da kitsawa Mubeenah abubuwa har yamma ta gabato sannan ta mata sallama ta tafi bayan ta kwashi manyan atamfofi biyu da lesuna cikin kayan da aka kaiwa Mubeenah na fadar kishiya bayan ta gama kwashe musu albarka, ji fa!. Mubeenah ta dawo daga rakiyar ta ta tsaya ta leka dakin Abbu, tun jiya daya dawo daga gidan Nafeesah ya leka ya gaya mata ya dawo tare da fada mata ya raba musu girki kwanaki bibbiyu bata sake ganin shi ba. Yanzu ma baya nan gashi akwai maganganu da take so suyi.
Dakinta ta koma, magungunan da Saddiqa ta kai mata suna zube akan gado, ta zauna a gefen gado tare da kura musu idanu kamar wadda take muhawara, ta saki ajiyar numfashi tare da tashi tsam ta dauki magungunan. Toilet ta shiga ta zazzage su a cikin masai tare da yin flushing, dama turaren data kai mata Harira ta ba ta jefa shi cikin kwatami. Daya daga cikin manyan abubuwa da Mubeenah bata so kuma bata ma yarda dasu ba shine bin malamai da bokaye, tana mamakin yadda mata suke yarda da karerayi da soki-burutsun bokaye da malamai, a ganinta in kura na maganin zawo to tayi wa kanta mana?? Shi yasa tasu ta matukar zuwa daya da Shakira kanwar su, sam bata cikin harkar bin malaman da sauran en uwansu suke yi, ta kan ce ita tafi ganewa tayi yaki akan abu ta yadda idan ta mallakeshi zata yi alfahari da cewa saida ta share zufa ta sha wahala kafin ta same shi ba wai a ruwan sanyi ta hanyar bokaye da yan tsibbu ba, kuma gaskiyarta.
Tunda gari ya waye take leke-leke da zarya daga falo zuwa dakinta. Ta kula kwata-kwata ya daina zama a cikin gidan, tana mamakin inda yake zuwa cikin kwanaki biyun daya mata. Tana nan zaune a daki taji tashin muryoyin su dasu Qaseem wadanda suke hutun makaranta ranar, Sai data ji shiru alamun ya shiga dakinshi sannan ta tashi tsam!.
“ok baby sai na iso, kar ki manta anjima da yamma dai zamu fita in fara koya miki tuki" na danyi tsalle daga zaune din da nake, “yeyh! Abbu na, sai kazo. Please ka taho da wuri fa!" yayi er dariya, “missing me that much??" dariya kawai nayi na kashe wayar. Shima dan murmushi yayi ya ajiye wayar yaci gaba da shirya takardu a cikin brief case din shi.
‘Baram!! Karan sautin turo kofar dakin nashi kenan kamar tashin duniya. Tun kafin ya juya yasan ko waye ya shigo, haka take shigowa dakin babu knocking balle sallama, kofar dakin ma haka take turo ta, duk ranar data shigo a hankali to ranar nema take a wajen shi.
Bata yi magana ba ta coge a bakin kofa, shi kuwa yaki daga kai ya kalleta yaci gaba da abinda yake yi har ya gama ya rufe brief case din. Wardrobe ya bude ya fara ciro kaya, ta kankance idanu cike da masifa ganin yadda yake abubuwan shi kamar bai san da Allah yayi ruwan tsirarta a cikin dakin ba.
“Ibrahim! Ina so muyi magana da kai!" ta fadi kanta tsaye cikin izza, ya juya a hankali tare da kallonta. Wani malulun bakin ciki da bacin rai suka kawo mishi wuya, wasu pyjamas ne a jikinta daga ganinsu sun dauki lokuta ba a wanke ba, ta kawo wata hular beanie ta maka a kanta fara ce amma tayi bakikkirin ta dafe alamun ta kwana biyu, gashin kanta da yayi cukus-cukus a cikin hular ya maida ta kamar irin sababbin kamun nan. Ya hade fuska sosai wadda tasa ta shiga hankalinta ba shiri amma hakan bai hanata yin dibar albarkar data kawo ta ba. “Ibrahim mai kake nufi da nine, an kawo amarya ban ga kalarta ba, ka kama ka killace ta a waje guda saboda ita er goal ce, er nasiha ta hadin kai da naji mazaje na hada matansu waje guda su musu kai baka yi hakan ba, ka dawo daga gidanta kaxo nawa amma har ka gama kwanakin ka amma sau daya na saka ka a cikin idanuna, anya Ibrahim baka dauko hanyar da amaryar ka zata raina ni ba kuwa??" ya jingina da jikin wardrobe din yana watsa mata kallon uku-taro, sai data dire aya sannan ya ajiye numfashi, “killace amarya kamar yadda kika ce nayi sabida ta kai matsayin a killace ta dinne, Nafeesah ba er gwal bace er diamond ce Mubeenah. Kawo amarya gidanki damka amana ni na hana saboda ban ga dalili ba, ke kanki ya kike kula da taki rayuwar balle har ki kula da rayuwar er wasu? Maganar rashin gani na da baki yi ina ji kin manta ne, dama can muna daukar satika ma bamu ga juna ba alhalin muna gida daya yanzun ma ina ga ai bata canza zane ba koh?" tayi tsuru tana zare idanu, maganar daya fada haka take, ita kanta bata san dalilin sako maganar ba, kawai maganar has been eating her brain ne dole ta fade ta ko ta samu sawaba.
Tayi gyaran murya tare da cewa “whatever! Amma kasan dai saboda Allah baka kyauta ba, kuma naji ance ka sai mata manyan motoci har guda biyu bayan ni ka bar ni da tsohuwa ina fama, tun kafin tafiya tayi nisa zaka fara shimfida rashin adalcin da ake cewa dama a jinin ku maza yake?" yayi murmushi cike da takaici, dama yasan duk inda zata je ta dawo dai maganar kenan. Ya daga kafada, “mota yeah, ni na sai mata daya Daddyn ta ya sai mata daya, ina ce kema lokacin da aka kawo ki an sai miki mota?" “karya ne!" ta fadi cikin hargowa, “karya kake yi kai ka sai mata, motar da kake fada ai Mahaifinka ne ya sai min da kudinshi ba naka ba mai ya hana kai ka saya min da kudin ka ko kuma yanzu daka sai mata nima ka sai min idan ba rashin adalci ba??"
Ranshi ya baci sosai, ya sha daukar fiye da haka daga wajen Mubeenah, ya sha jin munanan kalmomi daga gareta duk yana shanyewa amma yau baya jin zai iya shanyewa. Yana da hakuri sosai, sai dai duk ranar da aka kai shi bango akwai matsala. Tun daga tsawar daya daka mata Mubeenah tasan cewa ranar ta tsallake layin hakurin Abbu. Idanunshi sun juye saboda bacin rai, “enough Mubeenah! Ya ishe ki, ya ishe ni haka nan. Mota bani na sai mata duka biyu ba amma da ace idan nayi hakan Nafeesah zata karba happily da wallahi sai na sai mata fiye da mota biyu. Kin san saboda me? Saboda Ina Son Ta!! Saboda tana kula da farin cikina, saboda ita kadai nake kallo in san cewa yes! Ina da mata, in san cewa akwai wani da zan ba umarni kai tsaye yayi, akwai wadda bata zartar da komi sai da yawuna, akwai wadda zan bugi kirji ince Matata ce in kuma nuna ta a koina cikin duniyar nan ba tare da fargabar zata muzanta ni ba. Saboda ita kadai ce take bani hakkina ba tare da na biya ta ko sisi ba, saboda itace matar da nake sa ran zata haifa min yara ta kuma shayar dasu ba tare dana biya ta kudin shayarwa ba!! Saboda... Nafeesah itace komi nawa!! Zaki ga laifina idan na sayi jirgin sama na damkawa wannan matar kuwa?".
Mubeenah tayi shiru kanta a kasa, tunda take dashi bai taba mata ihu irin na ranar ba, bai taba daga murya kamar haka ba, duk abubuwan daya fada ta aikata har da ma wadanda bai fada ba duk tayi kuma sun faru, kalma daya data doke ta... “Kana Son ta?? Ni fa?! That means baka so na kenan?" without second thought ya gyada mata kai, “kwarai Mubeenah! Ni dake duk mun san cewa zaman hakuri da zaman ‘ya‘yanmu muke yi, amma zancen ‘so' kin san cewa babu shi a tsakaninmu" ta fara girgiza kai, bai jira mai zata sake ce mishi ba ya warci brief case dinshi a fusace ya ratsa ta gefenta zai fita, kofar dakin ma ko albarkacin ta rufe ta bata samu ba, tsoron shi daya Allah yasa cikin yaran babu wanda yayi over hearing din conversation dinsu yasan may be ya saka confusion a cikin kansu. Ranshi ya kara baci da wannan tunanin, daga bayan shi ya juyo muryarta a kausashe “Nafeesah!...." tun ma kafin ta gama fadin abinda tayi niyya ya juyo a fusace, “don't you ever dare drag her into this, ba irinki bace ita saboda haka ke kici gaba da laluben duniya ki barta taci gaba da laluben lahirar ta!" ya juya a fusace ya bar gidan zuciyar shi na azalzalarshi cike da bacin rai ko sallama bai wa yaran nashi ba da suke dakinsu suna kallo.
Mubeenah ta bishi da kallo cikin bacin rai na maganganun daya yaba mata yanxu, fargaba da tsoron anya bata bari kwabarta tayi ruwa ba kuwa? Dana sanin ina ma tayi amfani da magungunan da Saddiqa ta kawo mata???
******
Muna gama waya dashi falo na koma ina jiran karasowar shi. Ina cikin zaman jiran ne Zaynab ta fito daga dakin dana ware mata a sukwane tana ihu, “Anti Nafeesah.... Anty Sadiya ta haihu yanzu!!" nayi ihun nima tare da direwa cikin murna, sai da muka gama iface-ifacen na tambayeta abinda ta haifa tace Mace. Ba bata lokaci ta shirya ta tafi ganin baby. Na zauna ina jiran dawowar Abbu impatiently ina jin kamar inyi fuffuke inje inda suke. Ina dakina ina canza kaya daga shigar da nayi ta wani mini daya tsaya min a gwiwa da half vest mai hannu daya ta taryar Abbu zuwa riga da zani na atamfa, ban san ya dawo gidan ba sai dana leka waje naga motar shi a fake sannan. Abin ya bani mamaki, nayi tunanin zai shigo dakina direct idan bana falon kamar yadda yake yi, ban kawo komi a raina ba na nufin dakin da saurina cike da doki. Na tura kofar ko sallama doki bai bani damar yi ba na fara zuba mishi bayanai, “Abbu yanxu Sadiya ta haihu, kazo ka kaini in ga baby ka ji??" kwance yake yayi rub da ciki ya tura kan shi cikin filo, na zauna a gefen gadon ina dan jijjiga shi alamun ya tashi, “Abbu.... Abbu kaji?" nan ma shiru babu magana, ban sani ba common sense ne ya dauke min ko kuwa? Ban yi tunanin ina takura mishi ba ko barci yake yi naci gaba da jijjiga shi, “Abbu kazo ka kaini in ga baby kaji? Abbu??"
Juyowa yayi a fusace, cikin muryar dake hauhawa da bacin rai yace “Oh God Nafeesah!! Will you please just shut up and leave me alone??" jikina yayi sanyi ganin yadda fuskar shi take cike da bacin rai, “amma Abbu.." na fara magana in protest, “leave me alone!!" ya fada cikin karaji, sai kuma naga ya dafe kanshi da sauri, ya lumshe idanunshi na en sakanni kafin ya bude su, “please!!" ya fadi cikin sanyin murya wannan karon. Jiki na rawa na tashi na fita daga dakin ina tambayar kaina me ya hau kan shi??
Kujera na laluba na zauna cikin tsananin sanyin jiki, ban iya daurewa kwallar data taran min ba sai data gangaro kan kumatuna, gabadaya sai na dora laifin fushin Abbu a kaina. Watakila ni na dame shi da hayaniya har ranshi ya baci, kila barci yake yi na tashe shi da hayaniya kun san yadda mutane kan zama moody idan sun tashi daga barci balle shi da naje ina jijjigawa abinda Anty Shafa tace mata basa tashin mazajen su daga barci ta wannan hanyar. Ko kuma yana bukatar kadaici ne ni kuma ban kula da hakan ba? Idan haka ne kuwa ai laifi na ne. Tashi na sake yi na koma dakin, lekawa nayi kamar munafuka wannan karon yayi rigingine, na shiga dakin a hankali tare da maida kofar na rufe, barci yake yi. A hankali na dauki bargo na rufa mishi, na juya kenan naji an riko hannuna na juya da sauri. Ya bude idanunshi da suka shige ciki har sun canza kala ya kalleni dasu, take naji wani irin bacin rai na shige ni. Na samu kaina da tuhumar kaina da responsibility na bacin rai da yake ciki, a hankali nace mishi “kayi hakuri Abbu!" janyo ni yayi na fada kan gadon tare da jana jikinshi ya rungume ni, ina jin yadda zuciyar shi take bugawa da sauri, yace “noo, am sorry! I shouted at you bayan baki yi mun laifin komi ba" na kwantar da kaina akan kirjinshi ina shafa saitin zuciyar shi da hannuna, “Allah ya huci zuciyar ka Abbu na. Wanda ya bata maka rai bai kyauta min ba ni kam tunda nima yasa nawa ran ya baci" kuma gaskiya na fada, raina ya baci kwarai daga ganin bacin ran dake dankare akan fuskar shi. Yayi dan murmushi tare da jan bargo ya rufe mu dashi muka shiga barci.
Koda muka tashi ran shi wasai babu bacin rai a tattare dashi. Da yamma na lallaso shi da kyar muka je gidan Sadiya muka ga baby don da cewa Yayi wai ya za ayi in fara fita ina amaryar sati daya? Da kyar da jibin goshi ya bar ni bayan na dauki alkawarurruka da dama wadanda sirrin mu ne, daga can muka wuce ya fara koya min mota sai gab da magrib muka koma gida. Kwana biyu da yin haka visar mu ta fita kasashen ketare yawon bude ido (honey moon) ta fita. Da kaina na zauna na fitar da kasashe biyar wadanda nake matukar so da burin ziyarta a rayuwata. Muka fara shirye-shiryen tafiya amma fa bayan anyi sunan Sadiya.
~Daga yanzu ba zaku dinga ganin posting dina akai-akai ba gaskiya, mun koma school kuma things are somehow... Kun dai san lamurran en makaranta ina fata za ayi mun uziri?
#TeamAbnaf
#AnaTare
A rana ta uku da haihuwar na kara komawa gidan Sadiya daga can bayan Abbu yaje ya dauke ni da dare muka biya ta can babban gida gidan su Abbun muka gaida iyayen shi, Hajiya Siyama mutuniyar kirki ta amshe mu da hannu bibbiyu har da dan guntun fadanta wai me yasa ya barni na fara fita yanzu? Har tana karawa da cewa wai ai su a zamanin su amarya sai tayi rabin shekara kafarta bata taka kofar gidanta ba., na kama baki a raina na kara da lallai kuwa! Bayan mun gaisa ta saka mana albarka muka wuce sashen Hajja Fati itama muka gaida ta. Nan ta hada ni dasu tarkacen daddawa da sauran su. Mahaifinsu kuwa kwaryar zuma farar saka mai kyau ya bani, daga nan muka juya gida hannu riki-riki da tsaraba.
Ranar sunan kuwa da safe na tafi. Muna ta ayyuka da tsare-tsaren wajen da baki zasu zauna bayan falo. Sai bayan la'asar su Anty Mubeenah suka iso gidan ita da yaranta lokacin muna can bayan gidan muna suyar samosa wadda ake ba baki.
Ni'imah data kai wa su Anty Ameenah wadda muka soya ta dawo, ta daddabo ni tare da rada min “ga fa uwargidan ki can tazo!" naji kamar zuciyata zata faso kirjina saboda bugawar da tayi, ganin yadda nayi kuru-kuru da ido yasa tayi dariya, “haba babe cool mana, sai kace wadda zata cinye naman jikin ki?" nayi murmushin yake kawai.
Ni'imah ba zata gane halin da nake ciki ba, ba wai tsoron Anty Mubeenah nake ji ba, kawai ina fargabar yadda karon mu da ita zai kasance a matsayina na matar Abbu-Mijinta a halin yanzu, nasan ko kallon banza ba zan samu ba wannan karon, fatana daya mu rabu da ita lafiya ba tare da rayuka sun baci ba. Don haka nayi gefe daya da tunanin naci gaba da rolling din da nake yi.
Har inda muke Hafsy ta lalubo ni, nan ta zauna tana ta zuba min labarai har muka gama, aka shiga da wadanda muka yi ciki mu kuma muka shiga BQ muka yi wanka muka gyara jikinmu.
Wata uwar sun shadda muka saka a matsayin ankon suna, dark purple ta sha aikin pink din zare, Ya Allah! Zo kuga yadda na fita a cikin kayan nan. Kyawuna ya fita sosai kamar ka sace ni ka gudu, muka tsaya muka dan karkashe flashes kafin muka koma cikin gida. Bayan dogon hesitating da tunanin zanyi ko ba zan yi ba, daga karshe dai nayi sallama dakin maijego na shiga cikin dakiya duk da cewa zuciya na wani mayen tsere take yi a cikin kirjina.
Ina shiga muka
Showing 99001 words to 102000 words out of 122880 words
Dakinta ta koma, magungunan da Saddiqa ta kai mata suna zube akan gado, ta zauna a gefen gado tare da kura musu idanu kamar wadda take muhawara, ta saki ajiyar numfashi tare da tashi tsam ta dauki magungunan. Toilet ta shiga ta zazzage su a cikin masai tare da yin flushing, dama turaren data kai mata Harira ta ba ta jefa shi cikin kwatami. Daya daga cikin manyan abubuwa da Mubeenah bata so kuma bata ma yarda dasu ba shine bin malamai da bokaye, tana mamakin yadda mata suke yarda da karerayi da soki-burutsun bokaye da malamai, a ganinta in kura na maganin zawo to tayi wa kanta mana?? Shi yasa tasu ta matukar zuwa daya da Shakira kanwar su, sam bata cikin harkar bin malaman da sauran en uwansu suke yi, ta kan ce ita tafi ganewa tayi yaki akan abu ta yadda idan ta mallakeshi zata yi alfahari da cewa saida ta share zufa ta sha wahala kafin ta same shi ba wai a ruwan sanyi ta hanyar bokaye da yan tsibbu ba, kuma gaskiyarta.
Tunda gari ya waye take leke-leke da zarya daga falo zuwa dakinta. Ta kula kwata-kwata ya daina zama a cikin gidan, tana mamakin inda yake zuwa cikin kwanaki biyun daya mata. Tana nan zaune a daki taji tashin muryoyin su dasu Qaseem wadanda suke hutun makaranta ranar, Sai data ji shiru alamun ya shiga dakinshi sannan ta tashi tsam!.
“ok baby sai na iso, kar ki manta anjima da yamma dai zamu fita in fara koya miki tuki" na danyi tsalle daga zaune din da nake, “yeyh! Abbu na, sai kazo. Please ka taho da wuri fa!" yayi er dariya, “missing me that much??" dariya kawai nayi na kashe wayar. Shima dan murmushi yayi ya ajiye wayar yaci gaba da shirya takardu a cikin brief case din shi.
‘Baram!! Karan sautin turo kofar dakin nashi kenan kamar tashin duniya. Tun kafin ya juya yasan ko waye ya shigo, haka take shigowa dakin babu knocking balle sallama, kofar dakin ma haka take turo ta, duk ranar data shigo a hankali to ranar nema take a wajen shi.
Bata yi magana ba ta coge a bakin kofa, shi kuwa yaki daga kai ya kalleta yaci gaba da abinda yake yi har ya gama ya rufe brief case din. Wardrobe ya bude ya fara ciro kaya, ta kankance idanu cike da masifa ganin yadda yake abubuwan shi kamar bai san da Allah yayi ruwan tsirarta a cikin dakin ba.
“Ibrahim! Ina so muyi magana da kai!" ta fadi kanta tsaye cikin izza, ya juya a hankali tare da kallonta. Wani malulun bakin ciki da bacin rai suka kawo mishi wuya, wasu pyjamas ne a jikinta daga ganinsu sun dauki lokuta ba a wanke ba, ta kawo wata hular beanie ta maka a kanta fara ce amma tayi bakikkirin ta dafe alamun ta kwana biyu, gashin kanta da yayi cukus-cukus a cikin hular ya maida ta kamar irin sababbin kamun nan. Ya hade fuska sosai wadda tasa ta shiga hankalinta ba shiri amma hakan bai hanata yin dibar albarkar data kawo ta ba. “Ibrahim mai kake nufi da nine, an kawo amarya ban ga kalarta ba, ka kama ka killace ta a waje guda saboda ita er goal ce, er nasiha ta hadin kai da naji mazaje na hada matansu waje guda su musu kai baka yi hakan ba, ka dawo daga gidanta kaxo nawa amma har ka gama kwanakin ka amma sau daya na saka ka a cikin idanuna, anya Ibrahim baka dauko hanyar da amaryar ka zata raina ni ba kuwa??" ya jingina da jikin wardrobe din yana watsa mata kallon uku-taro, sai data dire aya sannan ya ajiye numfashi, “killace amarya kamar yadda kika ce nayi sabida ta kai matsayin a killace ta dinne, Nafeesah ba er gwal bace er diamond ce Mubeenah. Kawo amarya gidanki damka amana ni na hana saboda ban ga dalili ba, ke kanki ya kike kula da taki rayuwar balle har ki kula da rayuwar er wasu? Maganar rashin gani na da baki yi ina ji kin manta ne, dama can muna daukar satika ma bamu ga juna ba alhalin muna gida daya yanzun ma ina ga ai bata canza zane ba koh?" tayi tsuru tana zare idanu, maganar daya fada haka take, ita kanta bata san dalilin sako maganar ba, kawai maganar has been eating her brain ne dole ta fade ta ko ta samu sawaba.
Tayi gyaran murya tare da cewa “whatever! Amma kasan dai saboda Allah baka kyauta ba, kuma naji ance ka sai mata manyan motoci har guda biyu bayan ni ka bar ni da tsohuwa ina fama, tun kafin tafiya tayi nisa zaka fara shimfida rashin adalcin da ake cewa dama a jinin ku maza yake?" yayi murmushi cike da takaici, dama yasan duk inda zata je ta dawo dai maganar kenan. Ya daga kafada, “mota yeah, ni na sai mata daya Daddyn ta ya sai mata daya, ina ce kema lokacin da aka kawo ki an sai miki mota?" “karya ne!" ta fadi cikin hargowa, “karya kake yi kai ka sai mata, motar da kake fada ai Mahaifinka ne ya sai min da kudinshi ba naka ba mai ya hana kai ka saya min da kudin ka ko kuma yanzu daka sai mata nima ka sai min idan ba rashin adalci ba??"
Ranshi ya baci sosai, ya sha daukar fiye da haka daga wajen Mubeenah, ya sha jin munanan kalmomi daga gareta duk yana shanyewa amma yau baya jin zai iya shanyewa. Yana da hakuri sosai, sai dai duk ranar da aka kai shi bango akwai matsala. Tun daga tsawar daya daka mata Mubeenah tasan cewa ranar ta tsallake layin hakurin Abbu. Idanunshi sun juye saboda bacin rai, “enough Mubeenah! Ya ishe ki, ya ishe ni haka nan. Mota bani na sai mata duka biyu ba amma da ace idan nayi hakan Nafeesah zata karba happily da wallahi sai na sai mata fiye da mota biyu. Kin san saboda me? Saboda Ina Son Ta!! Saboda tana kula da farin cikina, saboda ita kadai nake kallo in san cewa yes! Ina da mata, in san cewa akwai wani da zan ba umarni kai tsaye yayi, akwai wadda bata zartar da komi sai da yawuna, akwai wadda zan bugi kirji ince Matata ce in kuma nuna ta a koina cikin duniyar nan ba tare da fargabar zata muzanta ni ba. Saboda ita kadai ce take bani hakkina ba tare da na biya ta ko sisi ba, saboda itace matar da nake sa ran zata haifa min yara ta kuma shayar dasu ba tare dana biya ta kudin shayarwa ba!! Saboda... Nafeesah itace komi nawa!! Zaki ga laifina idan na sayi jirgin sama na damkawa wannan matar kuwa?".
Mubeenah tayi shiru kanta a kasa, tunda take dashi bai taba mata ihu irin na ranar ba, bai taba daga murya kamar haka ba, duk abubuwan daya fada ta aikata har da ma wadanda bai fada ba duk tayi kuma sun faru, kalma daya data doke ta... “Kana Son ta?? Ni fa?! That means baka so na kenan?" without second thought ya gyada mata kai, “kwarai Mubeenah! Ni dake duk mun san cewa zaman hakuri da zaman ‘ya‘yanmu muke yi, amma zancen ‘so' kin san cewa babu shi a tsakaninmu" ta fara girgiza kai, bai jira mai zata sake ce mishi ba ya warci brief case dinshi a fusace ya ratsa ta gefenta zai fita, kofar dakin ma ko albarkacin ta rufe ta bata samu ba, tsoron shi daya Allah yasa cikin yaran babu wanda yayi over hearing din conversation dinsu yasan may be ya saka confusion a cikin kansu. Ranshi ya kara baci da wannan tunanin, daga bayan shi ya juyo muryarta a kausashe “Nafeesah!...." tun ma kafin ta gama fadin abinda tayi niyya ya juyo a fusace, “don't you ever dare drag her into this, ba irinki bace ita saboda haka ke kici gaba da laluben duniya ki barta taci gaba da laluben lahirar ta!" ya juya a fusace ya bar gidan zuciyar shi na azalzalarshi cike da bacin rai ko sallama bai wa yaran nashi ba da suke dakinsu suna kallo.
Mubeenah ta bishi da kallo cikin bacin rai na maganganun daya yaba mata yanxu, fargaba da tsoron anya bata bari kwabarta tayi ruwa ba kuwa? Dana sanin ina ma tayi amfani da magungunan da Saddiqa ta kawo mata???
******
Muna gama waya dashi falo na koma ina jiran karasowar shi. Ina cikin zaman jiran ne Zaynab ta fito daga dakin dana ware mata a sukwane tana ihu, “Anti Nafeesah.... Anty Sadiya ta haihu yanzu!!" nayi ihun nima tare da direwa cikin murna, sai da muka gama iface-ifacen na tambayeta abinda ta haifa tace Mace. Ba bata lokaci ta shirya ta tafi ganin baby. Na zauna ina jiran dawowar Abbu impatiently ina jin kamar inyi fuffuke inje inda suke. Ina dakina ina canza kaya daga shigar da nayi ta wani mini daya tsaya min a gwiwa da half vest mai hannu daya ta taryar Abbu zuwa riga da zani na atamfa, ban san ya dawo gidan ba sai dana leka waje naga motar shi a fake sannan. Abin ya bani mamaki, nayi tunanin zai shigo dakina direct idan bana falon kamar yadda yake yi, ban kawo komi a raina ba na nufin dakin da saurina cike da doki. Na tura kofar ko sallama doki bai bani damar yi ba na fara zuba mishi bayanai, “Abbu yanxu Sadiya ta haihu, kazo ka kaini in ga baby ka ji??" kwance yake yayi rub da ciki ya tura kan shi cikin filo, na zauna a gefen gadon ina dan jijjiga shi alamun ya tashi, “Abbu.... Abbu kaji?" nan ma shiru babu magana, ban sani ba common sense ne ya dauke min ko kuwa? Ban yi tunanin ina takura mishi ba ko barci yake yi naci gaba da jijjiga shi, “Abbu kazo ka kaini in ga baby kaji? Abbu??"
Juyowa yayi a fusace, cikin muryar dake hauhawa da bacin rai yace “Oh God Nafeesah!! Will you please just shut up and leave me alone??" jikina yayi sanyi ganin yadda fuskar shi take cike da bacin rai, “amma Abbu.." na fara magana in protest, “leave me alone!!" ya fada cikin karaji, sai kuma naga ya dafe kanshi da sauri, ya lumshe idanunshi na en sakanni kafin ya bude su, “please!!" ya fadi cikin sanyin murya wannan karon. Jiki na rawa na tashi na fita daga dakin ina tambayar kaina me ya hau kan shi??
Kujera na laluba na zauna cikin tsananin sanyin jiki, ban iya daurewa kwallar data taran min ba sai data gangaro kan kumatuna, gabadaya sai na dora laifin fushin Abbu a kaina. Watakila ni na dame shi da hayaniya har ranshi ya baci, kila barci yake yi na tashe shi da hayaniya kun san yadda mutane kan zama moody idan sun tashi daga barci balle shi da naje ina jijjigawa abinda Anty Shafa tace mata basa tashin mazajen su daga barci ta wannan hanyar. Ko kuma yana bukatar kadaici ne ni kuma ban kula da hakan ba? Idan haka ne kuwa ai laifi na ne. Tashi na sake yi na koma dakin, lekawa nayi kamar munafuka wannan karon yayi rigingine, na shiga dakin a hankali tare da maida kofar na rufe, barci yake yi. A hankali na dauki bargo na rufa mishi, na juya kenan naji an riko hannuna na juya da sauri. Ya bude idanunshi da suka shige ciki har sun canza kala ya kalleni dasu, take naji wani irin bacin rai na shige ni. Na samu kaina da tuhumar kaina da responsibility na bacin rai da yake ciki, a hankali nace mishi “kayi hakuri Abbu!" janyo ni yayi na fada kan gadon tare da jana jikinshi ya rungume ni, ina jin yadda zuciyar shi take bugawa da sauri, yace “noo, am sorry! I shouted at you bayan baki yi mun laifin komi ba" na kwantar da kaina akan kirjinshi ina shafa saitin zuciyar shi da hannuna, “Allah ya huci zuciyar ka Abbu na. Wanda ya bata maka rai bai kyauta min ba ni kam tunda nima yasa nawa ran ya baci" kuma gaskiya na fada, raina ya baci kwarai daga ganin bacin ran dake dankare akan fuskar shi. Yayi dan murmushi tare da jan bargo ya rufe mu dashi muka shiga barci.
Koda muka tashi ran shi wasai babu bacin rai a tattare dashi. Da yamma na lallaso shi da kyar muka je gidan Sadiya muka ga baby don da cewa Yayi wai ya za ayi in fara fita ina amaryar sati daya? Da kyar da jibin goshi ya bar ni bayan na dauki alkawarurruka da dama wadanda sirrin mu ne, daga can muka wuce ya fara koya min mota sai gab da magrib muka koma gida. Kwana biyu da yin haka visar mu ta fita kasashen ketare yawon bude ido (honey moon) ta fita. Da kaina na zauna na fitar da kasashe biyar wadanda nake matukar so da burin ziyarta a rayuwata. Muka fara shirye-shiryen tafiya amma fa bayan anyi sunan Sadiya.
~Daga yanzu ba zaku dinga ganin posting dina akai-akai ba gaskiya, mun koma school kuma things are somehow... Kun dai san lamurran en makaranta ina fata za ayi mun uziri?
#TeamAbnaf
#AnaTare
*♡Jeedderh♡*
*NI DA ABOKIN BABA NA....!*
*©°•Jeedderh Lawals•°*
*®°•Fikrah Writers Association°•*🖋
*53*
A rana ta uku da haihuwar na kara komawa gidan Sadiya daga can bayan Abbu yaje ya dauke ni da dare muka biya ta can babban gida gidan su Abbun muka gaida iyayen shi, Hajiya Siyama mutuniyar kirki ta amshe mu da hannu bibbiyu har da dan guntun fadanta wai me yasa ya barni na fara fita yanzu? Har tana karawa da cewa wai ai su a zamanin su amarya sai tayi rabin shekara kafarta bata taka kofar gidanta ba., na kama baki a raina na kara da lallai kuwa! Bayan mun gaisa ta saka mana albarka muka wuce sashen Hajja Fati itama muka gaida ta. Nan ta hada ni dasu tarkacen daddawa da sauran su. Mahaifinsu kuwa kwaryar zuma farar saka mai kyau ya bani, daga nan muka juya gida hannu riki-riki da tsaraba.
Ranar sunan kuwa da safe na tafi. Muna ta ayyuka da tsare-tsaren wajen da baki zasu zauna bayan falo. Sai bayan la'asar su Anty Mubeenah suka iso gidan ita da yaranta lokacin muna can bayan gidan muna suyar samosa wadda ake ba baki.
Ni'imah data kai wa su Anty Ameenah wadda muka soya ta dawo, ta daddabo ni tare da rada min “ga fa uwargidan ki can tazo!" naji kamar zuciyata zata faso kirjina saboda bugawar da tayi, ganin yadda nayi kuru-kuru da ido yasa tayi dariya, “haba babe cool mana, sai kace wadda zata cinye naman jikin ki?" nayi murmushin yake kawai.
Ni'imah ba zata gane halin da nake ciki ba, ba wai tsoron Anty Mubeenah nake ji ba, kawai ina fargabar yadda karon mu da ita zai kasance a matsayina na matar Abbu-Mijinta a halin yanzu, nasan ko kallon banza ba zan samu ba wannan karon, fatana daya mu rabu da ita lafiya ba tare da rayuka sun baci ba. Don haka nayi gefe daya da tunanin naci gaba da rolling din da nake yi.
Har inda muke Hafsy ta lalubo ni, nan ta zauna tana ta zuba min labarai har muka gama, aka shiga da wadanda muka yi ciki mu kuma muka shiga BQ muka yi wanka muka gyara jikinmu.
Wata uwar sun shadda muka saka a matsayin ankon suna, dark purple ta sha aikin pink din zare, Ya Allah! Zo kuga yadda na fita a cikin kayan nan. Kyawuna ya fita sosai kamar ka sace ni ka gudu, muka tsaya muka dan karkashe flashes kafin muka koma cikin gida. Bayan dogon hesitating da tunanin zanyi ko ba zan yi ba, daga karshe dai nayi sallama dakin maijego na shiga cikin dakiya duk da cewa zuciya na wani mayen tsere take yi a cikin kirjina.
Ina shiga muka
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34 Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41