kuma in capital letter....... *"TOI ET MOI POUR TOUJOURS! (You And Me Forever!)"* Na danyi tsaki kadan, ban san me yasa Abbu yake son rubuta min abu da wani yare na aljanu ba, saboda Allah how in hell would I be able to understand what is written there?? Na kara jan tsaki naje na rataye frame din a jikin bango.





*♡Jeedderh♡*
[12/10, 20:45] 💖💖💖💖💖: *NI DA ABOKIN BABA NA....!*

*©°•Jeedderh Lawals•°*




*31*


*So I made a mistake in the previous Chapter... TOI ET MOI TOU POUJOURS means 'You and Me Forever' in French. TU ME MANQUES ne I Miss You in French, Hope you guys wouldn't mind??*

☆☆☆☆☆


Abinci nake ci amma gabadaya hankalina baya kan abincin na dai san kawai ina kwaso abinci da spoon ina saka shi a cikin bakina, tunanina ya tafi ga yadda Mommy take acting weird tun zuwan Abbu, no tun zuwan Hafsy ma. Bayan su Abbu sun tafi jiya, mun gama dinner kenan na shiga daki Mommy ta biyo bayana, sam babu alamun wasa a fuskarta ta kalleni, "Ummiey me ke tsakanin ku da Baban Hafsat?" na kalleta da sauri kuma cike da mamaki, tambaya ce mai sauki, haka kuma amsar ta ba mai wahala bace, amma me yasa naji kamar ba'a taba tambayana tambaya mai wahala irin wannan ba? Saboda ni a karan kaina ban san me ke tsakanin mu ba. Kai na girgiza mata, "Mommy me kika gani ne?" ta Harare ni, "Ummiey ba cewa nayi ki tambaye ni ba, amsa nake bukatar ji; Me Ke Tsakanin Ku Ke Da Baban Hafsat?" na danyi shrugging kafadata ina kokarin nuna babu komi, "me ke tsakanin mu kuwa Mommy? He's just Daddy's Friend, and I stayed with them for a while I think that's all!" tace "That's all?!" na jinjina mata kai cikin tabbatarwa, "yes!" tayi shiru tana kallona kafin ta sauke ajiyar zuciya, "ko ma dai Menene Ummiey, Ina fata zaki tsaya a iya inda Allah ya ajiye ki, and alakarku ta tsaya a haka Nafeesah, No more.... Bana son wani magana ya fita daga baya kina jina??" kallonta nake cike da mamaki, me ke damun Mom ne haka yau? Duk da hakan ban fasa daga mata kai ba, sai lokacin naga tayi murmushi. "good! Hurry up and go to bed then" nan ma Kai na sake gyada mata, "sure Mom, good night" tayi murmushi ta juya ta bar dakin tare da ja min kofa. Sosai maganganun Mom suka tsaya min a rai, ranar haka na kwanta ina nanata maganar ta, 'In tsaya a matsayin da Allah ya ajiye ni?? Kada wata magana ta sake fita bayan alakar mu ta yanzu? Tana nufin kenan ba zata amshi Abbu a matsayin miji na ba? 'Miji??' naji na sake maimaita kalmar., wa yace Abbu zai zama mijina? Ni kadai nake imagining komi a cikin raina ba tare da tunanin shi Abbu din me yake tunani ba. Ni kadai nake tunanika na na manta da cin amanar da nake shirin yi, to cin amana mana! Na zauna lafiya qalau da iyalan Abbu cikin mutunci da girmamawa, daga karshe kuma kawai sai aji na aure mai gida? Anya na kyautawa kaina dasu kuwa? Me zan ce musu to? Me zasu daukeni, maciya Amana ko me? Su Qaseem.......... Shit!!! Me zasu dauke ni yanzu? Suddenly naji wata irin kunyar kaina ta kama ni, I wasn't thinking straight and smart. Ni da Abbu belongs to different worlds, I think it's time for me to let him go., let my dreams scattered just like how I did with my first love; Muneer!! Zuciyata tayi zafi sosai, m really an unlucky being!! Me yasa ban taba samun nasara akan soyayya ba a rayuwata? I mean me na rasa? I am a very beautiful and attractive young lady in my twenties, ina da kyau ina da diri ina da duk abinda namiji yake bukata a jikin mace but why?? Why???.......

Ramlah ta dawo da hankalina cikin restaurant din ta hanyar jijjiga ni, "hey babe!! Come back to your senses!!" na zabura ina kallonta a tsorace kafin in Harare ta, "What?!" na fada almost shouting, tace "Ke zan tambaya, you were deep in a thought and you suddenly became teary, me ke faruwa dake ne yau?" na kai yatsa na dan taba idanuna, da gaske kuwa I was about to cry ga ruwan hawaye nan ya fara taruwa a idanuna. Ta rungume hannayenta a kirji tana kallona cike da tuhuma, na sauke kaina kasa kawai ina wasa da cokalina a cikin plate, I wasn't ready to discuss the matter with anyone a lokacin, I wanted to dealt with anything on my own don haka na share Ramlah kamar ban san abinda take nufi da hakan ba har sai data kai ga yin magana, "ba zaki magantu bane har sai na matse bakin ki?" na kalleta, "Ramlah am sorry ok? When I'm really, zamu yi maganar please!!" na fada pleadingly don nasan halinta zata iya takura ni, hakan kuwa daidai yake da saka kuka na a cikin restaurant din makarantar mu. Tace "da gaske?" na gyada mata kai, tace "ok, kar ya dade fa kin san bana son jira koh?" na sake gyada mata kai. Na dauki lemun exotic na pineapple na kai bakina, kamar ruwa haka na dinga zugar shi sai kwalin kawai na ajiye kasa. A tare muka mike muka fita daga restaurant din, muna fita naji Ramlah tana xunguri na a bayana, na harareta, baki ta tabe cikin gulma ta rada min "mutumin ki is coming" na kalli inda ta nuna min da idanunta, Muneer ne tafe shi da abokanan shi suna tahowa inda muke da alamu restaurant din zasu zo. Naji ana zancen auren shi da aka daura last week, personally ya turo min Invitation Card na bikin nashi amma a take na aika aka maida mishi Ita don ban ga abinda zan je inyi a wajen bikin ba. Tsaki naja na fara tafiya abina, Ramlah ta biyo bayana, muka yi clashing dasu amma Muneer ko glancing at our side bai yi ba. Na kara jan tsaki a raina nace "banza dan akuya!" satika uku da suka wuce he was still following me around like crazy yana begging dina akan in bashi second chance shine yanzu daga yin aure Sati daya yana share ni irin yaji dadin Amarya dinnan, na kara jan tsaki. As if I give a damn! Kamata yayi inji da damuwata ba wai ta wani Muneer ba. Hostel muka wuce ni da Ramlah saboda bamu da lectures ranar, next week zamu fara exams already mun yi covering lectures dinmu. Muna kan gadonta muna solving din wata problem a Calculus wayar ta tayi kara ta daga, ta dauki wayar ta kalli caller ID din, "Ni'ima ce" ta daga kiran tare da sakata a hands-free, "Guess what guys??" muryar Ni'imah ta doki kunnenmu cikin farinciki, muka hada baki wajen cewa "ya ne? Bamu mu sha please!" tace "umh.... Dama......" ta fara kauce kauce, Ramlah taja tsaki, "malama aiki muke yi idan ba zaki fada ba ki kashe wayar kawai" sai data gama kauce-kaucenta sannan tace "aure aka sa mana.... Nan da one month!!" "WHAT??!" muka fada cikin karaji in Unison.

"What the f**k! Wannan ai rashin mutunci ne Ni'imah" inji Ramlah tana hararar wayar kamar Ni'imar tana gabanta ne, nima nace "Lallai mu da aka raina ne sai yanzu ake fada mana, ba zan zo ba don ma kiji" Ramlah ma ta cafe nan ma muka hau korafe-korafe har sai da muka rasa abin cewa sannan muka yi shiru, Ni'imah dai saurarenmu kawai take yi, ina jiyo dariyar Sa'adiya daga background din wayar. Tace "duka-duka jiya ne aka yi abin fa!" muka yi kus, ta cigaba, "muma bamu yi zaton abun will be so soon ba kawai jin su muka yi Kun gane? Now na isar da sakon da zan isar shikenan, Kun dai san you guys are needed one week before a fara bikin ko?" muka yi dariya ni da Ramlah, "yeah of course, ai dole ne. Thank God we're finishing our exams nan da sati biyu" muka yi sallama dasu, littafin da muke karantawa muka maida gefe muka fara hirar yadda zamu gudanar da bikin, wannan hirar ita ta dauke min tunanina gabadaya akan maganar Mom da sauran su.

*****

Daddy ya kalleni, "yanzu Har Sati daya kawai saboda biki Uwata?" na turo baki gaba, "haba Daddy, su Ni'imah ne fa, kuma lokacin muna free tunda mun gama exams dinmu fa!" ya rausayar da kai, "ai shikenan! Allah ya kaimu" nayi tsalle akan kujera daga zaunen da nake ina clapping hannu, "nagode Daddy! That's why you're always the best!" na mishi thumbs up da duka hannuwana, yayi dariya. Naci gaba da duba littafin hannuna shi kuma ya cigaba da kallon tashar Sports. Can na tambayeshi game da DE form din da yace zai sa a cika min, yace "ni na ma manta wallahi. Bari zan sake yiwa Ibrahim Magana inji yadda ake ciki" nace "Daddy Abbu kuma? Me yasa shi? Ni da ABU nake so in cike?" yace "ba kya son zuwa BUK din ne, me yasa?" na turo baki na, "ni nafi so ina kusa daku Daddy yadda kullum ba zan sha wahalar ganin ku ba!" yayi dariya yace "Uwata kenan! To in kika yi aure kuma fa? Kin san dai dole ki bar gidan nan koh?" na sake turo wani bakin, Mommy ta shigo dakin hannunta dauke da plate wanda aka yanka fruits a ciki. Ta kalleni kafin ta maida kallonta ga Daddy, "Habibty ina fata ba gulma ta kuke yi ba koh?" Daddy yace "mun isa! Diyar ki ce take zancen bata so ta rabu damu" Mommy ta ajiye plate din a tsakiyar dakin duk muka sauka kan carpet tace "Rabuwa kuwa ai ya zama dole tunda dai ke diya mace ce kuma Aure zaki yi" 'Ai fa an tabowa Mommy inda yake mata kaikayi' na fada a cikin raina, kwana biyun nan dama Mommy kamar mai jira, da an danyi magana zata hau zancen aure da waye da waye. Sai da muka cinye fruits din tas na dauke plate din tare da musu sai da safe, na kai plate din kicin kafin na wuce dakina nayi shirin kwanciya barci. Na budo hoton Abbu a cikin gallery dina ina kallo kamar yadda ya zama Al'adar rayuwata kowane dare, na janye idanuna daga kan hoton nashi na maida su kan frame din daya bani. Ban san meye dalilin da yasa ya bani frame din ba, ban san me yasa nake jin wani irin warmness da calmness a tare dani a duk lokacin dana kalli frame din ba. Koma dai menene na yanke shawarar janye Idanuna da Zuciyata daga kan Abbu. We didn't Deserve Each Other.





*♡Jeedderh♡*
[12/11, 20:53] 💖💖💖💖💖: *NI DA ABOKIN BABA NA....!*

*©°•Jeedderh Lawals•°*




*32*



Harith yayi parking motar shi a kofar gidanmu, da yake ya dawo tun last week. Yau tsokana muka fita, gidan su Ikram budurwar shi muka je da yake itama tazo hutu. Har kofar gidansu muka je aka mata sallama ta fito da saurinta ita ala dole masoyinta yazo, yadda tayi turus ganina akan motar shi ina wasa da keys din motar shi sai daya kusa bata mana budget, kaina na kawar gefe ina boye dariyar data kama ni. Haka ta daure ta karaso wajenmu muka gaisa Harith ya gabatar dani a matsayin sister dinshi, suka dan fara hira da ita, mintuna biyar basu cika ba na kalli Harith ina hamma nace "Hari, mu tafi gida!" da sauri ya mata sallama muka shige mota muka tafi, tana tsaye a inda take har muka bar layin. Dariyar abun muke yi har muka shiga gida kamar wasu sabbin mahaukata. Idanuna suka tsaya cak akan Abbu dake zaune akan fararen kujeru inda Daddy ya saba zama yana shan iska ko karatun jarida mostly on weekends. Kamar koda yaushe, babu abinda ya canza daga bugun da zuciyata take a duk lokacin dana ganshi, rawar da kafafuna suke da wani irin doki daya mamaye ni, makaman yakin dana tanada domin yakar zuciyar dake kayata min Abbu naji sun min nauyin dauka. Idanunshi fes akan mu suke, na kalli Harith a nutse nace "ina xuwa" ya gyada min kai. A hankali na fara tafiya zuwa inda yake zaune, kafafuna rawa suke yi saboda yadda nake jin idanun shi masu kaifi a kaina, da taimakon Allah dai na karasa inda yake. Na dan duka a hankali nace "Abbu barka da yamma" ya gyada kai, "barka dai Nafeesah. Daga ina haka?" na rasa abinda zan ce mishi saboda ba makaranta naje ba saboda ranar bamu yi exams ba, nace "mun dan fita ne" ya kalli kofar da Harith ya bi ya shiga falo ya kara kallona fuskar shi dauke da wani irin kallo daya kada min sassan jiki, "and who is he??" nima na kalli kofar, nasan da Harith yake, nace "Harith...." na rasa abin cewa saboda yadda idanunshi suke zagaye fuskata gabadaya sun dauke min kuzari, ganin nayi shiru babu amsa ya gyada kai, "well dama naso ganin Daddyn ki ne shi yasa na zauna jiran shi nayi zaton zai dawo da wuri don na biya ta ofishin shi baya nan, but bana tunanin zan cigaba da jira kam. Zan kira shi kawai" ya tashi yana gyara wuyan rigar shaddar daya saka, ya kalleni har zuwa lokacin normal kallonshi bai dawo ba, yace "Kano na nufa yanxu in shaa Allah. Nan da sati daya zaki zo bikin su Ni'imah koh?" na gyada mishi kaina a hankali, yace "good! Sai mun hadu kenan" ya fara tattaki xuwa inda ya ajiye motar shi, na samu kaina da take mishi baya har gaban motar. Ya saka makulli ya bude motar ya shiga ya kunna, sai lokacin ya juyo ya kalleni yana dan murmushi, Ya Allah! Da ba dan motar shi dana rike da hannuna ba da babu abinda zai hana ni faduwa a lokacin, na rasa irin effect din da Abbu yake dashi a tare dani. Yace "so??" nayi saurin kallonshi saboda gabadaya hankalina ya dauke daga gare shi, nayi saurin daidaita natsuwata nace "Allah ya sauke ka lafiya Abbu, a gaida su Anty Mubeenah da Hafsy" yayi murmushi wannan karon genuinely wanda tunda yaxo sai lokacin naga murmushin shi irin haka, yace "Ameen Nafeesah, zasu ji in shaa Allah!" yaja motar shi ya tafi nima na wuce cikin gida, a bakin kofa muka ci karo da Harith zai fito, yana gani na yace "sai anjima koh babe?" na harare shi ya danyi dariya saboda yasan na tsani sunan, ya wuce abinshi ni kuma na shige gida. Sai dana biya ta dakin Mommy na gaya mata na dawo, ta kalleni fuskarta babu yabo babu fallasa, "kin ga Baban Hafsat a waje kuwa?" gabana ya dan fadi, Allah dai yasa ba wani fadan zan sha ba. Nace "ehh, ya ma tafi ai" Mommy ta kalleni cikin tuhuma, na sadda kaina kasa ina wasa da jakar hannuna, tace "na tambaye ki abinda ke tsakaninku kin ce babu komi, yanzu kuma me ya kawo shi wajen ki?" na kalleta da sauri, "ni fa ba wajena yazo ba wajen Daddy yazo, ya gaji da jiran dawowar shi ne shi yasa ya tafi" tace "haka ya gaya miki?" nace "ehhh, ba haka bane?" ta dan harare ni na kauda kaina, tace "shi kenan je ki" kamar jira nake yi dama, da sauri na bar mata dakin na wuce nawa ina ajiye numfashi a hankali. Duk yadda Tunanin Abinda Mommy take nufi da Tunanin makomar rayuwata da Abbu suka so dabaibaye ni haka naki basu dama, na dage da karatun exams sosai. Cikin ikon Allah cikin sati daya muka gama exams dinmu, cikin lokacin mun kara zuwa gidan su Ikram sau biyu. Wato idan na tuno diramar da muka buga a zuwanmu na karshe gidansu dariyar dake kama ni koh??

Sai ana washegari a fara harkokin bikin su Ni'imah sannan na tafi Kano. Gidan Anty Ameenah muka sauka directly saboda a can amaren suke zaman biki, su Hafsy suka fito suka min oyoyo yaran sun wani kara girma, ban taba sanin nayi kewar su sosai ba sai dana dora idanuna a kansu. Qaseem ne ya dauki jakar hannuna na kama hannun Hafsy Abdullahi ya biyo mu a baya muka shiga gidan. Tarbar dana samu daga Anty Ameenah ta bani mamaki, har uwar dakinta ta kaini inda na samu su Anty Raliya da wasu abokan su, na gaida su suka amsa Anty Raliya na min korafin na tafi babu sallama ni dai nawa bada hakuri ne kawai don nasan cewa m at fault. Na shiga bandakin ta na watsa ruwa na fito nayi sallar Laasar, kafin in gama har an shirya min abinci a tsakiyar dakin ina gamawa na zauna na fara ci. Sai dana gama sannan aka kaini inda amaren suke. Dakine guda
Showing 51001 words to 54000 words out of 122880 words