nima bada sona suke zubowa ba, wani irin tsoro nakeji a raina, saina dinga ganin kamar gilmawar inuwa kuma idanuna, sannan a ƙasan zuciyata wani irin zafi nakeji, kamin addu'a a cikin ruwa”. Kafeta yay kawai da idanu na wasu sakanni, ya ɗan ciza leɓensa na ƙasa yana jawota jikinsa ya rungume. “Ki daure kinji, ki dinga ƙarfafa zuciy
arki, insha ALLAHU babu abinda zai faru ALLAH na tare damu da duk al'amuranmu, kefa jarumace na sani, ko kinaso suci galaba a kanki?”. A hankali na girgiza masa kaina hawayen da nake maƙalewa na sauka masa saman ƙirji, nace, “Insha ALLAH zanyi kamar yanda kace”. Yace, “Yauwa my sweet princess, tashi kici abinci ki manta da komai dake zo miki a rai kinji”.
Munkai tsahon mintuna uku a haka kafin ya ɗagoni, addu'ar yaymin a cikin ruwa kamar yanda na buƙata ya bani na sha, a take na fara zufa duk da kuwa falon fanka na aiki, wata nutsuwace ta fara saukarmin a hankali har naji nauyin da kaina yayi ya ragu sosai, sai ajiyar zuciya kawai naketa saukewa. Da kansa ya bani naman, duk da a kunyace nake matuƙa haka na daure naci, sai dai banci da yawaba nace na ƙoshi, amma ƙin saurarena yayi ya cigaba damin ɗurar dole. Daƙyar na samu ya barni, tashi yay babu jimawa ya dawo ɗauke da ɗan box a hannu, ni dai harma na ɗan fara gyangyaɗi dan sosai naji nutsuwa a daga ruɗanin dana fara shiga ɗazun, dama ga yunwa kuma. magani ya bani na sha.
“Tashi kije ki kwanta dare na sake yi”. Kaina dake a ƙasa na ɗaga masa na miƙe, rashin gyalenan a jiki duk jina nake a matuƙar takure.
Jay ya bita da kallo harta shige, ajiyar zuciya ya sauke a hankali yana jingina da kujerar tare da lumshe idanunsa, tausayi take bashi sosai, kallo ɗaya zakai mata ka fahimci tanada damuwa sosai, yasan zafin rashin iyaye, dan haka yake tausayin duk wanda bai dasu, balle mace ma mai rauni irinta dake zagaye da ruɓaɓɓun dangi gaba ɗaya, garashi dangin uwa na ɗauke masa kewa da damuwa ma. Yanzukam ya samu kwanciyar hankali duk wani motsinta zai kasance a kan idanunsa, a yanzune zai binciko abinda ke binne da iznin ALLAH.
Da wannan tunanin ya tashi ya shiga ɗakinsa, wanka yayi da ruwa mai zafi yay shafa'i da wutiri, maganin shima yasha dan kansa ciwo yake masa sosai dauriya kawai yakeyi.
★★★★★★
Kasancewar maganin da ya bata harda na barci tuni barcin yay awan gaba da ita, kayantane a jikinta bata canjaba, hakan ya saka Jawaad daya shigo tsura mata idanu, komanta ya ƙara canjawa, musamman ma fatarta tai wani irin gogewa sai ƙyalli takeyi, a fuskarta kawai zaka karanci bata da son hayaniya, komai nata tsaka tsakine, hakan yasa ƙyawunta ya kasance mai sanyi, a kallo ɗaya bazaka taɓa ganin sirrin ƙyawunta ba dan batada cika ido irin na Shahudah, yanda take nutsatstsiya haka ƙyawuntama a hankali yake bayyana ga mai kallonta. Tanada kwarjini da cikar haiba na isassun mata masu kamun kai. Yaɗan lumshe ido ya sake buɗewa a kanta, a fili ya furta, ‘Sai jan ajin tsiya da miskilanci ga tsoro kuma ba’. Yay maganar yana nufar akwatinta da aka jiye alamar kayantane a ciki, buɗewa yay, a sama yaci karo da kayan barci har kala uku, doguwar riga da bazata wuce rabin cinyaba, sai riga da wando kala biyu. Riga da wandon ya ɗauka dan sun ɗanfi kauri da mutunci, yasan dai saka matasu akayi daga gani. Zama yay bakin gadon kusa da ita, ya janye bargon data rufama ƙafafunta zuwa ƙugu, zif ɗin rigar ya janye ƙasa bayan ya zame ɗan kwalinta gashinta da yasha gyara yanata ƙamshi ya bayyana.
Cikin barci naji ana ƙoƙarin ciremin kaya, da ƙyar na buɗe idanuna sai naci karo da shi, ai babu shiri na miƙe zaune duk da jikina babu wani ƙarfi, na dafe rigar da har ya ciren hannu guda batare da na yarda mun haɗa ido ba.
Kayan daya ɗakko mata ya ajiye saman cinyarta yana miƙewa, “Ki canja waɗanan kayan dan zasu takuraki sunyi nauyi da kwanciya barci”.
Da kallo kawai na iya bin bayansa ina haɗiye tsoron da saura kaɗan ya hudan zuciya, gaba ɗaya mamaki al'amarinsa ke bani, wai dama haka yake boss ɗinan ashe, yanzu daban farkaba nufinsa shine zai sauyan kayan? Tabɗi wlhy daya gama dani kuwa. Saida yaje ƙofa zai fita sannan ya juyo yana kallona, “Idan kika bari mintunan dana ɗiba miki ya cika baki tashi kin sauya kayan nanba, hummm..” yay maganar murya ƙasa-ƙasa amma daɗan karsashi sannan ya fice.
Kamar nayi kuka haka naji, na kalli kayan barcin da ya ajiyemin tare da ɗagasu, riga ce ƙarama dan ko ɗuwawuna bazata saukaba, hannunta ɗan si
riri sai wando da nasan iyakar gwiwa zai tsaya min. Sanin halinsa ya sakani miƙewa ina sauke ajiyar zuciya, dan nasan zaiyi duk abinda yace ɗin, canja kayan nai ina addu'ar ALLAH yasa bazai dawo ba dai. Ina kammalawa na kwanta. sallamarsa ta daki dodon kunnena.
Sosai na waro idanu waje naja bargo na rufe duk jikina, ganin ya zagaya ya kwanta ta ɗayan gefen Cikin in ina nace, “A a..nan za.. ka kwanta?”. Ba tare daya kalleniba yace, “Uhmm”. Baki na tura ina lullumshe idanu, Cikin ɗan haushi-haushi nace “Ammafa kowa ance da ɗakinsa ai”. Ganin ya juyo yana kallona, nai saurin jan bargon na rufe har saman kaina da shi. Murmushin da baiyi niyyar yi bane ya suɓuce masa, ya matso inda take sosai tare da ɗaga bargon ya shiga shima, saka hannu yay ya yaye na saman fuskartata tare da ɗora kansa saman filon data kwanta suna fuskantar juna, tuni jikinta ya fara tsuma, ta kuma rumtse ido kam, fuskarta duk ta bayyana tsoronta a fili. Hannunsa ya ɗora saman kanta ya shafa gashinta dake kwance luf yasha gyara tun daga goshinta har inda yake ɗaure da ribbon, a hankali ya zame ribbon ɗin gashin ya warware. Ƙoƙarin danne dariyar dake neman kufce masa ya keyi. Tsabar yanda take a tsorace har bugun zuciyarta yanaji dan suna gab da junane sosai, hannunta data sakane ta matse ƙirjinta yay musu kantanga. Da biyu ya tura yatsun hannunsa cikin gashin nata da wani irin salo.
“Na shiga uku ni balki”. Ta faɗa babu shiri muryarta na rawa tamkar zata fashe da kuka tare da ware idanunta gaba ɗaya kansa. Jay daya kasa riƙe dariyarsa yanzun kam ya saki lallausan murmushi da ɗora goshinsa saman nata, “Kinsan baki da ƙarfi miyasa kika nemi faɗan?”. “To yi haƙuri dan ALLAH” ta faɗa tana son jan jikinta baya. “Daga baya kenan yarinya” ya bata amsa shima da sake matsota jikinsa sosai ya matse yanda tilas ta janye hannunta data kare ƙirji da shi dan taji numfashinta na neman barin ƙirjinta. Jawaad kam da yasan da biyu ya matsetan dama ya sake sakin murmushi da manna dukan fuskarsa akan tata har labbansa na gogar nasa. Cikin raɗa-raɗa yace, “Nifa idan aka takaloni faɗa banajin bari saina maida raddi”. Hawayen da bily ke maƙalewane suka zubo mata a kumatu, tace, “To ai na baka haƙuri ko”. “Ni kuma sai ban haƙura ba ai hajjaju” yay maganar da manne laɓɓansu yanda babu damar sake magana ma. Duk yanda take mutsu-mutsu ya hanata kowacce irin damar da take buƙata, karan farko a rayuwarta da hakan ta faru da ita, abinda takema kallon ƙazanta idan ta gani a film yau shine ake mata a zahiri, ba kowa ke matanba kuma sai boss, innalillahi...... itakam taga takanta dama haka mutuminnan yake.......?
(To nima dai bansan hakan yakeba bily sai yanzun, duk zatona waliyyine fa kamar yanda Jabeer ya faɗa😂🚴🏼🚴🏼😜).
★★★★★★★★★
Barcin da suka gaza samunyi da wurine ya ja musu makara, Jay ya janye bilkisu daga jikinsa da ƙyar ya tashi zaune bayan ya kunna fitilar ɗakin, hannunsa dafe da kansa da har yanzu yake jingim alamar ciwon bai saukaba gaba ɗaya, bargon ya gyara mata yana kallon fuskarta da duk hawayen da tai suka bushe, idanunsa yaɗan lumshe yana mai tunanin yanda zasu kwashe da wannan uwar tsoron randa yace mai gaba ɗaya zaiyi, a daren jiyanma ba wani abun kirki yay mataba amma tabi ta ishesa da kuka. Numfashi ya sauke da sauka a gadon. Yasan tilas ne yay wanka kafin yace zaiyi salla, dan haka ya fita zuwa ɗakinsa a gaggauce kafin a tada sallar.
A hankali na buɗe idanuna dake jingim da barci nabi bayansa da kallo harya fice, tunda ya motsa nima na farka, sai dai matsananciyar kunyarsa da nakeji bazata barni na nuna masa na farka ɗinba, abinda ya faru daren jiya ya shiga rige-rigen dawomin a zuciya, hannuna na ɗora saman laɓɓana da sukasha gurza a hannunsa, da wanine ya cemin abinda yay a daren jiya zai iya wlhy sai na ƙaryata, kamar ba boss ɗin nanba na office gwanin hayaƙi da mazurai, sai yaso kaga walwalarsa balle akai ga dariya, yanda yake mara hayaniya a zahiri haka yake a komaima nasa babu hayaniyar, ajiyar zuciya na sauke murmushi na suɓuce mani, tashi nai nima dan ina buƙatar gyara jikina dukda barcin da nakeji na fitar hBilyn Abdull 📚:
ankali. Gadon na gyara sannan na nufi bayi, wanka nai da ruwa mai zafi ina addu'a a raina ALLAH yasa kar jinin nan ya ɗauke yau, dan nasan a ƙa'idar kwanakin da nakeyi zuwa rana zai ɗauke, dama yanzun kaɗanma na gani a jikin pad ɗin amma bai ɗaukeba, to na tabbata zuwa azhar bazan gansaba. Ina fitowa doguwar riga na zura na koma gadon dan har wani jiri-jiri nake gani saboda barci, yau ko azkar na kasayi, aiko kafin na farga na lula.
Ɓangaren Jawaad ma ana idar da salla da ƙyar ya daure yay azkar ɗin, yana kammalawa ya nufo gida, sama-sama suka gaisa da maigadi ya shigo gidan, yasan Bilkisu barci take tunda dai ba salla zata tashi yiba. Ɗakinsa ya shige, jallabiyar jikinsa kawai ya zare ya haye gadonsa shima sai barci.
_________________________________
Da ƙyar likitoci suka samu Shahudah ta farfaɗo kusan ƙarfe biyun dare, ba ita kanta dake cikin mawuyacin halinba harsu kansu sunyi matuƙar jigata, gasu Dad duk sunbi sun ruɗa musu asibiti sai kace ran ƴar tasu a hannunsu yake. Aiko koda ta farfaɗo allurar barci kawai sukai mata ta sake komawa, suna fitowa su Momy dake wujiga-wujiga suka yo musu caa da tambaya. A yanzu bazasu iya wani zaman musu bayaniba dan haka sukace kawai ta farfaɗo.
Koba komai su Dad sun sami kwanciyar hankali, dan shi kansa ɗazun harda hawaye yayi, baisan irin ƙaunar da yakema Shahudah ba a rayuwarsa, musamman ma a rin wannan lokacin da wani gagarumin abu mai taɓa zuciya da tashin hankali keson faruwa da ita, sam zuciyarsa bazata iya ɗaukaba gaskiya, bama zai yuwuba, dolene ya nema mafita kafin lokaci ya ƙure. Shahudah sa, ɗiya mafi soyuwa a zuciyarsa, kai ina bazai yuwuba, dolene yasan mai yuwuwa, ya yarda ya rasa komai akan Shahudah wlhy.
Haka suka kwana a asibiti hankalinsu tashe har ALLAH ya wayi gari lafiya.
Misalin takwas na safe Shahudah ta farfaɗo bakinta na kiran sunan Jawaad, kuka take rurus da roƙon a kira mata Jawaad ya saki Bilkisu inba hakaba zata kashe kanta.
Kasancewar har mama Atika da bama lafiyar ƙafane da itaba tazo asibitin itama tunda safe suka rufu kanta suna lallashi da bata baki akan cewar ai Bilkisu bata tareba wai, kuma ta kwantar da hankalin Jawaad zaizo anjima kaɗan. Sam taƙi sauraren kowa, daga ƙarshe dai dole Doctor ya sake zuwa yay mata allurar barci mai ƙarfi dan jininta yay masifar hawa.
Doctor ya kalli Dad da Momy dake zaune a gabansa bayan ya gama rubuce-rubuce a takarda. Momy ta sake share hawayen da tun ɗazu ke mata ambaliya a saman kumatunta, “Doctor ka sakamu a duhu, kace muzo kuma kaƙi kace mana komai, mike faruwa ne da yarinyarmu?”. Numfashi Doctor ya saki yana goga biron hannunsa saman gira, kafin ya sake ɗagowa ya kallesu. “Maganar gaskiya bazan ɓoye mukuba yarinyarku na cikin haɗari, jininta ya hau ƙololuwa kasancewar tana ɗaukar abu da girma fiye da kima, wannan shine karo na biyu datai irin faɗuwar da ba'ason duk mai hawan jini irin nata da yi, dan kai tsaye take kaisu ga paralysis, yakamata ku daure ku sama mata abinda ta keso koku ɗauki ɗammarar ƙwantar mata da hankali ta hanyar data dace. sannan akwai wani ciwo da muka gano tana dashi wanda ita kanta da wahala ace tasan a kwashi, dan baikai lokacin da har yanzu zai fara ciwon da zatajisa a jikinta ba”. Cikin matsanancin ruɗani Dad da Mom ke tambayarsa wane ciwo ne?. Kafaɗunsa yaɗan ɗage yana sauke numfashi, “Karku damu bamai ɗaga hankali bane can sosai, domin ko babu ciwon ai sai ALLAH ya ƙaddara mutum zai haihu a duniya dama. Alamu sun nuna yarinyarku ta taɓa cire ciki, bincikenmu da hasashenmu ya nuna mana kuma kamar wata allura tayi yayin zubarwar, a zahiri wannan allurar tana aiki fiye da zato ga mace mai son zubda ciki, dan a ƙanƙanin lokaci take rugurguje ɗan tayin dake mahaifa ta kuma ɓarosa waje, sai dai idan akai rashin sa'a da yanayin jinin mutum takan haifar da matsala a mahaifa daga baya musamman idan anyita babu ƙa'ida, sai bayan wasu shekaru kuma ake gani illar da taima mace, wata macen haihuwace bata sakewa kwata-kwata, wata kuwa ruɓarmata da mahaifar takeyi har sai an cire mata, to Alhmdllh ita duk hakan basu
kasance a gareta ba”. Ajiyar zuciyar Dad da Mom suka sauke lokaci guda, Doctor ya cigaba da faɗin, “Sai dai wani ƙari ya fito a bakin mahaifar, a hankali kuma zai rinƙa girma inhar ba'ai mata aiki ba, zaita girmane cikinta na girma kamar mai ciki, idan tsautsayi yasa ya fashe kuma sai ta ringa zubar da ruwa mai wari”. Idanu a waje cike da tsoro su Dad suke kalon Doctor, cikin rawar baki Dad yace, “Likita amma ai kace ana cirewa?”. “ƙwarai Alhaji ana cirewa, sai dai itamafa cirewar nada nata haɗarin, dan zaku iya rasata a dalilin cirewar, idan kuma an dace za'a cire lafiya ta tashi”. Kuka Mom ta fashe dashi iya ƙarfinta, shi kansa Dad dauriya kawai yakeyi, amma kallo ɗaya zakai masa ka fahimci tsagwaron tashin hankalinsa. Murya a sanyaye yace, “Wannan itace kaɗai mafitar Doctor?”. Doctor yace, “Eh to akwai wata mafitar bayan wannan”. Cikin rawar jiki Mom tace, “Wacece Doctor faɗa mana ita dan ALLAH”. “Hajiya mafitar ƙarshe itace shan magani, zamu iya bata maganin da zata shashi a sati sau ɗaya, ya kama a wata guda sau huɗu kenan, sai dai yanada matuƙar tsada, sannan zata cigaba da shansane har illa masha ALLAH, amfanin shansa anan bazai bar wannan ƙarin ya cigaba da girmaba, sannan bazata sake samun cikiba sai abinda ALLAH ya ƙaddara wannan ikonsane da rahamarsa idan yaso, nidai iya hasashena na faɗa sanin gaibu kuma sai ALLAH”.
________________________________
Knocking ƙofa da akeyine ya saka Jawaad farkawa, guntun tsaki yaja yana buɗe idanunsa akan agogon ɗakin nasa, ƙarfe goma harda mintuna sha bakwai, ya ɗan lumshe idanu ya sake buɗewa kafin ya tashi zaune da ƙyar. Lallai yasha barci sosai ashe. Sauka yay daga gadon ya nufi toilet, fuska ya wanko ya kuskure baki ya fito, jallabiyar da yaje masallaci ya ɗauka ya zira.
A falo suka haɗu da Bilkisu wadda itama bugun ƙofarne ya tasheta, nbatare da ita tama gansaba ta buɗe ƙofar. Nabeelah ce ɗauke da basket.
Murmushi nai mata ina matsawa na bata hanya ta shigo tana ƴar dariya damin shaƙiyanci. “Ta wajena naga duk kinyi wani laushi, ko Yayanmu ya angwanc..........”
Jin tayi shiru tare da jan biriki bata ƙarasaba ya sani maida ƙofar na rufe na juyo. zaune yake saman kujera ya ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya yay bala'in ɗaure fuska da tsatstsareta da idanunsa masu ban tsoro ga marajin magana. Ba itaba hatta ni saida na tsume, dan a bazata na gansa tunda sanda na wuce ban ganshi a wajenba.
Yaƙi cewa komai kuma yaƙi daina kallonta, a hankali takai ƙasa ta durƙusa kamar wata munafuka, muryarta har rawa take wajen faɗin, “Yayanmu ina kwana”. Bai amsa mataba, sai sake ɗaure fuska da yay yace, “Ƙarasa abinda kika fara”..................✍
ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.
SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;
ƊAURIN ƁOYE
ALƘAWARIN ALLAH.
HAFSAT RANO tazo muku da;
SAUYIN ƘADDARA
ƊAURIN GORO
MAMU GEE tazo muku da;
BURI ƊAYA
ƘAUNAR MU.
MISS XOXO tazo muku da;
KAIMIN HALACCI
Showing 132001 words to 135000 words out of 249282 words
arki, insha ALLAHU babu abinda zai faru ALLAH na tare damu da duk al'amuranmu, kefa jarumace na sani, ko kinaso suci galaba a kanki?”. A hankali na girgiza masa kaina hawayen da nake maƙalewa na sauka masa saman ƙirji, nace, “Insha ALLAH zanyi kamar yanda kace”. Yace, “Yauwa my sweet princess, tashi kici abinci ki manta da komai dake zo miki a rai kinji”.
Munkai tsahon mintuna uku a haka kafin ya ɗagoni, addu'ar yaymin a cikin ruwa kamar yanda na buƙata ya bani na sha, a take na fara zufa duk da kuwa falon fanka na aiki, wata nutsuwace ta fara saukarmin a hankali har naji nauyin da kaina yayi ya ragu sosai, sai ajiyar zuciya kawai naketa saukewa. Da kansa ya bani naman, duk da a kunyace nake matuƙa haka na daure naci, sai dai banci da yawaba nace na ƙoshi, amma ƙin saurarena yayi ya cigaba damin ɗurar dole. Daƙyar na samu ya barni, tashi yay babu jimawa ya dawo ɗauke da ɗan box a hannu, ni dai harma na ɗan fara gyangyaɗi dan sosai naji nutsuwa a daga ruɗanin dana fara shiga ɗazun, dama ga yunwa kuma. magani ya bani na sha.
“Tashi kije ki kwanta dare na sake yi”. Kaina dake a ƙasa na ɗaga masa na miƙe, rashin gyalenan a jiki duk jina nake a matuƙar takure.
Jay ya bita da kallo harta shige, ajiyar zuciya ya sauke a hankali yana jingina da kujerar tare da lumshe idanunsa, tausayi take bashi sosai, kallo ɗaya zakai mata ka fahimci tanada damuwa sosai, yasan zafin rashin iyaye, dan haka yake tausayin duk wanda bai dasu, balle mace ma mai rauni irinta dake zagaye da ruɓaɓɓun dangi gaba ɗaya, garashi dangin uwa na ɗauke masa kewa da damuwa ma. Yanzukam ya samu kwanciyar hankali duk wani motsinta zai kasance a kan idanunsa, a yanzune zai binciko abinda ke binne da iznin ALLAH.
Da wannan tunanin ya tashi ya shiga ɗakinsa, wanka yayi da ruwa mai zafi yay shafa'i da wutiri, maganin shima yasha dan kansa ciwo yake masa sosai dauriya kawai yakeyi.
★★★★★★
Kasancewar maganin da ya bata harda na barci tuni barcin yay awan gaba da ita, kayantane a jikinta bata canjaba, hakan ya saka Jawaad daya shigo tsura mata idanu, komanta ya ƙara canjawa, musamman ma fatarta tai wani irin gogewa sai ƙyalli takeyi, a fuskarta kawai zaka karanci bata da son hayaniya, komai nata tsaka tsakine, hakan yasa ƙyawunta ya kasance mai sanyi, a kallo ɗaya bazaka taɓa ganin sirrin ƙyawunta ba dan batada cika ido irin na Shahudah, yanda take nutsatstsiya haka ƙyawuntama a hankali yake bayyana ga mai kallonta. Tanada kwarjini da cikar haiba na isassun mata masu kamun kai. Yaɗan lumshe ido ya sake buɗewa a kanta, a fili ya furta, ‘Sai jan ajin tsiya da miskilanci ga tsoro kuma ba’. Yay maganar yana nufar akwatinta da aka jiye alamar kayantane a ciki, buɗewa yay, a sama yaci karo da kayan barci har kala uku, doguwar riga da bazata wuce rabin cinyaba, sai riga da wando kala biyu. Riga da wandon ya ɗauka dan sun ɗanfi kauri da mutunci, yasan dai saka matasu akayi daga gani. Zama yay bakin gadon kusa da ita, ya janye bargon data rufama ƙafafunta zuwa ƙugu, zif ɗin rigar ya janye ƙasa bayan ya zame ɗan kwalinta gashinta da yasha gyara yanata ƙamshi ya bayyana.
Cikin barci naji ana ƙoƙarin ciremin kaya, da ƙyar na buɗe idanuna sai naci karo da shi, ai babu shiri na miƙe zaune duk da jikina babu wani ƙarfi, na dafe rigar da har ya ciren hannu guda batare da na yarda mun haɗa ido ba.
Kayan daya ɗakko mata ya ajiye saman cinyarta yana miƙewa, “Ki canja waɗanan kayan dan zasu takuraki sunyi nauyi da kwanciya barci”.
Da kallo kawai na iya bin bayansa ina haɗiye tsoron da saura kaɗan ya hudan zuciya, gaba ɗaya mamaki al'amarinsa ke bani, wai dama haka yake boss ɗinan ashe, yanzu daban farkaba nufinsa shine zai sauyan kayan? Tabɗi wlhy daya gama dani kuwa. Saida yaje ƙofa zai fita sannan ya juyo yana kallona, “Idan kika bari mintunan dana ɗiba miki ya cika baki tashi kin sauya kayan nanba, hummm..” yay maganar murya ƙasa-ƙasa amma daɗan karsashi sannan ya fice.
Kamar nayi kuka haka naji, na kalli kayan barcin da ya ajiyemin tare da ɗagasu, riga ce ƙarama dan ko ɗuwawuna bazata saukaba, hannunta ɗan si
riri sai wando da nasan iyakar gwiwa zai tsaya min. Sanin halinsa ya sakani miƙewa ina sauke ajiyar zuciya, dan nasan zaiyi duk abinda yace ɗin, canja kayan nai ina addu'ar ALLAH yasa bazai dawo ba dai. Ina kammalawa na kwanta. sallamarsa ta daki dodon kunnena.
Sosai na waro idanu waje naja bargo na rufe duk jikina, ganin ya zagaya ya kwanta ta ɗayan gefen Cikin in ina nace, “A a..nan za.. ka kwanta?”. Ba tare daya kalleniba yace, “Uhmm”. Baki na tura ina lullumshe idanu, Cikin ɗan haushi-haushi nace “Ammafa kowa ance da ɗakinsa ai”. Ganin ya juyo yana kallona, nai saurin jan bargon na rufe har saman kaina da shi. Murmushin da baiyi niyyar yi bane ya suɓuce masa, ya matso inda take sosai tare da ɗaga bargon ya shiga shima, saka hannu yay ya yaye na saman fuskartata tare da ɗora kansa saman filon data kwanta suna fuskantar juna, tuni jikinta ya fara tsuma, ta kuma rumtse ido kam, fuskarta duk ta bayyana tsoronta a fili. Hannunsa ya ɗora saman kanta ya shafa gashinta dake kwance luf yasha gyara tun daga goshinta har inda yake ɗaure da ribbon, a hankali ya zame ribbon ɗin gashin ya warware. Ƙoƙarin danne dariyar dake neman kufce masa ya keyi. Tsabar yanda take a tsorace har bugun zuciyarta yanaji dan suna gab da junane sosai, hannunta data sakane ta matse ƙirjinta yay musu kantanga. Da biyu ya tura yatsun hannunsa cikin gashin nata da wani irin salo.
“Na shiga uku ni balki”. Ta faɗa babu shiri muryarta na rawa tamkar zata fashe da kuka tare da ware idanunta gaba ɗaya kansa. Jay daya kasa riƙe dariyarsa yanzun kam ya saki lallausan murmushi da ɗora goshinsa saman nata, “Kinsan baki da ƙarfi miyasa kika nemi faɗan?”. “To yi haƙuri dan ALLAH” ta faɗa tana son jan jikinta baya. “Daga baya kenan yarinya” ya bata amsa shima da sake matsota jikinsa sosai ya matse yanda tilas ta janye hannunta data kare ƙirji da shi dan taji numfashinta na neman barin ƙirjinta. Jawaad kam da yasan da biyu ya matsetan dama ya sake sakin murmushi da manna dukan fuskarsa akan tata har labbansa na gogar nasa. Cikin raɗa-raɗa yace, “Nifa idan aka takaloni faɗa banajin bari saina maida raddi”. Hawayen da bily ke maƙalewane suka zubo mata a kumatu, tace, “To ai na baka haƙuri ko”. “Ni kuma sai ban haƙura ba ai hajjaju” yay maganar da manne laɓɓansu yanda babu damar sake magana ma. Duk yanda take mutsu-mutsu ya hanata kowacce irin damar da take buƙata, karan farko a rayuwarta da hakan ta faru da ita, abinda takema kallon ƙazanta idan ta gani a film yau shine ake mata a zahiri, ba kowa ke matanba kuma sai boss, innalillahi...... itakam taga takanta dama haka mutuminnan yake.......?
(To nima dai bansan hakan yakeba bily sai yanzun, duk zatona waliyyine fa kamar yanda Jabeer ya faɗa😂🚴🏼🚴🏼😜).
★★★★★★★★★
Barcin da suka gaza samunyi da wurine ya ja musu makara, Jay ya janye bilkisu daga jikinsa da ƙyar ya tashi zaune bayan ya kunna fitilar ɗakin, hannunsa dafe da kansa da har yanzu yake jingim alamar ciwon bai saukaba gaba ɗaya, bargon ya gyara mata yana kallon fuskarta da duk hawayen da tai suka bushe, idanunsa yaɗan lumshe yana mai tunanin yanda zasu kwashe da wannan uwar tsoron randa yace mai gaba ɗaya zaiyi, a daren jiyanma ba wani abun kirki yay mataba amma tabi ta ishesa da kuka. Numfashi ya sauke da sauka a gadon. Yasan tilas ne yay wanka kafin yace zaiyi salla, dan haka ya fita zuwa ɗakinsa a gaggauce kafin a tada sallar.
A hankali na buɗe idanuna dake jingim da barci nabi bayansa da kallo harya fice, tunda ya motsa nima na farka, sai dai matsananciyar kunyarsa da nakeji bazata barni na nuna masa na farka ɗinba, abinda ya faru daren jiya ya shiga rige-rigen dawomin a zuciya, hannuna na ɗora saman laɓɓana da sukasha gurza a hannunsa, da wanine ya cemin abinda yay a daren jiya zai iya wlhy sai na ƙaryata, kamar ba boss ɗin nanba na office gwanin hayaƙi da mazurai, sai yaso kaga walwalarsa balle akai ga dariya, yanda yake mara hayaniya a zahiri haka yake a komaima nasa babu hayaniyar, ajiyar zuciya na sauke murmushi na suɓuce mani, tashi nai nima dan ina buƙatar gyara jikina dukda barcin da nakeji na fitar hBilyn Abdull 📚:
ankali. Gadon na gyara sannan na nufi bayi, wanka nai da ruwa mai zafi ina addu'a a raina ALLAH yasa kar jinin nan ya ɗauke yau, dan nasan a ƙa'idar kwanakin da nakeyi zuwa rana zai ɗauke, dama yanzun kaɗanma na gani a jikin pad ɗin amma bai ɗaukeba, to na tabbata zuwa azhar bazan gansaba. Ina fitowa doguwar riga na zura na koma gadon dan har wani jiri-jiri nake gani saboda barci, yau ko azkar na kasayi, aiko kafin na farga na lula.
Ɓangaren Jawaad ma ana idar da salla da ƙyar ya daure yay azkar ɗin, yana kammalawa ya nufo gida, sama-sama suka gaisa da maigadi ya shigo gidan, yasan Bilkisu barci take tunda dai ba salla zata tashi yiba. Ɗakinsa ya shige, jallabiyar jikinsa kawai ya zare ya haye gadonsa shima sai barci.
_________________________________
Da ƙyar likitoci suka samu Shahudah ta farfaɗo kusan ƙarfe biyun dare, ba ita kanta dake cikin mawuyacin halinba harsu kansu sunyi matuƙar jigata, gasu Dad duk sunbi sun ruɗa musu asibiti sai kace ran ƴar tasu a hannunsu yake. Aiko koda ta farfaɗo allurar barci kawai sukai mata ta sake komawa, suna fitowa su Momy dake wujiga-wujiga suka yo musu caa da tambaya. A yanzu bazasu iya wani zaman musu bayaniba dan haka sukace kawai ta farfaɗo.
Koba komai su Dad sun sami kwanciyar hankali, dan shi kansa ɗazun harda hawaye yayi, baisan irin ƙaunar da yakema Shahudah ba a rayuwarsa, musamman ma a rin wannan lokacin da wani gagarumin abu mai taɓa zuciya da tashin hankali keson faruwa da ita, sam zuciyarsa bazata iya ɗaukaba gaskiya, bama zai yuwuba, dolene ya nema mafita kafin lokaci ya ƙure. Shahudah sa, ɗiya mafi soyuwa a zuciyarsa, kai ina bazai yuwuba, dolene yasan mai yuwuwa, ya yarda ya rasa komai akan Shahudah wlhy.
Haka suka kwana a asibiti hankalinsu tashe har ALLAH ya wayi gari lafiya.
Misalin takwas na safe Shahudah ta farfaɗo bakinta na kiran sunan Jawaad, kuka take rurus da roƙon a kira mata Jawaad ya saki Bilkisu inba hakaba zata kashe kanta.
Kasancewar har mama Atika da bama lafiyar ƙafane da itaba tazo asibitin itama tunda safe suka rufu kanta suna lallashi da bata baki akan cewar ai Bilkisu bata tareba wai, kuma ta kwantar da hankalin Jawaad zaizo anjima kaɗan. Sam taƙi sauraren kowa, daga ƙarshe dai dole Doctor ya sake zuwa yay mata allurar barci mai ƙarfi dan jininta yay masifar hawa.
Doctor ya kalli Dad da Momy dake zaune a gabansa bayan ya gama rubuce-rubuce a takarda. Momy ta sake share hawayen da tun ɗazu ke mata ambaliya a saman kumatunta, “Doctor ka sakamu a duhu, kace muzo kuma kaƙi kace mana komai, mike faruwa ne da yarinyarmu?”. Numfashi Doctor ya saki yana goga biron hannunsa saman gira, kafin ya sake ɗagowa ya kallesu. “Maganar gaskiya bazan ɓoye mukuba yarinyarku na cikin haɗari, jininta ya hau ƙololuwa kasancewar tana ɗaukar abu da girma fiye da kima, wannan shine karo na biyu datai irin faɗuwar da ba'ason duk mai hawan jini irin nata da yi, dan kai tsaye take kaisu ga paralysis, yakamata ku daure ku sama mata abinda ta keso koku ɗauki ɗammarar ƙwantar mata da hankali ta hanyar data dace. sannan akwai wani ciwo da muka gano tana dashi wanda ita kanta da wahala ace tasan a kwashi, dan baikai lokacin da har yanzu zai fara ciwon da zatajisa a jikinta ba”. Cikin matsanancin ruɗani Dad da Mom ke tambayarsa wane ciwo ne?. Kafaɗunsa yaɗan ɗage yana sauke numfashi, “Karku damu bamai ɗaga hankali bane can sosai, domin ko babu ciwon ai sai ALLAH ya ƙaddara mutum zai haihu a duniya dama. Alamu sun nuna yarinyarku ta taɓa cire ciki, bincikenmu da hasashenmu ya nuna mana kuma kamar wata allura tayi yayin zubarwar, a zahiri wannan allurar tana aiki fiye da zato ga mace mai son zubda ciki, dan a ƙanƙanin lokaci take rugurguje ɗan tayin dake mahaifa ta kuma ɓarosa waje, sai dai idan akai rashin sa'a da yanayin jinin mutum takan haifar da matsala a mahaifa daga baya musamman idan anyita babu ƙa'ida, sai bayan wasu shekaru kuma ake gani illar da taima mace, wata macen haihuwace bata sakewa kwata-kwata, wata kuwa ruɓarmata da mahaifar takeyi har sai an cire mata, to Alhmdllh ita duk hakan basu
kasance a gareta ba”. Ajiyar zuciyar Dad da Mom suka sauke lokaci guda, Doctor ya cigaba da faɗin, “Sai dai wani ƙari ya fito a bakin mahaifar, a hankali kuma zai rinƙa girma inhar ba'ai mata aiki ba, zaita girmane cikinta na girma kamar mai ciki, idan tsautsayi yasa ya fashe kuma sai ta ringa zubar da ruwa mai wari”. Idanu a waje cike da tsoro su Dad suke kalon Doctor, cikin rawar baki Dad yace, “Likita amma ai kace ana cirewa?”. “ƙwarai Alhaji ana cirewa, sai dai itamafa cirewar nada nata haɗarin, dan zaku iya rasata a dalilin cirewar, idan kuma an dace za'a cire lafiya ta tashi”. Kuka Mom ta fashe dashi iya ƙarfinta, shi kansa Dad dauriya kawai yakeyi, amma kallo ɗaya zakai masa ka fahimci tsagwaron tashin hankalinsa. Murya a sanyaye yace, “Wannan itace kaɗai mafitar Doctor?”. Doctor yace, “Eh to akwai wata mafitar bayan wannan”. Cikin rawar jiki Mom tace, “Wacece Doctor faɗa mana ita dan ALLAH”. “Hajiya mafitar ƙarshe itace shan magani, zamu iya bata maganin da zata shashi a sati sau ɗaya, ya kama a wata guda sau huɗu kenan, sai dai yanada matuƙar tsada, sannan zata cigaba da shansane har illa masha ALLAH, amfanin shansa anan bazai bar wannan ƙarin ya cigaba da girmaba, sannan bazata sake samun cikiba sai abinda ALLAH ya ƙaddara wannan ikonsane da rahamarsa idan yaso, nidai iya hasashena na faɗa sanin gaibu kuma sai ALLAH”.
________________________________
Knocking ƙofa da akeyine ya saka Jawaad farkawa, guntun tsaki yaja yana buɗe idanunsa akan agogon ɗakin nasa, ƙarfe goma harda mintuna sha bakwai, ya ɗan lumshe idanu ya sake buɗewa kafin ya tashi zaune da ƙyar. Lallai yasha barci sosai ashe. Sauka yay daga gadon ya nufi toilet, fuska ya wanko ya kuskure baki ya fito, jallabiyar da yaje masallaci ya ɗauka ya zira.
A falo suka haɗu da Bilkisu wadda itama bugun ƙofarne ya tasheta, nbatare da ita tama gansaba ta buɗe ƙofar. Nabeelah ce ɗauke da basket.
Murmushi nai mata ina matsawa na bata hanya ta shigo tana ƴar dariya damin shaƙiyanci. “Ta wajena naga duk kinyi wani laushi, ko Yayanmu ya angwanc..........”
Jin tayi shiru tare da jan biriki bata ƙarasaba ya sani maida ƙofar na rufe na juyo. zaune yake saman kujera ya ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya yay bala'in ɗaure fuska da tsatstsareta da idanunsa masu ban tsoro ga marajin magana. Ba itaba hatta ni saida na tsume, dan a bazata na gansa tunda sanda na wuce ban ganshi a wajenba.
Yaƙi cewa komai kuma yaƙi daina kallonta, a hankali takai ƙasa ta durƙusa kamar wata munafuka, muryarta har rawa take wajen faɗin, “Yayanmu ina kwana”. Bai amsa mataba, sai sake ɗaure fuska da yay yace, “Ƙarasa abinda kika fara”..................✍
ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.
SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;
ƊAURIN ƁOYE
ALƘAWARIN ALLAH.
HAFSAT RANO tazo muku da;
SAUYIN ƘADDARA
ƊAURIN GORO
MAMU GEE tazo muku da;
BURI ƊAYA
ƘAUNAR MU.
MISS XOXO tazo muku da;
KAIMIN HALACCI
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45 Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84