Ranar tare dashi muka yi girkin, muka koma falo muka karya muna hirarrakin mu cike da nishadi, ranar ko nan da can Abbu bai fita ba, yana manne dani kamar chewing gum. Da haka rayuwar auren mu ta koma normal kamar, ko ma in ce fiye da da.
Bayan kamar sati biyu da yin haka, ina zaune a falo Abbu ya dawo daga office. Da murnata na tare shi, na taimaka mishi yayi wanka tare da cin abinci. A wajen cin abincin ne yake bani labarin yadda suka kare da Dr Lubah yace; “ai kin amsa laifinta tayi sai dana kai karar ta ga hukumar makaranta sannan, yanzu dai an mata warning game da haka. Ance idan ta sake a bakin aikinta, shine fa bayan mun fito wai take bani hakuri wai sharrin shaidan ne, ni dai na gaya mata idan ta kara bari ma muka hada hanya da ita to ta tabbatar sai na kai karar ta” nayi dariya nace “ashe da gaske ita din ce dai?” ya girgiza kai, “ai ki daina wasa da lamarinta, matar bata da mutunci da kike ganinta. Sai da maganar ta kai ga sauran malamai nake jin ashe an taba kwantar da wata budurwa a asibiti data taba ganinta a tsaye ita da saurayinta, itace fa ta dauka ta maka mata a kai. Sai daga baya ma ake fada mata ashe er uwar saurayin ce, sanadin rabuwar su dashi dai kenan" na kama baki cike da mamaki, nace “to Allah ya shirye ta tare da masu hali irin nata” Abbu yace “ameen”...
A karshen watan muka koma ainihin gidan da zamu zauna. Wani dankareren babban gida a cikin Lamido Crescent, flat ne da dakuna bila adadin. Babban falo daya dauke saitin kujeru biyu, kicin, store, sai wani corridor wanda idan ka bishi zai sada ka da wani karamin falon inda anan Dinning yake sai dakunan much ni da Anty Mubeenah. Dakin mu ciki ne da falo, sai dakin Abbu, na yara da kuma study room inda muke zuwa mu yi karatu abinmu. Komi na gidan sabo ne dal wanda Abbu ne ya dauki nauyin yin hakan, duk da dai akwai daki na musamman anan kusa da dakina wanda aka ajiye min jeren da Daddy yayi min.
Zaman gashi nan kadaran-kadahan. Muna zaune lafiya daga uwar har yayanta da maigidan, batun hali a wajen Anty Mubeenah har yanzu bata canza zani ba, tana nan kamar da da rashin kula da kanta, mijinta da rayuwar aurenta gabadaya. Abbu ya dauko en aiki wadanda suke zuwa suyi shara, goge-goge da sauran su, da kaina nake girki na in kuma gyara dakunan mu dana Abbu. Ina ji shi yasa hatta da yaran suke dokin zagayowar ranar girkina saboda dadadan abincin da nake dafa musu ba kamar abincin Harira da har lokacin tana manne damu ba.
Ranar va sai ga en uwan Anty Mubeenah a gidan ba?? Shakira da Umaimah kamar daga sama. Muna falo ina koyawa Hafsy assignment lokacin, na daga kai da er fara'ata saboda nasan ba abin arziki ne ya kawo su ba, na gaida su. Suka amsa suna wani yatsine yatsine, wai “ina uwargida ran gida mai babban matsayi a gidan Ibrahim Galadanchi?” abin ma ya bani dariya, na girgiza kai kawai. Umaimah taja tsaki, “kamar fa wannan dangin masu kwacen mijin kallon uku-saura take mana, irin wuyanta ya isa yanka dinnan” Saddiqar tace “kyaleta, karyar banza take. Yo ni Allah na tuba idan da ba don albarkacin Mubeenah ba wannan er tsakin ta isa in kalleta? Taci gaba da abinda take yi wallahi yanzu zan kwantar da mutum a kasa”.
Daidai lokacin Anty Mubeenah ta shigo falon, ganin en uwanta ta hau fara'ah, Umaimah tace “yauwa Yaya, wannan er iskar matar fa tana nema ta raina mana hankali, kinga wani kallo da take jefa mana ni da Anty Saddiqa??” Mubeenar ta kalle su kafin ta sake kallona, dan murmushi tayi ni na ma yi zaton ko zagi zata auna min, sai kawai naji tace musu “ko zo muje daki mana” da alamu suma abin ya basu mamaki ganin yanda suka hangame baki, can Saddiqa ta gyada kai, ta jefa min harara ta shura takalmi tayi gaba Umaimah tabi bayanta, Anty Mubeenah ta kallemu tace “kiyi hakuri fa!” tayi gaba ba tare da taga yadda na hangame baki a dimauce na bita da kallo ba, abin ya matukar bani mamaki kwarai ba kadan ba. Nayi zaton zata goyi bayan en uwanta ne su hadu su zageni kila ma har da duka kamar yadda naji ana bada labari, sai naga akasin haka, har da bada hakuri ma. Na jinjina kaina tare da tsintar kaina ina mata addu'ar Allah ya dawo da ita kan hanya.
Da zasu tafi ma haka suka same mu a falon ni da Hafsy, ko er Allah ya kiyaye hanya din da na musu Allah bai basu ikon amsawa ba. Na tabe baki tare da daga kafadata, basu dameni ba ko Kaden, in dai muna zaman lafiya da abokiyar zama na to shikenan ni kam.
*****
Ba a wani jima ba aka yi auren Harith shi da Ikram, na samu da kyar an bar ni naje wajen daurin aure. Wannan shine zuwana Kaduna na uku tun bayan da aka min Aure.
Ni'imah ta haifi santaleliyar yarinya mace taci sunan Halima mahaifiyar Basheer sai suke kiranta da Amal. A daren ranar ina kwance akan gadona a gajiye Abbu ya shigo dakin da yake ranar girki ta ce. Kan gadon ya hayo ya dauki kafafuna ya dora akan cinyoyin shi ya fara matsa min su, idanu na lumshe tare da kara lafewa akan gadon. Abbu yace “dube ta don Allah! Sai kije kiyi ta faman yin aiki da kai da kawo sai dare yayi kuma kizo ki dinga min raki” cikin muryar barci nace “to Abbu menene a ciki, yiwa wani yiwa kai balle su Ni'imah ne fa, idan na hidimta musu kamar kaina na hidimtawa” ya kuta, “just wait and see, idan kika haihu duk wadda bata miki wahalar da kike musu ba sai na bata musu rai” dan murmushi kawai nayi tare da maida idanuna na lumshe.
Ya juyo dani na koma rigingine, hannu ya kai yana dafa cikina, “wai ni tsaya, har yanzu ban yi ajiya anan wajen bane duk kokarin da nake yi?? Lokaci ya fara ja fa, muna bukatar jin kukan jarirai a gidan nan” nace “Allah bai kawo ba har yanzu Abbu” yace “ki ce in kara kaimi kawai” da sauri na girgiza kai, “a'ah, ba sai ka kara ba wallahi. Zan taya mu addu'ar Allah ya kawo su kawai Abbu” kai ya girgiza kamar wani karamin yaro, “naki wayon....” wuta ya kashe mana tare da janyo ni cikin jikinsa...
So how r u doing outta there #TeamAbnaf?? Abubuwa ne suka min yawa fiye da tunaninku shi yasa kwana biyu kuka ji ni shiru. We are almost there in shaa Allah?? Just about 2-3 episodes?? Ina fata zaku ci gaba da hakuri?? Enxs
Na fito daga dakin Abdullahi hannuna dauke da tarin kayan wankin dana fiddo mishi. Duka yaran suna zaune akan kujera, Abdullahi da Qaseem suna game na Super Mario, Hafsy kuma tana wasa da wayata. Anty Mubeenah kuma tana gefen Hafsy tana duba jarida.
Abdullahi ya kalleni yayin dana harare shi nace “kalleshi dirty guy kawai, sai aukin fi'ili da gayu, idan ya dau wani wankan sai kayi zaton abin har dakin shi ne sai ka shiga labari ya sha babban” Abdullahi yayi kasa da kai yayin da Qaseem yasa dariya, shima na harare shi.., “see who's laughing! Jiya dana shiga dakinta kasa numfashi nayi sai dana sa mask, wai anya kuna ma yin wanka??” Anty Mubeenah ta dan saki dariya, da sauri na juya na kalleta. Ganin ina kallonta yasa ta dauke kanta da sauri, nayi dan jim ina kallonta.
Kwanaki biyun nan ina ganin wasu canji a tare da ita, fuskarta tayi rama sosai, haka zan ga ta zauna tayi shiru cikin tunani gashi har zuwa lokacin bata bani fuskar da zamu yi sabon da zan tambayeta abinda yake damunta ba. Damuwar da take ciki na damu na, I really want to help. Na juya kaina daga kanta a hankali na tunkari kofa, Shuaibu mai mana wanki da guga na ba kayan na koma falo.
Na kallesu, “daga yau duk wanda ya cire kaya kar ya kuskura ya maida su cikin drawer, a sa a laundry bin sai a wanke, kuna ji na? Manya daku saboda Allah amma wallahi Hafsy ta ma fiku tsafta” Abdullahi ya turo baki yana hararar Hafsy da take mishi gwalo, yace “ai saboda ita gyara mata daki ake yi, mu fa?” na Harare shi, “saboda ita yarinya ce, ku kuma kun girma, kayan da aka cire should always be put in a laundry bin ok??" suka gyada kai, nace “good!" na wuce dakina.
Ina shiga karan wayata ya min oyoyo, na dauki wayar tare da duba sunan mai kiran, ganin waye yasa na dauka da shakiyanci na “amarya, amarya!!" daga can cikin wayar Ramlah ta amsa, “ke dallah can! Aure fiye da wata biyar amma kina wani ce min amarya?" watanni biyar da suka wuce muka sha bikinta ita da Ayan wanda ana daurawa suka wuce states inda a can ne yake aiki, bayan bikin da wata daya muka gama karatun mu, yanzu dai fitar sakamako muke jira kawai.
Nace “haba wata biyar ne fa kawai ba wasu watanni ba, Allah na tuba ni ko da ‘yayan ki ma amarya zan dinga ce miki" taja tsaki, “to Allah ya kyauta miki, ya zancen turarukan da na turo miki? Kin amso su kuwa?" nace “ai da kanta ma ta kawo min har gida, Masha Allah sun yi kamshi sosai, kuma suna da kyau wallahi" tace “ai sai dana fada miki, yanzu ya za ayi wajen sauran abubuwan nan da nace a kawo min?" nace “idan na hada komi zan kira ita Nadiya din, sai ta taho miki dasu koh?" tace “to shikenan... Ina Abbu?" nayi murmushi, “Abbu yaje Beijing, suna da wani meeting ne a kamfani shine ya tafi" tace “ranar nan ai na kalli show din da aka bashi award din best prof na Universities din fadin Nigeria, naji ana maganar bashi VC a BUK koh?" na gyada kai, “yeah, he deserve it ai" tace “indeed, ana fadar ayyukan shi da sadaukarwar shi indai ta fannin karatu ne ai, Allah ya kara taimako" na amsa da “ameen" daga haka muka yi sallama da ita.
Toilet na fada na dauro alwala na fito nayi sallar La'asar, bayan na gama na hau en gyare-gyare a dakin babu kakkautawa da yake ba wani aikin yi ne dani ba duk da cewa ranar girki na ce dai. Wajen karfe biyar na tashi na shiga kicin din, Anty Mubeenah tana tsaye a gaban gas cooker da frying pan akai da alamu tana frying abu, na kalleta cike da mamaki ita kuma ta kalleni da blank expression, tunda muke da matar nan sai ranar na taba ganinta a kicin wai da sunan girki, sai na dake kawai na shiga cikin store na fito da duk abubuwan da zan bukata. Da yake babban kicin ne, kuma yawanci komi na amfani a kicin din guda biyu ne sai na kunna wani gas din na fara girkina. Cikin kankanin lokaci kamshi ya bade ko'ina na gidan, ta gefen ido nake kallon Anty Mubeenah ina wasi-wasin dalilinta na yin girki yanzu. Har ta gama soya dankalin ta juye a cikin plate ta kashe gas din ta fita, na tabe baki naci gaba da aiki na. Ba a jima sai gata ta fado kicin din, ta tangwarar da plate din a cikin sink ta juya kamar cikin fushi.
Sai dana gama girkina idanu na ya sauka akan dankalin, na dauki kwara daya na kai bakina, frowning nayi. Dankalin tauri kamar danye ga dan banzan gishiri da yaci. Na gyada kai a hankali tare da zubar da dankalin na wanke kayan dana bata naje na jera girkin na shige daki. Wanka na fara yi kafin nayi sallah na jira aka kira Isha'i nayi kafin na fita falo muka fara dinner. Tun a wajen jikina ya fara rawa, sanyi yake shigar ko wace kofa ta jikina sosai.
Hafsy ta kalleni tace “Anty Nafee, jikinki rawa yake yi baki da lafiya ne?" nace “zazzabi ne, yanzu zan shiga in sha magani ai" tayi shiru tana kallona, can tace “ko dai in kira Anty Raliya?" nayi saurin cewa “a'ah da wannan daren? Mura ce take shirin kama ni zan sha magani" tace “to Allah ya sauwake" bayan mun gama cin abincin muka dan yi kallo kowa ya wuce dakin shi. Shirin kwanciya barci nayi naja bargo na rufe jikina, rawar sanyi nake yi ina jin kamar an watsa ni cikin ruwan kankara hakorana har haduwa suke yi waje guda. Ina cikin wannan halin Hafsy tazo ta same ni, da sauri ta hayo kan gadon tana jijjiga ni amma na kasa daga kai in kalleta, fita tayi da sauri sai gata ta dawo ita da Anty Mubeenah. Da sauri ta dago ni tana tamvayar lafiya?? Ganin na kasa yin magana yasa ta hau daga drawers har ta lalubo paracetamol, Hafsy ta miko ruwa Anty ta bani maganin nasha na koma na kwanta. Ba a jima ba barci ya dauke ni, ban san sanda suka bar dakin ba.
Da asubahi koda na tashi babu zazzabin sai mura data min mugun kamu, nayi sallah ina ta atishawa da tari ba kakkautawa. Na shirya break fast na kai kan dinning na ajiye, ina cikin shiryawa din Anty Mubeenah ta fito daga dakinta, nan ta min ya jiki na amsa da sauki tare da mata godiyar dawainiyar ta a gare ni a daren jiya, ta wuce dakinta. Nima dakina na koma na kira Abbuna muka sha hirar mu har sai da Hafsy ta leko ta kirani sannan muka yi sallama na fita muka karya. Yaran makaranta suka wuce ni kuma na zauna anan falo ina kallo Anty Mubeenah kuma ta shige dakinta, na kula kwana biyun nan bata cika fita ba.
Wajen karfe goma na safe sai ga su Anty Ameenah da Anty Rahila sun zo wai ashe Hafsy ce ta kira su a waya tace musu bani da lafiya, na kama baki ina dariya nace “Lallai ma Hafsy! Zazzabi ne nayi jiya da dare fa, mura nake yi sai kuma nayi wankan yamma ina jin shine ya saukar mun da zazzabin, amma shine har da shela??" Anty Raliya tace “ai ba shela bace ba Nafeesah, gaskiya ce. Idan wani abu fa ya faru??" nace “babu abinda zai faru ma in shaa Allah. Ai Hafsy din da Anty Mubeenah suka kula dani" na lura da kallon mamakin da suka jefe ni dashi kafin suka basar, Anty Ameenah tace “To Allah ya kara lafiya" nace “Ameen" sai ga Anty Mubeenah ta fito, nan ta samu waje ta zauna suka gaisa, basu jima ba suka mana sallama suka tafi suna jaddada min idan dai naji ciwon ya dawo in kira su fa, nace toh.
*****
Mun fito daga cikin jifatu ni da Hafsy mun je shopping, ina kokarin bude mota mu shiga naji an kira sunana daga bayanmu cikin wata irin murya da naji kamar na san ta, “Nafeesah??" ga namaki na koda na juya Muneer na gani a tsaye, dauke a kafadar shi wata dan yaro ne zai kai kimanin shekaru hudu kila. Ya matso yace “Allahu Akbar! Ashe dai ke din ce, ya kike?" nayi murmushi, shekaru masu yawa sosai rabon da mun hadu kenan tun ma kafin in bar Kadpoly. Nace “lafiya na qalau Muneer, kai fa?" ya kalli Hafsy dake tsaye a gefena tana kallon shi cikin alamun rashin sanayya, yace “diyar ki ce?" ni abin sai ma ya bani dariya, ya kalli zankadediyar budurwa kamar Hafsy yace wai diya ta?? Nace “ehh, baka ga muna kama ba?" sai yayi er dariya, ya nuna min yaron hannunshi yace “dana kenan, Suleiman... Ke fa?" na daga kafada, “Allah bai kawo ba har yanxu" yace “to Allah ya kawo masu Albarka" nace “Ameen" daga haka muka yi sallama kowa ya shiga motar shi yaja. A cikin mota nayi murmushi tare da gyada kai cikin kara sakankancewa da Girma na Subhanah! Lallai Hausawa sun yi gaskiya da suka ce wani baya auren matar wani kamar yadda wani baya haihuwar dan wani...
A daren ranar misalin karfe sha daya na dare na fito daga dakina da niyar zuwa kicin dauko ruwa, naci karo da Anty Mubeenah Zaune akan kujera cikin duhun falon wanda hasken dake waje ne daya dan shigo ta labulaye yasa na ganta, da farko tsoro ta bani kafin na dan matsa zuwa gabanta nace “Anty Mubeenah baki da lafiya ne?" ta dan dago a firgice ta kalleni kafin ta kauda kai, kai ta girgiza tace “lafiya ta qalau... Babu komi" kamar zan yi magana sai na fasa, na tunkari kicin kafin in dakata dalilin
Showing 114001 words to 117000 words out of 122880 words
Ranar tare dashi muka yi girkin, muka koma falo muka karya muna hirarrakin mu cike da nishadi, ranar ko nan da can Abbu bai fita ba, yana manne dani kamar chewing gum. Da haka rayuwar auren mu ta koma normal kamar, ko ma in ce fiye da da.
Bayan kamar sati biyu da yin haka, ina zaune a falo Abbu ya dawo daga office. Da murnata na tare shi, na taimaka mishi yayi wanka tare da cin abinci. A wajen cin abincin ne yake bani labarin yadda suka kare da Dr Lubah yace; “ai kin amsa laifinta tayi sai dana kai karar ta ga hukumar makaranta sannan, yanzu dai an mata warning game da haka. Ance idan ta sake a bakin aikinta, shine fa bayan mun fito wai take bani hakuri wai sharrin shaidan ne, ni dai na gaya mata idan ta kara bari ma muka hada hanya da ita to ta tabbatar sai na kai karar ta” nayi dariya nace “ashe da gaske ita din ce dai?” ya girgiza kai, “ai ki daina wasa da lamarinta, matar bata da mutunci da kike ganinta. Sai da maganar ta kai ga sauran malamai nake jin ashe an taba kwantar da wata budurwa a asibiti data taba ganinta a tsaye ita da saurayinta, itace fa ta dauka ta maka mata a kai. Sai daga baya ma ake fada mata ashe er uwar saurayin ce, sanadin rabuwar su dashi dai kenan" na kama baki cike da mamaki, nace “to Allah ya shirye ta tare da masu hali irin nata” Abbu yace “ameen”...
A karshen watan muka koma ainihin gidan da zamu zauna. Wani dankareren babban gida a cikin Lamido Crescent, flat ne da dakuna bila adadin. Babban falo daya dauke saitin kujeru biyu, kicin, store, sai wani corridor wanda idan ka bishi zai sada ka da wani karamin falon inda anan Dinning yake sai dakunan much ni da Anty Mubeenah. Dakin mu ciki ne da falo, sai dakin Abbu, na yara da kuma study room inda muke zuwa mu yi karatu abinmu. Komi na gidan sabo ne dal wanda Abbu ne ya dauki nauyin yin hakan, duk da dai akwai daki na musamman anan kusa da dakina wanda aka ajiye min jeren da Daddy yayi min.
Zaman gashi nan kadaran-kadahan. Muna zaune lafiya daga uwar har yayanta da maigidan, batun hali a wajen Anty Mubeenah har yanzu bata canza zani ba, tana nan kamar da da rashin kula da kanta, mijinta da rayuwar aurenta gabadaya. Abbu ya dauko en aiki wadanda suke zuwa suyi shara, goge-goge da sauran su, da kaina nake girki na in kuma gyara dakunan mu dana Abbu. Ina ji shi yasa hatta da yaran suke dokin zagayowar ranar girkina saboda dadadan abincin da nake dafa musu ba kamar abincin Harira da har lokacin tana manne damu ba.
Ranar va sai ga en uwan Anty Mubeenah a gidan ba?? Shakira da Umaimah kamar daga sama. Muna falo ina koyawa Hafsy assignment lokacin, na daga kai da er fara'ata saboda nasan ba abin arziki ne ya kawo su ba, na gaida su. Suka amsa suna wani yatsine yatsine, wai “ina uwargida ran gida mai babban matsayi a gidan Ibrahim Galadanchi?” abin ma ya bani dariya, na girgiza kai kawai. Umaimah taja tsaki, “kamar fa wannan dangin masu kwacen mijin kallon uku-saura take mana, irin wuyanta ya isa yanka dinnan” Saddiqar tace “kyaleta, karyar banza take. Yo ni Allah na tuba idan da ba don albarkacin Mubeenah ba wannan er tsakin ta isa in kalleta? Taci gaba da abinda take yi wallahi yanzu zan kwantar da mutum a kasa”.
Daidai lokacin Anty Mubeenah ta shigo falon, ganin en uwanta ta hau fara'ah, Umaimah tace “yauwa Yaya, wannan er iskar matar fa tana nema ta raina mana hankali, kinga wani kallo da take jefa mana ni da Anty Saddiqa??” Mubeenar ta kalle su kafin ta sake kallona, dan murmushi tayi ni na ma yi zaton ko zagi zata auna min, sai kawai naji tace musu “ko zo muje daki mana” da alamu suma abin ya basu mamaki ganin yanda suka hangame baki, can Saddiqa ta gyada kai, ta jefa min harara ta shura takalmi tayi gaba Umaimah tabi bayanta, Anty Mubeenah ta kallemu tace “kiyi hakuri fa!” tayi gaba ba tare da taga yadda na hangame baki a dimauce na bita da kallo ba, abin ya matukar bani mamaki kwarai ba kadan ba. Nayi zaton zata goyi bayan en uwanta ne su hadu su zageni kila ma har da duka kamar yadda naji ana bada labari, sai naga akasin haka, har da bada hakuri ma. Na jinjina kaina tare da tsintar kaina ina mata addu'ar Allah ya dawo da ita kan hanya.
Da zasu tafi ma haka suka same mu a falon ni da Hafsy, ko er Allah ya kiyaye hanya din da na musu Allah bai basu ikon amsawa ba. Na tabe baki tare da daga kafadata, basu dameni ba ko Kaden, in dai muna zaman lafiya da abokiyar zama na to shikenan ni kam.
*****
Ba a wani jima ba aka yi auren Harith shi da Ikram, na samu da kyar an bar ni naje wajen daurin aure. Wannan shine zuwana Kaduna na uku tun bayan da aka min Aure.
Ni'imah ta haifi santaleliyar yarinya mace taci sunan Halima mahaifiyar Basheer sai suke kiranta da Amal. A daren ranar ina kwance akan gadona a gajiye Abbu ya shigo dakin da yake ranar girki ta ce. Kan gadon ya hayo ya dauki kafafuna ya dora akan cinyoyin shi ya fara matsa min su, idanu na lumshe tare da kara lafewa akan gadon. Abbu yace “dube ta don Allah! Sai kije kiyi ta faman yin aiki da kai da kawo sai dare yayi kuma kizo ki dinga min raki” cikin muryar barci nace “to Abbu menene a ciki, yiwa wani yiwa kai balle su Ni'imah ne fa, idan na hidimta musu kamar kaina na hidimtawa” ya kuta, “just wait and see, idan kika haihu duk wadda bata miki wahalar da kike musu ba sai na bata musu rai” dan murmushi kawai nayi tare da maida idanuna na lumshe.
Ya juyo dani na koma rigingine, hannu ya kai yana dafa cikina, “wai ni tsaya, har yanzu ban yi ajiya anan wajen bane duk kokarin da nake yi?? Lokaci ya fara ja fa, muna bukatar jin kukan jarirai a gidan nan” nace “Allah bai kawo ba har yanzu Abbu” yace “ki ce in kara kaimi kawai” da sauri na girgiza kai, “a'ah, ba sai ka kara ba wallahi. Zan taya mu addu'ar Allah ya kawo su kawai Abbu” kai ya girgiza kamar wani karamin yaro, “naki wayon....” wuta ya kashe mana tare da janyo ni cikin jikinsa...
So how r u doing outta there #TeamAbnaf?? Abubuwa ne suka min yawa fiye da tunaninku shi yasa kwana biyu kuka ji ni shiru. We are almost there in shaa Allah?? Just about 2-3 episodes?? Ina fata zaku ci gaba da hakuri?? Enxs
*♡Jeedderh♡*
*NI DA ABOKIN BABA NA...!*
*©Jeedderh Lawals*
*®Fikrah Writers Association* 🖊🖊
*58*
*BAYAN SHEKARU BIYU DA RABI!*
Na fito daga dakin Abdullahi hannuna dauke da tarin kayan wankin dana fiddo mishi. Duka yaran suna zaune akan kujera, Abdullahi da Qaseem suna game na Super Mario, Hafsy kuma tana wasa da wayata. Anty Mubeenah kuma tana gefen Hafsy tana duba jarida.
Abdullahi ya kalleni yayin dana harare shi nace “kalleshi dirty guy kawai, sai aukin fi'ili da gayu, idan ya dau wani wankan sai kayi zaton abin har dakin shi ne sai ka shiga labari ya sha babban” Abdullahi yayi kasa da kai yayin da Qaseem yasa dariya, shima na harare shi.., “see who's laughing! Jiya dana shiga dakinta kasa numfashi nayi sai dana sa mask, wai anya kuna ma yin wanka??” Anty Mubeenah ta dan saki dariya, da sauri na juya na kalleta. Ganin ina kallonta yasa ta dauke kanta da sauri, nayi dan jim ina kallonta.
Kwanaki biyun nan ina ganin wasu canji a tare da ita, fuskarta tayi rama sosai, haka zan ga ta zauna tayi shiru cikin tunani gashi har zuwa lokacin bata bani fuskar da zamu yi sabon da zan tambayeta abinda yake damunta ba. Damuwar da take ciki na damu na, I really want to help. Na juya kaina daga kanta a hankali na tunkari kofa, Shuaibu mai mana wanki da guga na ba kayan na koma falo.
Na kallesu, “daga yau duk wanda ya cire kaya kar ya kuskura ya maida su cikin drawer, a sa a laundry bin sai a wanke, kuna ji na? Manya daku saboda Allah amma wallahi Hafsy ta ma fiku tsafta” Abdullahi ya turo baki yana hararar Hafsy da take mishi gwalo, yace “ai saboda ita gyara mata daki ake yi, mu fa?” na Harare shi, “saboda ita yarinya ce, ku kuma kun girma, kayan da aka cire should always be put in a laundry bin ok??" suka gyada kai, nace “good!" na wuce dakina.
Ina shiga karan wayata ya min oyoyo, na dauki wayar tare da duba sunan mai kiran, ganin waye yasa na dauka da shakiyanci na “amarya, amarya!!" daga can cikin wayar Ramlah ta amsa, “ke dallah can! Aure fiye da wata biyar amma kina wani ce min amarya?" watanni biyar da suka wuce muka sha bikinta ita da Ayan wanda ana daurawa suka wuce states inda a can ne yake aiki, bayan bikin da wata daya muka gama karatun mu, yanzu dai fitar sakamako muke jira kawai.
Nace “haba wata biyar ne fa kawai ba wasu watanni ba, Allah na tuba ni ko da ‘yayan ki ma amarya zan dinga ce miki" taja tsaki, “to Allah ya kyauta miki, ya zancen turarukan da na turo miki? Kin amso su kuwa?" nace “ai da kanta ma ta kawo min har gida, Masha Allah sun yi kamshi sosai, kuma suna da kyau wallahi" tace “ai sai dana fada miki, yanzu ya za ayi wajen sauran abubuwan nan da nace a kawo min?" nace “idan na hada komi zan kira ita Nadiya din, sai ta taho miki dasu koh?" tace “to shikenan... Ina Abbu?" nayi murmushi, “Abbu yaje Beijing, suna da wani meeting ne a kamfani shine ya tafi" tace “ranar nan ai na kalli show din da aka bashi award din best prof na Universities din fadin Nigeria, naji ana maganar bashi VC a BUK koh?" na gyada kai, “yeah, he deserve it ai" tace “indeed, ana fadar ayyukan shi da sadaukarwar shi indai ta fannin karatu ne ai, Allah ya kara taimako" na amsa da “ameen" daga haka muka yi sallama da ita.
Toilet na fada na dauro alwala na fito nayi sallar La'asar, bayan na gama na hau en gyare-gyare a dakin babu kakkautawa da yake ba wani aikin yi ne dani ba duk da cewa ranar girki na ce dai. Wajen karfe biyar na tashi na shiga kicin din, Anty Mubeenah tana tsaye a gaban gas cooker da frying pan akai da alamu tana frying abu, na kalleta cike da mamaki ita kuma ta kalleni da blank expression, tunda muke da matar nan sai ranar na taba ganinta a kicin wai da sunan girki, sai na dake kawai na shiga cikin store na fito da duk abubuwan da zan bukata. Da yake babban kicin ne, kuma yawanci komi na amfani a kicin din guda biyu ne sai na kunna wani gas din na fara girkina. Cikin kankanin lokaci kamshi ya bade ko'ina na gidan, ta gefen ido nake kallon Anty Mubeenah ina wasi-wasin dalilinta na yin girki yanzu. Har ta gama soya dankalin ta juye a cikin plate ta kashe gas din ta fita, na tabe baki naci gaba da aiki na. Ba a jima sai gata ta fado kicin din, ta tangwarar da plate din a cikin sink ta juya kamar cikin fushi.
Sai dana gama girkina idanu na ya sauka akan dankalin, na dauki kwara daya na kai bakina, frowning nayi. Dankalin tauri kamar danye ga dan banzan gishiri da yaci. Na gyada kai a hankali tare da zubar da dankalin na wanke kayan dana bata naje na jera girkin na shige daki. Wanka na fara yi kafin nayi sallah na jira aka kira Isha'i nayi kafin na fita falo muka fara dinner. Tun a wajen jikina ya fara rawa, sanyi yake shigar ko wace kofa ta jikina sosai.
Hafsy ta kalleni tace “Anty Nafee, jikinki rawa yake yi baki da lafiya ne?" nace “zazzabi ne, yanzu zan shiga in sha magani ai" tayi shiru tana kallona, can tace “ko dai in kira Anty Raliya?" nayi saurin cewa “a'ah da wannan daren? Mura ce take shirin kama ni zan sha magani" tace “to Allah ya sauwake" bayan mun gama cin abincin muka dan yi kallo kowa ya wuce dakin shi. Shirin kwanciya barci nayi naja bargo na rufe jikina, rawar sanyi nake yi ina jin kamar an watsa ni cikin ruwan kankara hakorana har haduwa suke yi waje guda. Ina cikin wannan halin Hafsy tazo ta same ni, da sauri ta hayo kan gadon tana jijjiga ni amma na kasa daga kai in kalleta, fita tayi da sauri sai gata ta dawo ita da Anty Mubeenah. Da sauri ta dago ni tana tamvayar lafiya?? Ganin na kasa yin magana yasa ta hau daga drawers har ta lalubo paracetamol, Hafsy ta miko ruwa Anty ta bani maganin nasha na koma na kwanta. Ba a jima ba barci ya dauke ni, ban san sanda suka bar dakin ba.
Da asubahi koda na tashi babu zazzabin sai mura data min mugun kamu, nayi sallah ina ta atishawa da tari ba kakkautawa. Na shirya break fast na kai kan dinning na ajiye, ina cikin shiryawa din Anty Mubeenah ta fito daga dakinta, nan ta min ya jiki na amsa da sauki tare da mata godiyar dawainiyar ta a gare ni a daren jiya, ta wuce dakinta. Nima dakina na koma na kira Abbuna muka sha hirar mu har sai da Hafsy ta leko ta kirani sannan muka yi sallama na fita muka karya. Yaran makaranta suka wuce ni kuma na zauna anan falo ina kallo Anty Mubeenah kuma ta shige dakinta, na kula kwana biyun nan bata cika fita ba.
Wajen karfe goma na safe sai ga su Anty Ameenah da Anty Rahila sun zo wai ashe Hafsy ce ta kira su a waya tace musu bani da lafiya, na kama baki ina dariya nace “Lallai ma Hafsy! Zazzabi ne nayi jiya da dare fa, mura nake yi sai kuma nayi wankan yamma ina jin shine ya saukar mun da zazzabin, amma shine har da shela??" Anty Raliya tace “ai ba shela bace ba Nafeesah, gaskiya ce. Idan wani abu fa ya faru??" nace “babu abinda zai faru ma in shaa Allah. Ai Hafsy din da Anty Mubeenah suka kula dani" na lura da kallon mamakin da suka jefe ni dashi kafin suka basar, Anty Ameenah tace “To Allah ya kara lafiya" nace “Ameen" sai ga Anty Mubeenah ta fito, nan ta samu waje ta zauna suka gaisa, basu jima ba suka mana sallama suka tafi suna jaddada min idan dai naji ciwon ya dawo in kira su fa, nace toh.
*****
Mun fito daga cikin jifatu ni da Hafsy mun je shopping, ina kokarin bude mota mu shiga naji an kira sunana daga bayanmu cikin wata irin murya da naji kamar na san ta, “Nafeesah??" ga namaki na koda na juya Muneer na gani a tsaye, dauke a kafadar shi wata dan yaro ne zai kai kimanin shekaru hudu kila. Ya matso yace “Allahu Akbar! Ashe dai ke din ce, ya kike?" nayi murmushi, shekaru masu yawa sosai rabon da mun hadu kenan tun ma kafin in bar Kadpoly. Nace “lafiya na qalau Muneer, kai fa?" ya kalli Hafsy dake tsaye a gefena tana kallon shi cikin alamun rashin sanayya, yace “diyar ki ce?" ni abin sai ma ya bani dariya, ya kalli zankadediyar budurwa kamar Hafsy yace wai diya ta?? Nace “ehh, baka ga muna kama ba?" sai yayi er dariya, ya nuna min yaron hannunshi yace “dana kenan, Suleiman... Ke fa?" na daga kafada, “Allah bai kawo ba har yanxu" yace “to Allah ya kawo masu Albarka" nace “Ameen" daga haka muka yi sallama kowa ya shiga motar shi yaja. A cikin mota nayi murmushi tare da gyada kai cikin kara sakankancewa da Girma na Subhanah! Lallai Hausawa sun yi gaskiya da suka ce wani baya auren matar wani kamar yadda wani baya haihuwar dan wani...
A daren ranar misalin karfe sha daya na dare na fito daga dakina da niyar zuwa kicin dauko ruwa, naci karo da Anty Mubeenah Zaune akan kujera cikin duhun falon wanda hasken dake waje ne daya dan shigo ta labulaye yasa na ganta, da farko tsoro ta bani kafin na dan matsa zuwa gabanta nace “Anty Mubeenah baki da lafiya ne?" ta dan dago a firgice ta kalleni kafin ta kauda kai, kai ta girgiza tace “lafiya ta qalau... Babu komi" kamar zan yi magana sai na fasa, na tunkari kicin kafin in dakata dalilin
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39 Chapter 40Chapter 41