hakan sai ma mikar dani tsaye da yayi ya kalmashe ni a cikin jikinsa, ya dora habar shi a kan gashin kaina yace “babu gaisuwa ne yau?" kaina na kan kirjin shi na girgiza alamun a'ah, kaina ya sake dagowa nayi saurin kara rufe idanuna, peck naji ya bani a kunci da lebena kafin ya sake ni gaba daya, “it's okay, na fahimta. Kunya ta ake ji ko? Yanzu zan fita a dakin, yi sauri ki shirya kizo mu yi break fast, yau da kaina na tattare hannun riga ta na hada miki break fast" idanuna suka yi walai cikin rashin sanin nayi hakan da tsananin mamaki, dariya yayi tare da dan jan hancina, “thank goodness I've got to see this beautiful eyes, yes ni na hada break fast now yi sauri kizo muci kafin ya huce, ko In zo in shirya ki da kaina?" wayyo nayi saurin girgiza kaina, yayi er dariya ya fita. Wardrobe na bude na ciro wani tausassan yadi ruwan madara riga ne da siket na saka, na lalubi silifas mai taushi na zura tare da yafa dankwalin a kaina da yake babba ne na fita.
Yana zaune akan kujera yana duba waya ina fitowa ya tashi tsaye tare da wucewa wajen dinning nima na bi bayan shi, kujera yaja min na zauna a darare shima yaja ta kusa dani ya zauna. Kwallin kula daya ce a wajen sai flask na ruwan zafi da cups da kayan shayi. Ya hada mana tea tare da daukar plate ya bude kular ya juye abundance ke ciki, nayi shagaraa da baki ina kokarin tantance abinda yake gabana. What did you expect? Konanniyar wainar kwai ce tayi bakikkirin da ita, yasa fork ya yanki kadan ya kai bakinshi kamar mai testing, yace “kar ki samu da bakin da tayi pa, bata yi komi ba" a sanyaye na dauki fork nima na kwaikwayi yadda yayi, abu na farko daya fara ratsa min harshe shine dan banzan gishiri sai kuma dacin konewar da tayi ya biyo baya, ganin yana kallona yasa na takura tun karfina na hadiye kwan, take zuciyata ta tashi, ya daga min gira, “ya??" na dage tun karfina na kakaro yaken tare da mishi 👌 alamun good, yayi murmushi. Wata na sake cirowa na kai baki, wannan karon na jima a bakina kafin na iya hadiyeta. Na ja kofin shayin na fara sipping, gani ba gwanar shan shayi da madara bace. Shi kanshi daya kai loma ta biyu gani nayi ya dakata yana kallona, “kamar gishiri yayi yawa koh?" nace umh. Ya kara kai ta uku bakinshi na bishi da kallo tsigar jikina har tashi tayi, ba shiri ya furzar da ita ya lalubi kofin tea ya kora dashi.
Kallona yayi yace “sorry baby, ko zaki zan sama mana wani mu ci? Da alamu na manta yadda ake girki ko don na jima ban yi ba?" kamar jira nake, na tashi na hade kan kayan na nufi kicin. Store dinmu shakare yake da kayan masarufi wanda nasan kila zai iya daukarmu shekara kafin mu ci rabin kayan, murmushi kawai nayi tare da girgiza kai, Daddy!.
Cikin mintuna talatin na gama soya chips da plaintain, nayi vegetables sauce na dauka na kai mana muka yi break. Na tashi na hade kayan waje guda Abbu ya biyo ni da wasu. Na ajiye kayan tare da juyawa, da sauri Abbu ya riko hannuna, ban kalleshi ba na sadda kaina kasa, yace “are you ok Nafeesah?" na gyada mishi kai a hankali, yace “please Ki daina jin kunya na haka Baby, kin riga da kin zama ni kamar yadda na zama ke. I need you to be free, frank and comfortable idan muna tare, bana jin dadin hakan da kike yi. I know it'll be awkward, but still kiyi trying mana kinji?" na gyada mishi kai, yace “noo, amsa min da bakinki" na daga bakin da kyar nace “toh" ya kai bakinshi kan nawa ya dan tsotsi leben nawa kafin ya dago yana murmushi, “datz you baby...., zan fita yanzu me zan kawo miki?" nace “babu komi" yace “k, ki kunna kallo ko ki shiga dakina a study room akwai kayan exercise ko kuma just do anything so that you won't be bored don zan dan jima, sai na dawo" nace “a dawo lafiya, Allah ya kiyaye hanya" yace “Ameen Nafeesah ta" ya juya ya fita bayan ya bani peck a goshi. Ni kuma na fara wanke kayan da muka karya dasu.

Yinin ranar a kiraye-kirayen waya da chatting nayi shi, babu wanda ya leko gidan kamar yadda ban ga kiran kowa a waya na ba sai na Abbu yana tambayana me nake yi? Lokacin ina study room dinshi bayan na gama gyaran dakinshi da nawa dama gidan gabadaya, sai kuwa Anty Shafa data kira bayan rana ta daga sosai tana sanar dani a ranar da dare zata bi jirgi ta koma gida, na mata godiya game da Alkhairanta a gare mu, muka yi sallama da ita tana jaddada min in fa dinga shiga ruwan zafi har naji kunya ta kama ni. Daga nan naci gaba da gudanar da harkoki na. Abbu bai shigo gidan ba sai bayan la'asar, sai lokacin nayi lunch ko ince muka yi. Ba laifi na dan sake dashi ranar, ba wani awkwardness da strange feelings irin na jiya sai er kunya wadda itama kafin dare yayi na neme ta na rasa, not that I care don ni fa duk abinda zai saka Abbu na cikin farin ciki shi nake aiming yayin da yace shi fa kunyar nan ta dame shi don haka na jefa ta cikin kwandon shara.
Ranar ma a dakin shi na tarda shi bisa umarnin shi bayan nayi wanka na wadata jikina da turare, ya mana light off tare da jana cikin jikinsa ya fara lalubata at first shiru yayi, but lokacin da naji hannunsa a kan kirjina and things started becoming steamy, sai nayi sauri na janye bakina daga cikin nashi, jikina yana er rawa saboda tunano wahalar daren jiya, a hankali nace “Abbu ban warke ba fa!" muryar shi was hoarse and low at the same time yace “I know... Babu abinda zan miki baby, just a good night kiss" sai daya gama samun natsuwar shi ta hanyar ‘good night kiss' kamar yadda yace sannan yayi cuddling dina a cikin jikinshi kanshi a tsakiyar kirjina barci mai dadi ya dauke mu.
Ranar kam ya daga min kafa, wadda ta biyo bayanta kuwa yaki daga kafar despite magiyata da kukan shagwaba wadanda daga baya na fahimci cewar su suka kara karfafa mishi gwiwa ma, ranar data biyo baya ma haka and the day after that.... Soon, na zama gogayyiya kuma expert a cikin sabuwar rayuwar da Abbu ya bude min kofar ta. Mun kara karfafa Rayuwar aurenmu ta hanyar girmama Juna da shimfida kyakkyawa kuma tsaftacciyar rayuwar aure, kulawa da junanmu da tausayawa. A cikin en kwanakin kam duk wanda ya ganmu yaga wadanda suke kan ganiyar cin amarcinsu, na dan rame kadan amma still na kara yin fresh saboda kwanciyar hankalin dana samu. Abbuna kuwa ya kara kiba, jikinshi ya kara yin fresh ko ba komi nasan dadadan girke-girken da nake mishi kadai sun isa sa shi yayi kiba.
A kwana na biyar da tarewa ta, har ranar babu wanda ya leko gidanmu, Abbu ma bai cika fita sosai ba. Ina zaune da safiyar ranar a falo sanye da wasu Pakistan riga da wandon su, na gyara gashina ya kwanto har gadon bayana yana ta sheki da kamshi. Gate naji an bude, nayi murmushi nasan Abbu ne ya dawo daga fitar da yayi. Na kara gyara zamana ina fuskantar mota, yana shigowa na tare shi da murmushi. A bakin kofar ya tsaya shima yana murmushin, hannu ya mika min alamun inje, babu musu na tashi na fara tafiya cikin jan hankali ina jujjuya jikina kamar wadda take rawa, kasa daurewa yayi in karasa ya taka da sauri ya taro ni tare da rungume ni. Sai daya gama welcome kiss dinshi and stuffs sannan ya umarce ni da in dauko hijabi zai nuna min abu a waje, na shiga daki na saka na fita na same shi yana jirana, hannuna yaja muka fita compound din gidan, dalla-dallan motoci biyu Land Rover Discovery fara da Vibe ja daga ganin su sabbi ne saboda yadda suke ta sheki a cikin soft hasken ranar ta alhamis. Ya miko min keys guda biyu, cike da tsananin mamaki nake kallon su kafin na maida kallona ga motocin, da kyar na iya kakaro “wadannan keys din fa Abbu?" yayi murmushi much like a grinning, “for you baby!" na zaro idanu na cikin mamaki, “duka?" ya zagaya ta bayana tare da rungume ni, “wannan..." ya nuna min jar vibe din, “is from me.... Wannan kuma..." ya nuna farar Discovery din, “is from your Daddy" nace “Dad kuma?" ya daga kafadar shi, “yanzu aka kawo ta daga can Kaduna, sai dana fada mishi cewa na sai miki amma yace shima tunda ya siya sai ki hada duka biyun kiyi amfani dasu" Daddy, my Dad! He's really the best. Ban fada mishi ba amma already ya riga yasan da irin motar da nake muradi, nayi tsalle na juya tare da rataye hannayena a wuyan Abbu ina dariyar dake nuna tsananin murna da godiyar da nake mishi duk da bakina bai furta ba. Ya miko min kumatun shi ba bata lokaci na bashi peck a kunatun, peck din daya koma deep mouth to mouth French kiss in a wink, in another wink na tsinci kaina a tsakiyar gadon Abbu, kayan sawa suna yin koina a cikin dakin....

Later da yamma na kira Daddy na mishi godiyar Mota, “Haba Uwata bari mana kar ki bata min rai? Meye abin godiya dan uba yayi wa diyar sa abinda yake responsibility dinshi ne? Beside saboda wa nake neman kudin idan ba ke ba uwata? All I wish for you is to be happy kin gane? Sannan zan tura miki da kudin sadakin ki ta account gobe in shaa Allah" nayi saurin cewa “Daddy ka bar su a wajenka pls" yace “aah, ai hakkin ki ne Nafeesah kuma ma ni bana son kudin ki" nace “to a ba Mommy" yace “itama bata so" ba shiri na saki dariya, nan muka yi sallama dashi.
Washegari kuwa ya turo min da kudin, dubu dari biyu bayan dubu dari ne sadakin, na kira ina tambayar shi dalili sai cewa yayi ai sabida in dinga ba baki da kuma sauran kashe-kashe saboda baya son in cika tambayar mijina, sai kawai nayi murmushi tare da mishi godiya.
Ina zaune Abbu ya fito daga dakinshi yana gyara karin hularshi cikin shirin tafiya masallacin juma'ah. Na tashi na taya shi kafa hular tare da raka shi har bakin kofa, yace “In kawo miki su Hafsy ne su miki yini?" da sauri kuma cike da doki nace “ehh, please Abbu" yayi dan murmushi tare da juyawa ya tafi ina mishi Allah ya kiyaye hanya. Yana tafiya na fada kicin na hau shirya musu cookies da kayan motsa baki ga kuma abinci, ina kicin din ma suka shigo gidan su da Abbu da ihun su suna kiran sunana, da sauri na fita waje nan suka kwashi ihu suka rugo suka rungume ni, nima na rungume su ina murnar ganinsu, sai da muka nutsa sannan na dago kai ina kallon Abdullahi dake gefen Abbu a tsaye, na mishi dan murmushi ba tare dana damu da yadda bai yi joining dinsu ba. Daga baya dai muka tashi muka koma cikin falo, na dauko musu duk abubuwan dana shirya musu nan fa hira ta barke, bayan mun ci abinci Abbu ya tafi daki ya dan kwanta kafin a kira la'asar ya barmu muna ta hirarrakin mu, har baya muka fita muka danyi wasanni kafin muka dawo falon. Yini guda suka mana sai bayan magriba Abbu ya maida su gida, don Hafsy ma da kafewa tayi anan zata kwana sai da kyar Abbu ya lallasota ta hakura suka tafi. Na hada su da tarkacen sweets, chocolates da tarkace dai iri-iri suka tafi.
#TeamAbnaf
#OneLove
#AnaTare





*♡Jeedderh♡*
*NI DA ABOKIN BABA NA....!*


*©°•Jeedderh Lawals•°*

*®°•Fikrah Writers Association°•*🖋



*52*


Ban sani ba shagala ce ko kuwa mantuwa? Zancen cewa angwaye kwanaki bakwai suke yi a dakin amaren su su koma na uwargida, kai in fact na manta cewa ma ina da abokiyar zama kwata-kwata a lokacin, na manta cewa bani kadai bace wadda take da Abbu, na manta cewa Abbu yana da wasu iyalan daya kamata ya kula dasu. Muna cikin cin abinci yake fada min cewa washegari idan zai je gidan Mubeenah zai dauko cousin dinsu Zaynab diyar wata kanwar mahaifiyar su zata dinga zuwa tana taya ni kwana. Na maida spoon cikin plate dina na ajiye ina kallonshi cikin alamun tambaya, and that was when it downed on me, ranar na cika sati daya cif da tarewa which means washegari zai fita daga dakina. Jikina yayi wani irin sanyi har yana hadawa da rawa na dai daure na cije na gyada mishi kai naci gaba da tura abincin da taste dinshi ya bace a bakina.
Duk yadda naso na daure in nuna mishi hakan bai dame ni ba kasawa nayi, sai daya fahimci sanyin da jikina yayi. Ya riko hannuna ya zaunar dani akan cinyar shi tare da dago fuskata, na daga idanuna da suka fara cika da ruwa na kalleshi, yace “come on mana baby kar ki bayar dani, meye kwanaki biyu kadai? Besides, zan dinga zuwa kullum ina ganinki kinji? Kuma zamu kasance a waya a koda yaushe don haka ki daina bata ranki, ni naki ne ok? Oya, give me that gorgeous smile of yours baby" na kuwa saki murmushin tare da dora kaina akan kirjin shi.

Washegari da safe ya tattara ya tafi bayan ya jira Zainab tazo, yarinyar tana da kirki ga fara'ah, na dan girme mata da shekaru tunda shekarunta ashirin. Na raka Abbu har bakin mota duk da sallamar da muka gama yi a daki, yaso ya kaini gado a lokacin nace a'ah, ba zan shiga hakkin abokiyar zamana ba don nima bana so a shiga nawa hakkin. Haka ya tafi ina daga mishi hannu har sai daya fita daga gidan maigadi ya maida gate ya rufe kafin na juya cikin gida cike da kewar Abbu, zama nayi muka dan yi hira da Zaynab kafin na shige dakina na kwanta don jiya Abbu bai barmu mun yi barcin kirki ba.

☆☆☆☆☆

“Wannan yace a cikin abinci kamar miya ko fate zaki zuba mishi yaci, manta kowa kenan. Ina mai tabbatar miki da cewa idan har yaci wannan maganin to wallahi sai dai uwarshi ta sake haihuwar wani, kin dai ga yadda mijin Umaimah (er autar su) yake mata, uwar shi ma yanzu sai Umaimah taso yake ganinta balantana wata banzar bazara wai ita kishiya, kema to haka zaki mallakeshi..., wannan kuma...." Saddiqa ta fito da wani ruwa a cikin kwalba tana nunawa Mubeenah, “...a cikin ruwan wankan shi zaki zuba mishi, shi kuma zai sanya mishi matsanancin son ki ne, ya zama babu wata ‘ya mace a cikin idanuwan shi sai ke ina fada miki, boka Saddar ya bani tabbacin a ranar zai dankarawa ita waccar banzar kishiyar taki saki uku, shi da kara aure kuma sai a lahira. Don haka ki kula sosai, ki bi komi a hankali yadda ya dace don hakan mu ya cimma ruwa kin gane?" kamar wata kadangaruwa ta gyada kai, “yauwa, ina turaren dana kawo miki last week nace kiyi tsuguno dashi?" Mubeenah ta gyada kafada, “turare? Na ma manta inda na jefa shi" Saddiqa ta maka mata harara, “wai ke banzar wani gari ce? Duk inda yake ki lalubo shi kiyi tsuguno dashi yau ba gobe ba, yaushe girkin ki zai fita?" tace “gobe da safe" tace “bamu da lokacin batawa kenan, yau yakamata yaci maganin, yayi wanka kuma ya kusance ki kina jina? Abubuwan nan da muke yi is all for u Mubeenah, kin dai san kaf danginmu babu mai kishiya sai waccan banzar yarinyar (Shakira) don kishiyar Umaimah hoto ce, don haka kema ba zaki biyo sahu ba kin gane??" Mubeenah tace “ehh".
Tayi murmushi, “yauwa., kudin aiki dubu dari da hamsin tashi maza ki dauko min" Mubeenah ta zaro ido, “dari da hamsin?" ta harareta, “to meye dari da hamsin matukar an samu biyan bukata?" Mubeenah ta gyada kai, “hakane kam. Sai dae babu kudi a hannuna sai dai idan Ibrahim ya dawo sai in amsa a wajen shi" Saddiqa ta yago hakura, “to babu damuwa, amma to dari biyu zaki tura min tunda dai nasan kema in kika tashi ba a dari biyun zaki tsaya ba" suka kwashe da dariya.
Nan taci gaba
Showing 96001 words to 99000 words out of 122880 words