fuskantar juna, idanunsa a kaina yace, “Idan kuma na fara kikace zakimin barci saina ƙarya ƙasusuwanki”. A zuciyata nace, ‘Ai tun daren jiya ka kakkarya ƙasusuwan nawa da sauyamin kamanni Alhaji’. Dariyarsa da naji ciki-ciki ya sakani fahimtar maganar zuci ce ta fito fili. Baya nai zan juya yay saurin riƙoni ya maidoni, dole na haƙura tunda dai nariga nayi katoɓarar.
Yaɗanja hancina kaɗan, “Wato tun daren jiya na sauya miki kamanni da karya ƙasusuwan ki? To a yafeni bazan sakeba Zinaraina”.
Bance masa komaiba dan naji kunya. Ya fara shafa bayana a hakali da gyara kwanciya, “Jawaad Abdul-Azez Yuseef ɗane da ga. zuri'ar Alhaji Yuseef Tafida. Alhaji Yusif talaka ne mai rufin asirin ALLAH, domin kuwa manomine kuma makiyayi, duk dai a birni yake rayuwarsa da iyalansa to dukkan wani sabgoginsa na ƙauyensu, acan yake nomansa da kiwo, hakan yasa hankalinsa rabuwa biyu, harma zamansa a ƙauyensu ya so ya rinjayi zaman birnin. Matan Alhaji Yusif uku ne cif, kuma kowacce a cikinsu ALLAH ya azurtata da haihuwa, matarsa ta farko hajiya Atika yaranta shida huɗu duk maza biyu mata, sai ta biyu badiyya yaranta huɗu itama, mata uku namiji ɗaya, sai amarya Rahina ke da uku maza biyu mace ɗaya...............
Tunda ya fara nake hawaye, sanda ya dire ƙarshe tuni kuka yaci ƙarfina har ina shashasha, ya jani jikinsa ya rungume yana lallashi, “To kuka ya isa haka mana uhmyim, haka rayuwa take, ganin wani a cikin ni'imar rayuwa bashine yake nufi ya samu komai ba, kowacce irin rayuwa zaki samu akwai rauni da jarawa a cikinta, da yawan dariyar da mutane keyi idanda zaki zauna dasu kiji suwayesu zaki fahimci iyakarta haƙori ne kawai, Haƙuri rahamane, duk wanda yay haƙuri baya yin asara, idan kayi haƙuri kaga babu riba a cikinsa to ɗan kaɗan kayi, sannan ka binciki kanka maybe kana zaluntar waninka ne, dan bakowacce jarabawa bace ga ɗan adam take zama daga ƙaddararsa, wasu mutanen sune da kansu suke shuka sharri sai kiga suna ta naɗar sakamakonsa da sharrika suma. Duk sanda na samu wani bakin zare na binciken mahaifiyata koxan dace da samunta sai kaina ya kulle Miemaa, kiga hankalina ma da tunanina sun gushe daga wajen, bansan miyasa hakanba?”.
“Al'amarinta kamar akwai sihiri a ciki boss”.
Saurin ɗagoni yay daga jikinsa, yace, “Miyasa kikace haka?”. Hawayena na share ina ɗan jan hanci kaɗan, “Duk musulmin ƙwarai ya yarda akwai ƙaddarar mutuwa, kuma wajibice ga kowa babu fashi, a ganina rasuwar Abba bazata gusarma Mamah hankali ba, koda zata shiga ruɗani bazai yuwu ace na gushewar hankaliba har akai gayin haukan da za'a bar gida ma gaba ɗaya. Matar dana zauna da ita a saudia bansan asalin sunanta ba, amma haka kawai tun ganina da ita na farko naji ƙaunarta mai tsanani ta shigeni har nakanyi mamaki, itace mahaifiyar Anum da Anuwar, aɗan zamana da ita na fahimci abubuwa da yawa daga gareta waɗanda suka sakani a ruɗani, bazan yanke hukunci akan gaibu ba, dan ALLAH shi kaɗaine masanin gaibu, saidai ga shawara”.
“Wace irin shawara?”. “Mizai hana muje Saudia a zuwan kamar na kai mata kai ku gaisa, dan dama ta roƙeni akan wataran na kai mata kai, haka kawai a ranta takejin son ganin mij.......”
“Ƙarasa mana to”.
Fuskata na ɓoye cikin ƙirjinsa ina murmushi. Murmushin shima na jiyo yanayi, ya tura hannunsa cikin sumata yana yamutsawa kamar maimin susu. Tsawon lokaci muka ɗauka a haka babu wanda ya sake magana, daɗin yan
da yakemin a cikin kai ya sakani fara lumshe idanun barci, cikin mintuna ƙalilan kuwa barcin yay gaba dani.
Tunda Bilkisu tai barci sai idanun Jawaad suka sake bushewa, kalamanta kawai yakema fashin baƙi dalla-dalla, daga ƙarshema zameta yay daga jikinsa a hankali ya kwantar, bayi ya shiga ya ɗauro alwala yazo yayta nafilfili, ya jima yana miƙama ALLAH kukansa cikin ƙanƙan da kai da ƙasƙantarwa, harda hawayensa shaɓe-shaɓe, fatansa ALLAH ya buɗa masa haske akan al'amarin nan ya fahimci sirrin dake ɓoye, duhun dake lulluɓe da shi da matarsa ALLAH ya yaye musu shi ya zama haske. Bai kwantaba sai kusan ƙarfe uku. Yana kwanciya barcin yay gaba dashi dan idanunsa dama har zafi suke saboda barcin.
Kiran sallar asuba da aka ƙwalane ya sakashi farkawa a ɗan firgice hannunsa dafe da kansa, sai da ya jero addu'ar tashi barci kafin ya iya furta Aunty Mah-mah, yau kam ya sake mafarkinsa daya saba na ƙaddarar jini a cikin jini, sai dai yau ya farka bai manta fuskar matar dake masa kalaminba, Gwaggonsa ce Rahma wadda suke kira da Aunty Mah-mah. Juyawa yay ya kalli Bilkisu data cure waje guda cikin bargo ta rufe har rabin fuskarta. Yaɗan lumshe idanu ya buɗe yana sauke ajiyar zuciya, tsahon lokaci yana kallon Bilkisun da nazarin abubuwa masu yawa har aka fara kiraye-kirayen sallar shiga masallaci. Nannauyan numfashi ya sauke sannan ya sauka a kan gadon da ƙyar dan jikinsa ko ina ciwo yake masa alamar barcin bai ishasa ba.
Alwala yayo, ya fito a gaggauce ya tada Bilkisu sannan ya fice masallaci.
Sukuku na tashi da ƙyar nai alwala, raina cike da wasuwasi akan mafarkin da nayi maiban mamaki da al'ajabi, gashi komai dalla-dalla a zuciyata ban manceba kamar azahiri komai ya farumin ba'a mafarkiba. Bayan na idan da sallar ina cikin yin azkar ya dawo, baimin maganaba ya cire jallabiyar jikinsa kawai ya haye gadon ya kwanta daga shi sai boxer. Kallo kawai na iya binsa dashi haryaja bargo ya lulluɓa sannan ya miƙomin hannu alamar nazo. Janye idanuna nai daga garesa ina faɗin, “Ban kammala azkar ba fa”. Baice komaiba ya maida hannunsa a bargon ya lumshe idanu.
Lokacin dana kammala azkar haryay barci, dan saukar numfashinsa kawai nake jiyowa a hankali. Lallaɓawa nai na fice daga ɗakin danni idanun nawama sun bushe banajin barcin kuma. Ɗakinsa na nufa na fara gyarowa dukda babu wani datti tunda bawai zama akeba, kuma yau ba'a nan muka kwanaba, daga nan na dawo falonsa sai babban falo kuma har zuwa nawa falon tunda dama ƙananane su, turaren wuta da air fresheners na baza ko ina, nan take gidan ya ɗau ƙamshi. Jina nai tiɓis da gajiya, nifa dama can na tsani mopping yasin, babu abinda nake kallo mai wahala a aikin gida irin mopping da wanke-wanke, na tsani wanke-wanke fiye da zato, to amma yaya na iya haka zankeyi dole, idan wahalarce dama mun riga mun saba da ita ai tun ƙuruciya, to yanzukam data kasance dole kuma mai muhimmanci a gareni ai dole na zage nayi, sai dai harna fara tausayin kaina idan na koma aiki, lallai zanci ƙaniyata da ayyuka.
Agogo na kalla ƙarfe tara harda wasu mintuna, cikin jan jiki na nufi kitchen, ina tsaye da tunanin miya dace nayi mai sauƙi da bazan sake jigata kainaba naji ana knocking ƙofar falo. Fita nai kasancewar jikina da hijjab, na buɗe ƙofar. Drivern gidan Ummah ne ɗauke da kwando. Ya gaisheni sannan ya miƙamin basket ɗin, amsa nai da masa godiya, nakumace ya miƙa mana godiyarmu ga Ummah kafin muyi kiranta.
Sauƙi dana samu bazanyi girkiba kenan, sai kawai na shirya komai a D/table ɗin. Nagama zubama maigadi abinci a kularsa ya fito. Ɗagowa nai na kalli sashen da nakejin motsi, yana daga tsaye jikin glass ɗin daya raba falona da babban falon hannayensa duka a harɗe saman ƙirji. “Barka da tashi”. Na faɗa kaina a ƙasa ina ɗan murmushi.
Baice dani komaiba ya tako zuwa Dining ɗin yana wani yamutse fuska na alamun bai jima a tashi barci ba. Hannuna da nake rufe kulan ya kamo cikin nashi, cikin yanayin muryan wanda ya tsashi a barci yace, “Haka ake gaida miji dama hajjaju?”. Ɗagowa nai naɗan kallesa na ɗauke idanuna, “Nifa idan aka cigaba da takalata faɗa zan
maida murtani”. Yay maganar da ɗora bakinsa saman goshina ya sumbata sannan ya ɗago haɓata ya haɗe ba....🙄😏
Da ƙyar na samu ya barni mukai zaman yin breakfast, a hakanma ba tsira naiba dan kallonsa kawai ya isheni. Muna tsaka dacin abincin kira ya shigo wayarsa, ɗauka yayi, yanda naji yana amsawa da girmamawa ya sakani fahimtar da Umman su Nabeelah yake. Har muka kammala cin abincin basu kammalaba, na fahimci maganar tasu duk akan Anuwar ne, Nabeelah takai bayani kenan, nidai kwashe kayan nai na nufi kitchen domin wankewa, shi kuma ya ɗauka abincin maigadi ya fita.
Na kammala wanke-wanken na nufi ɗakina zanyi wanka, ina gama cire kaya na ɗaura towel sai gashi ya shigo tsulum babu zato. Kunya naji kamar in nutse, shiko ya wani fuske abinsa saima jallabiyar sa shima ya cire, sama kawai naji anyi dani, hakan ya sakani tsorata nai saurin zagaye hannayena a wuyansa. Ƙaramar dariya yayi da ranƙwafowa ya sumbaci gashina yana faɗin, “Ki rage tsoro yarinyarnan wlhy”.
Ban iya bashi amsaba muka shige bathroom. tunda na fahimci yana nufin muyi wanka tare na shiga zare idanu, ‘kutt inani ina wanka da sangamemen ƙaton nan’. Cikin marairaicewa na shiga roƙonsa akan ya barni na fita idan ya gama sai nayi nima.
Towel ɗin jikina ya sunce yana faɗin, “Barma wahal da kanki Zinaran”. Saurin juya masa baya nai ina rumtse idanu da ƙarfi, sai kawai jinsa nai ya sakani jikinsa da saukar ruwa a kanmu lokaci guda. Sassanyar ajiyar zuciya na saki.
Duk wani noƙe-noƙena akan wankan nan dole na sake mukai wankan nan tare yanda ya keso, dan hanyoyin da ya ringabi dani bazasu yuwu na iya cigaba da bijirewanba. duk yanda zan fassara muku dodon nan nawa da wahala ku yarda dani, dan haka bara kawai nai zipping🤐 bakina kamar zaifi sauƙi.
Man ma tare muka shafa, yaymin drying kaina da yake wuta ta kwana har yanzu akwai, tsaf ya gyaramin shi tamkar wani mai'aikacin gidan saloon. Kayan sawama shine ya zaɓamin zani da riga na wani lass mara nauyi, sai dai ya haɗu harma ya gaji da haɗuwar, zaunar dani yay wai zai ɗauran ɗan kwali, nikam yau naga idi an maidani kamar wata doll. Tunda aka fara ɗaura ɗan kwalin nake gumtse dariya, sai kace irin yadikkon nan na cikin ruga, kasa jurewa nai na ƙyalƙyale da dariya, ya dunguremin kai shima yanayi da faɗin, “Ai dai nayi ƙoƙari”.
Nace, “To dama waye zaice bakayiba ya kwana a call”. “Ashe kin gane karatun ta wajena, muje a ramawa kura aniyarta nima a shiryani yanda Ummah zatazo ta tabbatar ɗanta ya gama dacewa a duniya sai fatan lahira”.
Murmushi nayi ina rufe fuska. sai kuma na buɗe da tambayarsa zuwa zasuyi?. Kansa ya ɗagamin, “Nabeelah takai gulma ta kasa haƙuri sai tazo taji bayani, dama kuma akwai wani abun a ƙasa, zasuzo itada Ummah ƙarama”. Daɗi naji ya sake kamani dan ƙaunarsu nake bayin ALLAHn nan, yaja hannuna muka tafi ɗakinsa, tsareni yay na zaɓo masa kayan shima, ya kuma rantse nice zan shiryashi babu ɗaga ƙafa. Jama'a yau nasha kunya fiye da hasashe, shi dai wannan boss ɗin ku gansa kawai ku barsa inda yake, sanin wanene shi saini matarsa😉 (karfa aimin snatching ƴammatan Bilyn Abdull😝. Lol😂).
Tsaf na shirya abuna ina ƙuƙƙumshe fuska na feshesa da kalolin turarensa masu daɗin ƙamshi, kiransa da akai a wayane ya bani damar gudowa nawa ɗakin na gyara nai zaman ɗaura ɗan kwali, sai da na tabbatar nayi dai-dai buƙatar mai kallo sannan na ƙara turare na fito ina tunanin abinda zan girkama baƙina da rana.
Na shiga kitchen ɗin ina nazari da duba abinda muke dashi ya shigo. “Ki rubuta abinda zaki buƙata ga Sadiq nan yazo zaiyo cefane”. Kaina na jinjina masa.
Ina gama rubuta abinda zan buƙata na dawo kitchen ɗin na fara ɗaura abinda ke a hannu, a mamakina sai gani nai shima ya shigo, riga ya ɗauka ya miƙamin wai na ɗaura masa. Na ɗan waro idanu waje da faɗin, “Namiji da girki?”. Ido ɗaya ya kannemin da faɗin, “Bakiso nai koyi da ƙyawawan halayen MANZON ALLAH (S.A.W)? Miemaa insha ALLAH zaki sami mijinki a cikin gidanki fiye da yanda kike zato, zan riritaki na shagwaɓaki na gatantaki, idan saɓani ya shigo a tsa
kaninmu muyi haƙuri da juna mu daure wajen yima juna uzuri da ƙyaƙyƙyawan zato, bance dake niɗin na daban bane, bankuma miki alƙawarin zama na daban ba, sai dai insha ALLAH zan kasance miki mai sauƙi da rangwame kamar yanda nake fata daga gareki, randa kuma zan ƙara aure ki kwantarmin da hankalinki kamar kinyi baƙo ya mutu”. Harara na zuba masa batare da nayi zatoba ina mai zumɓura baki da juya masa baya. Ya ƙyalƙyale da dariya yana rungumoni jikinsa, “Oh gulmammiyar matata ashe tana sona take basarwa, garama ki shirya yarinya mata huɗu zanyi gangariya”. Ƙin tanka masa nayi, dan jinai zuciyata ta kumbura, har nai mamaki dan bansan dalilin hakanba.
Bai fasa tsokanata ba har Sadiq ya kawo cefanen muka shiga yin aikin girkin ni da shi, yanda yake komai a nutse ya sani fahimtar ya iya girki shima, ban tambayesa ba dai har muka kammala komai, sai dai lokaci-lokaci yakan fita Dining ya amsa wayarsa daya bari a can sai ya dawo................✍
😵kuttt addu'arkufa ta cini da yawa words 4412😫🤒
Barka da juma'a😍😍😘😘.
ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.
SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;
ƊAURIN ƁOYE
ALƘAWARIN ALLAH.
HAFSAT RANO tazo muku da;
SAUYIN ƘADDARA
ƊAURIN GORO
MAMU GEE tazo muku da;
BURI ƊAYA
ƘAUNAR MU.
MISS XOXO tazo muku da;
KAIMIN HALACCI
IGIYAR ZATO.
BILYN ABDULL tazo muku da;
WUTSIYAR RAƘUMI...
GUDU DA WAIWAYE....
abin birgewa books ɗinan duk sun wanzune akan farashi mai rahusa, guda goma duka 1k ne, guda biya 500, guda huɗu 450, guda uku 400, guda biyu 300, ɗaya 200 gamai buƙata zai iya tun tuɓar wannan numban domin samunsu a documents dan an kammalasu.
Katin waya mtn za'a turaahi tanan. 09032345899
sai kunma masu tura kuɗi ta bank zaku tura tanan 0225878823
Hafsat Kabir Umar GTB.
Saiku tura shaidar biyanku ta wannan number 0803 081 1300
Sai kunzo😍😍😍😘.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
Domin samun littafin Ƙwai cikin ƙaya daga farkon ko taɓa Link ɗin da ke ƙasa.
👇👇👇👇
.
https://www.facebook.com/groups/2803452939899949/?ref=share
[1/11, 10:48 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: Bilyn Abdull 📚:
Page 46
..................Tsaf muka kammala komai tare da shi, kiran sallar zuhur da akayine ya sakashi fita ya barni ina ƙarasa sauran abubuwan. Nima a gurguje na ƙarasa komai na fito yin sallar. Na idar kenan ina addu'a naji ana sallama, kafin na miƙe na fita ganin wanene Nabeelah ta shigo ɗakin.
Murmushi mukaima juna, ta ƙaraso ta rungumeni tana faɗin “Amarsu ta ango mai daɗin suna, bara na faɗa a hankali kar yauma nai suɓutar baki ya jini ya markaɗa”. Dariya ta bani sosai, dan haka na shiga yi. “Hum ke dariyama abin ya baki, wlhy kaɗan daga aikinsa yamin casar gyaɗa indai yayanmu ne. Ina fata baya nan?”. Toilet na nuna mata da ahannu ina faɗin, “Yana ciki kuwa”. Sosai ta waro idanu waje da faɗin, “Na shiga Uku dan ALLAH da gaske kikeyi?”. Yanda ta rikice ɗinne ya sakani sakeyin murmushi, na ajiye abin sallar dana linke, “Wai ke kaɗai kikazo ne?”. “A'a ni da su Ummah ne fa, suna falo”. Ban bata amsaba na fito batare dana cire hijjabin ba.
Tunda na fito suka zubamin idanu har abin ya bani kunya, na ƙarasa inda suke kaina a ƙasa, har ƙasa na durƙusa inai musu sannu da zuwa. Cikin fara'a suka amsamin har suna haɗa baki wajan faɗin nazo garesu. A kunyace na kuma tashi naje gabansu dab zan sake tsugunnawa Ummah babba ta riƙoni, tsakkiyarsu ta zaunar dani tare da rungumeni jikinta tana sauke wani nannauyan numfashi daya bani mamaki matuƙar gaya, itama Ummah ƙarama saita riƙo hannuna da faɗin, “ALLAH yaymiki albarka kinji, lallai ƙaunar da muke miki da gaske ta wuce ta surukuta kawai”. Ban fahimci zancen nataba nidai, na ɗago daɗan satar kallon Ummah babba da naga kamar tana hawaye. Kaina na maida a ƙasa nace, “Bara na kawo muku ruwa”.
Ummah ƙarama da itama na ga tana share hawayen tace, “Bara mu fara yin salla ɗiyata, dan ta riskemu a hanya saboda go-slow ɗin garin nan da baya ƙarewa”. Kaina na jinjina musu tare da miƙewa nai musu jagora har cikin ɗakina. Sai da na saka musu abin salla sannan na fito dan na basu waje suyi.
Kwance na iske Nabeelah na danna waya, na zauna kujerar dake kallonta, “K bazakiyi sallarba madam?”. Wayar ta janye daga fuskarta tana tashi zaune, “Aini shehi yamin”. Nace, “Okay to acigaba da gashi”. Dariya ta sanya tana ƙoƙarin komawa ta kwanta, ni kuma na miƙe dan naje na shirya abincin a dining, harna miƙe na dawo na sake zama. “Nabeelah niko kinga abinda na gani kuwa? Saifa naga kamar su Ummah kuka sukai?”. Kallona tai tana murmushi, “Nima dai ba komai na saniba akai, amma tabbas akwai wani abu da suka sani game dake wanda na lura shine dalilin kukan nasu”. Babu shiri na koma na zauna a kujerar sosai ina faɗin, “Game dani kuma Nabeelah?”. “Lah bafa wani abu mara ƙyau bane naga kamar kin ruɗe”. Ajiyar zuciya naɗan sauke duk da bawai na gamsu da amsar tata bane, na sake miƙewa na nufi kitchen. Abincin dana shirya a kuloli na fara fiddowa, ganin hakan Nabeelah ta taso ta tayani muka shirya komai. Falon muka sake dawowa muka zauna, Nabeelah ta fara zubamin surutu, nidai nawa murmushi ne, wani gurin kuma nakan jinjina wautarta sosai. zamanmu baifi da mintuna goma ba su Ummah suka fito, miƙewa nai ina musu sannu. Fuskokinsu ɗauke da murmushi suka amsamin suna zama. Ina fara zuba musu ruwan dana ajiye ya shigo falon da sallama.
Tsokanarsa suka shigayi da faɗin ga ango ga ango. Yay murmushi mai sauti cike da
Showing 159001 words to 162000 words out of 249282 words
Yaɗanja hancina kaɗan, “Wato tun daren jiya na sauya miki kamanni da karya ƙasusuwan ki? To a yafeni bazan sakeba Zinaraina”.
Bance masa komaiba dan naji kunya. Ya fara shafa bayana a hakali da gyara kwanciya, “Jawaad Abdul-Azez Yuseef ɗane da ga. zuri'ar Alhaji Yuseef Tafida. Alhaji Yusif talaka ne mai rufin asirin ALLAH, domin kuwa manomine kuma makiyayi, duk dai a birni yake rayuwarsa da iyalansa to dukkan wani sabgoginsa na ƙauyensu, acan yake nomansa da kiwo, hakan yasa hankalinsa rabuwa biyu, harma zamansa a ƙauyensu ya so ya rinjayi zaman birnin. Matan Alhaji Yusif uku ne cif, kuma kowacce a cikinsu ALLAH ya azurtata da haihuwa, matarsa ta farko hajiya Atika yaranta shida huɗu duk maza biyu mata, sai ta biyu badiyya yaranta huɗu itama, mata uku namiji ɗaya, sai amarya Rahina ke da uku maza biyu mace ɗaya...............
Tunda ya fara nake hawaye, sanda ya dire ƙarshe tuni kuka yaci ƙarfina har ina shashasha, ya jani jikinsa ya rungume yana lallashi, “To kuka ya isa haka mana uhmyim, haka rayuwa take, ganin wani a cikin ni'imar rayuwa bashine yake nufi ya samu komai ba, kowacce irin rayuwa zaki samu akwai rauni da jarawa a cikinta, da yawan dariyar da mutane keyi idanda zaki zauna dasu kiji suwayesu zaki fahimci iyakarta haƙori ne kawai, Haƙuri rahamane, duk wanda yay haƙuri baya yin asara, idan kayi haƙuri kaga babu riba a cikinsa to ɗan kaɗan kayi, sannan ka binciki kanka maybe kana zaluntar waninka ne, dan bakowacce jarabawa bace ga ɗan adam take zama daga ƙaddararsa, wasu mutanen sune da kansu suke shuka sharri sai kiga suna ta naɗar sakamakonsa da sharrika suma. Duk sanda na samu wani bakin zare na binciken mahaifiyata koxan dace da samunta sai kaina ya kulle Miemaa, kiga hankalina ma da tunanina sun gushe daga wajen, bansan miyasa hakanba?”.
“Al'amarinta kamar akwai sihiri a ciki boss”.
Saurin ɗagoni yay daga jikinsa, yace, “Miyasa kikace haka?”. Hawayena na share ina ɗan jan hanci kaɗan, “Duk musulmin ƙwarai ya yarda akwai ƙaddarar mutuwa, kuma wajibice ga kowa babu fashi, a ganina rasuwar Abba bazata gusarma Mamah hankali ba, koda zata shiga ruɗani bazai yuwu ace na gushewar hankaliba har akai gayin haukan da za'a bar gida ma gaba ɗaya. Matar dana zauna da ita a saudia bansan asalin sunanta ba, amma haka kawai tun ganina da ita na farko naji ƙaunarta mai tsanani ta shigeni har nakanyi mamaki, itace mahaifiyar Anum da Anuwar, aɗan zamana da ita na fahimci abubuwa da yawa daga gareta waɗanda suka sakani a ruɗani, bazan yanke hukunci akan gaibu ba, dan ALLAH shi kaɗaine masanin gaibu, saidai ga shawara”.
“Wace irin shawara?”. “Mizai hana muje Saudia a zuwan kamar na kai mata kai ku gaisa, dan dama ta roƙeni akan wataran na kai mata kai, haka kawai a ranta takejin son ganin mij.......”
“Ƙarasa mana to”.
Fuskata na ɓoye cikin ƙirjinsa ina murmushi. Murmushin shima na jiyo yanayi, ya tura hannunsa cikin sumata yana yamutsawa kamar maimin susu. Tsawon lokaci muka ɗauka a haka babu wanda ya sake magana, daɗin yan
da yakemin a cikin kai ya sakani fara lumshe idanun barci, cikin mintuna ƙalilan kuwa barcin yay gaba dani.
Tunda Bilkisu tai barci sai idanun Jawaad suka sake bushewa, kalamanta kawai yakema fashin baƙi dalla-dalla, daga ƙarshema zameta yay daga jikinsa a hankali ya kwantar, bayi ya shiga ya ɗauro alwala yazo yayta nafilfili, ya jima yana miƙama ALLAH kukansa cikin ƙanƙan da kai da ƙasƙantarwa, harda hawayensa shaɓe-shaɓe, fatansa ALLAH ya buɗa masa haske akan al'amarin nan ya fahimci sirrin dake ɓoye, duhun dake lulluɓe da shi da matarsa ALLAH ya yaye musu shi ya zama haske. Bai kwantaba sai kusan ƙarfe uku. Yana kwanciya barcin yay gaba dashi dan idanunsa dama har zafi suke saboda barcin.
Kiran sallar asuba da aka ƙwalane ya sakashi farkawa a ɗan firgice hannunsa dafe da kansa, sai da ya jero addu'ar tashi barci kafin ya iya furta Aunty Mah-mah, yau kam ya sake mafarkinsa daya saba na ƙaddarar jini a cikin jini, sai dai yau ya farka bai manta fuskar matar dake masa kalaminba, Gwaggonsa ce Rahma wadda suke kira da Aunty Mah-mah. Juyawa yay ya kalli Bilkisu data cure waje guda cikin bargo ta rufe har rabin fuskarta. Yaɗan lumshe idanu ya buɗe yana sauke ajiyar zuciya, tsahon lokaci yana kallon Bilkisun da nazarin abubuwa masu yawa har aka fara kiraye-kirayen sallar shiga masallaci. Nannauyan numfashi ya sauke sannan ya sauka a kan gadon da ƙyar dan jikinsa ko ina ciwo yake masa alamar barcin bai ishasa ba.
Alwala yayo, ya fito a gaggauce ya tada Bilkisu sannan ya fice masallaci.
Sukuku na tashi da ƙyar nai alwala, raina cike da wasuwasi akan mafarkin da nayi maiban mamaki da al'ajabi, gashi komai dalla-dalla a zuciyata ban manceba kamar azahiri komai ya farumin ba'a mafarkiba. Bayan na idan da sallar ina cikin yin azkar ya dawo, baimin maganaba ya cire jallabiyar jikinsa kawai ya haye gadon ya kwanta daga shi sai boxer. Kallo kawai na iya binsa dashi haryaja bargo ya lulluɓa sannan ya miƙomin hannu alamar nazo. Janye idanuna nai daga garesa ina faɗin, “Ban kammala azkar ba fa”. Baice komaiba ya maida hannunsa a bargon ya lumshe idanu.
Lokacin dana kammala azkar haryay barci, dan saukar numfashinsa kawai nake jiyowa a hankali. Lallaɓawa nai na fice daga ɗakin danni idanun nawama sun bushe banajin barcin kuma. Ɗakinsa na nufa na fara gyarowa dukda babu wani datti tunda bawai zama akeba, kuma yau ba'a nan muka kwanaba, daga nan na dawo falonsa sai babban falo kuma har zuwa nawa falon tunda dama ƙananane su, turaren wuta da air fresheners na baza ko ina, nan take gidan ya ɗau ƙamshi. Jina nai tiɓis da gajiya, nifa dama can na tsani mopping yasin, babu abinda nake kallo mai wahala a aikin gida irin mopping da wanke-wanke, na tsani wanke-wanke fiye da zato, to amma yaya na iya haka zankeyi dole, idan wahalarce dama mun riga mun saba da ita ai tun ƙuruciya, to yanzukam data kasance dole kuma mai muhimmanci a gareni ai dole na zage nayi, sai dai harna fara tausayin kaina idan na koma aiki, lallai zanci ƙaniyata da ayyuka.
Agogo na kalla ƙarfe tara harda wasu mintuna, cikin jan jiki na nufi kitchen, ina tsaye da tunanin miya dace nayi mai sauƙi da bazan sake jigata kainaba naji ana knocking ƙofar falo. Fita nai kasancewar jikina da hijjab, na buɗe ƙofar. Drivern gidan Ummah ne ɗauke da kwando. Ya gaisheni sannan ya miƙamin basket ɗin, amsa nai da masa godiya, nakumace ya miƙa mana godiyarmu ga Ummah kafin muyi kiranta.
Sauƙi dana samu bazanyi girkiba kenan, sai kawai na shirya komai a D/table ɗin. Nagama zubama maigadi abinci a kularsa ya fito. Ɗagowa nai na kalli sashen da nakejin motsi, yana daga tsaye jikin glass ɗin daya raba falona da babban falon hannayensa duka a harɗe saman ƙirji. “Barka da tashi”. Na faɗa kaina a ƙasa ina ɗan murmushi.
Baice dani komaiba ya tako zuwa Dining ɗin yana wani yamutse fuska na alamun bai jima a tashi barci ba. Hannuna da nake rufe kulan ya kamo cikin nashi, cikin yanayin muryan wanda ya tsashi a barci yace, “Haka ake gaida miji dama hajjaju?”. Ɗagowa nai naɗan kallesa na ɗauke idanuna, “Nifa idan aka cigaba da takalata faɗa zan
maida murtani”. Yay maganar da ɗora bakinsa saman goshina ya sumbata sannan ya ɗago haɓata ya haɗe ba....🙄😏
Da ƙyar na samu ya barni mukai zaman yin breakfast, a hakanma ba tsira naiba dan kallonsa kawai ya isheni. Muna tsaka dacin abincin kira ya shigo wayarsa, ɗauka yayi, yanda naji yana amsawa da girmamawa ya sakani fahimtar da Umman su Nabeelah yake. Har muka kammala cin abincin basu kammalaba, na fahimci maganar tasu duk akan Anuwar ne, Nabeelah takai bayani kenan, nidai kwashe kayan nai na nufi kitchen domin wankewa, shi kuma ya ɗauka abincin maigadi ya fita.
Na kammala wanke-wanken na nufi ɗakina zanyi wanka, ina gama cire kaya na ɗaura towel sai gashi ya shigo tsulum babu zato. Kunya naji kamar in nutse, shiko ya wani fuske abinsa saima jallabiyar sa shima ya cire, sama kawai naji anyi dani, hakan ya sakani tsorata nai saurin zagaye hannayena a wuyansa. Ƙaramar dariya yayi da ranƙwafowa ya sumbaci gashina yana faɗin, “Ki rage tsoro yarinyarnan wlhy”.
Ban iya bashi amsaba muka shige bathroom. tunda na fahimci yana nufin muyi wanka tare na shiga zare idanu, ‘kutt inani ina wanka da sangamemen ƙaton nan’. Cikin marairaicewa na shiga roƙonsa akan ya barni na fita idan ya gama sai nayi nima.
Towel ɗin jikina ya sunce yana faɗin, “Barma wahal da kanki Zinaran”. Saurin juya masa baya nai ina rumtse idanu da ƙarfi, sai kawai jinsa nai ya sakani jikinsa da saukar ruwa a kanmu lokaci guda. Sassanyar ajiyar zuciya na saki.
Duk wani noƙe-noƙena akan wankan nan dole na sake mukai wankan nan tare yanda ya keso, dan hanyoyin da ya ringabi dani bazasu yuwu na iya cigaba da bijirewanba. duk yanda zan fassara muku dodon nan nawa da wahala ku yarda dani, dan haka bara kawai nai zipping🤐 bakina kamar zaifi sauƙi.
Man ma tare muka shafa, yaymin drying kaina da yake wuta ta kwana har yanzu akwai, tsaf ya gyaramin shi tamkar wani mai'aikacin gidan saloon. Kayan sawama shine ya zaɓamin zani da riga na wani lass mara nauyi, sai dai ya haɗu harma ya gaji da haɗuwar, zaunar dani yay wai zai ɗauran ɗan kwali, nikam yau naga idi an maidani kamar wata doll. Tunda aka fara ɗaura ɗan kwalin nake gumtse dariya, sai kace irin yadikkon nan na cikin ruga, kasa jurewa nai na ƙyalƙyale da dariya, ya dunguremin kai shima yanayi da faɗin, “Ai dai nayi ƙoƙari”.
Nace, “To dama waye zaice bakayiba ya kwana a call”. “Ashe kin gane karatun ta wajena, muje a ramawa kura aniyarta nima a shiryani yanda Ummah zatazo ta tabbatar ɗanta ya gama dacewa a duniya sai fatan lahira”.
Murmushi nayi ina rufe fuska. sai kuma na buɗe da tambayarsa zuwa zasuyi?. Kansa ya ɗagamin, “Nabeelah takai gulma ta kasa haƙuri sai tazo taji bayani, dama kuma akwai wani abun a ƙasa, zasuzo itada Ummah ƙarama”. Daɗi naji ya sake kamani dan ƙaunarsu nake bayin ALLAHn nan, yaja hannuna muka tafi ɗakinsa, tsareni yay na zaɓo masa kayan shima, ya kuma rantse nice zan shiryashi babu ɗaga ƙafa. Jama'a yau nasha kunya fiye da hasashe, shi dai wannan boss ɗin ku gansa kawai ku barsa inda yake, sanin wanene shi saini matarsa😉 (karfa aimin snatching ƴammatan Bilyn Abdull😝. Lol😂).
Tsaf na shirya abuna ina ƙuƙƙumshe fuska na feshesa da kalolin turarensa masu daɗin ƙamshi, kiransa da akai a wayane ya bani damar gudowa nawa ɗakin na gyara nai zaman ɗaura ɗan kwali, sai da na tabbatar nayi dai-dai buƙatar mai kallo sannan na ƙara turare na fito ina tunanin abinda zan girkama baƙina da rana.
Na shiga kitchen ɗin ina nazari da duba abinda muke dashi ya shigo. “Ki rubuta abinda zaki buƙata ga Sadiq nan yazo zaiyo cefane”. Kaina na jinjina masa.
Ina gama rubuta abinda zan buƙata na dawo kitchen ɗin na fara ɗaura abinda ke a hannu, a mamakina sai gani nai shima ya shigo, riga ya ɗauka ya miƙamin wai na ɗaura masa. Na ɗan waro idanu waje da faɗin, “Namiji da girki?”. Ido ɗaya ya kannemin da faɗin, “Bakiso nai koyi da ƙyawawan halayen MANZON ALLAH (S.A.W)? Miemaa insha ALLAH zaki sami mijinki a cikin gidanki fiye da yanda kike zato, zan riritaki na shagwaɓaki na gatantaki, idan saɓani ya shigo a tsa
kaninmu muyi haƙuri da juna mu daure wajen yima juna uzuri da ƙyaƙyƙyawan zato, bance dake niɗin na daban bane, bankuma miki alƙawarin zama na daban ba, sai dai insha ALLAH zan kasance miki mai sauƙi da rangwame kamar yanda nake fata daga gareki, randa kuma zan ƙara aure ki kwantarmin da hankalinki kamar kinyi baƙo ya mutu”. Harara na zuba masa batare da nayi zatoba ina mai zumɓura baki da juya masa baya. Ya ƙyalƙyale da dariya yana rungumoni jikinsa, “Oh gulmammiyar matata ashe tana sona take basarwa, garama ki shirya yarinya mata huɗu zanyi gangariya”. Ƙin tanka masa nayi, dan jinai zuciyata ta kumbura, har nai mamaki dan bansan dalilin hakanba.
Bai fasa tsokanata ba har Sadiq ya kawo cefanen muka shiga yin aikin girkin ni da shi, yanda yake komai a nutse ya sani fahimtar ya iya girki shima, ban tambayesa ba dai har muka kammala komai, sai dai lokaci-lokaci yakan fita Dining ya amsa wayarsa daya bari a can sai ya dawo................✍
😵kuttt addu'arkufa ta cini da yawa words 4412😫🤒
Barka da juma'a😍😍😘😘.
ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.
SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;
ƊAURIN ƁOYE
ALƘAWARIN ALLAH.
HAFSAT RANO tazo muku da;
SAUYIN ƘADDARA
ƊAURIN GORO
MAMU GEE tazo muku da;
BURI ƊAYA
ƘAUNAR MU.
MISS XOXO tazo muku da;
KAIMIN HALACCI
IGIYAR ZATO.
BILYN ABDULL tazo muku da;
WUTSIYAR RAƘUMI...
GUDU DA WAIWAYE....
abin birgewa books ɗinan duk sun wanzune akan farashi mai rahusa, guda goma duka 1k ne, guda biya 500, guda huɗu 450, guda uku 400, guda biyu 300, ɗaya 200 gamai buƙata zai iya tun tuɓar wannan numban domin samunsu a documents dan an kammalasu.
Katin waya mtn za'a turaahi tanan. 09032345899
sai kunma masu tura kuɗi ta bank zaku tura tanan 0225878823
Hafsat Kabir Umar GTB.
Saiku tura shaidar biyanku ta wannan number 0803 081 1300
Sai kunzo😍😍😍😘.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
Domin samun littafin Ƙwai cikin ƙaya daga farkon ko taɓa Link ɗin da ke ƙasa.
👇👇👇👇
.
https://www.facebook.com/groups/2803452939899949/?ref=share
[1/11, 10:48 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: Bilyn Abdull 📚:
Page 46
..................Tsaf muka kammala komai tare da shi, kiran sallar zuhur da akayine ya sakashi fita ya barni ina ƙarasa sauran abubuwan. Nima a gurguje na ƙarasa komai na fito yin sallar. Na idar kenan ina addu'a naji ana sallama, kafin na miƙe na fita ganin wanene Nabeelah ta shigo ɗakin.
Murmushi mukaima juna, ta ƙaraso ta rungumeni tana faɗin “Amarsu ta ango mai daɗin suna, bara na faɗa a hankali kar yauma nai suɓutar baki ya jini ya markaɗa”. Dariya ta bani sosai, dan haka na shiga yi. “Hum ke dariyama abin ya baki, wlhy kaɗan daga aikinsa yamin casar gyaɗa indai yayanmu ne. Ina fata baya nan?”. Toilet na nuna mata da ahannu ina faɗin, “Yana ciki kuwa”. Sosai ta waro idanu waje da faɗin, “Na shiga Uku dan ALLAH da gaske kikeyi?”. Yanda ta rikice ɗinne ya sakani sakeyin murmushi, na ajiye abin sallar dana linke, “Wai ke kaɗai kikazo ne?”. “A'a ni da su Ummah ne fa, suna falo”. Ban bata amsaba na fito batare dana cire hijjabin ba.
Tunda na fito suka zubamin idanu har abin ya bani kunya, na ƙarasa inda suke kaina a ƙasa, har ƙasa na durƙusa inai musu sannu da zuwa. Cikin fara'a suka amsamin har suna haɗa baki wajan faɗin nazo garesu. A kunyace na kuma tashi naje gabansu dab zan sake tsugunnawa Ummah babba ta riƙoni, tsakkiyarsu ta zaunar dani tare da rungumeni jikinta tana sauke wani nannauyan numfashi daya bani mamaki matuƙar gaya, itama Ummah ƙarama saita riƙo hannuna da faɗin, “ALLAH yaymiki albarka kinji, lallai ƙaunar da muke miki da gaske ta wuce ta surukuta kawai”. Ban fahimci zancen nataba nidai, na ɗago daɗan satar kallon Ummah babba da naga kamar tana hawaye. Kaina na maida a ƙasa nace, “Bara na kawo muku ruwa”.
Ummah ƙarama da itama na ga tana share hawayen tace, “Bara mu fara yin salla ɗiyata, dan ta riskemu a hanya saboda go-slow ɗin garin nan da baya ƙarewa”. Kaina na jinjina musu tare da miƙewa nai musu jagora har cikin ɗakina. Sai da na saka musu abin salla sannan na fito dan na basu waje suyi.
Kwance na iske Nabeelah na danna waya, na zauna kujerar dake kallonta, “K bazakiyi sallarba madam?”. Wayar ta janye daga fuskarta tana tashi zaune, “Aini shehi yamin”. Nace, “Okay to acigaba da gashi”. Dariya ta sanya tana ƙoƙarin komawa ta kwanta, ni kuma na miƙe dan naje na shirya abincin a dining, harna miƙe na dawo na sake zama. “Nabeelah niko kinga abinda na gani kuwa? Saifa naga kamar su Ummah kuka sukai?”. Kallona tai tana murmushi, “Nima dai ba komai na saniba akai, amma tabbas akwai wani abu da suka sani game dake wanda na lura shine dalilin kukan nasu”. Babu shiri na koma na zauna a kujerar sosai ina faɗin, “Game dani kuma Nabeelah?”. “Lah bafa wani abu mara ƙyau bane naga kamar kin ruɗe”. Ajiyar zuciya naɗan sauke duk da bawai na gamsu da amsar tata bane, na sake miƙewa na nufi kitchen. Abincin dana shirya a kuloli na fara fiddowa, ganin hakan Nabeelah ta taso ta tayani muka shirya komai. Falon muka sake dawowa muka zauna, Nabeelah ta fara zubamin surutu, nidai nawa murmushi ne, wani gurin kuma nakan jinjina wautarta sosai. zamanmu baifi da mintuna goma ba su Ummah suka fito, miƙewa nai ina musu sannu. Fuskokinsu ɗauke da murmushi suka amsamin suna zama. Ina fara zuba musu ruwan dana ajiye ya shigo falon da sallama.
Tsokanarsa suka shigayi da faɗin ga ango ga ango. Yay murmushi mai sauti cike da
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54 Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84