Sir, ai da naga ma irin sabuwar motarka a traffic yanzu har na ɗauka kaine”. “Kaga manta da wannan, wa yake ja a motar?”. “Alhaji Sadi Kokino ne sir” “Ka tabbata shine?”. “Wlhy shine Sir”. Shiru Jay yayi yana murza goshinsa, ya sauke zazzafan numfashi da faɗin, “Amma kacemin Drivern Mr Gebrail ne ai?”. “Wlhy Sir tunda na fara aikin nan tare da shi nake ganinsa, ni kaina yau da naga ya ɗauki Alhaji Kokinon nasha mamaki, shiyyasa ban gazaba wajen bibiyarsu”. Sitiyari Jay ya sake daka da ƙarfi, “Hameed akwai matsala, kodai sun shirya bada ƙafane dama dankar a bibiyesu, kokuma sunada tabbacin akwai mai bibiyarsu, yanzu haka suna ina?”. “To Sir nikam ka sakani a ruɗani, amma gamu a anguwar Sanni zasu shiga wani gida mai farin gate”. “Maza kabar wajennan Hameed, kuma duk abinda ka gani bai makaba ka tabbatar ka kirani, gobe idan ALLAH ya kaimu kazo ka sameni a A.Y street”. Cikin mamakin da babu damar tambaya Hameed yace, “Okey Sire”. Yanke wayar Jay yayi ya maida akalar kiran ga Jabeer, yana ɗagawa shima bai saurari tsokanar da yake masaba ta ango ango yace, “Jabeer kuna Office ne?”. “Eh muna Office, lafiya naji muryarka haka?”. “Jabeer inason yanzun nan ku bincikamin Number da Gimba yay wayar ƙarshe da ita a randa aka ɗaukesa, a ina mai ita yake yanzu haka? Sannan macece ko namiji?”. “Okey boss ina zuwa”. Yanke kiran Jawaad yayi ya tada motarsa yabar wajen, kansa tsaye tashar da ake hawan motar garin su Gimba ya nufa. Nesa da wajen yay fakin tare da kiran Dattijon nan a waya. Mintuna uku kuwa basu cikaba sai gashi. Motar ya buɗe masa ya shiga sannan ya maida ya rufe. Saida suka gaisa Jay yace, “Ka tabbatar yarinyarnan tana mana aikin da muke buƙata?” “Sosai kuwa Alhaji, ai itama kanta batasan aiki take manaba a kansa, yanzu haka ɗazun take sanarmin wai yau zasuje wani gidan dirama wani mawaƙi zaiyi wasa na musamman akan soyayyarsu da ɓalerun”. Murmushi Jay dake ɗan wasa da yatsun hannunsa saman sitiyari yayi, “Address ɗin wajen, sunan mawaƙin, time ɗin da zai shiga wajen da tashinsa?”. Dattijo yay ƴar dariya da faɗin, “Ai Alhaji kamar dama nasan zaka tambaya duk sai da na samo waɗanan amsoshin kaf, gasu a rubuce”. Amasar takardar Jay yayi yana jinjina kai, ya ciro kuɗi ya miƙa masa yana faɗin, “Ga cikon kuɗin aikinka nagode”. Baki a washe dattijo yac

e, “Nine da godiya ai Alhaji, ALLAH ya ƙara buɗi na alkairi, idan wani aikinma ya taso wlhy a kawo zanyi”. Jawaad baice komaiba sai murmushi kawai.
     Dattijo na fita kiran Jabeer na shigowa, ɗagawa yay yasa a kunne batare da yayi magana ba. Daga can Jabeer yace, “Tabbas Boss mace ce, sunan da tai register layin dashi shine Safara'u Hashimu, kakanta Bala, sunan mahaifiyarta Indo, kakaninta na wajen uwa Hassan da Baraka, shekarunta sittin da huɗu a duniya, asalinta ƴar garin Tsamiya ce, yanzu haka alama ta nuna ana amfani da layin a anguwar Habbun.........” Jay ya katsesa da faɗin, “Habbun kuma? Ba garin nan bafa kenan?”. “Kwarai hakane”. Baya Jay yay ya jingina da kujerar yana furzar da huci, kafin yace, “Hasashena ba dai-dai bane kenan?”. Daga can Jabeer yace, “Kai minene hasashen naka da?”. “Jabeer akwai wata mata lokacin case ɗin nan na Alhaji kokino mun haɗu da ita a gidansa idan baka mantaba itace ta taimakemu sosai har muka ɗauke mata yaro mai suna Yazeed, da ina zargin itace Gimba ke magana a gidan Alhajin nan da bai ƙarisa faɗaba”. “Tabbas Boss hasashenka ba kuskure bane, tun a wancan lokacin naso nace muku kodai Alhaji Kokino Gimba ke nufi, dan na taɓa ganinsa a ƙofar gidan farkon fara maka aiki lokacin bikinmu da Surayya, kasan matar Alhaji kokino ƙanwar maman tace, yanzu abinda za'ai shine kabani daga nan zuwa safiya insha ALLAHU zan bincika komai”. “Okey babu damuwa, shima yaron nan yau insha ALLAHU zan kamashi dan na kula akwai wani abu damu bamu saniba”. “A'a haba boss, ka bari wani a cikinmu ya kamashi mana, karka shigarma Mami lokacinta, amma mika hasaso mana”. “Da kaina zan kamashi Jabeer, dan akwai saƙon da nakeson bari a kamun nasa, abinda na hasaso kuma sai mun haɗu zamu tattauna”. Ya kashe ƙittt batare da ya jira amsar Jabeer ɗinba.
     Wayar Bilkisu ya kira, sai da ta kusa tsinkewa ta ɗaga dan bata kawo a ranta shi bane, ba Number data sani bace. Shiru tai taƙi magana, dan haka shi yay sallama. Yanda ta amsa sallamar ne yasashi fahimtar ta gane wanene yanzun, zamansa ya gyara da ƙoƙarin dai-daita muryarsa dake cike da ɓacin rai, “Am sorry kicema ƙawayenki suje kawai zan haɗu dasu zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu, wani uziri yane ya riƙeni gaba ɗaya shiyyasa ban dawo ba”. Murya a sanyaye bily tace, “To zan faɗa musu, amma bakaci abinciba fa, haka kake yawo da yunwa?”. Idanun Jawaad ya lumshe yana murmushi, ji yay duk ɓacin ran da ya tarar masa a ƙirji yana guduwa, yace, “Karki damu da anyi magriba zan dawo isha ALLAH, jin muryarki kawai tasa nama ƙoshi, ke dai ki shirya amsar angonki kawai ƙanwar Jay.......” ƙittt ta yanke wayar daga can.
        Jawaad ya girgiza kansa yana murmushi har kumatunsa na loɓawa, motar ya tada yay gaba har lokacin murmushi ya gaza barin fuskarsa.

      
___________________________

             Tunda su Zuhrah suka wuce sai naji gidan duk babu daɗi, ga wani motse-motse da naketa famanji amma narasa takamaimai a ina nake jinsan, nai jarumtar dakewa dan bana son na ruɗar da kaina, sai kuma na koma ganin tamkar gittawar inuwoyi ta jikin Windows, da farko dai naso fita na leƙa waje, sai kuma wata zuciya ta gargaɗeni dayin hakan, yanda kaina ya farayin nauyine yasa na jawo wayata na kunna karatun Al-Qur'ani mai girma, a hankali nutsuwa ta fara saukarmin, naji kaina ya saki na koma normal, gidan kuma yay wani irin yin tsitt mai ban mamaki, babu motsin nan sam, ko ƙarar na'urorin dake aiki da wutar dake a kwai duk bakajin ƙararsu, ban ɗauki hakan komaiba na cigaba da zama a falon har aka fara kiraye-kirayen sallar magriba, Miƙewa nai da shirin sake wanka, dan ɗazun lokacin sallar azhar da zanyi salla ganin ɗingon jini yasa banyi ba, amma yanzu dana duba gab da su Ummie zasu wuce kuma ya sake ɗaukewa, dama nasan ɗazun nayi gaggawar yin wanka dan ƙa'idane sai bayan sallar azhar nake wanka ko la'asar duk da lokaci kan ɗan canja min wani watan.
       Wayar na ɗauka na shige bedroom, Kayan da zan saka na fara cirowa a drawer na ajiye, dan waɗan nan dazan cire ɗin jini yaɗan ɗiga a sket ɗin kaɗan sai yanzu na kula ma. Batare dana kashe karatunba nabar wayar a saman gado na cire

kayan na shiga bayin, ban jimaba na fito gudun kar lokacin salla ya ƙwace min. Saida na farayin sallar magriba sannan. Saboda wutar dake akwai sai na jona hand dryer a soket kawai, nai zaman fara busar da gashina.
       Karatun Al-Qur'anin dana sakane yasa sam banji motsin shigowarsa ɗakin ba, sai da yay sallama, da sauri na juyo dan banyi tunanin ganinsa ba.
     Jay da tun ɗazun yaketa faman sallama ya ɗan tsura mata idanu, daya shigo baiga kowa a falo ba, har yay tunanin nufar nasa ɗakin sai kuma ya nufo nan saboda jiyo sautin karatu.
     Towel ɗin dana tsane kai na ɗauka na ɗaura a kafaɗa ta ya ɗan rufemin ƙirji, wanda na ɗaura ɗin kuma sai faman jansa nake ƙasa dan cinyoyina duk a waje suƙe. Ganin ya ɗauke kansa tamkar baiga abinda nakeyinba ya sakani saurin cemasa, “Sannu da zuwa”. “Yauwa sannunki kema”. Ya faɗa yana ƙarasowa cikin ɗakin sosai. Zama yay a bakin gadon yana sauke numfashi alamar gajiya. Daurewa nai na tashi, na raɓa ta gefensa na ɗauka kayana dake saman gadon zan nufi bayi dan na saka sannan na dawo ɗauka masa ruwa da zaman busar da kan.
          “Da miye na saurin yin wankan tunda kinsan bai tafiba?”. Maganarsa tazomin a bazata. Cak na tsaya tare dayin ƙasa da kaina dan ni bansan wace amsa zan bashi ba nikam, yaushe yasan nayi wankan to? Anya boss bai gani har hanji kuwa?.
       Ganin yanda ta wani tsume waje guda ya sakashi miƙewa yana girgiza kansa, zare rigarsa yayi ya raɓata ya wuce batare da ya sake cewa komai ba.
          Ganin ya shige bayi nai azamar saka kayan sauri-sauri sannan na fita na ɗaukko masa ruwa, zaman busar da kan na sakeyi yanzun kam hankalina kwance, saukar laimar ruwa da naji a kan hannuna ya sakani saurin ɗagowa na kalli mirror'n, shine tsaye a bayana, sakar masa hand dryern da yake ƙoƙarin amsa a hannuna nayi ina rumtse idanu, dan wani irin masifaffen harbawa zuciyata tayi, karan farko da naga namiji a tuɓe kamar haka a gabana bayan jazuga da baida wani fasalin kirki irin na zaratan maza. a raina rayawa nake, ‘Wai miyasa maza sam basu da kunya ne? Daga shi fa sai towel iya ƙugu zuwa gwiwa amma ya iya fitowa gabana ya tsaya’.
       Jay da duk yana kallon yanda ta rikice ta cikin mirror'n yay guntun murmushi kawai yana ƙarasa busar mata da kan, sai da ya gama tsaf ya ɗauki ribbon ɗin da yaga ta ajiye ya ɗaure matashi tsaf fiyema da yanda zatayi, harda su mata wani ɗan style da brush. Kujerar ya juya ya maido fuskarta inda yake kafin ya miƙar da ita tsaye ya ɗaura duka hannayenta saman ƙirjinsa daketa raɓar ruwan wanka. “Buɗe idonki” ya faɗa babu wasa.
          Hannunta dake ɗan rawa tai ƙoƙarin zamewa tana maƙe kafaɗa alamar “Ah-ah”. hannun nata ya maida da ƙyau, yana bin fuskarta da kallo. A bazata ya sumbaci inda batai zatoba duk da akwai riga a jikinta. A take ta waro idanu waje da masifar sauri tare da buɗe baki. Babu shiri Jay ya ƙyalƙyale da dariyar da bai niyyaba, dan yaga tsoron nata fiyye da yanda yake son gani.
       Bilkisu tai saurin duƙewa tana matse hannayenta duka biyu a ƙirjinta tare da cusa kanta duka a cikin cinyoyinta tana murmushi, dan ita kanta tabama kanta dariyar abinda tayin. Ga kunya mai tsanani akan abinda yayi ta lulluɓeta. Kafaɗunta ya kama ya ɗagota yana murmushi, duk yanda yaso su haɗa ido taƙi, daga ƙarshema saita ɗora kanta a ƙirjinsa ta ɓoye fuskar. Rungumeta yay da duka hannayensa yana murmushi tare da shaƙar ƙamshin da gashinta keyi da jikinma nata ya lumshe idanu. Kusan mintuna biyu suna a haka sannan ya zauna a bakin gadon ya ɗaurata saman cinyarsa. Fuskarta ya ɗago yanda zata kallesa duk da dai tanata faman yin ƙasa da idanu amma tana ganin fuskar tashi. Laɓɓansa ya nuna mata da ɗan yatsa yana wani ƙanƙance idanunsa. Kafaɗa ta maƙe da sake maida kanta a ƙirjinsa.
     “Ni ai sai nayi” yay maganar yana yin baya dasu a kan gadon ya birkiceta ta koma ƙasa. A take idanun bily sukayo waje, hanata dukkannin dama yay ya shiga yin yanda yaso da ita.
                Kiran sallar isha'i ne ya ƙwaci Bilkisu a hannun Boss, shima da ƙyar, dan daga kiss sai salon ya nema canjawa. Tunda ta samu ya barta ta cusa kanta cikin filos. Baice da i

ta komaiba shima ya fice yana murmushi. Ɗakinsa ya nufa ya sake ɗaura alwala da canja kayansa zuwa blue jeans da t-shirt itama Blue, ya saka turare kaɗan da ɗaukar wata ƴar ƙaramar bindiga ya saka a gefen ƙugunsa sannan ya fito. Ɗakin Bilkisu ya koma. isketa yay ta fito daga toilet fuska a jiƙe alamar alwala tayo. Ruwan data ajiye masa ɗazun ya ɗauka yana sha idonsa a kanta. Kofin ya ajiye yana kallon agogon hannunsa, “Bara naje za'a shiga salla, idan an idar zan ɗan ƙarasa wani waje insha ALLAH kafin goma zan dawo.
        Da sauri Bilkisu ta kallesa idanu cike da ƙwalla, “Dan ALLAH mu tafi tare, nidai tsoro nakeji”. Yanda ta kumbura baki taso bashi dariya, amma sai ya danne abinsa ya taka zuwa inda take tsaye, fuskarta data duƙar yasa hannu ya ɗago, acan ƙasan maƙoshi yace, “Kin taɓa ganin amaryar kwana ɗaya a gidan miji ta fita?”. “To ai babu wanda zaisan na fita tunda dare ne”. Fuskar tata ya saki yana ɗan ɗage kafaɗa, “Okey, ki shirya kafin na dawo salla saimu je”. Cike da murna ta amsa masa da to. Goshinta ya sumbata ya juya ya fice yana murmushi dan wayo kawai yay mata ba dawowa zaiyi ba.

        Ana idar da salla Jay ya fito daga massallaci, motarsa da dama ya bari a waje bai shiga da ita gida ba ya shiga ya bar anguwar, kai tsaye address ɗin da dattijon nan ya bashi ya nufa, anguwace irin sabuwar anguwarnan da uncompleted building sukama fi yawa, sai dai inda gidan drama'n yake anɗan gaggama wasu gidajen dan wajen harya fidda santa ɗoɗar, bakajin hayaniyar komai saina Genretor ɗin da suka kunna da ƴar hayaniyarsu alamar basu gama zuwa ba, akwai ƙwayayen wuta a waje da suka haska kusan rabin layin, sai mai Nama daketa faman haɗa wuta, gefensa mutum biyune ɗaya mai ruwa ɗa kayan drinks, sai saurayi da budurwa dake can gefe suna hira, sai kuma masu shiga da fita cikin gidan ɗai-ɗai dan yanzu suke kan zuwa. Waya ya ɗauka yay kiran wani abokinsa da ya kasance ainahin police, saida suka gaisa ya gama tsokanarsa da ango-ango, sannan Jay yace, “Auwal kuna garin nan amma tsageru har suke da lasisin buɗe wuraren iskanci irin haka?”. Daga can Auwal yace, “Haba dai Jay, kaima kasan hakan bazai kasanceba”. “Gashi kuwa na gani da idona, akwai wani gidan Drama a sabuwar anguwar nan data kusa haɗewa da jan-ɓauna, inason ƙarfe goma da rabi kuzo wajen kuyi kamen kan mai uwa da wabi”. Bai jira cewar Auwal ba yace, “Mu kwana lafiya” ya yanke wayar. facemask ya ɗauka ya saka tare da facing cap,  kallon kasan yayi a madubi ya tabbatar komai yayi kafin ya fito bayan ya kashe motar. Sai da ya tabbatar babu wanda yaga fitowarsa sannan ya nufi gidan.

★★★★★★

         Ina idar da salla na koma bakin gado nai zaman jiransa, ganin shiru-shiru sai kawai nahau yin game a waya, hamma na farayi ɗai-ɗai alamun inajin barci, nayi guntun tsaki da kallon agogon ɗakin, tara saura minti ashirin, zamewa nai na kwanta tare da jan filo na ɗaura kaina na cigaba da game ɗin, tun ina ƙoƙarin damƙe wayar dake neman suɓuce min harna yaddata batare dana saniba.
              A firgice na farka jikina na wani irin ƙyarma, ‘innalillahi wa'inna ilaihirraji'un’ na shiga ambata ganin ɗakin dunɗum da duhu bayan kuma nasan fitilar a kunne take, dariyar da aka tuntsure da ita ta sakani sake firgicewa nahau laluben gadon.....
        “Bilkisu! Kenan mai gadon zinari, wato ke amarya ko? Azatonki zaki iya tsere minne? Ke da kina tunanin na barki? Wannan gurɓataccen tunanine bilkisa, na rantse miki yau saina amshi abinda ya kasance cikar burina dan bazan rasa komai a dalilinki ba wannan gangan ne hhhhhhhhhh!!!!!!!!.................✍

ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.

SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;
ƊAURIN ƁOYE
ALƘAWARIN ALLAH.

HAFSAT RANO tazo muku da;
SAUYIN ƘADDARA
ƊAURIN GORO

MAMU GEE tazo muku da;
BURI ƊAYA
ƘAUNAR MU.

MISS XOXO tazo muku da;
KAIMIN HALACCI
IGIYAR ZATO.

BILYN ABDULL tazo muku da;
WUTSIYAR RAƘUMI...
GUDU DA WAIWAYE....

abin birgewa books ɗinan duk sun wanzune akan farashi mai rahusa, guda goma duka 1k ne, guda biya 500, guda huɗu 450, guda uku 400, guda biyu 300, ɗaya 200 gama
[1/11, 10:48 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: 🥚Ƙwai Cikin Ƙaya🥚
.
Book Two
.
Bilyn Abdull 📚:
Page 42

..................Inda mai naman nan yake ya tsaya, batare da yayi magana ba ya miƙama mai-naman 1k tare da nuna masa naman. Kallonsa yay a ƙufule, “Haba malam, ya zakazo waje babu ko sallama ka miƙomin dubu wai na baka nama? An faɗa maka ni irin sakarkarun masu saida naman nan ne da kuke rainama hankali, nibanma taɓa ganinka a gidannan ba, kai wane?”. Jay ya danne takaicinsa cikin salon maganar kurame yay masa nuni wai shi bebe ne”. Mai nama yace, “Oh to yanzu naji batu, kasan rainin tsagerun gidannan ne bazan iya ɗaukaba shiyyasa kaima nai zaton kalarsu ne, na duka kake so?”. Kai Jay ya jinjina masa. Mai nama ya fara yankowa yana sawa a takarda da raira ƴar waƙarsa ta shata mai taken “Natsaya ga annabi Muhammadu.......” Jay dai kallonsa yake da nazarin wajen harya kammala yanka masa, amsa yay da masa godiya ya juya zai tafi, sai kuma ya juyo da sauri irin kamar yayi mantuwar nan. Ƴar takarda ya ciro a aljihun wandonsa ya miƙama mai nama. Mai nama ya amsa da faɗin, “Miye kuma wannan? Nifa kunsan ba wani boko nayiba amma kuyitamin wani lagude-laguden jaraba. Kai Hamusu zo duba mi ya keso kuma?”. Wanda aka kira Hamisu dake gaban lemuka ya amsa da “To baba”. Takardar ya amsa ya duba sannan ya kalli mai naman, “Baba wai gidan Ɗan Alhaji ya keson a nuna masa”. Shiru mai naman yay yana kallon Jawaad, mikuma ya tuna oho masa sai ya washe baki, “Af to inaga irin abokansa ne daya ɗan gayyato, kasan yau zaiyi ajo”. Jinjina da hannu Jay yayma Mai nama irin ka gane ɗinan. Mai-nama ya sake washe baki da nunama Jawaad wani gida dake can kusan ƙarshen layin. Cikin alamar maganar kurame yayma Jay yay masa godiya da nufar inda aka nuna masan.
          Rufe gidan yake dan haka ya ƙwanƙwasa, sai da yay sau kusan baƙwai sannan akazo aka ɓuɗe cike da masifa.
      “Wai wane shegene yake bugama mutane gida haka? Sai kace ya bada ajiya ko an ci masa bashi, idan akai haƙuri dai ai zan fito ba sai ansama lokacina ido b.....” hankaɗa shin
Showing 141001 words to 144000 words out of 249282 words