ciki ba, amma tunda hakan ba zai samu ba zan rike komi har sai an kaiki gidana baby, ranar...." sai kuma yayi shiru yana girgiza kai, “it will be a surprise, sai kin zo kawai zaki gani" ya duba agogon hannunshi, motar ya bude ya fito da leda ya miko min, tun kafin in amsa nasan ko menene a ciki, kaza ce gasasshiya sai tashin kamshi da tururi take yi, yace “bana son farin cikin ciyar da amaryata a daren aurenmu ya wuce ni duk da cewa ba ni da kaina zan ciyar dake ba" nasa hannu na amsa tare da mishi godiya, yace “you must be tired, jeki ki kwanta, nima zuwa zan yi inyi barci don ji na nake yi very exhausted Allah ma dai yasa in iya yin barcin" ni dai ban tanka mishi ba na daga Baki da kafa a lokaci guda nace “sai da safe".
Suddenly naji an janyo hannuna an dawo baya dani, kafin inyi yunkurin kwace hannuna da kaina gabadaya ko kuma ma in tantance abinda ya faru na tsinci kaina akan faffadan kirjin Abbu, yasa hannu daya ya dago habata ya kalli tsakiyar idanu na, abubuwan dana karanta a idanunshi a lokacin suna da yawa, zallan so, tsabar kawa, raw lust Ya Allah I couldn't take it, idanuwana na kame don ba zan iya cigaba da karbar sakonnin dake fita daga cikin idanunshi ba, naji hucin numfashin shi akan fuskana ban taba kawo komi ba sai da naji bakin shi akan nawa, it was as if duniya ta tsaya cak da juyawa, ya dago ya kalli fuskana da idanuwan suke rufe yace “it's something that I've wanted to do decades ago but being the good man I am holding it in, I Love You Nafeesah!!" abubuwan sun yi wa kwalwa ta yawa a lokacin har na rasa da wanne iri ne zan ji, his sudden kiss ko kuma sudden kalmar yana so na daya furta?? Na daga idanuna da suka min nauyi na sauke su a fuskar shi, kallona yake fervently, sai naji ni kamar wata danyar nama a gaban zaki, da dan sauri na janye hannuna daga nashi hannun, cikin sauri na juya na fara tafiya ina jin kamar wadda ake turawa don har ga Allah ban san ina nake jefa kafa na ba, ni kaina nasan ikon Allah ne ya kaini daki, nayi jifa da ledar daya bani akan slab na zube akan gado kamar kayan wanki na rufe kaina rikib da bargo, Firdausi ta bini da kallo baki a bude naji dadi da bata yi magana ba. Allah kadai yasan lokacin dana share a kwance a cikin bargon nan, daga karshe dai na mike saboda ihun da cikina yake yi na yunwa, tun macaroni din da muka ci da Ramlah da rana ban kara cin komi ba, na sauka daga kan gadon na dauki plate na bude ledar har da yoghurt a ciki mai sanyi duk da zafin kazar ya rage mishi sanyi, na dora ta akan plate da fork da er wuka na kai kan dan karamin bench da muka mayar kamar dinning na dora, na dauko kofuna da yoghurt din suma na ajiye, da hannu na wa Firdausi nuni alamun ta taso don ba zan iya daga baki in mata magana ba ma. Ta taso ta zauna a gefena tana wabi smirking, “Anya zan iya cin kazar amarcin nan kuwa? Idan aka tashi tambayana ita ya zan yi kenan?" nayi banza da ita na fara cin kazar, itama ta fara ci. Tace “ni naga kin wani firgice ne ko dai anyi abin ne?" na harareta tayi dariya kasa-kasa tace “dama sai dana gaya miki ai, mu dai ki rufa mana asiri ki bari sai mun kaiki kafin ki samu ciki kinji??" nan ma ban tanka mata ba, to ai ko nayi niyar tanka mata ma bani da kuzarin yin hakan. Ita kanta kazar jin ta nake yi tayi wani iri na bakina bana jin dadinta, sai yoghurt nayi ta kwankwada don shine mai sauki tunda hadiya kawai zanyi, sauran kazar Firdausi ta nade a cikin takardar ta ta saka a cikin fridge dinta. Littafai na dauko na dare kan study table ni ala dole zan yi karatu, koda na zauna babu abinda yake yawo akan littafin sai fuskar Abbu da murmushin shi, duk yadda naso inyi karatu a daren ranar abin yaci tura dole na hakura na koma kan gado na kwanta hannuna dafe da lebena wanda har lokacin nake jin tausasan lebunan Abbu akan su, it felt so awkward yet so good my body was shaking with desire.

Sai bayan da nayi sallar asubahi sannan na samu na kara bitar karatu. Karfe tara muka fara exam dinmu muka fito kafin sha biyu, daga nan barci nayi don jiya kam ban samu nayi barcin kirki ba. Sai da su Ni'ima suka zo sannan na tashi daga barci lokacin wajen karfe biyu ne, sai da nayi sallah sannan muka shiga shirye-shiryen zuwa wajen Reception din. Suka wanke min kai suka kafar dashi kafin suka gyara min shi sai sheki yake yi da tashin kamshi, nayi wanka na fito nan ma aka shiga yin kwalliya kuma. Da aka kira la'asar muka yi saurara muka yi sallah sannan muka ci gaba, na zura doguwar rigar shaddar da Abbu ya kawo min, Ramlah ta daura min dankwalin rigar yayi kamar gwaggwaro, na saka dankunne, sarka da awarwaro masu ratsin brown a ciki, muna cikin yin shirin wanda aka turo ya dauke mu ya yi waya yace ya iso, da yake suma a shirye suke sai duk muka rankaya muka tafi. Wata er ubansun Range Rover ce baka tana ta sheki tazo daukar mu, aka bude mana muka shiga maza biyu ne a gaban motar don haka muka shiga baya muka tafi, daya daga cikinsu ya juyo muka gaisa har da yin shakiyancin su na abokanan ango, su Firdausi ne masu tare min ni kam kaina yana kasa, duk inda muka wuce sai an bimu da kallo wanda probably nasan cewa motar suke kallo don kuwa haduwarta ya wuce misali.
Tafiya muke yi a hankali har Hotoro, aka yi horn a kofar wani gida aka bude muka tura hancin motar muka shiga, anyi decorating din wajen da kayan ado da ake yi wajen bukukuwa ga kujeru an shirya, wajen cike yake da mutane ana ta hada-hada, aka yi parking sannan muka fita. Wasu mata gungu guda suka zo suka ja mu har wajen da na tabbatar saboda ango da Amarya aka yi shi saboda wajen ya fita daban, wasu royal kujeru guda biyu a kasan canopy an sa tuntu akai a kasa kuma an shimfida wani babban carpet me fadi da laushi. Mai gayya mai aiki Abbu yana zaune a kujera daya, munyi anko da kayan jikinshi shadda light brown mai surfanin zare dark brown, leather brown cover shoes da hular zanna bukar itama brown, kaina a kasa yake ban yi gigin daga ido na dubi Abbu ko tarin mutanen da hankulan su ya dawo gare mu har suka taimaka min na zauna a kujerar kusa da Abbu, in a wink sun bace daga wajen, photographer yazo ya fara haskemu da flashes ya dauki kamar guda goma kafin ya tafi. Abbu ya dan matso saitin kunnena ya rada min “kin yi kyau sosai amaryata" na danyi murmushi ina wasa da yatsun hannuna. Mutanen wajen basu da yawa duk da haka na hango wasu daga cikin dangina na Malumfashi mazan, Aminu, Haruna da Samir duk diyan kanne da Yayin Daddy ne, a matan wajen kuma na hangi Anty Amina da Anty Rahina, Sadiya, Saratu, Da Halima su kuma cousin din su Sadiya dinne, sauran matan kuwa da zasu kai guda goma ban san su ba na dai yi zaton kila matan abokan Abbu dinne. Ba wani bata lokaci aka fara gabatar da walimar, wani daga cikinsu ya bude taro da addu'ah, ya mana fatan alkhairi ana yi ana raha ana ta shan dariya saboda jokes din da mutumin ya dinga cracking, daga nan kuma aka yi en ciye-ciyen snacks da aka raba da kuma drinks, daya bayan daya suka dinga zuwa kowa da matar shi, mu gaisa dasu su mana fatan alkhairi su bamu kyauta, wani a cikin wrapping sheet wani kuma a envelope har su Anty Aminah dasu Ni'imah, daga nan kuma aka shiga daukar hotuna kamar me?! A haka har duhu ya fara shigowa, sannan ne fa aka kara rufe taro da addu'ah muka fara sallama dasu suna shiga motocin su suna tafiya, kafin dai a kira magriba an barmu daga mu sai mu, su Anty Ameenah ma suka mana sallama suka tafi, su Ni'imah sun bi mazajen su sun tafi sai Ramlah tabi bayan su Sadiya. Muka shiga falon matar gidan mai suna Farha ta mana jagora ni da Firdausi har cikin bedroom dinta muka yi sallah, matar tana da fara'ah ga kirki, muna gama sallah muka fara hira wadda yawancin ta akan rayuwar aure ne, challenges din dake cikin shi da shawarce-shawarce akan zamantakewa da kuma wasu shawarwarin da suka sa ni sunke kaina cikin gyale na, tace “kunya kike ji? Wallahi idan kika ce zaki saka kunya cikin rayuwar aurenki to zaki samu cikas kuwa more especially ke mai kishiya, ai wallahi dagewa zaki yi ki cire kunyar nan ki kama mijinki tsam kafin kishiya ko wata a waje ta miki kwacen shi" na gyada kaina cikin yarda da maganganunta. Su Abbu basu shigo gidan ba sai bayan sallar Isha, Farha tayi-tayi damu akan mu tsaya mu ci abinci muka ce a'ah, ta bude wani karamin Kit, tana bude shi wani kamshi mai dadi ya hade dakin, ta dauko kwalaben humra guda biyu ta bani ita kuma Firdausi ta bata turare, tace min “sai dai humra din nan ki bari sai kin tare kafin ki fara amfani da ita Zai fi" muka mata sallama muka fita waje inda Abbu yake jiranmu, muka sake sallama da Farha da maigidanta muka shiga mota muka tafi. Babu wanda yayi magana a cikin motar har muka isa makaranta, Abbu yana yin parking Firdausi ta bude motar ta fita bayan ta wa Abbu sai da safe shi kuma ya mata Allah huta gajiya. Tana fita kamar wanda yake jira ya kamo hannuna, bai damu da yadda nayi gaggawar kwace hannuna ba ya sake janyo hannun nawa yana caressing da thumb dinshi, “kunshin nan yayi kyawu sosai, idan ya goge ki sake yin wani kinji? Shima idan ya goge ki sake wani, I'd like to be seeing it kinji??" na gyada mishi kai a hankali, yayi murmushi “good girl, amma ni sai wani noke-noke kike yi da wani kauda fuska, kin daina min magana, laifin me na miki iye?" ban yi magana ba sai kaina dana girgiza yace “ikon Allah! Aikuwa ba zamu yi haka dake ba, za kina bude baki ne kina min magana idan ba haka ba kuma raina zai baci fa, and u wouldn't like me idan hakan ya faru, ok?" na sake gyada kai, sai kuma nayi sauri nace “toh" yace “na fara nema mana visa fa, wani gari kike so kije for our honeymoon?" na dan zare ido, “honeymoon?" yace “ehh mana, da kin gama exams kin koma za a dawo min dake daga nan kuma zamu tafi honeymoon dinmu" nace “amma da aka ce sai session dinnan ya kare?" ya wani zaro ido kamar wadda ta fadi wani sabo, “ses... me? Ni dai nasan da bakina baki ji na fadi haka ba koh?" nace “ai nayi zaton haka ne" tun kafin in gama yake girgiza kai, “no! Ba haka bane. Gidan da zamu zauna is ready, komi ya riga ya kammala, kun gama jarabawar ku to me zan jira kuma? kin dai san ba zan barki kici gaba da zaman hostel ba kuma yanzun ma don we've already agreed on it ne shi yasa kika ga nayi shiru amma maganar gaskiya ban jin dadin zaman ki anan" na wani yi rau-rau da idanu, ya dage gira, “Allah baby kina jin dadin ki, kuka zaki yi kuma, me na miki?" ya kai hannunshi na dama ya tallabo kuncina dashi yana caressing din kuncina, hannunshi was very warm, na lumshe idanu na a hankali, na jiyo yatsar shi a saman idanu na yana shafawa, “zan ga yadda zamu kare da rigimar ki baby, dama ana haka ne? Daga magana sai ki kama kuka irin daddyn ki ya shagwaba ki koh?" na turo baki tare da janye fuskata daga hannunshi wadanda suka fara sanya min sayingsanyin jiki, murmushi kawai yayi. “Wadannan kyautukan da kika samu ban san ya zanyi dasu ba, do u have any idea ko wajen da zaki ajiye su?" nace “ka ajiye min su a wajenka" yace “to shikenan, zan kaisu gidanmu in ajiye, idan kin zo sai mu bude tare koh?" na rufe fuskata shi kuma yayi dariya, “nasan akwai kudi a ciki su kuma zan saka su cikin account ko ya kika ce?" nace hakan ma yayi, nan ma yace ok. Muka dan yi shiru na dan lokaci kafin ya duba hadaddiyar agogon fata dake daure a lallausan hannunshi, “to nine, yakamata kije ki kwanta yanzu koh?" nace “to, sai da safe" dama duk a wani takure nake ji na, na kama murfin motar zan fita ya sake janyo hannuna da bai jima da saki ba ya juyo dani, “not so soon baby, babu ko sallama?" na danyi frowning in confusion, wace sallama yake so muyi bayan wadda na mishi yanzu? Ban kai ga furta abinda nayi niyya ba naji ya hade goshina da nashi waje guda, irin sallamar jiya ya min sai dai ta yau tafi zurfi da demanding, ya sake ni a hankali idanunshi a lumshe, har lokacin goshin mu a hade yake, numfashi yake ajiyewa a hankali can kuma sai ya sake ni gabadaya, “Goodnight Amour" ya fada cikin whisper, cikin salubewar jiki na fita daga cikin motar. Ina shiga daki text dinshi ya shigo wayata, “make sure to eat something kafin ki kwanta, sweet dreams" na girgiza kai kawai na ajiye wayar akan gado na fara zare kayan jikina, ruwa na watsa na dawo nayi shirin kwanciya barci. Ba wata yunwa nake ji ba don haka na kwanta kawai, Abbu da Al'amuran shi masu ban mamaki suke min yawo a kwalwa, abubuwan da yake min were very new to my innocent life, ban san ya zan kamanta abinda nake ji a cikin raina ba amma ina jin kamar abin is wrong, anya ban yi kuskure ba kuwa?? Nayi juyi akan gado tare da tura kaina cikin pillow.
~Hii there dearies, so me zaku ce game da chapter din yau?
#TeamAbNaf! Hahh! Wata Fan ta kirkiro da sunan nan, ya burge ni kam sosai, what did you think?
#AnaTare





*♡Jeedderh♡.



*NI DA ABOKIN BABA NA....!*


*©°•Jeedderh Lawals•°*

*®°•Fikrah Writers Association°•*🖋



*48*



Ranar Talata bamu yi exams ba sai ranar Laraba. Misalin karfe tara muna cikin exam hall muna jiran invigilators su shigo, sanye nake da doguwar riga dinkin Stella sai mayafi dana yafa mai yalwar fadi, fuskata daga hoda sai kwalli ko janbaki ban shafa ba saboda a sukwane na fita ranar don na kusa makara. Much to my surprise na tsinci Abbu cikin invigilators din, idanunshi suka zagaye ajin har sai da suka lalubo ni ya sakar min kyakkyawan murmushin shi da sai da yasa naji gwiwoyina sun sage, a dan kunyace na maida mishi martani tare da sadda kaina kasa ina tuno yadda muka rabu dashi a jiya da yamma da yazo wajena, yana insisting lallai sai munje ya nuna min gidan da zan zauna ni kuma nace mishi ba sai na gani ba, da yaga alamun ba zan bishi ba sai ya fara min abubuwan nashi da har lokacin kwakwalwata ta kasa daukar su ko sabawa dasu, da kyar na samu na zame na tsere.
Lokacin dana sake kallon inda yake hararata yake yi kasa-kasa fuskar shi na nuna bacin rai, gabana ya fadi, crap! Me nayi? Ko dai tun laifin jiya ne har yanzu yake fushi dani don naga tun daga lokacin bamu sake waya ba kamar yadda bai turon text ba duk da cewa dai na tura mishi wani yau da safe amma bai turo min da reply ba. Aka fara raba mana answer booklet ya dauki wasu yayi row din dake gefenmu na dama, yadda na bishi da ido haka na tsinci idanun yawancin ‘yanmatan ajin suna bin shi da kallo, naji wani takaici da bacin rai yana lullube ni, meye nasu na Kalle min miji? Sai naji kamar in tashi in fidda shi daga cikin ajin, na dai daure ban yi anything silly ba har ya juyo ta bangarenmu. Yazo saitina ya tsaya yana kokarin ciro booklet din, kamshin turaren Armani Code ya mamaye wajen naja na shaka har da lumshe ido, a hankali nace mishi “Abbu good morning!" lokacin daya danyi leaning akan desk din da nake ya ajiye mun takardar, “me yasa kika fito da wadannan kayan a jikin ki?" ya fada muryar shi na nuna bacin rai da distaste, na kalleshi tare da kallon kayan jikina, saboda Allah meye aibun su? Gyalena mai fadi ne ya rufe duk inda ake bukatar ya rufe, kafin in samu ince wani abu ya kara gaba zuwa ga desk din bayana, na danyi shrugging slightly na fara rubuta sunana akan takardar.
Showing 84001 words to 87000 words out of 122880 words