Nabeelah ce ai, ina ka samo mana ita ne haka? Ko dai ta biyu ce?”. Yanzun kam ƙaramar dariya Jabeer yay yana girgiza kansa, “Wai Ummah ta biyu kuma? A wannan marrar ɗayarma ya aka ƙare, sai dai idan zaki nemarwa ɗanki ne, shine gwauro, wajen aikinmu ɗaya da Mom ɗinmu” ya ƙare maganar idonsa a kaina.
Dariya tayi tana sake riƙo hannuna, cikin sigar tambaya tace, “ɗiyata kina son ɗana?”. Kasa cemata komai nai sai ƙasa dana ƙarayi da kaina, a raina ina faɗin, ‘Ni inada Yah Qaseem ɗina’. Jin bance komaiba ta maida kallonta ga Jabeer,
Cike da mamaki tace, “Waima tsaya Jabiru, kana nufin itama irin aikin naku takeyi?”. “Sosaima kuwa Ummah” ya bata amsa cike da karsashi. Haɓa ta riƙe tana sake damƙe hannuna, “Oh ni ɗiyata, kekuma abinda ya burgeki kenan? To Nabeelah kinji fa jaruman mata, ba irinki matsoraciya ba” Nabeelah da mamaki ya kashe tace, “Wai dan ALLAH da gaske?”. Hararta Jabeer yay yace, “Da gaske mana”. Nabeelah tace, “Tab, wlhy bari Yah Jay ya warke nima ƴar sanda zan zama”. dariya Umma da Jabeer sukai mata, nidai na murmusa ina kallonta da faɗin, “Dakin burge kuwa, kinga ƙawata ta dawo kusa dani”. Da sauri ta cafe da faɗin, “Karki damu ƙawa in
a nan tafe, kam Nabeelah ƴar sanda, ashe zan ragargaji ƙattai”.
Jabeer yace, “ko kuma ke su ragargajeki ba”. Ɓata fuska tai da tura baki, “A'a wlhy Yah Jabeer kar kai min baki tun yanzu”.
Kafin ya bata amsa Ummah tace, “Kaga Jabiru kubar wannan ba gajiya zataiba, ku shiga yana ciki, amma ban saniba ko idonsa biyu dan Doctor ya saka masa ruwa tun ɗazun”.
Miƙewa mukai muna faɗin ALLAH ya bashi lafiya.
Oga Jabeer na gaba ina biye da shi har cikin ɗakin nasa da ya gama haɗuwa, babu wani datti balle tarkace, nayi zaton zamu sami matarsa a cikin ɗakin, amma sai naga shi kaɗaine kwance a kan gado lulluɓe da farin bargo, hannunsa ɗaya liƙe da ruwan da ake saka masa, ya ɗora ɗayan saman cikinsa, fuskarsa tayi wani irin fayau alamar yaɗan rame. Yauce rana ta farko dana iya masa kallon kai tsaye kuma na tsawon mintuna, ƙyaƙyƙyawane, komai nasa dai-dai da fuskarsa.........
“Momcy zauna mana” Oga Jabeer ya faɗa cikin katsemin tunani, kaina na jinjina na zauna saman stool ɗin daya ajiyemin kusa da gadon kaɗan, shi kuma ya zauna a bakin gadon kusa da shi, hannu yakai saman kansa yanason jin yanayin jikin nasa, ni dai ɗauke kaina nai na maida wajen kallon ƙaramin hoton dake drawer gefen gadon, da gani tsohon hotone, ƙyawawan mata da miji da suke a ganiyar shekarun ƙuruciya, sunyi ƙyau sosai da dacewa da juna, ga hoton ya ɗauku duk da bana wannan zamanin bane.
Jawaad ya buɗe ido a hankali saboda hannu da Jabeer ya ɗaura masa a goshi, akan Bilkisu dake saitinsa ya saukesu, ya ɗan lumshe ya sake buɗewa akan nata, sunɗan kumburo sannan sun sake girma, daga ciki sunyi jaa kaɗa alamar dai bayajin daɗi. Jabeer ya kalla kafin ya sake maida idonsa kan Bilkisu, ya kuma janyewa yabi inda yaga idonta na kallo shima, hankalinta nakan kallon hoton Mamansa da Abbansa daya ajiye a bed side drawer, shima Jabeer kallon wajen yayi, amma a mamakinsa sai yaga Jawaad yakai hannu ya juya hoton. Murmushi Jabeer yay yana girgiza kansa.
Hankalina na dawo ganin an juya hoton, nai saurin bin hannun daya juyaɗin da kallo har zuwa fuskar mamallakin hannun, idanunsa a kaina suke, dan haka na janye nawa ina ɗan yamutsa fuska, a raina nace, ‘Baida lafiya ma bazai bar shegen kallon mutane ba’.
Jabeer dake binsu da kallo shidai yay ƴar dariya kawai, kafin yace, “A kacema ka warke mu tashi muje kawai?”. Harara Jawaad ya zuba masa, sai kuma ya miƙa masa hannunsa da aka saka ruwan, yay masa alama da ido akan ya cire masa. Kallon ledar ruwan Jabeer yay, yace, “Ya za'a cire bai ƙareba?, saura kaɗan ai, kaɗan sake haƙuri”. Jawaad da sai yanzune zaiyi magana ya yamutse fuska da motsa laɓɓansa a hankali saboda rashin jin ƙarfin jiki, “To sannu likita, kaga ni ciremin, dama Ummah ce ta takura aka sakan”.
Kafin Oga Jabeer yace wani abu na katsesu da cewar, “Ina yini, ya jiki”. Ban yarda na kallesa ba. hakan yasan bansan a yanda ya amsa minba.
Kallonta Jawaad yay ya janye idanunsa, akan laɓaɓansa yace, “Alhmdllh”.
Sallamar Ummah yasa duk muka kalli ƙofa, tace, “A ya ake cire ruwan bai ƙareba?”. Jabeer yace, “Wlhy Ummah kema ƙya faɗa, cayay a cire wai”. Ummah tace, “Kaci gidanku Jawaad, saurin mikake to? Duk abinka dai bazaka fita aikiba yau, dan a gidannan ma zan yini, dan karna tafi ka saci jiki kace zaka tafi ma agogo sarkin aiki”. Fuska ya ɓata, yace, “Kai Ummah ni nagaji da kwanciyarnan, kumafa naji sauƙi” “Haka mukeso dama ai kasamu sauƙin, amma babu inda zakaje, barama na haɗa maka ruwa kai wanka kaji daɗin jikinka”.
Yanda ya cuskule fuska ni saima yaban dariya, a raina nace ‘duk girman ɗa a gaban uwa shi yarone’ Har Ummah ta nufi haɗa masa ruwan sai naga kamar bai dace ba ina zaune na barta da aiki, miƙewa nai ina faɗin, “Ummah ki barshi bara na haɗa, inane bayin?”. Murmushi Umma tayi tana kallon Bilkisu da yaba hankalinta, tace, “To ɗiyata kuma Yayata nagode kinji, ga shinan shiga”. Kaina na jinjina mata na nufi inda ta nuna mani.
Jabeer da yaji daɗin abinda Bilkisun tayi yay murmushi yana kallon Jay, “Jay wlhy yarinyar nan tanada hankali”. Banza Jawaad yay m
asa tamkar baijiba. Jabeer yace, “Nasanfa kaji minace”. “Malam ka cikani da surutu, zaka fita a ɗakinan fa” dariya Jabeer ya kwashe da ita, dan shikam dai ransa na bashi abubuwa da dama. Idanun Jawaad dake harar Jabeer tamkar zasu faɗo ya nuna masa hanyar fita. Jabeer yace, “ALLAH babu inda zani, dama kasamu mukazo dubaka, bara na kira su Hafiz nace karma suzo ka warke”.
Koda na shiga toilet ɗin saida na tsaya nagama ƙare masa kallo, ‘Humm’ kawai na iya faɗa, dukda babu wani datti sai naga dacewar fara wankewa kafin na haɗa ruwan, cikin mintuna ƙalilan na gama tsaftace bayin kafin na haɗa masa ruwa mai zafi sosai, a ganina idan yazo bai masa dai-daiba sai ya sake sirkawa, lokacin dana fito iskesa nai zaune a bakin gadon, kayan barcine jikinsa farare, wandon dogo har ƙasa, hakan yasa banji na takuraba, maganar aiki sukeyi yanzunkam, sai dai shi yana dafe da kansa alamar yana masa ciwo ko yay masa nauyi. nace, “An haɗa ruwan”. Jabeer ne kawai yacemin “Sannu da aiki” shiko baima kalleniba ya miƙe ya nufi bayin yana tafiya a hankali.
Bayan shigewarsa Oga Jabeer ya miƙe yana faɗin, “Bara na sayo masa abu na dawo, kiɗan gyara masa ɗakin”. Kaina kawai na ɗaga masa dukda banso hakanba, sai mita nake a raina akan ‘to ina matarsa da ita bazatazo ta gyaraba, ni kofa haɗa ruwan wankanma dan naga Ummah ce zatayi, a matsayinta na babba kuma bai kamata na bartaba bayan ina zaune a wajen’ haka naita mita ina aiki, na gyara gadon tsaf tare da jera filolin a wani style mai ƙyau, nidai kawai nayine saboda inason gyaran gado dama can, balle irin wannan da yaji kayan shinfiɗa na alfarma, ga filos da yawa. Ina cikin gyaran gadon ne Nabeelah ta shigo da kayan shara. Tace, “Lah ƙawata daga zuwa dubiya sai a sakaki aiki? Ummah tace kije ki huta bara na gyara”. Murmushi na mata nace, “A'a ki barsa kawai, ɗakinma ai babu datti”. ƙasa tai da murya tana kallon toilet tace, “Yayanmu ba'ai masa abin arziƙi ai, kaɗan daga aikinsa ya fito ya sakaki wani aikin kuma”. Tabani dariya yanda takeyi tana kallon bayin, nace, “Dama ya fito ya jiki”. Kafin na rufe baki ta fice a ɗakin da gudu tana faɗin, “Saikin fito, dama girki nake masa”. Kaina na girgiza kawai naci gaba da aikin ina jinjina wautarta, gata dai zamuyi sa'anni, amma nakula Nabeelah autace kodan shiriritarta.
Har na gama gyara komai tsaf bai fitoba, na kammala morping tsaf kafin na ɗauka turaren ɗaki dana gani saman ƴar dirowar farkon shigowa ɗakin kala-kala, ɗauka nai nahau fesawa jikin labuloli da saman gado dama ɗakin gaba ɗaya, a bazata naji an buɗe ƙofar bayin, hakanne ya sakani kallon wajen babu shiri, ai kallo ɗaya nai masa na juya da sauri na nufi ƙofar fita ɗakin, gwangwanin freshener ɗin na ajiye na ɗauki bokitin danai morping nai waje abuna.
Jawaad dai yana tsaye a ƙofar bayin yana binta da kallo harta fice, shima baiyi zaton samun kowa a ɗakinba shiyyasa ya fito kansa tsaye, dukda ma dai sanye yake da rigar wanka a jikinsa ba towel ba, cikin rashin jin ƙarfin jiki ya tako zuwa cikin ɗakin, har yanzu mararsa a ƙulle take, dukda dai bakamar jiya da dare ba, da kuma safiyar yau, danma ƙin faɗama Doctor ɗin ainahin abinda ke damunsa yay, cayay kawai zazzaɓine ke damunsa, shi kaɗai yasan yanda yakejin haushin Shahudah da kuma matakin dazai ɗauka a kanta. Idanunsa suka sauka akan gadon da yanda akaima filolin, kasa ɗauke idanunsa yay har na tsahon mintuna kusan biyu, sosai gadon yay masa ƙyau, sai yaga tamkar ba gadonsa ba.
Tunda na fito Ummah keta faman jeramin sannu, ni dai murmushi kawai nake, na gyara falon saman ma duk da babu datti, falon ƙasa dai Nabeelah na iske ta gyara harma tana morping. Kiran da Umma taimin daga kicin na amsa, ta miƙamin ƙaramin tire data ɗaura kofin tea a kai yanata turiri, “Yauwa ɗiyata dan ALLAH miƙama yayanku wannan ya fara sha kafin wannan uwar shiriritar ta kammala girkin, daga nan sai kiji ko yana buƙatar wani abun kuma”. “To” kawai na iya ce mata na amsa na fito. Koda na fito sai na roƙi Nabeelah tazo ta rakani, catai ALLAH naje ni kaɗai, dan inhar mukaje mu biyu cazai anmasa gayya.
Badan nasoba
na nufi saman ni kaɗai, addu'a nake a raina Oga Jabeer yazo mu wuce. Sai da nai knocking ya bani izinin shiga sannan na shiga da sallama, kaina a ƙasa ban yarda na kalli ko inaba sai gabana, saida naje dab da shine sannan na kallesa sau ɗauya na ɗauke idona, har ya saka kaya, baƙin wando da yellow ɗin riga folo, yana zaune ne a bakin gado da waya a hannunsa, hannunsa ɗaya dafe da kansa yanzu ma, nidai na ajiye tiren a gabansa ina faɗin, “Gashi inji Ummah, tace kanason wani abune?”. Banji ya tankaba, bankuma damu da yace ɗinba dama na miƙe zan fita.
“Zonan” ya faɗa a hankali. Dawowa nai ina jan numfashina da ƙyar, dan duk a takure nake, danma zuwa yanzu kamar naɗan fara sabawa da kasancewarmu tare zuciyata ta sassauta min wajen bugun da takeyi idan har muna tare. Nace, “Gani”. Shiru yaymin kamar ba shine yay kiranaba, sai da yaja wasu sakanni kafin ya nunamin dogon table ɗin dake a gaban gadon ta gaba, “Ɗauka waɗancan keys ɗin, kije Gimba ya kaiki station, zaki ɗakkomin abu a office”.
Duk yanda naso daurewa sai da gabana ya faɗi, ta yaya zanje na buɗe office ɗinsa nikam? A matsayin wa? Na shiga uku, mutumin nan nason jefani a matsala shidai na lura......
“Miemaa!” ya faɗa a ɗan tsawace ganin dukma bayanin da yake mata hankalinta baya tare da shi. Firgigit na kawo numfashi tare da kallonsa, yanda ya danƙaramin harara ya sakani saurin duƙar da kaina. “Ina miki magana kina wani banzan tunani”. “Sorry sir” na faɗa da sanyin murya, dan harga ALLAH banji miya faɗaba”. Ƙaramin tsaki yaja, ya miƙomin waya batare da ya ce min komaiba, amsa nai ina jiran ƙarin bayani, amma sai ya shareni yama ɗauki tea ɗinsa ya fara sha.
“Tashimin a kai kafin na canja miki kalar fuskarki”. Fuska na kumbura na juya na fita ina ƙunƙuni a raina.
Jawaad dake binta da harara yay ƙaramin tsaki da faɗin, “Miskilar banza kawai”.
Banason zuwa ni kaɗai, hakan yasani cema Nabeelah tazo muje ya aikemu, da yake batasan gaskiyar zancenba sai ta bini muka bar Ummah na haɗa masa abinci. A jikin mota muka iske gimba da alamar yasan da tafiyar, zai buɗe mana mota nace ya barsa kawai, murmushi yayi ya shiga mazaunin driver yana tambayarmu “ya jikin boss ɗin” da sauƙi, muka faɗa kusan a tare sannan muka gaidashi.
Tunda muka tafi Nabeelah ke zuba mana surutu, Gimba nata biye mata, nidai murmushi ne nawa idan sunyi wani abun dariyar, har mamaki nake yanda Nabeelah bata gajiya da zance saikace wata akku.
Nidai har Gimba yay fakin addu'a nake ALLAH yasa karna haɗu da Yah Qaseem, gefe kuma ga maganar shiga Office ɗinsa bansan yanda za'a fassarani ba, sauƙinma na taho da Nabeelah ne, tunanin zuwa office ɗin Oga Aliyu ko Hafiz nayi, saisu kaimu office ɗin, a ganina hakan sai yafi, jan Nabeelah nai zuwa Office's ɗin nasu sai dai munyi rashin sa'a duk a rufe alamar bamasa station ɗin kenan................✍
.............Babu yanda na iya dole naja hannun Nabeelah muka nufi office ɗin, sai dai tunma a hawan farko aka dakatar da Nabeelah, ni kaɗai aka bari na wuce, kamar na fasa kuka haka naji, sai dai nayi mamaki a raina yanda babu wanda ya tambayeni mizanje yi?.
Office ɗin na nan tsaf, duk da yau ba'a gyaraba tunda baizoba babu wani datti, yau kam ban cuci kainaba saida nagama ƙare masa kallo gabas da yamma kudu da arewa, hatta da hotunan saman tebir ɗinsa sai da na gama kalleso, tsabar jan magana irin tawa na zauna saman kujerarsa ina gwada yanda yake zama, nakai kusan mintuna huɗu ina shirirtata kafin kira ya shigo wayar da ya bani, ƙurama wayar ido nayi tamkar mai tsoron ɗauka har sai da ta kusa katsewa sannan na ɗauka nasa a kunne batare da nayi maganaba. Daga canma shiru anƙi cewa komai harna tsahon sakanni.
“Baki iya sallama bane?” muryarsa ta daki kunnena a bazata, idanu na zaro waje dan wlhy banyi zaton shi bane, nace, “Sorry Sir” bai amsa minba sai cewa da yay, ki buɗe ƙaraman drawer na jikin table akwai faran leda da kwali a ciki ki ciroshi” na amsa da “to”. Ina ƙoƙarin jawo ledan kwalin ya fita a ciki, hakanne ya sani cirosu ɗai-ɗai shi da ledan, haka kawai na tsinci kaina dason karanta abinda aka rubuta a kwalin, dan da alama na magani ne, shaf na manta da wayar a kunne take bai kasheba, na hau karatun rubutun jikin maganin ina faman zaro idanu saboda fahimtar danai maganin na miye. Daga can Jawaad da yaji a jikinsa akwai abinda ta nutsu takeyi wanda ya ɗaura zarginsa akan maganin cikin sanyin murya yay magana saboda cikinsa dake murɗa masa a lokacin, “Bincike kike mini?” a bazata naji maganar tasa, shiyyasa na saki kwalin ƙasa batare dana shirya ba, cikin rawar baki, nace, “A...a'a sir” shiru Jawaad baice komaiba idanunsa a lumshe yana faman cizon lip ɗinsa na ƙasa, sai da ya lafa masa sannan ya sake maida hankali akan wayar, nikam duk a tsorace nake, gani nake tamkar ya gane mi nakeyi, cigaba yay da lissafo min duk abinda yake buƙata, na sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya jin yabar waccan maganar, na ɗauka kwalin maganin na maida a ledar ina cigaba da ɗaukar duk abinda yace, inda kuma ya faɗa anan nake ganinsa, bayan na haɗasu na zuba a wata leda baƙa na fito.
A ƙasa na iske Nabeelah ta cika tai fam da haushi, taban dariya, hakan yasa na murmusa ina kamo hannunta, ƙwafa tai tace, “ALLAH yayanmun nan ko, saina rama abinda yay min”. Nace, “Miyay miki?” ta sake yin ƙwafa, “Bakiga yasa a hanani shiga office ɗinsa ba, ALLAH nima duk randa na fara aiki bazan bari yazomin office ba”. Yanzunkam kasa jurewa nai saida na dara, “Oh Nabeelah yaushe ya hanaki shiga Office ɗinsa, jami'anmu dai sun hanaki”.
“Kutt wlhy bakisan halinsaba ne, nasan shine yace karsu barni”. Nace, “To kiyi haƙuri, Yaya yayi laifi”. Tunanin zamu dawo yanzu da oga Jabeer yasa ban shiga ko inaba, Mun isa wajen Gimba ya ɗaukemu muka koma, yanzu kam a falon ƙasa muka iskesu harda su Aliyu, mamaki ƙarara na gani a idanun Rose saboda ganina, a tare na gaishesu gaba ɗayansu na ƙarasa gaban sarakin dake kwance a doguwar kujera, cikin girmamawa na ajiye ledan da keys ɗin da wayar a table ɗin dake gabansa nace, “Gashi”. Idanunsa dake rufe ya buɗe ya zubasu a kaina, “Dama tare da Nabeelah na aikeki?” yay maganar yana hararata. Ƙasa nai da idanuna ina girgiza masa kaina alamar a'a. Ƙwafa yay ya ɗauke kansa, ganin hakan yasani barin wajen da nufin bar musu falon ma.
“Waye zai ɗauke miki kayan nan”. juyowa nayi, kafin na ƙaraso wajensa Rose dake zaune a kujerar dake inda ƙafafunsa suke ta miƙe ta ɗauki ledan da cewar, “Ƙyale shashasha boss ina za'a kai?”. Banza yay bai tanka ba, niko na sake juyawa zan fita. “K! Ina wasa dake ko?”. Nazata da Rose ɗin yake hakan yasa nai yunƙuri cigaba da tafiyata Aliyu ya kirani.
“Momi zoki amsa ki kai masa sama kinji”. “To” nace, na dawo na miƙama rose dake ɗauke da ledan hannu alamar ta bani, wata banzar harara ta zubamin ta dangwarar da ledar ƙasa ta koma ta zauna, bance da ita uffanba na ɗauka ledar
Showing 33001 words to 36000 words out of 249282 words
Dariya tayi tana sake riƙo hannuna, cikin sigar tambaya tace, “ɗiyata kina son ɗana?”. Kasa cemata komai nai sai ƙasa dana ƙarayi da kaina, a raina ina faɗin, ‘Ni inada Yah Qaseem ɗina’. Jin bance komaiba ta maida kallonta ga Jabeer,
Cike da mamaki tace, “Waima tsaya Jabiru, kana nufin itama irin aikin naku takeyi?”. “Sosaima kuwa Ummah” ya bata amsa cike da karsashi. Haɓa ta riƙe tana sake damƙe hannuna, “Oh ni ɗiyata, kekuma abinda ya burgeki kenan? To Nabeelah kinji fa jaruman mata, ba irinki matsoraciya ba” Nabeelah da mamaki ya kashe tace, “Wai dan ALLAH da gaske?”. Hararta Jabeer yay yace, “Da gaske mana”. Nabeelah tace, “Tab, wlhy bari Yah Jay ya warke nima ƴar sanda zan zama”. dariya Umma da Jabeer sukai mata, nidai na murmusa ina kallonta da faɗin, “Dakin burge kuwa, kinga ƙawata ta dawo kusa dani”. Da sauri ta cafe da faɗin, “Karki damu ƙawa in
a nan tafe, kam Nabeelah ƴar sanda, ashe zan ragargaji ƙattai”.
Jabeer yace, “ko kuma ke su ragargajeki ba”. Ɓata fuska tai da tura baki, “A'a wlhy Yah Jabeer kar kai min baki tun yanzu”.
Kafin ya bata amsa Ummah tace, “Kaga Jabiru kubar wannan ba gajiya zataiba, ku shiga yana ciki, amma ban saniba ko idonsa biyu dan Doctor ya saka masa ruwa tun ɗazun”.
Miƙewa mukai muna faɗin ALLAH ya bashi lafiya.
Oga Jabeer na gaba ina biye da shi har cikin ɗakin nasa da ya gama haɗuwa, babu wani datti balle tarkace, nayi zaton zamu sami matarsa a cikin ɗakin, amma sai naga shi kaɗaine kwance a kan gado lulluɓe da farin bargo, hannunsa ɗaya liƙe da ruwan da ake saka masa, ya ɗora ɗayan saman cikinsa, fuskarsa tayi wani irin fayau alamar yaɗan rame. Yauce rana ta farko dana iya masa kallon kai tsaye kuma na tsawon mintuna, ƙyaƙyƙyawane, komai nasa dai-dai da fuskarsa.........
“Momcy zauna mana” Oga Jabeer ya faɗa cikin katsemin tunani, kaina na jinjina na zauna saman stool ɗin daya ajiyemin kusa da gadon kaɗan, shi kuma ya zauna a bakin gadon kusa da shi, hannu yakai saman kansa yanason jin yanayin jikin nasa, ni dai ɗauke kaina nai na maida wajen kallon ƙaramin hoton dake drawer gefen gadon, da gani tsohon hotone, ƙyawawan mata da miji da suke a ganiyar shekarun ƙuruciya, sunyi ƙyau sosai da dacewa da juna, ga hoton ya ɗauku duk da bana wannan zamanin bane.
Jawaad ya buɗe ido a hankali saboda hannu da Jabeer ya ɗaura masa a goshi, akan Bilkisu dake saitinsa ya saukesu, ya ɗan lumshe ya sake buɗewa akan nata, sunɗan kumburo sannan sun sake girma, daga ciki sunyi jaa kaɗa alamar dai bayajin daɗi. Jabeer ya kalla kafin ya sake maida idonsa kan Bilkisu, ya kuma janyewa yabi inda yaga idonta na kallo shima, hankalinta nakan kallon hoton Mamansa da Abbansa daya ajiye a bed side drawer, shima Jabeer kallon wajen yayi, amma a mamakinsa sai yaga Jawaad yakai hannu ya juya hoton. Murmushi Jabeer yay yana girgiza kansa.
Hankalina na dawo ganin an juya hoton, nai saurin bin hannun daya juyaɗin da kallo har zuwa fuskar mamallakin hannun, idanunsa a kaina suke, dan haka na janye nawa ina ɗan yamutsa fuska, a raina nace, ‘Baida lafiya ma bazai bar shegen kallon mutane ba’.
Jabeer dake binsu da kallo shidai yay ƴar dariya kawai, kafin yace, “A kacema ka warke mu tashi muje kawai?”. Harara Jawaad ya zuba masa, sai kuma ya miƙa masa hannunsa da aka saka ruwan, yay masa alama da ido akan ya cire masa. Kallon ledar ruwan Jabeer yay, yace, “Ya za'a cire bai ƙareba?, saura kaɗan ai, kaɗan sake haƙuri”. Jawaad da sai yanzune zaiyi magana ya yamutse fuska da motsa laɓɓansa a hankali saboda rashin jin ƙarfin jiki, “To sannu likita, kaga ni ciremin, dama Ummah ce ta takura aka sakan”.
Kafin Oga Jabeer yace wani abu na katsesu da cewar, “Ina yini, ya jiki”. Ban yarda na kallesa ba. hakan yasan bansan a yanda ya amsa minba.
Kallonta Jawaad yay ya janye idanunsa, akan laɓaɓansa yace, “Alhmdllh”.
Sallamar Ummah yasa duk muka kalli ƙofa, tace, “A ya ake cire ruwan bai ƙareba?”. Jabeer yace, “Wlhy Ummah kema ƙya faɗa, cayay a cire wai”. Ummah tace, “Kaci gidanku Jawaad, saurin mikake to? Duk abinka dai bazaka fita aikiba yau, dan a gidannan ma zan yini, dan karna tafi ka saci jiki kace zaka tafi ma agogo sarkin aiki”. Fuska ya ɓata, yace, “Kai Ummah ni nagaji da kwanciyarnan, kumafa naji sauƙi” “Haka mukeso dama ai kasamu sauƙin, amma babu inda zakaje, barama na haɗa maka ruwa kai wanka kaji daɗin jikinka”.
Yanda ya cuskule fuska ni saima yaban dariya, a raina nace ‘duk girman ɗa a gaban uwa shi yarone’ Har Ummah ta nufi haɗa masa ruwan sai naga kamar bai dace ba ina zaune na barta da aiki, miƙewa nai ina faɗin, “Ummah ki barshi bara na haɗa, inane bayin?”. Murmushi Umma tayi tana kallon Bilkisu da yaba hankalinta, tace, “To ɗiyata kuma Yayata nagode kinji, ga shinan shiga”. Kaina na jinjina mata na nufi inda ta nuna mani.
Jabeer da yaji daɗin abinda Bilkisun tayi yay murmushi yana kallon Jay, “Jay wlhy yarinyar nan tanada hankali”. Banza Jawaad yay m
asa tamkar baijiba. Jabeer yace, “Nasanfa kaji minace”. “Malam ka cikani da surutu, zaka fita a ɗakinan fa” dariya Jabeer ya kwashe da ita, dan shikam dai ransa na bashi abubuwa da dama. Idanun Jawaad dake harar Jabeer tamkar zasu faɗo ya nuna masa hanyar fita. Jabeer yace, “ALLAH babu inda zani, dama kasamu mukazo dubaka, bara na kira su Hafiz nace karma suzo ka warke”.
Koda na shiga toilet ɗin saida na tsaya nagama ƙare masa kallo, ‘Humm’ kawai na iya faɗa, dukda babu wani datti sai naga dacewar fara wankewa kafin na haɗa ruwan, cikin mintuna ƙalilan na gama tsaftace bayin kafin na haɗa masa ruwa mai zafi sosai, a ganina idan yazo bai masa dai-daiba sai ya sake sirkawa, lokacin dana fito iskesa nai zaune a bakin gadon, kayan barcine jikinsa farare, wandon dogo har ƙasa, hakan yasa banji na takuraba, maganar aiki sukeyi yanzunkam, sai dai shi yana dafe da kansa alamar yana masa ciwo ko yay masa nauyi. nace, “An haɗa ruwan”. Jabeer ne kawai yacemin “Sannu da aiki” shiko baima kalleniba ya miƙe ya nufi bayin yana tafiya a hankali.
Bayan shigewarsa Oga Jabeer ya miƙe yana faɗin, “Bara na sayo masa abu na dawo, kiɗan gyara masa ɗakin”. Kaina kawai na ɗaga masa dukda banso hakanba, sai mita nake a raina akan ‘to ina matarsa da ita bazatazo ta gyaraba, ni kofa haɗa ruwan wankanma dan naga Ummah ce zatayi, a matsayinta na babba kuma bai kamata na bartaba bayan ina zaune a wajen’ haka naita mita ina aiki, na gyara gadon tsaf tare da jera filolin a wani style mai ƙyau, nidai kawai nayine saboda inason gyaran gado dama can, balle irin wannan da yaji kayan shinfiɗa na alfarma, ga filos da yawa. Ina cikin gyaran gadon ne Nabeelah ta shigo da kayan shara. Tace, “Lah ƙawata daga zuwa dubiya sai a sakaki aiki? Ummah tace kije ki huta bara na gyara”. Murmushi na mata nace, “A'a ki barsa kawai, ɗakinma ai babu datti”. ƙasa tai da murya tana kallon toilet tace, “Yayanmu ba'ai masa abin arziƙi ai, kaɗan daga aikinsa ya fito ya sakaki wani aikin kuma”. Tabani dariya yanda takeyi tana kallon bayin, nace, “Dama ya fito ya jiki”. Kafin na rufe baki ta fice a ɗakin da gudu tana faɗin, “Saikin fito, dama girki nake masa”. Kaina na girgiza kawai naci gaba da aikin ina jinjina wautarta, gata dai zamuyi sa'anni, amma nakula Nabeelah autace kodan shiriritarta.
Har na gama gyara komai tsaf bai fitoba, na kammala morping tsaf kafin na ɗauka turaren ɗaki dana gani saman ƴar dirowar farkon shigowa ɗakin kala-kala, ɗauka nai nahau fesawa jikin labuloli da saman gado dama ɗakin gaba ɗaya, a bazata naji an buɗe ƙofar bayin, hakanne ya sakani kallon wajen babu shiri, ai kallo ɗaya nai masa na juya da sauri na nufi ƙofar fita ɗakin, gwangwanin freshener ɗin na ajiye na ɗauki bokitin danai morping nai waje abuna.
Jawaad dai yana tsaye a ƙofar bayin yana binta da kallo harta fice, shima baiyi zaton samun kowa a ɗakinba shiyyasa ya fito kansa tsaye, dukda ma dai sanye yake da rigar wanka a jikinsa ba towel ba, cikin rashin jin ƙarfin jiki ya tako zuwa cikin ɗakin, har yanzu mararsa a ƙulle take, dukda dai bakamar jiya da dare ba, da kuma safiyar yau, danma ƙin faɗama Doctor ɗin ainahin abinda ke damunsa yay, cayay kawai zazzaɓine ke damunsa, shi kaɗai yasan yanda yakejin haushin Shahudah da kuma matakin dazai ɗauka a kanta. Idanunsa suka sauka akan gadon da yanda akaima filolin, kasa ɗauke idanunsa yay har na tsahon mintuna kusan biyu, sosai gadon yay masa ƙyau, sai yaga tamkar ba gadonsa ba.
Tunda na fito Ummah keta faman jeramin sannu, ni dai murmushi kawai nake, na gyara falon saman ma duk da babu datti, falon ƙasa dai Nabeelah na iske ta gyara harma tana morping. Kiran da Umma taimin daga kicin na amsa, ta miƙamin ƙaramin tire data ɗaura kofin tea a kai yanata turiri, “Yauwa ɗiyata dan ALLAH miƙama yayanku wannan ya fara sha kafin wannan uwar shiriritar ta kammala girkin, daga nan sai kiji ko yana buƙatar wani abun kuma”. “To” kawai na iya ce mata na amsa na fito. Koda na fito sai na roƙi Nabeelah tazo ta rakani, catai ALLAH naje ni kaɗai, dan inhar mukaje mu biyu cazai anmasa gayya.
Badan nasoba
na nufi saman ni kaɗai, addu'a nake a raina Oga Jabeer yazo mu wuce. Sai da nai knocking ya bani izinin shiga sannan na shiga da sallama, kaina a ƙasa ban yarda na kalli ko inaba sai gabana, saida naje dab da shine sannan na kallesa sau ɗauya na ɗauke idona, har ya saka kaya, baƙin wando da yellow ɗin riga folo, yana zaune ne a bakin gado da waya a hannunsa, hannunsa ɗaya dafe da kansa yanzu ma, nidai na ajiye tiren a gabansa ina faɗin, “Gashi inji Ummah, tace kanason wani abune?”. Banji ya tankaba, bankuma damu da yace ɗinba dama na miƙe zan fita.
“Zonan” ya faɗa a hankali. Dawowa nai ina jan numfashina da ƙyar, dan duk a takure nake, danma zuwa yanzu kamar naɗan fara sabawa da kasancewarmu tare zuciyata ta sassauta min wajen bugun da takeyi idan har muna tare. Nace, “Gani”. Shiru yaymin kamar ba shine yay kiranaba, sai da yaja wasu sakanni kafin ya nunamin dogon table ɗin dake a gaban gadon ta gaba, “Ɗauka waɗancan keys ɗin, kije Gimba ya kaiki station, zaki ɗakkomin abu a office”.
Duk yanda naso daurewa sai da gabana ya faɗi, ta yaya zanje na buɗe office ɗinsa nikam? A matsayin wa? Na shiga uku, mutumin nan nason jefani a matsala shidai na lura......
“Miemaa!” ya faɗa a ɗan tsawace ganin dukma bayanin da yake mata hankalinta baya tare da shi. Firgigit na kawo numfashi tare da kallonsa, yanda ya danƙaramin harara ya sakani saurin duƙar da kaina. “Ina miki magana kina wani banzan tunani”. “Sorry sir” na faɗa da sanyin murya, dan harga ALLAH banji miya faɗaba”. Ƙaramin tsaki yaja, ya miƙomin waya batare da ya ce min komaiba, amsa nai ina jiran ƙarin bayani, amma sai ya shareni yama ɗauki tea ɗinsa ya fara sha.
“Tashimin a kai kafin na canja miki kalar fuskarki”. Fuska na kumbura na juya na fita ina ƙunƙuni a raina.
Jawaad dake binta da harara yay ƙaramin tsaki da faɗin, “Miskilar banza kawai”.
Banason zuwa ni kaɗai, hakan yasani cema Nabeelah tazo muje ya aikemu, da yake batasan gaskiyar zancenba sai ta bini muka bar Ummah na haɗa masa abinci. A jikin mota muka iske gimba da alamar yasan da tafiyar, zai buɗe mana mota nace ya barsa kawai, murmushi yayi ya shiga mazaunin driver yana tambayarmu “ya jikin boss ɗin” da sauƙi, muka faɗa kusan a tare sannan muka gaidashi.
Tunda muka tafi Nabeelah ke zuba mana surutu, Gimba nata biye mata, nidai murmushi ne nawa idan sunyi wani abun dariyar, har mamaki nake yanda Nabeelah bata gajiya da zance saikace wata akku.
Nidai har Gimba yay fakin addu'a nake ALLAH yasa karna haɗu da Yah Qaseem, gefe kuma ga maganar shiga Office ɗinsa bansan yanda za'a fassarani ba, sauƙinma na taho da Nabeelah ne, tunanin zuwa office ɗin Oga Aliyu ko Hafiz nayi, saisu kaimu office ɗin, a ganina hakan sai yafi, jan Nabeelah nai zuwa Office's ɗin nasu sai dai munyi rashin sa'a duk a rufe alamar bamasa station ɗin kenan................✍
“Team Bil-Qas & Jay-Hud. Saura wani yace sunan baiyiba😏😜😂”
Fatan alkairi a gareku baki ɗaya😍😍😘👌🏼
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
[12/31/2020, 9:31 PM] Abubakar Saleh Kurami: Bilyn Abdull 📚:
Page 12
.............Babu yanda na iya dole naja hannun Nabeelah muka nufi office ɗin, sai dai tunma a hawan farko aka dakatar da Nabeelah, ni kaɗai aka bari na wuce, kamar na fasa kuka haka naji, sai dai nayi mamaki a raina yanda babu wanda ya tambayeni mizanje yi?.
Office ɗin na nan tsaf, duk da yau ba'a gyaraba tunda baizoba babu wani datti, yau kam ban cuci kainaba saida nagama ƙare masa kallo gabas da yamma kudu da arewa, hatta da hotunan saman tebir ɗinsa sai da na gama kalleso, tsabar jan magana irin tawa na zauna saman kujerarsa ina gwada yanda yake zama, nakai kusan mintuna huɗu ina shirirtata kafin kira ya shigo wayar da ya bani, ƙurama wayar ido nayi tamkar mai tsoron ɗauka har sai da ta kusa katsewa sannan na ɗauka nasa a kunne batare da nayi maganaba. Daga canma shiru anƙi cewa komai harna tsahon sakanni.
“Baki iya sallama bane?” muryarsa ta daki kunnena a bazata, idanu na zaro waje dan wlhy banyi zaton shi bane, nace, “Sorry Sir” bai amsa minba sai cewa da yay, ki buɗe ƙaraman drawer na jikin table akwai faran leda da kwali a ciki ki ciroshi” na amsa da “to”. Ina ƙoƙarin jawo ledan kwalin ya fita a ciki, hakanne ya sani cirosu ɗai-ɗai shi da ledan, haka kawai na tsinci kaina dason karanta abinda aka rubuta a kwalin, dan da alama na magani ne, shaf na manta da wayar a kunne take bai kasheba, na hau karatun rubutun jikin maganin ina faman zaro idanu saboda fahimtar danai maganin na miye. Daga can Jawaad da yaji a jikinsa akwai abinda ta nutsu takeyi wanda ya ɗaura zarginsa akan maganin cikin sanyin murya yay magana saboda cikinsa dake murɗa masa a lokacin, “Bincike kike mini?” a bazata naji maganar tasa, shiyyasa na saki kwalin ƙasa batare dana shirya ba, cikin rawar baki, nace, “A...a'a sir” shiru Jawaad baice komaiba idanunsa a lumshe yana faman cizon lip ɗinsa na ƙasa, sai da ya lafa masa sannan ya sake maida hankali akan wayar, nikam duk a tsorace nake, gani nake tamkar ya gane mi nakeyi, cigaba yay da lissafo min duk abinda yake buƙata, na sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya jin yabar waccan maganar, na ɗauka kwalin maganin na maida a ledar ina cigaba da ɗaukar duk abinda yace, inda kuma ya faɗa anan nake ganinsa, bayan na haɗasu na zuba a wata leda baƙa na fito.
A ƙasa na iske Nabeelah ta cika tai fam da haushi, taban dariya, hakan yasa na murmusa ina kamo hannunta, ƙwafa tai tace, “ALLAH yayanmun nan ko, saina rama abinda yay min”. Nace, “Miyay miki?” ta sake yin ƙwafa, “Bakiga yasa a hanani shiga office ɗinsa ba, ALLAH nima duk randa na fara aiki bazan bari yazomin office ba”. Yanzunkam kasa jurewa nai saida na dara, “Oh Nabeelah yaushe ya hanaki shiga Office ɗinsa, jami'anmu dai sun hanaki”.
“Kutt wlhy bakisan halinsaba ne, nasan shine yace karsu barni”. Nace, “To kiyi haƙuri, Yaya yayi laifi”. Tunanin zamu dawo yanzu da oga Jabeer yasa ban shiga ko inaba, Mun isa wajen Gimba ya ɗaukemu muka koma, yanzu kam a falon ƙasa muka iskesu harda su Aliyu, mamaki ƙarara na gani a idanun Rose saboda ganina, a tare na gaishesu gaba ɗayansu na ƙarasa gaban sarakin dake kwance a doguwar kujera, cikin girmamawa na ajiye ledan da keys ɗin da wayar a table ɗin dake gabansa nace, “Gashi”. Idanunsa dake rufe ya buɗe ya zubasu a kaina, “Dama tare da Nabeelah na aikeki?” yay maganar yana hararata. Ƙasa nai da idanuna ina girgiza masa kaina alamar a'a. Ƙwafa yay ya ɗauke kansa, ganin hakan yasani barin wajen da nufin bar musu falon ma.
“Waye zai ɗauke miki kayan nan”. juyowa nayi, kafin na ƙaraso wajensa Rose dake zaune a kujerar dake inda ƙafafunsa suke ta miƙe ta ɗauki ledan da cewar, “Ƙyale shashasha boss ina za'a kai?”. Banza yay bai tanka ba, niko na sake juyawa zan fita. “K! Ina wasa dake ko?”. Nazata da Rose ɗin yake hakan yasa nai yunƙuri cigaba da tafiyata Aliyu ya kirani.
“Momi zoki amsa ki kai masa sama kinji”. “To” nace, na dawo na miƙama rose dake ɗauke da ledan hannu alamar ta bani, wata banzar harara ta zubamin ta dangwarar da ledar ƙasa ta koma ta zauna, bance da ita uffanba na ɗauka ledar
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12 Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84