yake glaring din Harith da hot gaze dinshi wanda zai iya grilling din kifi, da sauri Harith ya mika mishi nashi hannun suka yi musabiha yace “Harith, fiancé din Ikram cousin din Sulaiman mijin Sadiya" sai lokacin fuskar Abbu ta dan warware kadan daga hadeta din da yayi amma bata koma normal ba har lokacin, suka dan gaggaisa a tsaitsaye ya dawo da kallonshi gareni da tun da naja gefe ban yi magana ba, kallon daya jefe ni dashi sai da yasa naji alamun kadawar ‘ya‘yan hanjina, yace “ki same ni a mota" da kyar na samu na iya daga mishi kai, ya wa Harith sallama ya nufi wata bakar Land Rover dake kusa da inda Harith yayi parking din tashi motar, haba ba mamaki ashe ya canza mota ne? Na kalli Harith daya jefe ni da murmushin mugunta, na harare shi ya wani yi shrugging yana daga gira sai kawai na girgiza kai don bani da lokacin biyewa tsokanar Harith, godiya na mishi muka yi sallama na wuce inda Abbu yake jirana na bude motar na shiga. Ina shiga yaja motar muka fara tafiya ba tare da yace uffan ba, na kalli fuskar shi har lokacin babu fara'ah a tattare dashi, da alamun na bata mishi rai sosai. Jikina yayi sanyi, na maida kallona ga tagar motar ina jin kamar in fita ta ciki, da alamun yau Abbu na baya cikin walwala, duk saboda ni!!

#TeamAbbu
#One Love
#AnaTare





*♡Jeedderh♡*
[1/1, 18:03] Hauwa-Jedderh💕: *NI DA ABOKIN BABA NA....!*


*©°•Jeedderh Lawals•°*



*45*



Shiru muna cin abinci a cikin restaurant din da muke zuwa lokaci zuwa lokaci, baka jin karan komi sai karan cokali da plate din dake gaban Abbu yana cin abinci yayin da na kurawa nawa plate din idanu kawai, duk yunwar da nake ji sai naji ta tafi, babu space din komi a cikina a lokacin sai na numfashin da nake shaka. Fushin Abbu ya takura ni, ya tsorata ni, gabadaya na rasa abinda yake min dadi a lokacin. Tunda ya sadda kanshi ga plate din gabanshi bai dago idanunshi ba, na kula yana gudun kallona ne kamar yadda na kula cusa abincin kawai yake yi ba wai don yana jin dadin shi ba. A hankali nace “Abbu!" ya dakata da cin abincin da yake yi kafin ya dago ya kalleni, kyawawan idanuwan shi da a koda yaushe suke farare tas-tas suna sheki suna kallona cike da so da kulawa, sun rine daga ainihin kalar su zuwa ja-brown, gaba na ya fadi sosai ban taba ganin wannan kamar ta Abbu ba, ya maida kanshi kasa ya cigaba da cin abincin. Nace “Abbu don Allah kayi hakuri kar kayi fushi dani, kawai Harith yazo ne mu gaisa ba wani abu ba please" bai yi magana ba kamar yadda bai dakata da abinda yake yi ba, na sake cewa “kaji?? Please Abbu na!!" duk da cewa sau tari ya kan nuna bai son sunan amma na kula jin sunan daga bakina yana dadada mishi rai sai dai da alamun hakan bai yi tasiri ba yau, babu murmushin nan daya saba yi, bai yi scowling dinnan ba yana kallona dangerously kamar zai zuke ni da idanunshi, instead sai kawai ya kalleni yayi wani murmushi da bai ma gama hade fatar bakin shi ba balle fuskarshi, muryar shi tayi can kasa kamar wanda yake suffering daga cutar mura yace, “eat, Nafeesah!" ya cigaba da cin abincin, sai kawai naji gwiwoyina sun sage, me ke damun Abbu ne yau? Gabadaya ya wani rikice min kamar ba Abbun dana sani ba, ban taba ganin wannan Abbun da yake gabana ba don haka ne naji nima na gigice sosai. Na xuba duka tafukan hannuwa na biyu a cikin kumatuna kawai na kura mishi idanu, ban damu da cewa hakan zai takura shi ba ko kuma idon mutane dake cikin restaurant din, ni dai fata na da burina shine in karanto abinda yake damun Abbu inyi gaggawar magance mishi koma meye sai dai ban karanci komi ba, ya gama cin abincin ya dago ya kalli plate dina sai kuma ya tashi, yaje ya biya kudin abincin suka dawo tare da yaron wajen aka maida nawa abincin cikin take away muka fita daga restaurant din. Ko a cikin mota ma haka tafiyar ta kasance, yayi wani kicin-kicin da rai kamar wanda aka aikowa da sakon mutuwa. Har muka je bakin hostel ya samu waje a parking lot yayi parking. Na dan saci kallonshi kafin na yunkura da niyar fita daga cikin motar ya katse ni ta hanyar kiran sunana, “Nafeesah!" na dakata amma ban juya na kalleshi ba, na tsani ganin expression din fuskar shi kamar yadda na tsani mutuwata. Murya a hankali yace “kiyi hakuri don Allah" cike da tsananin mamaki na juya na kalleshi, fuskar shi nuna how apologetic he was, nace “me ya faru?" ya girgiza kanshi, “na saka ki cikin damuwa saboda son rai irin nawa, you didn't do anything wrong amma na saka ki gaba ina hade miki fuska, na..." ya sadda kanshi kasa saboda maganar data kakare mishi ni kuma na kura mishi idanu, he looks soooooo lovely and adorable, Anya soyayyar Abbu zata barni in rayu cikin dadin rai?? Ya sake dago kanshi ya kalleni, wannan karon babu bacin rai dake tattare dashi sai idanuwanshi dake nuna tsananin so, kauna, kulawa da wani abu kamar tsoro? I'm not sure. Yace “I was afraid" cikin mamaki na kalleshi nace “of what?" ya girgiza kanshi, “I don't know. Kawai tunda na ganki da wani a tsaye naji wani tsoro ya dabaibaye ni, I really cherish you alot Nafeesah, I was afraid of you leaving me ko wani ya juye miki tunani daga gareni, idan hakan ya faru ban san ya zan yi ba!" wannan ba Abbu Baban su Hafsat da Abdullahi bane, wannan Ibrahim ne a zamanin da yake kan ganiyar kuruciyar shi, na muskuta ta yadda zan fuskance shi sosai, “ni ko wanene kwanakin baya yake cewa ba zai zauna yana soyayya irin ta yara ba? I wonder ko wace kalar soyayya ce wannan?" ya dan jefe ni da harara, na danyi murmushi kafin nace “nima idan hakan ta faru ban san yadda tawa rayuwar zata kasance ba Abbu, idan hakan ta faru I'll be more shattered than u, gwanda kai kana da mata da ‘ya‘y'a ni kuwa dama daga kai sai Mommy da Daddy nake dasu" ya kura min idanu kaman wanda yake kokonton abinda nace, na saki murmushi reassuringly “kada ka damu Abbu, in shaa Allahu abinda kake tsammani ba zai taba faruwa ba, I am yours, and I'll always be in shaa Allah!" ya lumshe idanunshi for a second, daya bude duk wani duhu da rikicin dake cikin idanunshi sun yaye, damuwar data lullube shi ta tafi, Abbuna ya dawo kamar yadda yake, ya saki kayataccen murmushin nan nashi, “you are almost mine dai but at least am relieved, God! Kin tsorata ni wallahi, amma do you really mean what you said?" wai sai a lokacin naji kunya ta dabaibaye ni, nayi gaggawar Kai hannu na rufe fuskata, ina jin er dariyar da yayi, “ana so ana kaiwa kasuwa.... Zaki yi bayani ne idan aka miki snatching" fuskana na cikin tafukan hannuna nace “ai babu wanda ya isa ya kwace min abinda nake so!" ya rankwafo kanshi kusa dani yana wani smirking, ina kallonshi ta yatsun hannuna, yace “Ashe dai ana so na?" da sauri na bude murfin motar na fita na barshi yana dariya, da alamun abin ba karamin dadi yake mishi ba, haka kawai naji murmushi ya subuce min. Ya fito daga cikin motar shima, “tambayar ki fa nayi baki amsa min ba" inaa, ai nayi gaba abina. Yace “to tsaya ki amshi abincin ki" naja tunga na tsaya, ina ji ya bude motar ya dauko takeaway din ya tako zuwa inda na tsaya ya miko min, nasa hannu na karba ina wani sinke fuska, ya wani kuta kamar gaske “zaki yi bayani ne wallahi, sai ki wani dinga sinke fuska kina cuta na wai ke kunya, Allah ya kaimu ranar da zaki shigo hannuna" na saki murmushi, yace “dariya ma kike yi koh? Allah Nafeesah kina bukatar in gyara miki zama, dazu kin ce wai I was cute, yanzu kince ina soyayyar yara and ina magana kina dariya koh?? Sai na tabbatar dana hukunta bakin nan naki da baya jin magana wata rana" dariya na dan saki kasa-kasa, da alamun yau en rigimar ne akan Abbu. Naci gaba da tafiya abina, ya tsaya a inda yake yana magana cikin korafi, “wato ma tafiya kika yi kika barni koh? Ba komi, sai kinyi sati biyu baki sake ganin mai kama dani ba, kai sai ranar auren mu zaki sake ganina ma" na juyo ina kallonshi nace “to ka gaida gida dasu Hafsy" yayi wani irin chuckling daya sa ni bude baki ina kallonshi, ji nayi kamar in ruga da gudu in fada cikin faffadan kirjin shi, sai nayi murmushi kawai tare da girgiza kaina na wuce cikin hostel. Kafin in karasa daki kiran Anty Raheena ya shigo wayata, na daga muka gaisa da ita. Tace wai kira tayi in fada mata size dina zasu siyo under wears da za a saka a cikin kayan lefena, ni wallahi kunya ma ta bani. Da kyar na iya bude baki na fada mata, ko sallama bamu yi ba na kashe wayar.
Bayan kwana biyu aka kai akwatina gidanmu, guda takwas sai kit, sai ta waya Anty Uwani ta turo min akwatunan na gani, wasu azababbun akwatuna kirar kasar Italy na zallan fata kalar pink ne, kayan dake ciki kuwa kama daga shadda, lace, materials, atamfofi, takalma ma kadai daga na kamfanin vincci, dg, poshter, ga jakunkuna da jewelries duka babu kanana gaskiya ba karamin kokari Abbu yayi ba wajen hada kayan nan, na dinga gyada kai kawai lokacin dana dinga duba kayan, ‘kaya kam sun yi kyau gabadaya babu na yar wa sai dai fatan in more su a gidan aurena cikin tattali da soyayyar juna ni da mijina'., a cewar Anty Uwani, ni kam na amsa da ameen a cikin raina.

☆☆☆☆☆☆


A hankali ya gangara motar shi cikin gareji yayi parking, “Amour, sai anjima, take care" nace “toh Abbu na, take care too" yace “mimm, wai Abbu" dariya kawai na saki wadda nasan tana saka shi cikin nishadi na kashe wayar, yayi murmushi yana bin farar Toyota data shigo cikin gidan tayi parking a daidai inda yayi parking din tashi motar. Saddiqa babbar Yayar su Mubeenah ta fito daga cikin motar, shima fita yayi ya gaidata cikin girmamawa, ta amsa a tsaitsaye tana kumburi kafin ta wuce shi fuu, ya bita da kallo cike da mamaki, matar tana da kirki unlike sauran kannen Mubeenah da ita kanta Mubeenar, duk cikin danginta daga ita sai Shafa'atu ne masu sanyin hali a cikin su, yau kam ko mai ya hau kanta? Ya tabe baki ya wuce wajen maigadi suka dan yi en maganganu ya shige cikin gida. Tun daga cikin falo yake jiyo hayaniyar dake tashi daga can dakin Mubeenah. A can dakin na Mubeenah kuwa akwatuna ne a tsakiyar dakin manya har guda shida, Saddiqa na tsaye a gabansu ta kama kugu tana kallon Mubeenah dake kwance akan gado tana latsa waya, tun kayan barcin ranar data tashi dasu ne a jikinta bata canza ba gashi lokacin har karfe hudu na yamma, gashin kanta ya cukurkude ya cure waje daya, Saddiqa ta saki kugu data kama ta fara tafa hannayenta tana sallallami bayan ta gama sauraren abinda kanwar tata Mubeenah ta fada mata, “Innalillahi.... Mubeenah?! Anya kina da hankali kuwa? Kishiya ake shirin miki amma what?? You are cool with it?? Wai ke wace irin mahaukaciyar yarinya ce Mubeenah??" ta dago ta kalli Yayar tana gunaguni, “ni fa wannan aure za zai yi gaba ya kaini ba baya ba, kina kallon akwatunan daya zube min shake da kaya a matsayin kayan fadar kishiya, 5 millions ya bani in kara jarina bayan haka yana nan yana sake gina mana sabon gida kuma ya min alkawarin zai canza min kayan daki sababbi, bayan haka ita yarinyar da zai aura ta zauna damu anan, na riga da nasan halayenta ciki da bai na tabbata da cewa ba zata taba cutar dani ba balle ‘ya‘ya na ke in fact na tabbata Ibrahim ba wai don yana son ta zai auro ta ba sai don kawai ya bani haushi kamar yadda yake fada tun ba yau ba, to kin kuwa ga menene nawa na yin fushi ko in wani kama bori kamar yadda kike cewa inyi? Kin ganni nan wallahi ko a kwalar rigata, in dai aurene yaje yayi tayi ga fili ga mai doki" bayani take zubawa tun karfinta babu ko digon aya balle comma, yayin da Saddiqa ta sake baki da hanci tana kallon kanwar tata kamar wadda tayi gamo, ta jijjiga kai cike da takaici tace “naji dai ana cewa ke mahaukaciya ce, amma ban taba zaton cewa haukan naki ya kai mataki na farko ba sai yau. Ke don kaza kazar ki, (ta kawo zagi ta lailaya mata), kowace mace tana shiga cikin tashin hankali da fargaba idan za a mata kishiya, amma ke kina zaune hankalinki kwance kina gaya min wai an baki jari kuma za a miki sabbin kayan daki. Kudin banza kudin wofi? Ke don ubanki kin manta yadda muka sha dabi da amaryar Abban mu?" ta kuta, “koda yake kina yarinya dama ya za ayi ki tuna? Ga kuma wata irin kwalwa ta kifaye da Allah ya halitta miki?" ta wani cuno baki gaba, “Na gaya miki yarinyar tana da kirki sam ba halinta daya da sauran matan da kike fada ba..." Saddiqa ta warci kofin dake kan mirror ta saita bakinta ta jefeta dashi Allah yasa ta kauce da sauri, da sai ya dauke mata hakoran gaba biyu, Saddiqa tace “banza mahaukaciya wadda bata san inda yake mata ciwo ba. Kina ta daga murya kina wani fadan cewa kin san yarinya, kin san halinta ko tasan naki halin? Tazo gidanki ta zauna ta gama sanin sirrinki dana gidanki ciki da bai, taga weakness dinki taga komi naki, taje ta gama damarar kwace miki miji daga hannun ki amma kina zaune hankalinki kwance har kina da confidence din daga min wannan bakin naki ki ce wai kin san halinta?" da alamu ko kadan maganganun Saddiqa basa shiga kunnen Mubeenah, tace “ke ce kika kasa fahimtata dai, ni nasan Abinda nake yi. Da wadda ban sani ba ai gwara wadda na sani, ko babu komi yarinyar tana da biyayya sau da kafa, hakan zai bani damar juyata yadda nake so!!" Saddiqa ta dafe kanta da hannuwa biyu kamar zata kurma ihu, Mubeenah ta kalleta cikin mamaki, “wai ni kam don Allah menene damuwar ki akan maganar auren nan, ke za a yiwa kishiya ko ni?" Saddiqa tace “Yi miki kishiya fa kamar yi mana ne, kin sani kamar yadda nima na sani, Ibrahim zama yake yi da ke kawai ba wai don yana jin dadin zama dake ba, kin sani" Mubeenah ta katse ta, “ni nasan Ibrahim yana so na" Saddiqa ta daka mata wata tsawa data sa tashi zaune dangargar akan duwawunta babu shiri, tace “ki min shiru Mubeenah!! Ke ce banza da kika kasa tantance so da dole, idan kika kuskura kishiya ta tako kafarta cikin gidan auren ki wallahi ina mai tabbatar miki da cewa kashin ki ya bushe, idan kin san ma'anar OUT to tsab zata yi waje dake kuma ina mai tabbatar miki da cewa idan har kika sa kafa kika bar gidan Ibrahim to ki tabbata cewa kinyi sallama da aure, I am as sure as hell babu wanda zai yi marmarin daukar ki a matsayin mata a yadda kike dinnan, wallahi Ibrahim kadai ne rufin asirinki" Mubeenah tace “Ibrahim yana so na, ku daina cewa wai baya so na, auren da zai yi babu abinda zai ragu daga son da yake yi min" Saddiqa ta juya ta kara juyawa a cikin dakin kamar wadda take fareti, “idan na gama da case din auren ki I'll make sure to take you to psychiatrist for sure. Amma kafin nan bari inje in samu Haja (mahaifiyar su) babu macen data isa ta shigo gidannan wallahi" ta sa kafa ta bar dakin fuuu a matukar fusace kamar guguwa, Mubeenah ta daga kafada ta koma ta kwanta abinta. Saddiqa na fita taci Karo da Abbu a tsakiyar falo, bata damu da cewa yaji maganganun su ba ko bai ji ba ta shura kafa ta bar gidan. Ya girgiza kan shi a hankali yana murmushi amma fa can kasan xuciyar shi ji yake murmushin yafi mishi madaci ciwo, zuciyar shi kamar ana diga masa ruwan dalma saboda yadda take azalzalar shi da kuna, me yafi ciwo irin kaji cewa matar aurenka bata kishin ka??
~So what did you think about today's chapter?
~Kuna tunanin akwai mata irin Mubeenah a cikin duniyar nan kuwa? Idan akwai, wane irin hukunci kuke ganin ya dace da ire-iren su??
#TeamAbbu
#OneLove
#AnaTare🤝🤝





*♡Jeedderh♡*
[1/1, 18:03] Hauwa-Jedderh💕: *NI DA ABOKIN BABA NA....!*


*©°•Jeedderh Lawals•°*



*46*



Na cewa Jalilah class mate dina, “ki wuce hostel kawai, akwai inda zan je" tace toh sai kin dawo. Har ta fara tafiya sai kuma
Showing 78001 words to 81000 words out of 122880 words