takatse lokacin dasukaji fad'uwar Abu, koda suka waiga saiga innah jummai kwance wanwar.
Tashin hankali kenan, aii sai hajia babba takuma rikicewa da ihu, cikin gaggawa aka d'auketa zuwa asibiti.
Aysha tamatsa kusada su kubrah tana musu kallon raini, "manyan mata haka kuma rayuwa tak'are?, aiduk ABINDA KA SHUKA, SAIKA GIRBESHI glory da kubrah, ai babu mai babbar asara sama daku, garama su hajia khaltum, su sun haihu, kuko aurenma bakuyiba bare kubar Wanda zaimuku addu'a, ALLAH karabamu da asararriyar rayuwa irin taku dai, kud'in antara kuma babu amfanin cinsu, idan Na haihu zankawo muku babie har prison kukagani kunji😂👎🏻.

Bak'inciki tamkar yakarsu, wai wannan 'Yar yarinyarce ke fad'a musu magana haka?, kai kaiconsu dawannan rayuwa.

Khaleel kam kasa cema momy komai yayi, saidai kallon kallo tsakaninta dashi, a yaukam wani matsanancin tausayinta yaratsa zuciyarsa, amma yanaso tad'anyi zaman prison d'in koda Na wattannine ta d'and'ana taji, kodan zuciyarta takuma nadama da sassautowa, Kodan masu hali irin NATA karsuji sha'awar yi.
yaja hannun Aysha sukabar wajen.
Aysha tajuya tana musu gwalo😜..


Ho sholy, ho sholy🤣🤣🤣🤣🤸🏻‍♀


__________________________

Kulli nafsin za'ikatul maut...

Sakamakon abinda yafaru zuciyar innah jummai tabuga da ajali, fad'uwar datayi ko shurawa batayiba awajen, koda sukaje asibitima dubwar farko doctor Faisal yace saidai hak'uri tarasu.
Wayyo Ammah tasha kuka kuwa, itakad'ai gareta 'Yar uwa gashi tatafi tabarta, d'iya d'aya tilo data haifa kuma tak'are agidan prison, saidai jikoki da ALLAH yay nufin zata bari.
Zuwan su khaleel gida dai-dai dakawo gawar innah jummai.
Anmata suttura tareda sallah aka mik'ata makwancinta, sauran bayani yarage tsakaninta da ubangijinta.

Mudai namu ALLAH yajik'anta, Dan babu maishiga tsakanin bawa da ALLAH.😊


********

Bayan kai innah jummai kuma sai mufeedah tafara nak'uda, babu shiri aka kwasheta zuwa asibiti itama.
Tasha bak'ar wahala kam, harma anfidda rai daita saikuma tahaihu, amma d'iyar batazo da raiba, wannan yasaka aka mata allurar barci domin tahuta.
Sannan doctor yazo yasanar musu halin da'ale ciki.
Aunkar6i jariri k'yak'yk'yawa, kamar mai rai, sukaje aka binneta itama.

Mufeedah kuma tacigaba da jiyyar sati d'aya a asibiti, sannan aka sallamota.

Zancen yanke hukuncin su momy yazagaya ko ina acikin duniya, gidajen jaridu da redio, TV, social media daduk wata kafar yad'a labarai, akuma lokacinne khaleel yayarda 'yan jaridu sukai hira dashi.
Suma sauran jami'an tsaro d'innan anyanke musu hukuncin kisama a kotunansu.

__________

Alhmdllh hankalin khaleel ya kwantakam yanzu sosai, saidai 'Yar damuwa daba'a rasaba, Dan haryanzu yakasa mantawa da momy, shak'uwar shekaru talatin dawani Abu bawasaba fans, saidai kawai hak'uri dayawan addu'a.

Yanzunkam rayuwa tana cigaba da gara musu cikin farinciki, khaleel yana bama Aysha kulawa tamkar tsoka d'aya amiya, hakama su Anty Mamie, ammah jar wuya kam aiba'a magana, kayanta takwaso tadawo tana kwana 6angaren su khaleel, darana saita koma 6angarenta, duk tanayine dankar nak'udar dare takama Aysha, tace ya khaleel bashida hankalin sanin nak'uda🤣.
Aikam yahad'e fuska yana zabga mata harara.
"Yo mikika maidani jar wuya? haihuwarma saina kar6a, saidai kuji kukan jarirai".
" kai da Allah can dogon banza, yo banda rik'e bindiga da makar 'ya'yan jama'a uwarmi ka iya, sai mazurai ko?".
"Wanene zaibarka kar6ar haihuwa kamurd'e kan jaririn tunma baizo duniyaba".

" hhhh amma kinga inda nake barci jar wuya, shikenan duk abinda kikemin abakacin motarki to".
"A'a tsayamana kaji irorona, ainidaka babu haka, kaidai mik'o, indai kasiyi motarnan aizan barka, saina koma kan sultani d'in banzarcan".
" wlhy Ammah ki kiyayeni". 'Cewar sultan'.
"Ank'i kiyayarka d'in d'an kwal uba farin banza, gawasu shegun kunnuwanka falka-falka, gashinan ka gogama Sadiq wad'an nan kunuwan naka (d'ansa🤣)....."

"Nid'in?".
" eh kaid'in, kozakayi wani abune?".

"Hhhh bazanyi komaiba jar wuya, amma nima nafasa miki k'yauta d'innan".

"o, tsaya tsaya mutumina, kaikuma mizaka bani?".
" aina fasa, badai nine Sultani ba, mai falka-falkan kunnuwa kuma?".
"Kai haba, bafa kaiba gaye".

Gaba d'aya falon aka shek'e da dariya, dama suna 6angaren ya khaleel ne sunzoma Ammah hira, tunda idan dare yayi nan take dawowa.



___________________________

Khaleel Na kwance afalo, hannunsa rik'eda hisnul Muslim yana dubawa, Aysha tafito daga kichin tana tafiya ahankali, daka ganta kasan batada isashshen lfy, dauriyace kawai irin tata.
Ajiye kayan hannunta tayi bisa table d'in tsakkiyar falon, tad'an jawoshi gaban khaleel.
Sai asannan yad'ago ido yana kallonta, "A'eesha kina lfy kuwa?".
Murmushin yak'e tamasa, " mikagani Sadauki?, lafiyata lau, ciwon bayannan ne kawai, shikuma kasan kullumne babu fashi".
Littafin ya ajiye yatashi zaune sosai, har lokacin idonsa akanta, yakamo hannunta yazaunar da ita kusadashi.
"Kifad'amin gaskiya sholy, tunjiya da daddare nakula bak'yajin dad'i, mutsu-mutsufa kikaitayi awajen barci, nikaina banyi wani barcin kirkiba saboda motse-motsenki, hakama da safennan bakiyi barciba sosai, kodai wani gu namiki ciwo kuma?".

Fuskarta d'auke da murmushi tace, " a'a, ka kwantar da hankalinka, inhar naji ciwon aii zan fad'a😊".
"Shikenan my Angel". 'Yak'are maganar da furzo huci abakinsa'.
Itakuma tafara k'ok'arin bud'e masa fruit d'in dayasa ta yanka masa k'anana.
" gashi kasha, bara nak'arasa aikin danakeyi".
Harta yunk'ura zata mik'e yaruk'o hannunta, "kinga zauna ki huta, idan nagama zanje nak'arasa".
" kad'anfane aikin, kabarni ina motsa jikina, kaifa kayi komai d'azu da safe, please kahuta, bara nak'arasa, aii motsa jikin yanada k'yau shima."
Jin jina mata kai yayi sannan yasaki hannunta.
Tadafashi tatshi.

Akichin tana aiki tana cije le6e, idan azabar ciwo ta isheta kuma tatsaya, sai zufa takeyi, amma taurinkai irinna Aysha tak'i fad'ar batada lafiya.


***********

"Wlhy sainakeji kamar Aysha batada lfy". 'Anty Mamie tayi maganar tana kallon baffah'.

'Dan murmushi yamata, yace, " kai Bilkisu sarkin son 'ya'ya, ba mijinta Na nannaba agida?".
''Yana nan baffansu, ammani shirmen yarannan nake tsoro, zata iya kasancewa cikin ciwo tak'i fad'a, shikuma babana yakasa fahimta. tun ajiya nafara fahinmar tana nak'udar tsaye wlhy baffansu. kaga baradai naduba ko hankalina zai kwanta".
Guntun dariya yamata, "to saikin dawo, ALLAH yasa muji alkairi".
" ameen". 'tayi maganar tana saka takalmanta tafice da hanzari kuwa'.


*******

Hankalin khaleel kasa kwanciya yayi, yanashan fruits d'in amma zuciyarsa nakan Aysha dake kicin, baiyarda k'alau takeba.
Ajiye cokalin yayi yamik'e.
Shikagarsa kichind'in dai-dai da sakin wani marayan kuka da Aysha tayi saboda wani juyi da abinda ke cikinta yayi.
Da sauri nak'arasa yana kiran "A'eesha! A'eesha!! Lfy kuwa?..."

Ina Aysha batasan yanayiba, ya tallafota zuwa jikinsa, saiga Anty Mamie tafad'o falon.
Maganar khaleel tajiyo a kichin yana kiran A'eesha.
da sauri tak'arasa kichin d'in, salati Anty Mamie tafara, dukta rikice, tak'arasa inda suke.
Ya salam, babana garin Yaya haihuwa gadan-gadan amma bazaku iya kiran kowaba?".
"Wlhy Anty Mamie bansan haihuwa baceba, Na tambayeta tacemin lfyarta k'alau, Anty Mamie numfashinta baya fita da k'yau, a d'akko Mota.......

" ina, saidai akira Ammah, d'auketa kakaita bedroom, haihuwar tarigada tazo aii, maza da sauri.....
Da hanzari khaleel yad'auki Aysha daketa nishi da cije la66a.
Anty Mamie kuma takira Ammah arikice.
Mintuna baifi 5 ba saiga Ammah.


"Kai kajimin sakaran yaro, miye nad'orata kan gado itada take nak'uda, sakkota k'asa da sauri".
Khaleel ya sakko da Aysha k'asa sannan Ammah tak'arasa waje.
Cikin haushi yafita, danyafi son matarsa ta haihu agabansa, amma tsohuwarnan tawani korosa, saboda iyayi😏..............✍🏻






Kutanadi kayan babys🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀😜






*_ALLAH ka gafartama iyayenmu, dadukkan musulmai baki d'aya😭._*?*_Typing📲_*


🤰🏻
*_CIKI DA GASKIYA!!......._*
_{🔪wuk'a bata hudashi🗡}_


*_Bilyn Abdul ce🤙🏻_*


*_HASKE WRITERS ASSO......_*
_(Home of experts & perfect writer's)_


*_part 2_*
_(littafi na biyu📘)_

_ina kike *Asy khaleel*?, wanga page nakine, babanki khaleel namik'o gaisuwa ta musamman, taredani bilyn Abdul😊._👍🏻


Kuma banmanta dakuba wlhy.

Fatima Abubakar, Ummi Alhassan, Rabi Sanusi, Aaliyah, Fatima, Zainab Ahmad, Xeety, Sameera Bello.

Alkairin ALLAH ya iso gareku💋💋💋💋❤🤝🏻


4⃣9⃣

*_Monday morning_*
_Cote_.

A yau ranar litinin 8/9 aka shiga shari'arsu momy, abbabban kotun k'asa da k'asa ta Abuja.
Anyi zammne misalin 10am, tareda lauyoyi masu kare gwamnati dakuma lauya mai kare 'yan ta'addar wannan k'ungiya.
Bayan Alk'ali ya saurari k'arar dakuma jawabai abakin lauyoyin guda biyu.
Am fafata sosai, amma ba a yanke hukuncinba, sai azama Na gaba insha ALLAH.

Ran khaleel yad'an 6aci, soyayi ayita kawai yau ta k'are, amma babu komai, ALLAH ya kaimu randa alk'alin yasaka.

Aysha Na zaune afalo zama da k'yar tashi da dabara, dukda cikin nata bawani uban girma yayiba, kunsan cikin fari dama bakowanne keyin k'atoba.
Sallamar ya khaleel yasakata d'ago ido ta kalleshi.
Cikin murmushi tace, "sannu da zuwa sadauki na, yau da wuri haka?".
Kusada ita ya zauna yana murmushin shima, yadurk'uso ya sumbaci cikinta, " babies na inafata kuna cikin k'oshin lfy? Injidai maah-maah tabaku abinci?".
"Tab abinma dariya, ALLAH Sadauki idan kana wannan abun dariya kake bani, waya gayamaka yara biyune to?."
Matsawa yayi sosai, ya mannata da jikinsa, acikin kunne yarad'a mata abinda nima banjiba.
Aysha ta tureshi tana fad'i ''kai kai ALLAH nidai babu ruwana, saima Na fad'aka da Ammah".
"Hhh dubeta kamarma zata iya".
" OK haka kake zaton bazan iyaba ko? Kajira sammaci". 'Tayi maganar tana komawa k'asa'.
K'afarsa takamo tafara k'ok'arin cire masa takalman.
Shikuma yana fad'in "kibari kawai, kinma tunamin wlhy, wai shegen alk'alinnan dukda hujjoji da lauyanmu yabayar yad'aga zaman kotun nan harsai next week".
" to aii babu komai sadauki, dayau da wani satin duk d'ayane, insha ALLAH za'a yanke musu hukunci dai-dai dasu, wahalarmu bazata tafi abanzaba aii, mugodema ALLAH ma da nasarorin daya bamu duk aka kamasu".
"Hakane kuma sholyna, su john ma k'asarsu hukuncin kisa ta yanke musu".
" woow! Dan ALLAH da gaske sadauki!?".
"I'm telling you".
" kai alhmdllh, amma naji dad'i sosai wlhy, nasan Anty meerah saitafi kowa farinciki dahakan, tsinanne, dama dukmasu hali irinnasa k'arshensu kenan, sugama tara dukiyar kuma daga k'arshe tazama mara amfani agaresu, saidai wasu suci kuma".
"Hakane wlhy sholyna, gadai su momy nan inda suka k'are, ita wannan ciwonma data tsinci kanta kad'ai ya isheta, munyi magana da Anty zuwairah akan dukkan kud'ad'e da kaddarorin momyn, kawai zamu kaisu gidan marayu, danbanga amfaninsuba, baffah yace babu Wanda zaiyi amfani dasu agidannan".
''Hakan shine dai-dai aii sadauki, to Amma su Lola fa? naga suma sakasu akayi bashiga sukayiba".
" eh, hakane, amma kinsan mutanenmu da bushewar zuciya, dukda sunga an hukunta wad'annan bazaisasu dainaba suma, sunrigada sun saba da iskancin, dakuma kama kud'ad'e masu nauyi, yanzu koda an sakesu suma tasu dabar zasuje su kafa. Amma dai munan muna tattaunawa akansu, sauran yaran kuma duk mun maidasu hannun iyayensu".
"Aii kunyi dai-dai wlhy, jaridun k'asarnan gaba d'aya wannan satin labarinkune kawai aciki, nasan gaba d'aya idanun al'ummar Nigeria Na kanku yanzu, kai duniyama baki d'aya, jira kawai akeyi aji irin hukuncin daza'a yankema wannan k'ungiya".
"Hakane wlhy, yanzufa da k'yar Na kufto daga hannun 'yan jarida, Taheer nabar musu nagudo, saiya bar wajen yayta tsinemin azuciya d'an iskan".
Dariya Aisha tayi, tace, " aiini wlhy birgeni kukeyi, yanda kuke tafiya da rayuwarku a tsari, idan fannin aiki kuke komai cikin girmamawa suke makashi, basa kallon kaid'in abokinsune, hakama idan aka dawo fannin abota kashige cikinsu kuyita barkwanci, baka kallon kai ogansune awajan aiki, lamarinku daban dana sauran jama'a sadaukina."
"To miye duniyar Sholyna, watarana komai saikiga yazama tarihi, saidai atuna sunanmu badai mud'inba, su Youseef mutanene masu kwazo, kinga tunda nabasu shawarar mukafa k'ungiya taimakon matasa babu musu suka amincemin, yanzu haka nake fad'a miki mun samama matasa kusan 200 aiki wlhy, banda wad'anda muka samama sana'oi, dakuma wad'anda suka koma makaranta, aikinga wannan nasarace, watarana basaikiji sunkai irin dubu biyar d'innanba, inaga hakane yakamata masu kud'in k'asarmu sunayi, musamman ma 'yan arewa dan mutanan kudancin k'asarnan tuni sun waye da irin wad'annan taimakon, amma 'yan arewa ina, kowa burinshi akirashi wane, zakiga kowanne banki mutum yanada kud'i, gawasu agida, motocin hawa Na alfarma, saka manyan kaya masu tsada, agogo wannan saikiji Na million d'aya ahannunsa, 'ya'yansa kowanne yanada account nakansa, ga hannun jari a ma'aikatu daban-daban, shin dukmi zakayi dasu?, kasan dai baza'a gina rami arufeka dasuba ko?, kiga mutum yak'are rayuwarsa kaf aneman dukiya, babu kwakwkwarar ibadar dazai rik'e tazame masa guzurin shiga kabari, wlhy kaiconmu dawannan makauniyar rayuwa, bazakasan kana cikin babbar asaraba sai mala'ikin mutuwa yazo kanka, lokacin babu tsumi babu dabara kuma?".
"Wlhy hakane Sadauki, ai gaskiyafa 'yan arewa muna cikin halin hau, kowa dagashi sai 'ya'yansa, shiyyasa kullum kuma mune abaya, masu k'aunarmu da gaskiya dason dawomana da martabarmu irinsu BUHARI kuma toshewar basira tahanamu ganewa, munfison awatsa mana tsaba mu tsatstsage alokacin, batareda munyi tanadi wa gobenmuba, inhar za'a cigaba da tafiya haka aii wataran sai'an shafe tarihin arewa da al'ummar cikinta, shiyyasa nake tausayin 'ya'yanmu wlhy".
" dolene subaka tausayi, ayanzuma jibi yanda duniya take walagigi, inaga nanda shekaru 20 masu zuwa, ALLAH ka gafarta mana dai kawai."
"Ameen to". 'Aysha tafad'a tana yunk'urawa zata tamik'e'.
Saida ya taimaka mata sannan tasamu tatashi.
"Sannu sholyna kinji, insha ALLAH saura kad'andai ki juyomin babies d'ina ki huta muma mu huta".
"ALLAH ya kaimu, dama nagaji nikam, tashige kichin".
Shima mik'ewa yayi yana dariya dafad'in ''k'ya gaya musu yarinya, kina juyewa zankuma ajiye wani aii".😂😜


******

Rana bata k'arya.......

Yaukam kotu tacika dank'am da jama'a, su Kansu 'yangidansu ya khaleel kwansu da kwarkwata sun halarci zaman, harda innah jummai datak'i komawa Jigawa har yanzun🤣, saboda tsoron dariyar mutane, da anamusu fafa su masu kud'i.🤪
Tunda hajia babba taga gayyar 'yan gidansu taketa zubda hawaye, tama kasa had'a ido da kowa awajen, su kansu duk hankalinsu nakanta, ko kad'an Aysha bataji tausayin kowaba acikinsu, musamman ma hajia babba da hajia khaltum, glory, kubrah. Saima d'an karan dad'i dake ratsa zuciyarta da ruhinta, yauga mak'iyanta gurfane agaban kotu, abinda bata ta6a zaton zai faruba ko a mafarki, dantasha jin labarin makamanta wannan cases d'in natafiya abanza, batareda ankama koda masu laifinbama bare agurfanar dasu gaban kotu.

Kotu tayi tsit ana sauraren jawabi daga lauyoyin na 6angarori biyu, lauyan gwamnati yakawo kwararan hujjoji, tareda manyan shaidu irinsu ya khaleel, wad'anda ganaune ba jiyauba.
Shiru nawani lokaci Alk'ali yana bincika hukuncin dazai yanke.
Alfarma hutun mintuna talatin aka d'auka, Alk'ali da jama'arsa suka shiga wani d'aki domin tattaunawa.

Kusan mintuna talatin saigasu sun shigo, alk'ali ya zauna, bayan wasu 'yan mintuna yad'ago idonsa dake sakaye acikin glass yana kallon jama'ar kotu, yay gyaran murya tareda gyara zamansa.

"Wannan kotu mai alfarma tayankema wad'annan mutane hukuncin dai-dai da laifinsu, saboda fasa kaurin miyagun kwayoyi dasukeyi, dakuma safarar yara mata, tawani fanninma harda makamai, laifinsu yahad'u dayawa, wannan yasaka bamuda kwakwkwaran hukunci, bisa nazari dawannan kotu tayi, da taimakon manyan lauyoyi anyankema dukkan wani dake cikin wannan k'ungiya hukuncin d'aurin shekaru 40 babu Tara, sannan babu wani dakeda lasisisn fitar dasu koda wata gewamnati tazo annan gaba, akwai horo mai tsananin gaske da azabtarwa da'aka tanada musu agidan kaso.
Mutun uku acikinsu basuda isashshiyar lfy, d'aya tasamu sauk'i, za'a wuce da ita gidan kaso, amma akwai alfarmar idan anga ciwonta yatashi amaidota asibiti tacigaba da kar6ar
Showing 165001 words to 168000 words out of 181849 words