ta cancanci a fahimceta, kalaman baba ƙaurane suka faɗo masa cikin rai, addu'ar ya shiga karantowa yana tofa mata, idanunsa harsun ƙaɗa sunyi jazur saboda yanda yakeji a cikin ransa, gaba ɗaya yakan rasa wane tunani zaiyi akan lamarinnan, idan ya zurfafa tunaninma sai kiji kansa ya fara matsanancin ciwo, dole yake ajiye batun ya shiga wata sabgar badan kuma al'amarin baya cikin ransa baneba. Ahankali Bilkisu ta shiga sauke numfashi, zufar na tsafewa sanyin ac na ratsata, kusan mintuna goma suna a haka.

      Rose da tunɗazun tai sumar tsaye tai Luuuu zata faɗi saboda wata hajijiya data rufe ganinta. Da sauri Hafiz da isowarsa kenan dasu Jabeer ya tarota. tai ƙoƙarin ƙwacewa jikinta na rawa zata sake danna kai cikin office ɗin idanunta na zubar hawaye Hafiz yay saurin sake fusgota, cikin tsawa-tsawa yace, “Rose! Minene kikeyi hakane?”. Wasu irin zafafan hawayene suka shiga rige-rigen sake gangaro mata saman kumatu, ta tsare Hafiz da kallo, hannu na rawa ta nuna ƙofar office ɗin Jay, “Boss fa rungume da yarinyar nan”. Cikin takaici Hafiz yace, “Idan ya rungumeta sai akai me? Ba matarsa bace! matarsa ce ita halalinsa, ke kanki shedace akansa, inda Jay yana harkar mata ke zai fara lalatawa ai” ya ƙare maganar da balla mata harara yaja tsaki ya juya yabar wajen.
     Da sauri Rose ta maida kallonta ga Jabeer da Aliyu. Tace, “Kunajinfa miyace, miyasa Hafiz baya ƙaunata?”. Ɗan murmushi Jabeer yay yana girgiza kansa, “Hafiz ba ƙaunarkine bayayi ba, gaskiya ya faɗa miki, Mami matar Jay ce yanzun”. Daɓar Rose ta zauna ƙasa tana faɗin, “Jesus, shikenan na mutu Jabeer, yaushe akai musu auren?”. Duƙawa Aliyu yay gabanta cikin taushin murya yace, “Baki mutuba Rose, kisama ranki haƙuri dan ALLAH karki tada hankalinki kinji, ALLAH ya rubuta itace matarsa, kema naki mijin nanan zuw.......” “Aliy daina faɗamin maganar banza kaji, ni boss zai yaudara, dama tunda naga yarinyarnan na shige masa nasan zatai abinda yafi haka, nasan asiri tai masa kawai”. Ƴar Dariya Jabeer yay shima ya duƙa gabansu, “Rose na faɗa miki gaskiyar magana? Boss shike bin Mami ba ita ke binsa ba, tunda muke da ita bata taɓa nuna wanima a cikinmu ya taɓa koda birgetaba, shi kansa farautar soyayyarta yake amma sam taƙi bada ƙofar hakan, kullum ma nunawa take ita batama taɓa fahimtarsa ba, itaɗin mace ce mai AJI!, shine babban maganin asirinta akan zuciyar Boss, yakamata ki fahimci yana son mace mai suna mace, ma'ana mai Ajiiii!!”. ya ƙare maganar cike da salon iskanci yana salute ɗinta, miƙewa yay tare da mata nuni ta miƙe dan tayi sagafene tana kallonsa da fassara maganganunsa sala-sala.

           Sam Jay baiga Rose ba, Bily kanta data ganta halin data shiga yasa tama manta da ganin nata, ruwa ya ɗakko ya bata, babu musu ta amsa, yanda tasha ruwan sosai har mamaki ta bashi, ta miƙa masa kofin tana godiya, baice mata komaiba sai nuni da yay mata data tashi takoma kan kujera.
       Nima ina buƙatar hutawar, dan haka na tashi na koma saman kujerar na zauna tare da lumshe idanuna.
          Sosai nakeji a jikina kallona ake, ina buɗe idanu muka haɗa ido dashi, ɗauke kansa yay tamkar baniɗin yake kallonba, nima na janye na

wa a raina ina jinjina yanda ya ƙware a iya kallon mutum.
    Babu wanda ya sake shigowa office ɗin har aka kira sallar la'asar, shine ya fara shiga ya ɗaura alwala sannan yace naje nayi nima, lokacin dana fito tsaye na gansa, bance komaiba na nufi hanyar fita yana biye dani.

        Daƙyar Aliyu ya lallaɓa rose suka bar ƙofar office ɗin Jay, kuka take rurus cin ƙarfinta, a zuciyarta tana ayyana matakin gaggawa da zata ɗauka akan Bilkisu nan bada jimawa ba, bazai yuwu tazo jiya-jiya ta samu abinda ita ta kashe shekaru masu yawa tana bibiyaba, dolene kodai ita ta samu, kokima su rasa gaba ɗaya. Da wannan ƙudirin tabar office yau.

      Yau tare dashi mukabar office, a ƙasan raina cike nake da tuhumar ina Yah Qaseem ya shiga? Sam bana ganinsa a office tunda na dawo, mike faruwa dashi ne? Inason tambayar boss inajin tsoron buyaginsa. Munyi nisa a tafiya batare daya kalleniba yace, “Jazuga bai mutuba”. Da wani irin matsanancin sauri na juyo na kallesa, harma na manta dawa nake na kafesa da idanu ko ƙyaftawa banayi”. “Malama idanun nan sunmin yawafa”. Kumbura fuska nai na ɗauke kaina jin abinda yace, sai kuma na kasa haƙuri naɗan sake kallonsa na risinar da kaina, cikin zumuɗi nace, “Dan ALLAH da gaske boss?”. yace, “Mun fara ƴar wasane dake?” kaina na girgiza masa dukda nasan bani yake kalloba. Shiru bai sake cewa komaiba, har muka isa masarauta, dukda inason jin ƙarin bayani haka na daure na danne a raina, idan taƙamarsa jan aji gidan ya taras.
       A cikin ran Jay wani irin haushine ke cinsa, mamaki da takaicin miskilancinta yake, yayi shirune yaji kozata tambayesa cigaba labarin amma yanda yay shiru itama ta tsuke baki, shikuma inhar ba ita tanema jin yanda akaiba bazai faɗa mataba. Babu wanda ya sake yin magana tsakanina da shi har yasamu guri yay fakin gab da sashen gimbiya, dan yanzu shi babu shamaki an bashi damar shigowa cikin masarauta a duk sanda yaso. Yunƙurin buɗe motar nai ya riƙo hannuna. Daƙyar na iya danne abinda nakeji na kallesa, ganin ni yake kallo sai nai ƙasa da kaina, sakarmin hannu yay yana faɗin, “Saiki jira na gama tunda ba tauneki zanyi ba”. Nidai bance komaiba, ya miƙa hannu sit ɗin baya ya ɗakko leda viva sabuwa. “ga wannan, duk yanda zakiyi amfani dasu na rubuta miki, Karkiyi wasa Miemaa, dan ina buƙatar matata a kusa dani” yay maganar ahankali yana kafeni da idanu, saurin sadda kaina nai dan naji wata irin bahaguwar kunya ne. Jay dake kallonta yay wani lallausan murmushi da cigaba da faɗin, “dolene ta hanyarki zan gano bakin zaren matsalarmu, hakan kuma bazai yuwuba kai tsaye sai da taimakon UBANGIJI”. Kaina a ƙasa nace, “Insha ALLAHU zanyi Sir”. “ALLAH ya tabbatar”. Ya faɗa batare da ya da ɗauke kansa daga gareni.
        Nima saina fita a motar ɗauke da ledar da bag ɗina, ta sashensa na zagaya na sake masa godiya sannan na shige, tuni an amshi kayan hannuna tun fitowata a motar.
        Jay daya kafeta da kallo ta cikin mota yaɗan lumshe idanunsa yana sauke ajiyar zuciya lokacin data shige. Shima fitowar yayi. Masallacin masarauta yay salla har isha'i, kafin ya samu damar ganawa da gimbiya a tsaitsaye. Yamata bayanin abubuwa da dama a gurguje, itama ta sanar masa ƴar firar da sukai da Bily da abinda ta fahimta. Duk yanda taso yaci abinci ƙinci yay yauma yaymata sallama ya wuce.

______________________

         Tun daga wannan ranar gimbiya ta sake jan Bilkisu jikinta, riritata take tamkar uwa da ƴa, gefe ɗaya tana koya mata dabarun rayuwar aure cikin hikima kamar yanda itama Mommah tai mata gata, sannan a hankali take fahitar wasu abubuwa daga Bilkisu ta cikin hira. Magungunan da Jay ya kawo mata Amintacciyar baiwar gambiya tsaye take akan Bilkisu dan ganin tayisu kamar yanda ake buƙata, ga maganin sanyi shima da ake bata acewar gimbiya shine matakin farko.
    Kullum da safe driver zai kaita office da yamma idan an tashi Jawaad ya ɗakkota ya maidota, dukda babu wata hirar arziƙi a ciki, yakuma daina raɓarta koda wasa, yanzu sam basama haɗuwa sosai a station ɗin saboda baya zama aiki yaymasa yawa, su kansu yana wajigasu da ayyukan sosai.
     A haka aka shiga wata mai albarka na rama

dhana, manya da ƙananun yara harma da tsaffi kowa ya tashi da wannan ibada a baki cike da ɗoki da fatan kammalawa lafiya. Yayinda Bilkisu ke kallon ikon ALLAH wajensu gambiya dangane da alkairin da ake fita dashi domin talakawa. Abin sai ya birgeta, a cikin ranta tana fatan kwatantawa taji idan zata iya watanara, sannan har yau da take nufar sati na biyu a masarautar bata taɓa gamo da Sarki Sameer ba, Safah ta sanar mata yaje saudia hutawa shida amaryarsa da suke kira Ammi, sai azumi yaje tsakkiya zai dawo sukuma su tafi Umarah

      ★★★★

    Jay da muƙarrabansa sunyi busy matuƙa, ga aiki ga aikin sa kai gana hidimar bayin ALLAH duk ya haɗama kansa, burinsa ya kammala abubuwa da yawa cikin watannan, baya neman Bilkisu ne dan yana tausayinta sosai, ga azumi ga rana dan ruwa bai zaunaba sosai, gani yay ta rame masa a kwanakinan sosai sai tai haske kuma.
     Abin mamaki Rose kuma saita shiga ja baya dasu, har takai saida Jay yamata magana da kasa, ranar kam dai yaga taɓara da iyayi, gashi
Showing 117001 words to 120000 words out of 249282 words