kiran sunana da tayi “Nafeesah...!" na juya a hankali na kalleta “ma'am?" ta dan daburce, “umh... Koda yake ma ba komi, je ki kawai" na juya naje na bude fridge na dauko ruwa mara sanyi na sha anan cikin kicin din na maida goran ciki na fita.
Har lokacin Anty tana a yanayin tagumi kamar yadda na fara samunta daga farko, har zan wuce sai kuma na fasa. Na koma kusa da ita na zauna sosai ina fuskantar ta, hannunta na kamo cikin nawa na rike, a hankali nace “Anty Mubeenah..."...
*Gaisuwar ban gajiya zuwa ga en matan Amarya Anty Zee da sister Husnah.... Allah ya huta gajiya ya kuma kawo mana naku bikin mu sha shagali, lol.
~Ni Da Abokin Baba na fans, ya kuke? Sannan me kuke tunani game da canjin halin Mubeenah???
Nace “Anty Mubeenah.... Ni ba karamar yarinya bace ba, kina cikin damuwa naga hakan rubuce akan fuskar ki. Kai ko makaho ya shafa ki yasan cewa kina cikin damuwa.. Nasan cewa ban kai matsayi ko girman da zan zama abokiyar shawarar ki ba, amma idan kina ganin babu damuwa kuma zaki iya, y can't u just tell me?? I'll be a good listener and a judger" tayi shiru tana kallona cikin nuna can I trust you? Na kai daya hannuna na shafa bayan hannunta ina mata murmushi reassuringly, nace “trust me, wallahi u r safe with me... Ki yarda dani".
Numfashi ta ajiye a hankali, “na yarda dake Nafeesah, ke mutum ce ta gari mai hankali da natsuwa. Ina tunanin kila ki tsane ni akan abubuwan da na aikata...!!" tayi shiru tana kallona nima na kalleta ban yi magana ba sai data yi radin kanta kafin taci gaba da magana.
“Kamar yadda nasan cewa kin kula da yanayin zamana da Ibrahim Zama ne kawai muke yi wanda babu armashi ko na kankani. Auran hadi aka mana da Ibrahim ba tare da son mu ba, lokacin ina da wanda nake so. Haka aka kaini gidan Ibrahim ba don naso ba tunda duk yadda naso inyi akan kada ayi auren abin ya faskara. Ibrahim yana kyautata min a matsayin shi na wanda baya so na ma, amma ni na kasa yakar zuciyata akan ta so shi. Ina can ina karewa Mahmud wanda nake so mutuncina wanda kullum sai mun yi waya dashi ya jaddada min in rike mishi amana dai. Duk batanci na duniya babu kalar da ban yiwa Ibrahim akan ya sake ni ba amma yayi biris dani hakan shi yake kara min jin kin shi a raina. It took us almost a year kafin mu kusanci juna, shima ni da kaina naji ina son yin hakan na kai kaina gare shi. Daga nan muka ci gaba da rayuwar ma'aurata amma fa idan naga dama don wani lokacin ko ya neme ni ma sai inyi refusing dinsa, idan kuma ya matsa to sai dai ya biya ni kudin sannan..." tayi shiru hawaye ya zubo mata, yayin da nake jijjiga kai cikin mamaki. Ban taba zaton cewa alakar Abbu da Anty Mubeenah tayi muni irin haka ba, Anty taci gaba...
“Cikin haka na samu cikin Abdullahi, yeah naji dadin samun cikin saboda a lokacin zugar en uwana tayi tasiri akaina da suka ce idan na fara haihuwa a gidan Ibrahim yayana zasu zama magada saboda duk da cewa a lokacin yana karatun masters, amma yana da kudi don bai dogara da kudin mahaifin shi ba, ya dogara da kanshi. Sai dai bayan haihuwar Abdullahi da wata takwas dana kara samun wani cikin mai dan banzan wahala sai naji ina dana sani akan amincewata akan haihuwa. Mun sha danbarwa da Ibrahim akan cikin nan, nayi yunkurin zubar dashi sau ba adadi Allah ya nufa sai da yazo duniya. Wallahi Nafeesah sai da muka tsadance da Ibrahim ya biyani sannan na shayar da jaririn. Watan shi bakwai na yaye shi, babu ruwana da harkar yaran su duka shi yasa zaki ga shakuwar mu dasu bata yi zurfi sosai ba kamar yadda suka shaku da Ibrahim.
Bayan shekaru biyu na sake haihuwar Hafsy, daga nan ne naje asibiti aka saka min loop a mahaifa ta saboda bana son haihuwa da Ibrahim...."
Na zaro idanu waje sosai cikin tsananin mamaki, “loop Anty?" ta gyada kai, “abin ya ba Ibrahim haushi sosai, ya jima yana fushi dani kafin ya sauko ya hau lallashina akan in je a cire min ni kuma nayi biris dani har ya gaji ya daina yace zai karo aure, at first na firgita da jin haka daga karshe da naji shiru sai nayi zaton cewa tsakuwa ce yake taunawa don aya taji tsoro sai kwatsam naji zancen auren shi da ke. In fada miki na firgita ma bata baki ne, na shiga shock bana kadan ba sai dai na cije saboda a gani na bana son Ibrahim meye nawa na jin haushi don zai kara aure? Sai daga baya na fahimci I was wrong! Ina son Ibrahim rashin kulawa irin nawa ne ya hana ni gane hakan, sai daga baya ne bayan ya daga min murya a karo na farko a tarihin rayuwar auren mu, sannan na fahimci halin da zuciyata take ciki game dashi amma ban san ko ta wace hanya zan sanar dashi ba Don haka naja bakina nayi shiru. Amma a en kwanakin nan gabadaya na rasa abinda yake min dadi, shi kuma kamar ya sani, yanzu ko kiran shi nayi a waya baya dauka ma. Zuciyata tana azabtuwa da hakan ba zan iya cigaba da jurewa ba, amma da wani ido zan kalli Ubangijina bayan abubuwan dana aikatawa mijina? Tell me, bayan duk my man and abubuwan nan dana aikata, da wani ido kike so in kalli Ibrahim??".
Na kalleta tun daga sama har kasa, tabbas ta banbanta da Mubeenar dana sani a da. Wannan Mubeenar ba wadda take cike da self esteem bace, sai wata Mubeenah wadda nadama take nukurkusarta. Tausayinta ya mamaye ni matuka.
Nace “kada ki ce haka Anty, shi Allah Gafurur-Raheem ne, yana yafe kuskuran damu muka aikata a gare shi matukar tuban muke nema da gaske. Abbu ma haka ne, ina tabbatar miki da cewa shi zai fi ma kowa jin dadin canzawar ki Anty" ta kalleni da sauri, “da gaske?" na gyada mata kai ina murmushi. Tace “to yanzu me kike so inyi?" nace “abu na farko daya kamata kiyi shine kije ki cire loop din jikinki, bayan hana haihuwa yana da side effects a jikinmu ba kadan ba, bana tantama kibar jikinki loop ne ya assasa miki ita" ta gyada kai cikin nuna yarda da abinda nace, “nima nayi tunanin haka. In Allah ya yarda gobe zan koma asibitin a cire min" nayi murmushin jin dadi, “we will do the other things later then... Bari inje in kwanta haka nan" na mata sai da safe na wuce.
Har na kusa kofata naji ta kira sunana, “Nafeesah!" na juya a hankali, “it was not bad opening up to you.." nayi murmushi sosai, “Anytime Anty" na shige dakin tare da rufo kofata na koma kan gado na kwanta. Tunanin yadda muka kare da Anty na dinga yi, na tsinci kaina da addu'ar Allah yasa ta dore a haka, Allah kuma ya bamu zaman lafiyar da a kullum nake mana addu'ah. Da haka barci ya dauke ni cike da mafarkai iri-iri, mafi yawa daga cikin su shine na wani kyakkyawan yaro da yake bina da tuffa a hannu, na tashi da dan murmushi a fuskata. Addu'a nayi na shafa a fuskata na tashi na fada toilet na dauro alwala nazo nayi sallah.
Da yake ranar Anty ta karbi girki, ban fita falo ba sai da karfe tara tayi. Yara sun tafi makaranta, dana tambayi Harira Anty Mubeenah tace tace a fada min ta tafi asibiti, nayi murmushi kawai. Abinci na zauna naci, nayi gefe da plates din a zuciyata ina raya lokacin barin Harira gidan yayi.
Lokacin da Anty ta dawo har dakina ta leko ta same ni, tace “sun rubuta min magunguna in sha na sati daya sai in koma a cire min" nace “to Allah yasa mu dace" tace “ameen."
Daga ranar alakar mu da Anty Mubeenah ta canza, su kansu yaran sun yi mamaki kuma sun ji dadin hakan kada ma dai Abbu yaji labari wanda nake updating din shi da duk abinda ke faruwa. Ni'imah ta sake haihuwar diya Mace, a ranar muka je muka yi barka ni da Anty Mubeenah. A cikin mota muna dawowa nayi shiru ina tunanin anya a duniya zan ma haihu kuwa? Na tuna ina cikin shekarar aure ta uku kenan zuwa hudu amma har yau shiru babu bayani ko batan wata ban taba yi ba. Mommy tace wai itama hakan ce ta faru da ita, sai a cikin shekararta ta biyar ne sannan ta samu cikina, nayi ajiyar numfashi a hankali ina addu'ar idan da rabona Allah ya kawo masu albarka.
Anty Mubeenah taje an cire mata loop din, sai dai ance sabida jimawar abin a jikinta babu wata kulawa irin yadda ya kamata, ya taba mata mahaifa saboda haka da kyar mahaifar ta iya daukar ciki nan gaba. Hankalinta ya tashi kwarai da jin haka ni na dinga kwantar mata da hankali har ta nutsu. Ni na bata shawarar shiga From My Kitchen Institute da yake Allah ya budawa mai makarantar Hadiza Dogon Daji ta bude reshe anan Kano bayan na Abuja, inda ta fara koyon salon girke girke ina kuma taimaka mata da wasu abubuwa. A gefe guda kuma na dora ta akan weight loss da slimming. Kullum muna gym muna aikin motsa jiki. Abbu ya dawo yayi sati daya ya tafi wata seminar inda daya dawo za a bashi VC.
Cikin wata daya kacal idan ba mugun sanin Anty Mubeenah kayi ba idan ka ganta a hanya ba zaka gane ta ba. Wannan kibar marar fasali da rashin gyara duk ya tafi babu shi, ta dawo tayi wani fresh da ita Masha Allah! Duk da dai har yanzu da sauran kibar amma ta ragu sosai. Musamman ta siya form din wata islamiyah anan bayan gidanmu inda take zuwa daukar karatu kowace rana da yamma, karfe hudu zuwa shida. Ko a yanzu kam Alhamdulillah! Zama na da kishiyata ya canza, idan ka ganmu zaka yi zaton cewa wasu shakikai ne ba kishiyoyi ba.
Result dinmu ya fita, sakamako yayi kyau sosai. Nayi clearance da komi, Abbu kadai nake jira ya dawo in nemi izinin shi in fara aiki da Lab din Aminu Kano Teaching Hospital.
Muna zaune akan dinning muna cin abinci, ranar Anty Mubeenah ce mai girki kuma ita ta dafa mana abincin da kanta don tuni muka sallami Harira bayan mun danka mata kudi masu tsoka da zata ja jari dasu, duk da cewa har yanzu dai sai a hankali amma she's improving sosai. Ta kalli plates dinmu, Jollop spaghetti da sauce din hanta, soyayyiyar agada, da coleslaw. Ita kuma nata taliyar ce kadai sai tulin vegetables akai, ta kai spoonful of cabbage bakinta ta taune ta hadiye da kyar, ruwa ta tsiyaya ta kai bakinta. “Nafeesah! This is a torture wallahi! Haba!! Wata na nawa bani da abincin daya wuce kabeji? Gaskiya na gaji haka nan wallahi, I want to eat chicken!!" ta fada da karfi tana watsa hannuwana sama kamar wata yarinya, aikuwa nan muka samu abin dariya, ni da yaran muka kwashe da dariya sosai, ta nuna mu da yatsa “dariya ma kuke yi koh? Just wait nauyina ya dawo 65, idan na fara cin nama a gidan nan..." Qaseem yace “Mommy, Anty Nafeesah tace ko kin kai 65 din sau daya zaki dinga cin nama a sati fa!" ta harare shi, “inji wa? Kai dai ku jira in rage nauyin, babu wanda zai hana ni cin nama" ni dariya ma ta hana ni magana. A haka dai muka gama cin abincin cikin raha, na taya Anty Mubeenah muka kwashe kayan muka kai kicin muka wanke, daga nan na koma daki na kwanta wai in dan runtsa kafin La'asar tayi.
Ihun yara na jiyo a falo suna ga Abbu, haba! Na dira daga kan gadon da sauri na fita. A karamin falo muka ci karo dashi, tsaye a tsakiyar su Hafsy cikin suits bakake da farar shirt, na danne dokin in rungume shi da naji naje gefen shi kawai na zauna ina murmushi. Sai da yaran suka gama murnar su ya basu chocolates da tarkace ya tura su dakinsu sannan ya juyo gare ni.
Nade ni yayi cikin jikin shi cikin tattausar rungumar nan tashi. Nima na mayar mishi da wadda tafi tashi taushi, mun jima a haka muna jin dumin jikin juna kafin na zare jikina daga nashi a hankali, na kalleshi ina dan murmushi, “ya hanya?" ya jingina kan shi da jikin kunya, “it was tiresome but Alhamdulillah tunda na iso lafiya" nayi murmushi “you must be kam... Yakamata ka watsa ruwa koh?" na mike da brief case dinshi a hannuna.
Ya mike shima yana sassauta neck tie din wuyan shi, daidai lokacin Anty Mubeenah ta fito daga dakinta. Sanye take da doguwar rigar Shadda wadda tabi jikinta sosai, now that I look at her very well, tana da diri da halittun jiki Masha Allah. Haka kawai naji wani abu ya makale min a wuya ganin yadda Abbu ya saki baki yana kallonta yayin da take kallon shi cike da so da kewa. Ganin kallon nasu ba mai karewa bane ba yasa na danyi gyaran murya sai lokacin suka dauke idanunshi a kan juna, na danne takaicin daya zo mun wuya nayi dan murmushi tare da cewa “dama wanka wai zai je yayi, amma tunda gaki bari in barku tare, inje in dan kwanta" na mikawa Anty brief case din, ban jira sun ce wani abu ba na shige dakina da sauri na maida kofar na rufe.
Numfashi na dinga ajiyewa da sauri kamar wadda tayi tsere, tabdijam! Idan har haka zan dinga ji idan naga Abbu tare da Anty Mubeenah to akwai matsala, lallai yakamata in san abin yi.
Da dare muka hadu a dinning wajen cin abinci, daga jin taste din abincin nasan cewa Anty really put her best effort don kuwa yayi dadi sosai, duk yadda taso taja Abbu da hira a wajen abun ya faskara har naji ta bani tausayi, sai dai wani sashe na zuciyata na raya min cewa kawai burga ce yake yi, amma a dokance yake da ita, hakan shi yake kara tunzura ni.
Bayan mun ci abincin muka hada kan komi muka kai kicin muka dawo falo, Abbu da yaran shi suna hirarrakin su, sai muka ja kujera ni da Anty Mubeenah muna tamu hirar har wajen karfe tara da rabi, na tashi na musu sai da safe na shige dakina.
Wanka nayi na dauro alwala, anan cikin bayin nayi shafa ina karfafawa kaina gwiwa daga munanan tunanika da zuciyata ke kitsa min, babu abinda ya canza, Abbu yana nan a yadda yake kamar yadda Anty Mubeenah take, nayi dashe a zuciyar Abbu wanda babu wata 'ya macen data isa ta dakusar min dashi, sai dai ta nemi wani gurbin tayi nata dashen, da wannan naji karfin gwiwa ya shige ni. Don haka koda na fito nayi tozali da Abbu akan gado, murmushi nayi naje gefen shi na zauna. Lafiya lau muka yi sallama dashi, na raka shi har bakin kofa ya tafi bayan ya manna min pecks a kumatu da goshina. Na maida kofar na rufe, kan gado naje na kwanta na janyo wayata nayi en dube-dube da chatting har dare yayi kafin na kashe wayar nayi addu'ar kwanciya barci na shafa. Filo na janyo na rungume a kirjina na rufe idanuna, can kasar zuciyata Istigfar na dinga janyowa da hailala saboda korar shaidanin dake saka min abubuwa a cikin raina...
~Lol! Su Malama Hajiya Mubeenah an dawo kan hanya fa! Wa yaji dadin canzawar ta kuwa? Ni dai naji
~N please ina baran addu'o'inku...
#TeamAbnaf
#OneLove
Alhamdulillah! Rayuwa mai cike da inganci da zama lafiya muke shimfidawa mu da mijinmu. Mun hade kawunan mu waje guda domin samun kwanciyar hankalin mijinmu. Yes, akwai kishi, sai dai kishin zamani muke shimfidawa ba wai na dabbobi ba, kowa tana iyaka kokarinta wajen ganin ta faranta ran mijinta domin samun ragamar zuciyar shi don haka a takaice dai Abbu ya zama sha lelen mu.
Lokacin Hajji yazo, Abbu ya biya mana kujera mu duka banda Hafsy, muka je muka sauke farali. Bayan mun dawo naje Kaduna nayi kwana daya na dawo muka ci gaba da gudanar da rayuwar mu a nutse.
*****
Kallon shi nake yi idanuna na shekin bacin rai da tashin hankali, “ban gane ba? Kamar ya ba zan yi aiki ba, akan me??” tunda muka dawo daga aikin hajji na dame shi da maganar son fara aikina amma yayi biris dani, sai ranar ne ya bani amsa da cewa ai ba zai barni wae inyi aiki ba, duk wahalar dana sha!.
A nutse ya kalleni
Showing 117001 words to 120000 words out of 122880 words
Har lokacin Anty tana a yanayin tagumi kamar yadda na fara samunta daga farko, har zan wuce sai kuma na fasa. Na koma kusa da ita na zauna sosai ina fuskantar ta, hannunta na kamo cikin nawa na rike, a hankali nace “Anty Mubeenah..."...
*Gaisuwar ban gajiya zuwa ga en matan Amarya Anty Zee da sister Husnah.... Allah ya huta gajiya ya kuma kawo mana naku bikin mu sha shagali, lol.
~Ni Da Abokin Baba na fans, ya kuke? Sannan me kuke tunani game da canjin halin Mubeenah???
*♡Jeedderh♡*
*NI DA ABOKIN BABA NA...!*
*©Jeedderh Lawals*
*®Fikrah Writers Association* 🖊🖊
*59*
Nace “Anty Mubeenah.... Ni ba karamar yarinya bace ba, kina cikin damuwa naga hakan rubuce akan fuskar ki. Kai ko makaho ya shafa ki yasan cewa kina cikin damuwa.. Nasan cewa ban kai matsayi ko girman da zan zama abokiyar shawarar ki ba, amma idan kina ganin babu damuwa kuma zaki iya, y can't u just tell me?? I'll be a good listener and a judger" tayi shiru tana kallona cikin nuna can I trust you? Na kai daya hannuna na shafa bayan hannunta ina mata murmushi reassuringly, nace “trust me, wallahi u r safe with me... Ki yarda dani".
Numfashi ta ajiye a hankali, “na yarda dake Nafeesah, ke mutum ce ta gari mai hankali da natsuwa. Ina tunanin kila ki tsane ni akan abubuwan da na aikata...!!" tayi shiru tana kallona nima na kalleta ban yi magana ba sai data yi radin kanta kafin taci gaba da magana.
“Kamar yadda nasan cewa kin kula da yanayin zamana da Ibrahim Zama ne kawai muke yi wanda babu armashi ko na kankani. Auran hadi aka mana da Ibrahim ba tare da son mu ba, lokacin ina da wanda nake so. Haka aka kaini gidan Ibrahim ba don naso ba tunda duk yadda naso inyi akan kada ayi auren abin ya faskara. Ibrahim yana kyautata min a matsayin shi na wanda baya so na ma, amma ni na kasa yakar zuciyata akan ta so shi. Ina can ina karewa Mahmud wanda nake so mutuncina wanda kullum sai mun yi waya dashi ya jaddada min in rike mishi amana dai. Duk batanci na duniya babu kalar da ban yiwa Ibrahim akan ya sake ni ba amma yayi biris dani hakan shi yake kara min jin kin shi a raina. It took us almost a year kafin mu kusanci juna, shima ni da kaina naji ina son yin hakan na kai kaina gare shi. Daga nan muka ci gaba da rayuwar ma'aurata amma fa idan naga dama don wani lokacin ko ya neme ni ma sai inyi refusing dinsa, idan kuma ya matsa to sai dai ya biya ni kudin sannan..." tayi shiru hawaye ya zubo mata, yayin da nake jijjiga kai cikin mamaki. Ban taba zaton cewa alakar Abbu da Anty Mubeenah tayi muni irin haka ba, Anty taci gaba...
“Cikin haka na samu cikin Abdullahi, yeah naji dadin samun cikin saboda a lokacin zugar en uwana tayi tasiri akaina da suka ce idan na fara haihuwa a gidan Ibrahim yayana zasu zama magada saboda duk da cewa a lokacin yana karatun masters, amma yana da kudi don bai dogara da kudin mahaifin shi ba, ya dogara da kanshi. Sai dai bayan haihuwar Abdullahi da wata takwas dana kara samun wani cikin mai dan banzan wahala sai naji ina dana sani akan amincewata akan haihuwa. Mun sha danbarwa da Ibrahim akan cikin nan, nayi yunkurin zubar dashi sau ba adadi Allah ya nufa sai da yazo duniya. Wallahi Nafeesah sai da muka tsadance da Ibrahim ya biyani sannan na shayar da jaririn. Watan shi bakwai na yaye shi, babu ruwana da harkar yaran su duka shi yasa zaki ga shakuwar mu dasu bata yi zurfi sosai ba kamar yadda suka shaku da Ibrahim.
Bayan shekaru biyu na sake haihuwar Hafsy, daga nan ne naje asibiti aka saka min loop a mahaifa ta saboda bana son haihuwa da Ibrahim...."
Na zaro idanu waje sosai cikin tsananin mamaki, “loop Anty?" ta gyada kai, “abin ya ba Ibrahim haushi sosai, ya jima yana fushi dani kafin ya sauko ya hau lallashina akan in je a cire min ni kuma nayi biris dani har ya gaji ya daina yace zai karo aure, at first na firgita da jin haka daga karshe da naji shiru sai nayi zaton cewa tsakuwa ce yake taunawa don aya taji tsoro sai kwatsam naji zancen auren shi da ke. In fada miki na firgita ma bata baki ne, na shiga shock bana kadan ba sai dai na cije saboda a gani na bana son Ibrahim meye nawa na jin haushi don zai kara aure? Sai daga baya na fahimci I was wrong! Ina son Ibrahim rashin kulawa irin nawa ne ya hana ni gane hakan, sai daga baya ne bayan ya daga min murya a karo na farko a tarihin rayuwar auren mu, sannan na fahimci halin da zuciyata take ciki game dashi amma ban san ko ta wace hanya zan sanar dashi ba Don haka naja bakina nayi shiru. Amma a en kwanakin nan gabadaya na rasa abinda yake min dadi, shi kuma kamar ya sani, yanzu ko kiran shi nayi a waya baya dauka ma. Zuciyata tana azabtuwa da hakan ba zan iya cigaba da jurewa ba, amma da wani ido zan kalli Ubangijina bayan abubuwan dana aikatawa mijina? Tell me, bayan duk my man and abubuwan nan dana aikata, da wani ido kike so in kalli Ibrahim??".
Na kalleta tun daga sama har kasa, tabbas ta banbanta da Mubeenar dana sani a da. Wannan Mubeenar ba wadda take cike da self esteem bace, sai wata Mubeenah wadda nadama take nukurkusarta. Tausayinta ya mamaye ni matuka.
Nace “kada ki ce haka Anty, shi Allah Gafurur-Raheem ne, yana yafe kuskuran damu muka aikata a gare shi matukar tuban muke nema da gaske. Abbu ma haka ne, ina tabbatar miki da cewa shi zai fi ma kowa jin dadin canzawar ki Anty" ta kalleni da sauri, “da gaske?" na gyada mata kai ina murmushi. Tace “to yanzu me kike so inyi?" nace “abu na farko daya kamata kiyi shine kije ki cire loop din jikinki, bayan hana haihuwa yana da side effects a jikinmu ba kadan ba, bana tantama kibar jikinki loop ne ya assasa miki ita" ta gyada kai cikin nuna yarda da abinda nace, “nima nayi tunanin haka. In Allah ya yarda gobe zan koma asibitin a cire min" nayi murmushin jin dadi, “we will do the other things later then... Bari inje in kwanta haka nan" na mata sai da safe na wuce.
Har na kusa kofata naji ta kira sunana, “Nafeesah!" na juya a hankali, “it was not bad opening up to you.." nayi murmushi sosai, “Anytime Anty" na shige dakin tare da rufo kofata na koma kan gado na kwanta. Tunanin yadda muka kare da Anty na dinga yi, na tsinci kaina da addu'ar Allah yasa ta dore a haka, Allah kuma ya bamu zaman lafiyar da a kullum nake mana addu'ah. Da haka barci ya dauke ni cike da mafarkai iri-iri, mafi yawa daga cikin su shine na wani kyakkyawan yaro da yake bina da tuffa a hannu, na tashi da dan murmushi a fuskata. Addu'a nayi na shafa a fuskata na tashi na fada toilet na dauro alwala nazo nayi sallah.
Da yake ranar Anty ta karbi girki, ban fita falo ba sai da karfe tara tayi. Yara sun tafi makaranta, dana tambayi Harira Anty Mubeenah tace tace a fada min ta tafi asibiti, nayi murmushi kawai. Abinci na zauna naci, nayi gefe da plates din a zuciyata ina raya lokacin barin Harira gidan yayi.
Lokacin da Anty ta dawo har dakina ta leko ta same ni, tace “sun rubuta min magunguna in sha na sati daya sai in koma a cire min" nace “to Allah yasa mu dace" tace “ameen."
Daga ranar alakar mu da Anty Mubeenah ta canza, su kansu yaran sun yi mamaki kuma sun ji dadin hakan kada ma dai Abbu yaji labari wanda nake updating din shi da duk abinda ke faruwa. Ni'imah ta sake haihuwar diya Mace, a ranar muka je muka yi barka ni da Anty Mubeenah. A cikin mota muna dawowa nayi shiru ina tunanin anya a duniya zan ma haihu kuwa? Na tuna ina cikin shekarar aure ta uku kenan zuwa hudu amma har yau shiru babu bayani ko batan wata ban taba yi ba. Mommy tace wai itama hakan ce ta faru da ita, sai a cikin shekararta ta biyar ne sannan ta samu cikina, nayi ajiyar numfashi a hankali ina addu'ar idan da rabona Allah ya kawo masu albarka.
Anty Mubeenah taje an cire mata loop din, sai dai ance sabida jimawar abin a jikinta babu wata kulawa irin yadda ya kamata, ya taba mata mahaifa saboda haka da kyar mahaifar ta iya daukar ciki nan gaba. Hankalinta ya tashi kwarai da jin haka ni na dinga kwantar mata da hankali har ta nutsu. Ni na bata shawarar shiga From My Kitchen Institute da yake Allah ya budawa mai makarantar Hadiza Dogon Daji ta bude reshe anan Kano bayan na Abuja, inda ta fara koyon salon girke girke ina kuma taimaka mata da wasu abubuwa. A gefe guda kuma na dora ta akan weight loss da slimming. Kullum muna gym muna aikin motsa jiki. Abbu ya dawo yayi sati daya ya tafi wata seminar inda daya dawo za a bashi VC.
Cikin wata daya kacal idan ba mugun sanin Anty Mubeenah kayi ba idan ka ganta a hanya ba zaka gane ta ba. Wannan kibar marar fasali da rashin gyara duk ya tafi babu shi, ta dawo tayi wani fresh da ita Masha Allah! Duk da dai har yanzu da sauran kibar amma ta ragu sosai. Musamman ta siya form din wata islamiyah anan bayan gidanmu inda take zuwa daukar karatu kowace rana da yamma, karfe hudu zuwa shida. Ko a yanzu kam Alhamdulillah! Zama na da kishiyata ya canza, idan ka ganmu zaka yi zaton cewa wasu shakikai ne ba kishiyoyi ba.
Result dinmu ya fita, sakamako yayi kyau sosai. Nayi clearance da komi, Abbu kadai nake jira ya dawo in nemi izinin shi in fara aiki da Lab din Aminu Kano Teaching Hospital.
Muna zaune akan dinning muna cin abinci, ranar Anty Mubeenah ce mai girki kuma ita ta dafa mana abincin da kanta don tuni muka sallami Harira bayan mun danka mata kudi masu tsoka da zata ja jari dasu, duk da cewa har yanzu dai sai a hankali amma she's improving sosai. Ta kalli plates dinmu, Jollop spaghetti da sauce din hanta, soyayyiyar agada, da coleslaw. Ita kuma nata taliyar ce kadai sai tulin vegetables akai, ta kai spoonful of cabbage bakinta ta taune ta hadiye da kyar, ruwa ta tsiyaya ta kai bakinta. “Nafeesah! This is a torture wallahi! Haba!! Wata na nawa bani da abincin daya wuce kabeji? Gaskiya na gaji haka nan wallahi, I want to eat chicken!!" ta fada da karfi tana watsa hannuwana sama kamar wata yarinya, aikuwa nan muka samu abin dariya, ni da yaran muka kwashe da dariya sosai, ta nuna mu da yatsa “dariya ma kuke yi koh? Just wait nauyina ya dawo 65, idan na fara cin nama a gidan nan..." Qaseem yace “Mommy, Anty Nafeesah tace ko kin kai 65 din sau daya zaki dinga cin nama a sati fa!" ta harare shi, “inji wa? Kai dai ku jira in rage nauyin, babu wanda zai hana ni cin nama" ni dariya ma ta hana ni magana. A haka dai muka gama cin abincin cikin raha, na taya Anty Mubeenah muka kwashe kayan muka kai kicin muka wanke, daga nan na koma daki na kwanta wai in dan runtsa kafin La'asar tayi.
Ihun yara na jiyo a falo suna ga Abbu, haba! Na dira daga kan gadon da sauri na fita. A karamin falo muka ci karo dashi, tsaye a tsakiyar su Hafsy cikin suits bakake da farar shirt, na danne dokin in rungume shi da naji naje gefen shi kawai na zauna ina murmushi. Sai da yaran suka gama murnar su ya basu chocolates da tarkace ya tura su dakinsu sannan ya juyo gare ni.
Nade ni yayi cikin jikin shi cikin tattausar rungumar nan tashi. Nima na mayar mishi da wadda tafi tashi taushi, mun jima a haka muna jin dumin jikin juna kafin na zare jikina daga nashi a hankali, na kalleshi ina dan murmushi, “ya hanya?" ya jingina kan shi da jikin kunya, “it was tiresome but Alhamdulillah tunda na iso lafiya" nayi murmushi “you must be kam... Yakamata ka watsa ruwa koh?" na mike da brief case dinshi a hannuna.
Ya mike shima yana sassauta neck tie din wuyan shi, daidai lokacin Anty Mubeenah ta fito daga dakinta. Sanye take da doguwar rigar Shadda wadda tabi jikinta sosai, now that I look at her very well, tana da diri da halittun jiki Masha Allah. Haka kawai naji wani abu ya makale min a wuya ganin yadda Abbu ya saki baki yana kallonta yayin da take kallon shi cike da so da kewa. Ganin kallon nasu ba mai karewa bane ba yasa na danyi gyaran murya sai lokacin suka dauke idanunshi a kan juna, na danne takaicin daya zo mun wuya nayi dan murmushi tare da cewa “dama wanka wai zai je yayi, amma tunda gaki bari in barku tare, inje in dan kwanta" na mikawa Anty brief case din, ban jira sun ce wani abu ba na shige dakina da sauri na maida kofar na rufe.
Numfashi na dinga ajiyewa da sauri kamar wadda tayi tsere, tabdijam! Idan har haka zan dinga ji idan naga Abbu tare da Anty Mubeenah to akwai matsala, lallai yakamata in san abin yi.
Da dare muka hadu a dinning wajen cin abinci, daga jin taste din abincin nasan cewa Anty really put her best effort don kuwa yayi dadi sosai, duk yadda taso taja Abbu da hira a wajen abun ya faskara har naji ta bani tausayi, sai dai wani sashe na zuciyata na raya min cewa kawai burga ce yake yi, amma a dokance yake da ita, hakan shi yake kara tunzura ni.
Bayan mun ci abincin muka hada kan komi muka kai kicin muka dawo falo, Abbu da yaran shi suna hirarrakin su, sai muka ja kujera ni da Anty Mubeenah muna tamu hirar har wajen karfe tara da rabi, na tashi na musu sai da safe na shige dakina.
Wanka nayi na dauro alwala, anan cikin bayin nayi shafa ina karfafawa kaina gwiwa daga munanan tunanika da zuciyata ke kitsa min, babu abinda ya canza, Abbu yana nan a yadda yake kamar yadda Anty Mubeenah take, nayi dashe a zuciyar Abbu wanda babu wata 'ya macen data isa ta dakusar min dashi, sai dai ta nemi wani gurbin tayi nata dashen, da wannan naji karfin gwiwa ya shige ni. Don haka koda na fito nayi tozali da Abbu akan gado, murmushi nayi naje gefen shi na zauna. Lafiya lau muka yi sallama dashi, na raka shi har bakin kofa ya tafi bayan ya manna min pecks a kumatu da goshina. Na maida kofar na rufe, kan gado naje na kwanta na janyo wayata nayi en dube-dube da chatting har dare yayi kafin na kashe wayar nayi addu'ar kwanciya barci na shafa. Filo na janyo na rungume a kirjina na rufe idanuna, can kasar zuciyata Istigfar na dinga janyowa da hailala saboda korar shaidanin dake saka min abubuwa a cikin raina...
~Lol! Su Malama Hajiya Mubeenah an dawo kan hanya fa! Wa yaji dadin canzawar ta kuwa? Ni dai naji
~N please ina baran addu'o'inku...
#TeamAbnaf
#OneLove
*♡Jeedderh♡*
*NI DA ABOKIN BABA NA...!*
*©Jeedderh Lawals*
*®Fikrah Writers Association* 🖊🖊
*60 FiNaLe*
Alhamdulillah! Rayuwa mai cike da inganci da zama lafiya muke shimfidawa mu da mijinmu. Mun hade kawunan mu waje guda domin samun kwanciyar hankalin mijinmu. Yes, akwai kishi, sai dai kishin zamani muke shimfidawa ba wai na dabbobi ba, kowa tana iyaka kokarinta wajen ganin ta faranta ran mijinta domin samun ragamar zuciyar shi don haka a takaice dai Abbu ya zama sha lelen mu.
Lokacin Hajji yazo, Abbu ya biya mana kujera mu duka banda Hafsy, muka je muka sauke farali. Bayan mun dawo naje Kaduna nayi kwana daya na dawo muka ci gaba da gudanar da rayuwar mu a nutse.
*****
Kallon shi nake yi idanuna na shekin bacin rai da tashin hankali, “ban gane ba? Kamar ya ba zan yi aiki ba, akan me??” tunda muka dawo daga aikin hajji na dame shi da maganar son fara aikina amma yayi biris dani, sai ranar ne ya bani amsa da cewa ai ba zai barni wae inyi aiki ba, duk wahalar dana sha!.
A nutse ya kalleni
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40 Chapter 41