ya abi amma duk sun rasu bai samu ko guda ba a ciki”.
“Ha

kane Hamza, kasan idan UBANGIJI nason saukar da wata aya ga bayi saiya datse al'amarinsu ya ɓoyesa a rasa bakin zaren a dalilin ƙaddara, muduka ƙaddarace ta ɓoyemu dukda muna a cikin gari ɗaya, nima nasha bibiyar ahalinku dalilin son ganin ɗana ya dawo gareni, sai dai hakan bata kasanceba har gashi ƙasa ta rufe idanunsa, hakan jarabawace, dan tabbas tun daga Zazzafar soyayyar danaima Sa'a har zuwa zaman aurenmu da guduwarta da yarona duk jarabawace a garemu da wata hikima ta UBANGIJI, naso ace na sake ganinsa, naso ace na kwatanta sauke haƙƙinsa dake kaina matsayin mahaifi a garesa, naso ace shima ya tashi cikin ƴan uwansa da a yanzu sune suka zamema rayuwata haske, ALLAH ne yaymin komai da kaini matsayin da nake a yanzu amma ta dalilinsu ne, na yarda abinda kakeso bai zama lallai ya kasancema rayuwarka alkairiba, wanda kake ganin yay kutse ma rayuwarka sai kaga shine alkairin, naso Sa'a so mai tsanani, harnaso bijirema iyayena a kanta, sai dai itaɗin ashe ba itace abinda nake ma hasashenba, wadda iyayena suka auramin ina baƙin ciki da takaici, na ƙuntata rayuwarta a zamanmu sai tazama ashe itace abinda banyi zatonba, dan gashi yanzun albarkacin zuri'arta nakeci ita bata raye, wannan aya ce ga masu ZUCIYA irin tawa, ɗan adam shidai abinda akeso ya nema zaɓin ALLAH akan dukkan al'amarin sa ba wai son zuciyarsa ba”.
Sosai Malam ɗan inna keta faman jinjina kansa, Jawaad dai yana saurarensu amma bazaka taɓa fahintar yanayinsa ba sam, saida Alhaji babba ya gama share-sharen hawayensa sannan Jawaad ya ɗago ya sake kallon Malam ɗan inna, “Na biyu kuma zamuje da kai gidanda suka zauna danka nuna mana yarinyar, mu zamu ɗauketa mu riƙe, basai munsan gaskiyar yanda suka sametanba”.
Sosai ruɗani ya bayyana ga Malam ɗan inna, ya shiga matsar hawaye yana bada haƙuri da musu bayani akan suma basusan inda Bilkisu take zaune ba, amma kwanaki taɗan zazzo gaishesu, sai dai maganar gaskiya ko tazo ɗin basu wani sake mata fuska, danshi sau ɗayama ya taɓa ganinta, kusan shekara uku kenan ya kuma ja mata gargaɗi akan karta sake zuwa masa gida tunda basu da alaƙa da ita, dan saida ya titsiyetama yaji wanene ya nuna mata gidan kafin yaymata korar rashin arziƙi. to amma yaji kwanaki iyalinsa suna gulma wai tana zuwa wajen Ramatu, kuma ma har tayi aure kwana nannan ita Ramatun taje.
Kafesa kawai da kallo Jawaad yay ransa a matuƙar ɓace, ganin hakanne ya saka Alhaji babba riƙe hannunsa yana murzawa alamar lallashi, hannunsa ya zame ya tashi ya fice daga zauren.
Alhaji babba yay murmushi yana girgiza kansa, sannan ya maido kallonsa ga Malam ɗan inna da shima yabi Jawaad ɗin da kallo, “Haka yake yana da matuƙar zuciya, sai dai yanada kirki sosai, shine jikana na farko da ƙanwar Adamu mai suna Bilkisu ta wajen Amina kenan ta haifa, ɗan tsohon shugaban ƙasa da ALLAH yayma rasuwa Alhaji Abdul'aziz yusif tafida”. Idanu sosai malam ɗan inna ya zaro, cikin ɗan rawar baki yace, “Dama yarinyar wajenka ce matar marigayi A.Y tafida?”. “Hakane, gama yaronsu da ya bari nan”. “ALLAH maiyin yanda yaso, ALLAH mai hikima, lallai zaɓin ALLAH shine zaɓi kam bawai son zuciya ba, wanene zai iya mantawa da tsohon shugaban ƙasa Abdul-aziz Yusif Tafida a ƙasarnan ai saida azzalumi, adalin shugaba da har yanzu ba'a ƙara samun makamancinsa ba ma”. Murmushi Alhaji Babba ya dingayi jin ba'a manta da ɗan matarsa ba, surikinsa kuma uba ga babban jikansa. A take ya warwarema Malam ɗan inna gaskiyar al'amari dan gane da bilkisu harma aurenta da jikansa Jawaad, wanda a dalilin hakanne kuma yasaka su ma bincike har suka ganosu ta dalilin kamannin bilkisu da Adomu daya gani, da kuma ƴarsa data rasu Rahmah, wanda yake ganin bilkisu ta ɗakko kamanin Rahama ne saboda ƙarfin jini, to gashi sukuma sunmace basu yarda ADamun ta haifi bilkisu ba, to shi ina zasu kama su fahimci gaskiyar wannan ruɗanin ne. Al'ajabi ya sake kama Malam ɗan Inna har takaisa ga sharar hawaye, yayta ban haƙuri da neman afuwa ga alhaji Babba tundaga laifin da ƴar uwarsu ta zama sila har wanda suma suka tafka. Tarr syka fito har wajen mota yana bama Jawad da yay kicin-kicin da fuska haƙuri shima. Hannu kawai ya ɗaga

masa da jinjina kansa, dan ransa a ɓace yake, kuma bayaso kosau ɗaya fushinsa yakaisa ga aikata abinda bai daceba ga dattijon da zaiyi sa'a da mahaifinsa, gashi koba komai akwai alaƙa.
Sun rabu akan zai faɗama sauran ƴan uwansa komai auzo kuma har gida su ƙara bada haƙuri.


Lallashin Jawaad Alhaji babba yay tayi cikin hikima, tun yana baɓɓata fuska na shagwaɓa harya sake yana masa murmushi, gida suka maida Alhaji babba, batare da sun shigaba Sadiq yay reverse suka sake barin anguwar. Daga nan inda ya ajiye ɓaleru suka nufa kuma.
Tun shigar Jay ɗakin da ɓaleru yake jikinsa ya fara ɓari, ya ajiye abincin da yake ci gefe yana zazzare idanu, da hannu Jawaad yay masa nuni da abincin alamar ya ɗauka ya cigaba da ci. Babu musu ɓaleru ya ɗauka teakaway ɗin yana cusawa kamar yanacin maɗaci saɓanin yanda abincin ya fara masa daɗi da farko.
Ɗauke kai Jawaad yay daga garesa, saida ɓaleru ya cinye abincin tas ya ajiye batare da yaci kifin cikiba, ”Shikuma wannan waka barwa?”. Jawaad ya faɗa yana tsatstsaresa da idanu murya a kausashe. Ɗauka ɓaleru yay da sauri ya hau ci, ALLAH dai ya taimakesa ƙaya bata maƙale masaba ya gama lafiya. Hannu yaje ya wanko ya dawo, ya maƙure jikin bango hantar cikinsa na kaɗawar tsoro, dan har yanzu baibar jin ciwon jikin dukan daya shaba ranar. Jawaad ya ajiye wayarsa yana kallon ɓaleru da ƙyau. “Ka shirya faɗamin gaskiya ko sai mun sake kalar wasan ranar?”. “Wlhy duk abinda kake buƙata inhar na sanshi zan faɗa maka oga”. “Tunani mai ƙyai” Jay ya faɗa yana ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya. “A gidan wa kake aiki?”. “Mr Gebrail”. “Waya sakaka ka ɗauki Gimba a mota?”. Inda inda ɓaleru ya nema farawa Jay ya daka masa tsawa, “Wlhy ko sau ɗaya kamin ƙarya saina karyaka a wajenan na ɗauraka”. Sanin Jay zai iya aikatawa yasa ɓaleru haɗiyar yawu muƙutt, “Uh.. Uh... Uhmm ni dai kawai wata safiya ne aka kirani da kwatanta mini shi, bammayi zaton shi bane saida naje zan ɗaukesa”. “Waye ya kirakan?”. “Mr Gebrail ɗin”. “Ina ka kaishi?”. “Wlhy acan titin ƙatshen gari ya tareni ya amshesa?”. “Kenan dama ka saba musu irin wannan aikin? Koma shi kake musu?”. “Oga Wlhy.....” “Amsa kawai nake buƙata, duk abinda yazo a saɓaninta kai kuka da kanka”. Kansa ya ɗaga da sauri yana karkarwa. “Shi da waye suke sakaka? Kuma wanene ya kaika aiki gidansa?”. “Ɓaleru ya share hawayen da suka cika masa idanu, “A anguwar da gidan drama ɗin nan yake yake gini, wataran yazo wajen shine ya ganni”. “Sai kawai yace zoga aiki na baka?”. “A'a nine da kaina naje na tambayesa saboda a lokacin aikin nake mema, to da yake ina ɗibo yashi daga can wani rafin dake ƙasan anguwar ina kawoma masu gini na saya, lokacin ana aikin gininsa kuma nine mai ɗebo musu yashin, sai naji yana tambayar Engineer ɗin ko yasan wani driver? Dan yanason ɗaukar driver, drivernsa ya ajiye aiki saboda tsufa, to ahinefa nace zanyi da yake na iya mota. Da farko yayi kamar bazai ɗaukeniba sai kuma ya bani key yace na gwada ya gani, a take na amsa na shiga motarsa naɗan zagaya wajen, a lokacinma bai amsa zai ɗaukeniba ya tafi, sai bayan kwanaki biyu harma na fidda rai sannan yazo yace ya ɗaukeni”. “Daga nan sai ya maidaka kidnapper ko? Har takai kuɗi ya rufe idonka aka haɗa baki dakai aka kashe abokinka ɗan garinku?”. “Wlhy oga bada ni aka haɗa baki aka kashesa ba, hasalima nima mutuwarsa kawai naji, wlhy tunda gimba ya rasu ban sake samun kwanciyar hankaliba, oga ina tsaka mai wuya”. “Ai bama ka shigaba tukkunna indai tsaka mai wuya ce. Ya akai ka tuƙa Alhaji Kokino ranar kuma?”. “Alhaji Kokino kuma? Wlhy ni bamma sanshi ba”. “Humm kana wasa dani ko?”. “Wlhy oga da gaske nake maka”. Jay baice komaiba ya ɗauka wayarsa, hoton da yay musu lokacin da traffic light ya tsaidasu ya nuna masa, ɓaleru yace, “Aiho, ai yaje office ɗin Mr Gebrail ne sakan kasuwanci sai motarsa ta samu matsa, shine drivernsa ya ɗauka ya kai wajen gyara, to bai dawo da wuriba shi kuma ya gaji da jiransa shine yace na kaisa gida, wannan shine dalilin da yasa ka ganmu tare”.
Kafesa da kallo Jay yayi cike da nazarin maganarsa, bai sake cewa komaiba ya miƙe, fitowa yay abinsa. Ɓaleru ya bisa da kallo, daka ganshi kasan

a tsorace yake. Securitys ɗin dake kula da ɓaleru ya korama winning akan su kula dashi da ƙyau, duk kuskuren da aka samu sune zai fara hukuntawa. Daga haka ya shiga mota suka bar gidan.
Ganin lokacin sallar la'asar yayi saiya saka Sadiq tsayawa sukayi sannan suka ƙarasa gida.
★★★★
Bily na zaune da ƴammatan maƙwafta da suka shigo mata dan a gaisa asan juna ya shigo. Sannu da zuwa tai masa, suma suka shiga gaisheaa suna binsa da kallo tamkar wasu mayu. Kallo ɗaya yay musu ya amsa Sau ɗaya yay shigewar, miƙewa nayi, dan haka suma duk suka miƙe, sallama sukai man suka tafi, nai musu godiya nima sannan naje kicin na ɗauki kunun ayar da nayi na nufi ɗakin nasa. A bakin gado na iskesa zaune ya dafe kai, koda nai sallama bai ɗagoba yadai amsa mani. Naja ƙaramin table ɗin na ajiye. “Su wanene waɗanan?”. Ya faɗa batare da ya ɗago ba. “Nima ban sansuba, basu fi mintuna talatin da shigowaba, sunce min nan gidan maƙwaftan nan namu suke”. Amsar kofin dana miƙa masan yayi, yaɗa lumshe idanu sannan yasaka a bakinsa ya shanye gaba ɗaya alamar yanajin ƙishi sosai, kofin ya ajiye yana miƙewa, “Kidaiyi a hankali”. Ya faɗa yana cire maɓallan rigarsa. “Insha ALLAH zan kiyaye”. Na faɗa ina miƙewa.
Hannunsa ya miƙomin yana min nuni da rigar, dukda dai inajin nauyinsa haka na kama na taimaka masa muka cire, dan na lura shifa komai yafison ai masa. Na juya zan ajiye rigar naji kawai an kwasheni anyi sama dani, ina mamakin yanda ya ƙware da iya ɗaukar mutum babu ko ɗar, shi ko nauyina bayaji ma.
Ganin ya nufihanyar bayi nai saurin cewa, “Bandaɗe da yin wankaba fa ALLAH”. “Ke kika san wannan”. Ya shige toilet ɗin yana faɗa. Nidai balki naga ta kaina, inaji ina gani dole akai wankan nan, ni gaba ɗayama ya fara busarmin ido da salonsa. Haka mukai wankan muka fito, bayan mun kimtsa muka fita domin cin abinci.
★★★★★★★★
Yau kwanakinmu shida kenan da tarewa, zuwa yanzun bansan yanda zan lissafo muku abubuwan da boss ya koya minba, gaba ɗaya ya fetsarar dani, duk da dau bana fiddo zaƙewat dan akwai sauran lokaci, kunyarsa kuwa inajinta tamkar babu gobe, dan duk abinda zai sakani na masa inayi ina rufe idanu, mu'amular gadoce fa na kasa sabawa, dan duk sanda zaizo min babu fashi sai nayi kuka, har fargaba nake ya nuna buƙatarsa, duk da hutun amarci da aka bamu hakan bai hana boss aiki tuƙuruba a gida, ni kaina bai barni na hutaba, matan su Jabeer sunzo sun yinarmin, hakama su Safah an kawosu, Amina ma tazo ta yini randa matan su Jabeer sukazo, da yamma sai ga su Nazifa ma, maganar da muka tattauna ta sakani fahimtar sun shirya zuwanne dama, nayi farinciki sosai ganin maganar ƙungiya ta kankama, komai an kammala na shirye-shirye a satinan za'a fara fidda komi ta kafafen yaɗa labarai da yanar gizo kamar yanda aka tsara, dan aomuke mu fito da zafinmu, ga bikin Nazifa nata matsowa ita, dan ƙarshen wata mai kamawa ne.
Bayan tafiyarsu na gaji liɓis dan dan suma su Aliyun anan suka kusan yinar mana tare da boss, sauƙina ma basu bar gidanba saida suka tayani na gama komai tsaf gidan ya dawo normal, sanin ko nayi wanka idan ya dawo saina sake dole tare da shi dan kullum tare muke wankan dare sai kawai naƙiyi na dafa masa shayi na gyara fruit. Falonsa nakai komai sannan na shiga haɗa ruwan wanka, ina ciki kuwa ya shigo, sai kawai jinai an ringumeni ta baya. Murmushi kawai nayi na juyo muna kallon juna, murmushin shima yamin da kai hannu a.................🙄😣✍

ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.

https://www.facebook.com/groups/2803452939899949/?ref=share

[1/14, 6:29 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: Bilyn Abdull 📚:
Page 49

..............Kamar yanda Umm-Anum ta saba duk sanda takawa yazo Saudia ya kanzo har gidan su gaisa, domin dai a halin da take ciki su kaɗai takema kallon ƴan uwa, su kaɗai ta sani a yanzu sai mijinta sai ƴaƴan guda biyu, ta mance ita wacece? Ƴar wacece? Daga ina take? Daga ina ta fito?. Wani lokaci hikimar UBANGIJI kan sakata kawo wannan tunanin a zuciyarta, musamman ida tunaninta ya karaɗe ko ina a cikin duniya ta ga babu wanda ta sani sai ƴan Masarautar gagara badau, sai mijinta da danginsa dake anan, hakan kan ɗaure mata kai, sai dai duk yanda taso ta furta da baki kota tambaya bata iyawa. Idan hakan ta kasance takan zauna tasha kukanta ta share hawayenta.

    Yauma kamar yanda ta saba ɗin haka ta ƙimtsa ta fito cikin shirin zuwa gaida takawa, idan da Ummu yazo sukanje tare, idan kuma da amaryarsa ne tare itama suke zuwa, sai idan shi kaɗaine yazo sai taje tare da Anum su gaida shi ko Aunty Mahfuzah idan ta shigo. Yau kam sai suka ɗunguma gaba ɗaya, ita, Anum, Ummu, Bilkisu, sai Anuwar daya shigo gidan babu jimawa shima, dan tunda ya fita salla sai yanzu yake dawowa saboda baisan da Takawa sukazo ba balle yay tunanin harda Jawaad.
      Sallama sukai a ƙofar ɗakin aka amsa musu da ga ciki, tare da basu izinin shiga, jikin Umm-Anum sai tsuma yake tanata dai ƙoƙarin dannewa da karanto addu'a a zuciyarta. Anum da Bilkisu ne suka fara shiga, sai Ummu sai Umm-Anum, sai Anuwar a ƙarshe. Jay na kwance a kujera idanunsa a lumshe tamkar mai barci, sai dai shigowarsu falon ya saka ƙirjinsa wani irin mahaukacin bugu irin wanda tunda yake a rayuwarsa zai iya rantsuwa bai taɓa jiba, ya buɗe idanunsa a hankali zuciyarsa na wani irin masifaffen tsitstsinkewa. Akan Bilkisu da Anum da suka zauna gefen Abbun su Anuwar ya fara saukewa, ya maida kan Ummu da itama ta zauna a kujerar da takawa yake zaune, sai Anuwar dake tsaye tamkar gunki idanu a ware yana kallon Jawaad, da alama dai yayi sumar tsayene na bazata. Ya maida kallonsa ga dattijuwar mace data juya masa baya suna gaisawa da takawa, tana sanye da baƙar abaya ta naɗe kanta irin naɗin larabawa. Jiyay gaba ɗaya jinin jikinsa na wani bada zuuuu!! Zuuuu! Zuuuu, bazai iya daurewa har saita juyo garesa ba, a matuƙar ɗokance yake da son ganinta duk da cike yake da fargaba da tsoron kar hasashensu ya zama kuskurene kuma ba itaɗin bace ba. Ya miƙe a hankali ƙafafunsa na harharɗewa, yayinda bugun zuciyarsa da fitar numfarfashisa ke fita a matuƙar guje. Miƙewarsa tai daidai da miƙewar Umm-Anum itama fuskarta ɗauke da murmushi sun gama gaisawa da takawa tanason komawa kusa da mijinta ta zauna sai a ɗora firar, dauriya kawai take itama tana danne halin da take ciki. Lokaci ɗaya sukai tsaiii! Suna kallon juna, kallo mai wahalar fassara ga ma'abocin yinsa da wanda ke kallo, kallo mai saka razani da firgici da ban mamaki, kallo mai ɗarsa tausayi ga duk wanda idanunsa zai iya sauka a kansu shima.
          Ƙafafun Jawaad sun kasa ɗaukar gangar jikinsa, Mahaifiya ta wuce gaban wasa, jini ba ƙarya bane musamman irin na uwa da ƴaƴa, ko shekara dubu yay baigantaba saiya gane, shekarun data barsa bazai yuwu ya iya manta fuskartaba musamman da ya zam yana kallonta a hoto a koda yaushe, manyanta kawai da ƙiba da haske ta ƙara na alamun girma da jin daɗi. Ƙasa ya zube bisa gwiwoyinsa jikinsa na rawa, kansa na wani irin Masifaffen sara masa tamkar zai tsage gida biyu, cikin rawar harshe da kwararowar hawaye bisa kumatunsa yace, “Ummuna!”.
           Umm-Anum dake tsaye cikin mawuyacin hali da ruɗanin zuciya da gangar jiki idanunta kafe akan Jawaad ko ƙyaftawa batayi ta ɗaga hannu da ƙyar tana mai nuna shi da yatsanta manuniya jikinta na wani irin rawa, mai kama da Anuwar ɗinta! Wanene shi? Da ga ina yake? Ya akai kamaninsa da Anuwar ɗinta?! Mutum ɗaya tasan duk duniya yana kiranta da wannan sunan, sai dai wanene? A ina yake? A yaushe ne kuma?. Bakinta rawa yake amma ta gaza furta komai, sai tai luuuu baya zata faɗi.
      Wani irin wawan miƙewa Jawaad yayi ya tarota jikinsa, dai dai da zaburowar Anuwar shima yana ƙoƙarin tarota, sai kawai hanunsu ya haɗe waje guda suka tallafota a tare......
 

     Zumbur suma ƴan falon duk suka miƙe tsaye, banda Takawa kawai da ya dake abinsa duk da shima jikin nasa duk yay saƙwat. Da ga can Anum ta ƙwala kiran sunanta cikin kukan da takeyi tun farkon durƙushewar Jay a gaban Umm-Anum. Bilkisu ma hawayen takeyi.
      Abin tausayi da tashin hankali daga Jawaad har Anuwar kuka suke suna faman girgiza Umm-Anum da kiranta, Jay na faɗin, “Ummuna! Ummuna Please, Ummuna ki buɗe idanunki ki ganni, nine Jay-p ɗinku ke da Abbah, karkice ba hakaba dan ALLAH, dan ALLAH Ummuna zuciyata zata buga ki tashi ki ganni kicemin da gaske kece ba gizo idanuna keyiba, ba mafarkin dana sabayi bane, ba tunain danake dulmiyawa bane, ki tabbatarmin a zahirance kece tare dani Ummuna, kitashi kiga Jay-p ɗinku yazam Jay-p ɗin gaskiya, Dan ALLAH Ummuna karkice baki ganeniba  karkice baki sanibaaaaa”. Yaja (a) ɗin ƙarshe da  fashe da wanu irin kuka maiban tausayi da tsuma zuciya yana mai kife fuskarsa saman tata.
       Anuwar shima kukan yake yana faɗin, “Umm-Anum ki tashi da ALLAH, ki tashi ki faɗamin shiɗin ɗan uwanmu ne da gaske, wlhy inajin ƙaunarsa mai zafi a raina irin wadda ban taɓama wani mahaluki irinta ba, jinake tamkar
Showing 168001 words to 171000 words out of 249282 words