da roƙon Allah yasa kada tace komai nayi hanyar banɗaki da sauri,saida naga na shige na maida ƙyauren kafin naja ajiyar zuciya,wayyo ni Sumaimah nakawo kaina ga hallaka.
Bayan nagama gyaran na fito kenan daga ɗakin naga wata tashigo falon da sauri tana kuka kaman anyi mata mutuwa.
"Mommy mommy wayyo mommy"
Da ƙarfi take maganar,anty Maimuna tunda ta daga ido ta kalleta tacigaba da abinda take,da alama kenan ta saba hakan.
Hajiya maryam ce ta fito daga ɗakin tana kallon Fatee.
Tana ganinta kuwa da sauri tazo ta rungumeta tareda ƙara sautin kukanta.
Nidai gefe na koma ina kallon ikon Allah.
"Yau kuma meya faru,ke wai bakya girmane uhm kullum kina cikin rigima?"
"Ba.....bba carry over HOD ɗin mu ya bani ba wai....kuma yana sane fah wannan ce shakarata ta ƙarshe,naje barrack kuma na faɗawa Abbah yace wai dole saina jira wata shekarar na gyarata,nasan da Mulaifah ce ai da yayi magana an barta ta wuce yiiiiihhhihiiiiii"
Kuka take tsakaninta da Allah har ranta.
"Hmmm wlh mommy karki yarda da zancenta,tana sane fah da za'ayi exam ɗin amma tayi baccinta a gida,saboda ta saba Abbah yana magana a bata ta gyara,kuma dama tun wancan lokacin Abbah yace inta sake yin sakaci irin wannan bazai sake zuwa ba"
"Mommy karki yarda da itah wlh ba haka bane,ranar fah cikina ne yake ciwo"
"Yanzu dai duk ba wannan ba wanene HOD ɗinna ku?"
"Alh sama'ila ne"
Jeki ɗakinki ki huta kici abinci zanyi masa magana,yasaka miki gyarannata a first semester da za'a shiga"
"Mommmmmyyyyy........"
"Ya isa haka karki dameni,tunda bakiyi ta ba dole saikin gyara,karkuma ki dameni ki barni da abinda yake gabana"
Dariya anty Maimuna tafara yiwa Fatee wacce tacika kaman zata fashe,da tayi zaton intayi kukan basai ta gyaraba,amma tasan tunda mommy tace zata gyara to sai ta gyara ɗin.
"Ke kuma zan fita idan anjima,zan duba miki shari'ar ko kin gano kanta"
"Ahah mommy a dubamin,har yanzu bangano yanda zan bi da itaba"
Gwaliyo tayiwa Fatee lokacin da hajiyah maryam taje kusada ita tana duba abinda yake cikin system ɗinnata.
Ohhh inda ranka kasha kallo,sudai wannan familyn basa zama waje ɗaya kenan suyi shuru.
Ɗakinmu na nufa,ina shiga naji wayata tana ringing,dama jiya nayita ƙiran number Tunga amma bata shiga,ina dubawa kuwa naga shine yake ƙirana..
Da sauri na ɗaga tareda yin sallama..
"Hello Tunga ina ka shiga baka ɗaga waya?"
"Kiyi hakuri Sumaimah wlh munje sarin dankaline wani lungu jiyan,to basuda network wajen,ga innan dama tunda naga ƙiranki nasan su kike nema"
"Yawwa "
Muryar inna Mairo naji,bansan lokacin dana saki wani ajiyayyen murmushi ba.
"Innaaaa ina wuni ya gidan kuna nan ƙalau"
"Lafiya kalau ƴar nan ya wajen aikin,muna nan ƙalau ƙalau,gamunan ma Tunga ya kawo mana dankali mun dafa muna ci"
"Inna dama kin sani?"
"Nasan me?"
"Goje uhm......."
"Sumaimah ki bar zancennan,nasani amma babu abinda zan iya cemiki a yanzu saidai kiyi haƙuri da rufemiki danayi nasakaki a cikin duhu,amma babu yanda zanyi sai hakan"
"Bakomai inna nasan bazakiyi abinda zai cutar dani ba,amma abinkam akwai ɗaure kai sosai,kici gaba dayimin addu'a toh."
"Da yardar Allah kuwa,hakan ba zai gagaraba,nasan kinga abubuwa da dama a rayuwarki na jarabawa,kuma kuma jure kikayi haƙuri,yanzu ma ki ƙara komai zai wuce nan kusa da yardar Allah."
"Ina khadija da Sayyid banjisu ba?"
Na ɗauko wani zancenne saboda kawar da wancan,a tunani na babu amfani naci gaba da faɗamata,tunda nasan hakan ba wani amfani zayyi sosai ba,saima na ƙara tada mata da hankali. A yanda naga abubuwan suke gudana na tabbatar ba laifinta bane na boyemin da tayi,hasalima tayine saboda hakanne kaɗai zabinta.
"Gasunan fah suna jinki,khadija ce ma yanzu tafita kaiwa su gaji ɗaukin dankali"
"Ayyah nayi kewarku sosai,Sayyid ya daina kukan?"
"Hhhhhh ya daina mana,kijimin saikace dama ba tafiya kike makaranta ki barshi a gidaba,ya daina kuka yakama abincinsa"
"Shikenan sai anjima inna karna cinye masa katin waya,kucigaba da sakamu a addu'a"
Daga haka nayi sallama dasu na kashe wayar.
.........
Ahmad (POV)
Tun maganar danaji Sameer ya ambata har yanzu bayan na dawo office din ma na gagara aikata komai,gabaɗaya jin ƙwaƙwalwata nake a dagule.
Duk da cewar maganar tasa batada wani ma'ana zai iya yiyuwa wani yagani mai kamada ni,kuma dama gashi lokacin darene,amma nagagara barin zancen ya subuce a cikin kaina..
Abin ya faru a abuja ne,sannan kumadu a abuja na tashi na tsinci kaina. Kai ina dole sai nayi binciken wannan maganar,idan kuwa da gaske a tsawon wannan lokacin nayi aiki dasu,to ina buƙatar wannan memoryn,domin hakan zai bani sauƙin wajen gano inda suke.
Waya na ɗauka na ƙira Eemran akan maganar.
Bayan kaman minti talatin a zaune suke amma nagagara ce musu komai,suma kuma basuce dani ƙala ba.
Sai can bayan na gama yamutsa gashin kan kafin na ɗago na kallesu.
"Eemran da Neelah akwai wani aiki danake so na baku,please ya shafi aikinmu amma yafi shafar rayuwata,dan haka ban yarda kowa yaji ba harsai na gado ainihin mai yake faruwa tukunna.
"Shekara biyu baya na tashi na ganni a asibitin WUSE dake garinnan,inason ku samomin information na su waye suka kaini asibitin?"
Kallon juna suka farayi da alama tambayar tawa ta basu mamaki,tsawon wanna lokacin dana tashi,banama so a ɗago min zancen nayi rayuwa biyar bansani ba,amma yanzu inaso nagano a ina nake"
"Yallabai amma a baya idan akayi zancen bakaso,meyasa yanzu kuma lokaci ɗaya.......?"
Neelah ce tayi tambayar amma bata ƙarisa ba,saboda tansan nagane mai take nufi..
"Buƙatar hakance ta taso,har yanzunma bawai na damu nasani ɗin bane,amma tunda har yaci karo da wannan aikin to vanida zabi. Please ku bincika sosai,inta kama ku nuna musu hotona ma,saboda ba lallaine da sunana nake amfani ba a da ɗin"
"To shikenan zamu iya ƙoƙarinmu akan case ɗin"
"Ogah zakaci abinci ne nayi order dakai"
Saida yayi zancen abinci ma na tuna rabona dashi tun jiya da daddare.
"Sure"
"Eh gaskiya kam gwanda ka dunka cin abinci,aiki ciki bai ɗauka bama baya tafiyah daidai"
Cikeda zolaya yayi maganar kafin suka fita a tare,hmmm na koma tsohon aikinnawa wato tunani.
SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
Sister's duk wacce batayi anfani da sabulun mg's ba ko kit dinsu inamai shaidamuku anbarku acan baya domin duk wnd yajaraba mg's sai sanbarka duk wani Mai tantama Akan kayan gyaranjiki toh tabbas yacire sabulun mg's domin yahadu bakarya zegyarajiki yafidda dattin fata Dama duk wani matsalan fata duk Wanda kefama da matsalan fata walau pimples ko spot, sunburn acne,stretch mark dama dukkan wani prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari bayan jikinku yy fresh zaisa jikinku yy smooth yadinga glowing,gawanda basa San anfani da Mai zaku iya using mg's batare da kunbukaci wani Mai b🤗nd wnn new soap din💣ne,😯 bama cika Baki kujaraba kugane ma idanku domin ance gani yakoriji Kuma siyan daya maida kudi gida
You can check pic👇for the soap reviews🥰
Soap price:4k
maiso yy mgn
08062991549
07046881166
07067210195
Call 08064532391
Instagram:glow_with_mgs
Facebook: mg's skincare
Masu bukatar cream Shima munadashi harda ma complete set nagyaranjiki
Small 14k
Babba 16k
Munatura Kaya kowani gari dayardar Allah Amma delivery is not free
Be part of the glow team😍karkubari abaku lbr👏
*BOOK 2*
...11...
Bayan sati guda.....
Zuwa yanzu nafara daidaita rayuwata a katafaren gidan dana tsinci kaina dayin aiki a cikinsa.
Nasan halayen ƴan gidan kaff,da kuma yanda zan zauna dasu,musamman ma uban gayyar wato Ahmad.
Duk gidan na kula saleem,Maimuna sai hajiya Mammah sune masu sauƙin hali a gidan,amma Sameer kam wanda ya dawo jiya daga aikin daya tafi,da kuma fatee,hajiyah Maryam da Ubangidannawa dukkansu sha'aninsu babu sauƙi a ciki. Hakan in mutum yashiga shirginsu ma bazai wanye lafiya ba.
A sati ɗayan danayi muna gaisawa sama sama da anty Maimuna,Dr Saleem kuwa mun ɗan fara yin mutunci dashi,wani lokacin idan naganshi a lambu yakanmin tambayoyi da suka shafi karatu.
A bangaren Ahmad kuwa har yanzu indai zamu haɗu dashi naje masa aiki toh saimunyi sabani,komai mutum yayi laifi ne,tun ina jin ɗari ɗari yanzu babu abinda nakeji idan na yi masa wani abun.
Dan haka shi yanzu bana jinsa indai a yi masa aikine,don gabaɗaya nariga nagane lokacin dawowar sa da kuma na fitarsa,mai yake in a sashensa da kuma wa yake yiwa magana a gidan da wanda baya yimusu.
Wanda ya tsayamin a rai kuma nake jin tsoronsa da kuma kaidinsa hajiyah maryam ce..
Bata fiye zama a gidan ba sosai ba,a cewarta tana zuwa wajen aikinta na gidan marayunta,wanda nasan ba haka bane.
Babu abinda yake haɗani da itah daya wuce gaisuwar safe, amma kuma abu ɗaya dana kulada itah batada tsangwamawa mutane,ko takuramusu. Hasalima tana ɗakin zanshiga gogena saidai ta bani waje nayi na gama.
Batada takurawa,to mai yasa ta tsani Ahmad kuma,kodayake shi ɗan mijinta ne,kuma jininsu bai jitu ba.
Sai mai gidan shima dana kula babu soyayya da miji da mata tsakaninsu da itah,sannan babu ruwanta da Mammah kamar ba surukarta ba.
Jiya da daddare na fito yin fitari naga shigowarta wajen shabiyun dare, motoci biyune suka shigo suna haske,ta fito a tata motar a ɗayar kuma wata mata tafito. Magana sukeyi kafin daga baya ta karbi takaru a hannu waccar ɗin,ta shiga motarta ta fita ita kuma tashigo cikin gida. Ƴar wayata rakani kashi na kalla,ƙarfe shabiyu da rabi,. Haka kawai naji ban yarda da takardun ba,dolema sainayi kasada naga menene a ciki. Ai ka gane maƙiyinka ba laifi bane saboda ka kare kanka.
Wanki nakeyi na kayana,amma hankalina akan hanyar fita yake,jira nake hajiyah maryam ta fita nashiga ɗakinnata,dan yau laraba tana cikin ranar da take fita. bincike babu kyau amma wannan yazama wajibi,rayuwar uban ɗana ce a cikin hatsari. Dan haka sai inda ƙarfina ya ƙare.
Ajiye wankin nayi nashiga sashen nata,kaina tsaye na tafi saboda nasan babu wanda zayyi tunanin wani abun zanyi,yin aiki yayimin rana.
Ohh Allah na gode maka ɗakinta ba'a rufe yake ba,amma mai yasa ita da take irin wadannan abubuwan zata bar ɗakinnta ba'a kulleba.
Anya kuwa babu matsala?.
Tsayawa nayi ina nazartar ɗakin kafin na jawo drawer ta tagado,wannan irin drawer ana yawan ajiye abu a cikinsu,Ahmad ma yakan zuba nasa a ciki.
Wayam nagani babu komai a ciki sai wasu kwalabe marasa kyau,duk inda zan duba na duba amma babu komai a cikin.
Gwiwata a sanyaye na fito daga ɗakin,cikeda jin haushin rashin samun nasara,jina nake kamar marar amfani,nakasa taimakonsa da komai,duk kuwa yawanci akan idona yake faruwa.
Hoton dayake cikin drawer ne ya faɗomin a rai,hoton wata matashiya ce kamar fatee itada wani matashin da kuma jinjiri a hannunta tana dariyah,tsufan hoton mutum zaigani ya gane hajiyah maryam ce a jiki ba fatee ba,to wannan ɗin waye,inaga to baban su Fatee ne,kai anya kuwa? Duk da cewar hoton ya daɗe amma ba shi bane. "To wayeee"
Na fada a bayyane cikeda mamaki.
.......
Neelah ce ta kalli hajiyah Maryam wacce suke zaune a cikin mota suna kallon videon Sumaimah tana bincike ɗakin hajiya maryam.
Tun daga shigowarta ɗakin har zuwa fitarta duk suna kallonta, a cikin videon da camera take ɗauka.
Sai bayan sun gama kafin Neelah ta kashe tana kallon hajiyah maryam.
"Kingani koh? dama saida na faɗamiki jiya ta ganmu kika ce bata ganmu,kina kallonta kaman batasan mai take ba,amma itama ta wuce yanda kike zaton,wannan takardun na jiya take nema"
Hajiya Maryam ce tayi maganar cikin wani murmushi na gefen baki.
Cikeda mamaki Neelah tasake kallonta a videon kafin tace.
"To ita kuma mai nata nayin wannan binciken,batasan ma takardun menene ba,idan ma tasani mai zatayi dasu,tana bayan Ahmad ne?"
"Ohh tambaya ma kike bayan kinsan komai,uhhhh hakan da tayi kuma yasa ta burgeni,batada tsoro da duhun kai,tasan mai takeyi sannan na kula bakaman sauran ƴan aikin ba tasan mai takeyi,ta wuce yanda nayi zatonta ma"
"Hajiyah shikenan haka zamu barta bazamu tsayar da itah ba"
Jijjiga kai tayi tareda yin dariya.
"Batta tayi bincikenta,tana da damar yin hakan,karki hanata saima ki bata satar amsar hanya,duk abinda ta gano zanga shin zata iya ɗauka kokuma zata kasa,duk hakan yana cikin gwajinta kafin takai irin macen da nake so. Ko ajiyeni a wajen aiki ki wuce,kwanannan banason yaran sojojincan sun faye caja kai.....Daga can kije ki faɗamasa abinda na gaya miki na binciken dayace kuyi masa,karki yarda ki bari ku ƙara daga haka"
"An gama hajiyah zamuyi yadda kika ce"
Jan motar tayi zuwa inda hajiya Maryam take aiki,wani babban wajene ya haɗa komai da komai na taimakon talakawa da marayu,kama daga sana'a harma da koyarwa.
"Ki bari basai kin rakani ba san tafi,ki cewa samuel yazo da motata ya ɗaukeni in anjima"
"To"
Fita tayi daga cikin motar tashiga wajen,cikin tafiyar isa da aji take tafiyah har ta bace,a yanayin shekarunta ba mai cewa zata iya tafiya da irin wannan takalmin idan ba gani yayi ba.
Ƙirane ya shigo wayar Neelah wacce take ƙoƙarin tada mota,dakatawa tayi tareda dagawa.
"Ehh eemran kana inane,yanzunnan zan tafi headquater,kaima kayi sauri saimu haɗu a can"
Taka motar tayi da gudu domin isa inda zataje akan lokaci.
A tsaye yake a gaban mutumin wanda kamanninsa suka sauya baka gane komai a fuskarsa saboda wahala da kuma dukan dayasha.
Ɗayane daga cikin ƴan kungiyar BC wanda aka kama shekara biyu baya,duk yadda za'ayi dashi yayi magana amma yaƙi,da haushi ya ishi masu tambayar sukayi masa lahani sosai.
Yanzu ma cewa yace a kawo masa shi ko zai iya gane wani abun,duk sun tabbatar masa da yazama mahaukaci ai da daɗewa,shikaɗai sai yayi ta dariyah yana cizon baki.
Anyi kimanin awa guda kenan Gen Ahmad yana gabansa,amma yaƙi cewa komai.
"Kai ɗago ka kalleni shin ka sanni?"
Amma shuru kaman yana magana da kungi,wani yashigo wajen tareda sara masa,kana yafara da cewa.
"Gen Neelah da Eemran suna neman izinin shigowa,tun ɗazu suke waje"
"Kace musu su shigo"
Neelah ce tafara shigowa kana Eemran,gaisheshi sukayi kafin Neelah ta miƙa masa wani file..
"Yallabai ga bayanan da muka samu a asibitin,bayan tsawon bincike bamu samu komai ba,saida muka duba files na hotunan marasa lafiya har na shekara biyun kafin muka gano naka."
Tun kafin ta gama bayanin ya buɗe file ɗin yana kallo.
Hotone kawai a jiki sai suna ta sign.
"Gojee???"
Shine abinda Ahmad Ya faɗa cikeda mamaki..
"Miye kuma goje,narasa sunan da zanyi amfani dashi sai goje?"
"Eh goje ƙwarai kuwa goje,shine shugaba ai na yanzu goje baaa"
Mutumin dayake gabansu ne yafara faɗa yana wasa da babyn robar da take hannunsa.
Da sauri Ahmad ya tsugunna a gabansa tareda cewa.
"Eh shi kasanshi?"
"Hhhhhhhh goje bindigar roba ba"
Tsuka yayi ya tashi tareda sake kallon su Neelah.
"Shikenan iya abinda kuka samo,waye to ya kaini asibitin,ƙungiyar BC ce?"
Jijjiga kai Neelah tayi kafin tace.
"A yanda suka faɗa mana kuma kaga wannan saka hannun,sunce matarka ce ta kawoka asibitin,itace ma take zaune a wajenka har ranar daka tafi. Sannan bayan ka tafi tasuma suka karbeta a asibitin,har sukayi mata test na juna biyu....bayan sun sallameta kuma basusan ta da kuma daga inda take,amma sunce jininta ya hau sosai ga yaron ciki,da ƙyar idan batayi barin sa ba"
Zaro ido Ahmad yayi yana kallon Neelah kamar ya samu madubi,mata da kuma ciki nasa wai? Abin takaicin kuma bai tuna komai ba? Tabbas daya tashi kam yaga wata mace a gefen gadonsa a kwance,kaico da bai tasheta ba,yasan da duk baisha wannan wahalar ba.
"Taya zakuce to babu sunanta da kuma garin da take,wannna ba abune da hankali zai ɗauka,kuxo muje asibitin ina buƙatar duk wani bayani daya shafeta"
"Am sorry sir,amma mun iya ƙoƙarinmu amma bamu samu komai ba,ƙarshe ma sai suka ce wai anyi musu kutse waccar shekarar,to a lokacin sun rasa data da yawa na bayanai"
Wani gumi ne ya yanko masa,bai san lokacin daya samu waje ya zauna ba yana dafe kai,wannan wane irin abune ne haka.
Tashi yayi zai fita,har yaje bakin ƙofa mai kulada wajen yayi masa magana.
"Sir ya zamuyi da wannan mutumin?"
"Zai warkene?"
"Ahah ƙwaƙwalwarsa ta lalace ba lallai va"
"To kuyi duk yanda zakuyi dashi,kai Eemran ran ka rufemin office ɗina bazan koma ba,gida zan tafi"
A hanyar zuwa motarsa yaji wayarsa tayi ƙara,shareta yayi harta katse,saida aka sake ƙira kafin ya fito da itah ya duba.
Hajiyah maryam ce take ƙiransa,har bazai ɗaga ba saikuma ya danna ɗauka.
"Har haka na zama a wajenka saikaga dama ka ɗau ƙirana?"
"Shin me kike buƙata?"
"So nake kazo inda nake akwai maganar dazamuyi?"
"Inada........"
"In kanaso kaji sunan matarka da kuma a wanne gari take to kazo inda nake,sannan kayi abinda nace"
Tana gama faɗin hakan ta kashe wayar,sauƙe wayar yayi a kunnensa tareda runtse ido,abin bai wani bashi mamaki,domin hakan ba shine farau ba. Yarigada yasan bashida wani mutum ɗaya daya yarda dashi wanda ba nata bane.
Ƙofar motar ya buga tareda jingina kansa a jiki.
Yakai aƙallah minti biyu a haka kafin ya buɗe motar ya shiga.
Kai tsaye ma'aikatar data buɗe ya nufah,ransa badan yaso ba saidan bashida zabi.
Get ɗin aka buɗe masa ya shiga,mutane sai zirga zirgarsu sukeyi,a ransa yace hankalin su kwance kaman basu san da wacce suke zaune ba.
Bayan yayi parking kai tsaye makeken office ɗinta ya nufah,babu sallama kawai ya saka kai.
A zaune take a kan kujerar da take gaban makeken wani tebur,magana sukeyi da wata. Ta gefen ido ta kalleshi kafin ta cigaba da maganar ta.
Shikuwa ganin haka yasa yakama wata kujera a gefe ya hakimce akanta. Fuskarsa babu yabo ba fallasa,duk tururin dayake cikin zuciyarsa amma haka ya shanye shi ya bayyana tamkar a nutse yake a zahiri.
Bayan matar ta fita zuyawa hajiyah maryam tayi akan kujerarta tareda ƙare masa kallo daga inda take zaune.
"A tunanina ba ƙirana kikayi domin ki ƙaremin kallo ba,dan haka ki tafi kanki tsaye maganarki,mai kike buƙata?"
"Nima a nawa tunanin ko baka ɗaukeni uwaba,naci darajar na haifi yakai,kokuma na amsa sunan matar ubaka koh.....dan haka ba gaisuwa ne malam Ahmad?".
Ɗauke da murmushi akan fuskarta tayi maganar,inba wanda yasan abinda take aikata masa ba ko shi kansa,mutum zai ɗauka a yanzun ba kallon tsana take aika masa ba sai na ta raina wayonsa,ta guma dariyar yanda ya tsime fuska shi a dole kada ta rainashi.
SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
Sister's duk wacce batayi anfani da sabulun mg's ba ko kit dinsu inamai shaidamuku anbarku acan baya domin duk wnd yajaraba mg's sai sanbarka duk wani Mai tantama Akan kayan gyaranjiki toh tabbas yacire sabulun mg's domin yahadu bakarya zegyarajiki yafidda dattin fata Dama duk wani matsalan fata duk Wanda kefama da matsalan fata walau pimples ko spot, sunburn acne,stretch mark dama dukkan wani prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari bayan jikinku yy fresh zaisa jikinku yy smooth yadinga glowing,gawanda basa San anfani da Mai
Showing 15001 words to 18000 words out of 62659 words
Bayan nagama gyaran na fito kenan daga ɗakin naga wata tashigo falon da sauri tana kuka kaman anyi mata mutuwa.
"Mommy mommy wayyo mommy"
Da ƙarfi take maganar,anty Maimuna tunda ta daga ido ta kalleta tacigaba da abinda take,da alama kenan ta saba hakan.
Hajiya maryam ce ta fito daga ɗakin tana kallon Fatee.
Tana ganinta kuwa da sauri tazo ta rungumeta tareda ƙara sautin kukanta.
Nidai gefe na koma ina kallon ikon Allah.
"Yau kuma meya faru,ke wai bakya girmane uhm kullum kina cikin rigima?"
"Ba.....bba carry over HOD ɗin mu ya bani ba wai....kuma yana sane fah wannan ce shakarata ta ƙarshe,naje barrack kuma na faɗawa Abbah yace wai dole saina jira wata shekarar na gyarata,nasan da Mulaifah ce ai da yayi magana an barta ta wuce yiiiiihhhihiiiiii"
Kuka take tsakaninta da Allah har ranta.
"Hmmm wlh mommy karki yarda da zancenta,tana sane fah da za'ayi exam ɗin amma tayi baccinta a gida,saboda ta saba Abbah yana magana a bata ta gyara,kuma dama tun wancan lokacin Abbah yace inta sake yin sakaci irin wannan bazai sake zuwa ba"
"Mommy karki yarda da itah wlh ba haka bane,ranar fah cikina ne yake ciwo"
"Yanzu dai duk ba wannan ba wanene HOD ɗinna ku?"
"Alh sama'ila ne"
Jeki ɗakinki ki huta kici abinci zanyi masa magana,yasaka miki gyarannata a first semester da za'a shiga"
"Mommmmmyyyyy........"
"Ya isa haka karki dameni,tunda bakiyi ta ba dole saikin gyara,karkuma ki dameni ki barni da abinda yake gabana"
Dariya anty Maimuna tafara yiwa Fatee wacce tacika kaman zata fashe,da tayi zaton intayi kukan basai ta gyaraba,amma tasan tunda mommy tace zata gyara to sai ta gyara ɗin.
"Ke kuma zan fita idan anjima,zan duba miki shari'ar ko kin gano kanta"
"Ahah mommy a dubamin,har yanzu bangano yanda zan bi da itaba"
Gwaliyo tayiwa Fatee lokacin da hajiyah maryam taje kusada ita tana duba abinda yake cikin system ɗinnata.
Ohhh inda ranka kasha kallo,sudai wannan familyn basa zama waje ɗaya kenan suyi shuru.
Ɗakinmu na nufa,ina shiga naji wayata tana ringing,dama jiya nayita ƙiran number Tunga amma bata shiga,ina dubawa kuwa naga shine yake ƙirana..
Da sauri na ɗaga tareda yin sallama..
"Hello Tunga ina ka shiga baka ɗaga waya?"
"Kiyi hakuri Sumaimah wlh munje sarin dankaline wani lungu jiyan,to basuda network wajen,ga innan dama tunda naga ƙiranki nasan su kike nema"
"Yawwa "
Muryar inna Mairo naji,bansan lokacin dana saki wani ajiyayyen murmushi ba.
"Innaaaa ina wuni ya gidan kuna nan ƙalau"
"Lafiya kalau ƴar nan ya wajen aikin,muna nan ƙalau ƙalau,gamunan ma Tunga ya kawo mana dankali mun dafa muna ci"
"Inna dama kin sani?"
"Nasan me?"
"Goje uhm......."
"Sumaimah ki bar zancennan,nasani amma babu abinda zan iya cemiki a yanzu saidai kiyi haƙuri da rufemiki danayi nasakaki a cikin duhu,amma babu yanda zanyi sai hakan"
"Bakomai inna nasan bazakiyi abinda zai cutar dani ba,amma abinkam akwai ɗaure kai sosai,kici gaba dayimin addu'a toh."
"Da yardar Allah kuwa,hakan ba zai gagaraba,nasan kinga abubuwa da dama a rayuwarki na jarabawa,kuma kuma jure kikayi haƙuri,yanzu ma ki ƙara komai zai wuce nan kusa da yardar Allah."
"Ina khadija da Sayyid banjisu ba?"
Na ɗauko wani zancenne saboda kawar da wancan,a tunani na babu amfani naci gaba da faɗamata,tunda nasan hakan ba wani amfani zayyi sosai ba,saima na ƙara tada mata da hankali. A yanda naga abubuwan suke gudana na tabbatar ba laifinta bane na boyemin da tayi,hasalima tayine saboda hakanne kaɗai zabinta.
"Gasunan fah suna jinki,khadija ce ma yanzu tafita kaiwa su gaji ɗaukin dankali"
"Ayyah nayi kewarku sosai,Sayyid ya daina kukan?"
"Hhhhhh ya daina mana,kijimin saikace dama ba tafiya kike makaranta ki barshi a gidaba,ya daina kuka yakama abincinsa"
"Shikenan sai anjima inna karna cinye masa katin waya,kucigaba da sakamu a addu'a"
Daga haka nayi sallama dasu na kashe wayar.
.........
Ahmad (POV)
Tun maganar danaji Sameer ya ambata har yanzu bayan na dawo office din ma na gagara aikata komai,gabaɗaya jin ƙwaƙwalwata nake a dagule.
Duk da cewar maganar tasa batada wani ma'ana zai iya yiyuwa wani yagani mai kamada ni,kuma dama gashi lokacin darene,amma nagagara barin zancen ya subuce a cikin kaina..
Abin ya faru a abuja ne,sannan kumadu a abuja na tashi na tsinci kaina. Kai ina dole sai nayi binciken wannan maganar,idan kuwa da gaske a tsawon wannan lokacin nayi aiki dasu,to ina buƙatar wannan memoryn,domin hakan zai bani sauƙin wajen gano inda suke.
Waya na ɗauka na ƙira Eemran akan maganar.
Bayan kaman minti talatin a zaune suke amma nagagara ce musu komai,suma kuma basuce dani ƙala ba.
Sai can bayan na gama yamutsa gashin kan kafin na ɗago na kallesu.
"Eemran da Neelah akwai wani aiki danake so na baku,please ya shafi aikinmu amma yafi shafar rayuwata,dan haka ban yarda kowa yaji ba harsai na gado ainihin mai yake faruwa tukunna.
"Shekara biyu baya na tashi na ganni a asibitin WUSE dake garinnan,inason ku samomin information na su waye suka kaini asibitin?"
Kallon juna suka farayi da alama tambayar tawa ta basu mamaki,tsawon wanna lokacin dana tashi,banama so a ɗago min zancen nayi rayuwa biyar bansani ba,amma yanzu inaso nagano a ina nake"
"Yallabai amma a baya idan akayi zancen bakaso,meyasa yanzu kuma lokaci ɗaya.......?"
Neelah ce tayi tambayar amma bata ƙarisa ba,saboda tansan nagane mai take nufi..
"Buƙatar hakance ta taso,har yanzunma bawai na damu nasani ɗin bane,amma tunda har yaci karo da wannan aikin to vanida zabi. Please ku bincika sosai,inta kama ku nuna musu hotona ma,saboda ba lallaine da sunana nake amfani ba a da ɗin"
"To shikenan zamu iya ƙoƙarinmu akan case ɗin"
"Ogah zakaci abinci ne nayi order dakai"
Saida yayi zancen abinci ma na tuna rabona dashi tun jiya da daddare.
"Sure"
"Eh gaskiya kam gwanda ka dunka cin abinci,aiki ciki bai ɗauka bama baya tafiyah daidai"
Cikeda zolaya yayi maganar kafin suka fita a tare,hmmm na koma tsohon aikinnawa wato tunani.
SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
Sister's duk wacce batayi anfani da sabulun mg's ba ko kit dinsu inamai shaidamuku anbarku acan baya domin duk wnd yajaraba mg's sai sanbarka duk wani Mai tantama Akan kayan gyaranjiki toh tabbas yacire sabulun mg's domin yahadu bakarya zegyarajiki yafidda dattin fata Dama duk wani matsalan fata duk Wanda kefama da matsalan fata walau pimples ko spot, sunburn acne,stretch mark dama dukkan wani prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari bayan jikinku yy fresh zaisa jikinku yy smooth yadinga glowing,gawanda basa San anfani da Mai zaku iya using mg's batare da kunbukaci wani Mai b🤗nd wnn new soap din💣ne,😯 bama cika Baki kujaraba kugane ma idanku domin ance gani yakoriji Kuma siyan daya maida kudi gida
You can check pic👇for the soap reviews🥰
Soap price:4k
maiso yy mgn
08062991549
07046881166
07067210195
Call 08064532391
Instagram:glow_with_mgs
Facebook: mg's skincare
Masu bukatar cream Shima munadashi harda ma complete set nagyaranjiki
Small 14k
Babba 16k
Munatura Kaya kowani gari dayardar Allah Amma delivery is not free
Be part of the glow team😍karkubari abaku lbr👏
*BOOK 2*
...11...
Bayan sati guda.....
Zuwa yanzu nafara daidaita rayuwata a katafaren gidan dana tsinci kaina dayin aiki a cikinsa.
Nasan halayen ƴan gidan kaff,da kuma yanda zan zauna dasu,musamman ma uban gayyar wato Ahmad.
Duk gidan na kula saleem,Maimuna sai hajiya Mammah sune masu sauƙin hali a gidan,amma Sameer kam wanda ya dawo jiya daga aikin daya tafi,da kuma fatee,hajiyah Maryam da Ubangidannawa dukkansu sha'aninsu babu sauƙi a ciki. Hakan in mutum yashiga shirginsu ma bazai wanye lafiya ba.
A sati ɗayan danayi muna gaisawa sama sama da anty Maimuna,Dr Saleem kuwa mun ɗan fara yin mutunci dashi,wani lokacin idan naganshi a lambu yakanmin tambayoyi da suka shafi karatu.
A bangaren Ahmad kuwa har yanzu indai zamu haɗu dashi naje masa aiki toh saimunyi sabani,komai mutum yayi laifi ne,tun ina jin ɗari ɗari yanzu babu abinda nakeji idan na yi masa wani abun.
Dan haka shi yanzu bana jinsa indai a yi masa aikine,don gabaɗaya nariga nagane lokacin dawowar sa da kuma na fitarsa,mai yake in a sashensa da kuma wa yake yiwa magana a gidan da wanda baya yimusu.
Wanda ya tsayamin a rai kuma nake jin tsoronsa da kuma kaidinsa hajiyah maryam ce..
Bata fiye zama a gidan ba sosai ba,a cewarta tana zuwa wajen aikinta na gidan marayunta,wanda nasan ba haka bane.
Babu abinda yake haɗani da itah daya wuce gaisuwar safe, amma kuma abu ɗaya dana kulada itah batada tsangwamawa mutane,ko takuramusu. Hasalima tana ɗakin zanshiga gogena saidai ta bani waje nayi na gama.
Batada takurawa,to mai yasa ta tsani Ahmad kuma,kodayake shi ɗan mijinta ne,kuma jininsu bai jitu ba.
Sai mai gidan shima dana kula babu soyayya da miji da mata tsakaninsu da itah,sannan babu ruwanta da Mammah kamar ba surukarta ba.
Jiya da daddare na fito yin fitari naga shigowarta wajen shabiyun dare, motoci biyune suka shigo suna haske,ta fito a tata motar a ɗayar kuma wata mata tafito. Magana sukeyi kafin daga baya ta karbi takaru a hannu waccar ɗin,ta shiga motarta ta fita ita kuma tashigo cikin gida. Ƴar wayata rakani kashi na kalla,ƙarfe shabiyu da rabi,. Haka kawai naji ban yarda da takardun ba,dolema sainayi kasada naga menene a ciki. Ai ka gane maƙiyinka ba laifi bane saboda ka kare kanka.
Wanki nakeyi na kayana,amma hankalina akan hanyar fita yake,jira nake hajiyah maryam ta fita nashiga ɗakinnata,dan yau laraba tana cikin ranar da take fita. bincike babu kyau amma wannan yazama wajibi,rayuwar uban ɗana ce a cikin hatsari. Dan haka sai inda ƙarfina ya ƙare.
Ajiye wankin nayi nashiga sashen nata,kaina tsaye na tafi saboda nasan babu wanda zayyi tunanin wani abun zanyi,yin aiki yayimin rana.
Ohh Allah na gode maka ɗakinta ba'a rufe yake ba,amma mai yasa ita da take irin wadannan abubuwan zata bar ɗakinnta ba'a kulleba.
Anya kuwa babu matsala?.
Tsayawa nayi ina nazartar ɗakin kafin na jawo drawer ta tagado,wannan irin drawer ana yawan ajiye abu a cikinsu,Ahmad ma yakan zuba nasa a ciki.
Wayam nagani babu komai a ciki sai wasu kwalabe marasa kyau,duk inda zan duba na duba amma babu komai a cikin.
Gwiwata a sanyaye na fito daga ɗakin,cikeda jin haushin rashin samun nasara,jina nake kamar marar amfani,nakasa taimakonsa da komai,duk kuwa yawanci akan idona yake faruwa.
Hoton dayake cikin drawer ne ya faɗomin a rai,hoton wata matashiya ce kamar fatee itada wani matashin da kuma jinjiri a hannunta tana dariyah,tsufan hoton mutum zaigani ya gane hajiyah maryam ce a jiki ba fatee ba,to wannan ɗin waye,inaga to baban su Fatee ne,kai anya kuwa? Duk da cewar hoton ya daɗe amma ba shi bane. "To wayeee"
Na fada a bayyane cikeda mamaki.
.......
Neelah ce ta kalli hajiyah Maryam wacce suke zaune a cikin mota suna kallon videon Sumaimah tana bincike ɗakin hajiya maryam.
Tun daga shigowarta ɗakin har zuwa fitarta duk suna kallonta, a cikin videon da camera take ɗauka.
Sai bayan sun gama kafin Neelah ta kashe tana kallon hajiyah maryam.
"Kingani koh? dama saida na faɗamiki jiya ta ganmu kika ce bata ganmu,kina kallonta kaman batasan mai take ba,amma itama ta wuce yanda kike zaton,wannan takardun na jiya take nema"
Hajiya Maryam ce tayi maganar cikin wani murmushi na gefen baki.
Cikeda mamaki Neelah tasake kallonta a videon kafin tace.
"To ita kuma mai nata nayin wannan binciken,batasan ma takardun menene ba,idan ma tasani mai zatayi dasu,tana bayan Ahmad ne?"
"Ohh tambaya ma kike bayan kinsan komai,uhhhh hakan da tayi kuma yasa ta burgeni,batada tsoro da duhun kai,tasan mai takeyi sannan na kula bakaman sauran ƴan aikin ba tasan mai takeyi,ta wuce yanda nayi zatonta ma"
"Hajiyah shikenan haka zamu barta bazamu tsayar da itah ba"
Jijjiga kai tayi tareda yin dariya.
"Batta tayi bincikenta,tana da damar yin hakan,karki hanata saima ki bata satar amsar hanya,duk abinda ta gano zanga shin zata iya ɗauka kokuma zata kasa,duk hakan yana cikin gwajinta kafin takai irin macen da nake so. Ko ajiyeni a wajen aiki ki wuce,kwanannan banason yaran sojojincan sun faye caja kai.....Daga can kije ki faɗamasa abinda na gaya miki na binciken dayace kuyi masa,karki yarda ki bari ku ƙara daga haka"
"An gama hajiyah zamuyi yadda kika ce"
Jan motar tayi zuwa inda hajiya Maryam take aiki,wani babban wajene ya haɗa komai da komai na taimakon talakawa da marayu,kama daga sana'a harma da koyarwa.
"Ki bari basai kin rakani ba san tafi,ki cewa samuel yazo da motata ya ɗaukeni in anjima"
"To"
Fita tayi daga cikin motar tashiga wajen,cikin tafiyar isa da aji take tafiyah har ta bace,a yanayin shekarunta ba mai cewa zata iya tafiya da irin wannan takalmin idan ba gani yayi ba.
Ƙirane ya shigo wayar Neelah wacce take ƙoƙarin tada mota,dakatawa tayi tareda dagawa.
"Ehh eemran kana inane,yanzunnan zan tafi headquater,kaima kayi sauri saimu haɗu a can"
Taka motar tayi da gudu domin isa inda zataje akan lokaci.
A tsaye yake a gaban mutumin wanda kamanninsa suka sauya baka gane komai a fuskarsa saboda wahala da kuma dukan dayasha.
Ɗayane daga cikin ƴan kungiyar BC wanda aka kama shekara biyu baya,duk yadda za'ayi dashi yayi magana amma yaƙi,da haushi ya ishi masu tambayar sukayi masa lahani sosai.
Yanzu ma cewa yace a kawo masa shi ko zai iya gane wani abun,duk sun tabbatar masa da yazama mahaukaci ai da daɗewa,shikaɗai sai yayi ta dariyah yana cizon baki.
Anyi kimanin awa guda kenan Gen Ahmad yana gabansa,amma yaƙi cewa komai.
"Kai ɗago ka kalleni shin ka sanni?"
Amma shuru kaman yana magana da kungi,wani yashigo wajen tareda sara masa,kana yafara da cewa.
"Gen Neelah da Eemran suna neman izinin shigowa,tun ɗazu suke waje"
"Kace musu su shigo"
Neelah ce tafara shigowa kana Eemran,gaisheshi sukayi kafin Neelah ta miƙa masa wani file..
"Yallabai ga bayanan da muka samu a asibitin,bayan tsawon bincike bamu samu komai ba,saida muka duba files na hotunan marasa lafiya har na shekara biyun kafin muka gano naka."
Tun kafin ta gama bayanin ya buɗe file ɗin yana kallo.
Hotone kawai a jiki sai suna ta sign.
"Gojee???"
Shine abinda Ahmad Ya faɗa cikeda mamaki..
"Miye kuma goje,narasa sunan da zanyi amfani dashi sai goje?"
"Eh goje ƙwarai kuwa goje,shine shugaba ai na yanzu goje baaa"
Mutumin dayake gabansu ne yafara faɗa yana wasa da babyn robar da take hannunsa.
Da sauri Ahmad ya tsugunna a gabansa tareda cewa.
"Eh shi kasanshi?"
"Hhhhhhhh goje bindigar roba ba"
Tsuka yayi ya tashi tareda sake kallon su Neelah.
"Shikenan iya abinda kuka samo,waye to ya kaini asibitin,ƙungiyar BC ce?"
Jijjiga kai Neelah tayi kafin tace.
"A yanda suka faɗa mana kuma kaga wannan saka hannun,sunce matarka ce ta kawoka asibitin,itace ma take zaune a wajenka har ranar daka tafi. Sannan bayan ka tafi tasuma suka karbeta a asibitin,har sukayi mata test na juna biyu....bayan sun sallameta kuma basusan ta da kuma daga inda take,amma sunce jininta ya hau sosai ga yaron ciki,da ƙyar idan batayi barin sa ba"
Zaro ido Ahmad yayi yana kallon Neelah kamar ya samu madubi,mata da kuma ciki nasa wai? Abin takaicin kuma bai tuna komai ba? Tabbas daya tashi kam yaga wata mace a gefen gadonsa a kwance,kaico da bai tasheta ba,yasan da duk baisha wannan wahalar ba.
"Taya zakuce to babu sunanta da kuma garin da take,wannna ba abune da hankali zai ɗauka,kuxo muje asibitin ina buƙatar duk wani bayani daya shafeta"
"Am sorry sir,amma mun iya ƙoƙarinmu amma bamu samu komai ba,ƙarshe ma sai suka ce wai anyi musu kutse waccar shekarar,to a lokacin sun rasa data da yawa na bayanai"
Wani gumi ne ya yanko masa,bai san lokacin daya samu waje ya zauna ba yana dafe kai,wannan wane irin abune ne haka.
Tashi yayi zai fita,har yaje bakin ƙofa mai kulada wajen yayi masa magana.
"Sir ya zamuyi da wannan mutumin?"
"Zai warkene?"
"Ahah ƙwaƙwalwarsa ta lalace ba lallai va"
"To kuyi duk yanda zakuyi dashi,kai Eemran ran ka rufemin office ɗina bazan koma ba,gida zan tafi"
A hanyar zuwa motarsa yaji wayarsa tayi ƙara,shareta yayi harta katse,saida aka sake ƙira kafin ya fito da itah ya duba.
Hajiyah maryam ce take ƙiransa,har bazai ɗaga ba saikuma ya danna ɗauka.
"Har haka na zama a wajenka saikaga dama ka ɗau ƙirana?"
"Shin me kike buƙata?"
"So nake kazo inda nake akwai maganar dazamuyi?"
"Inada........"
"In kanaso kaji sunan matarka da kuma a wanne gari take to kazo inda nake,sannan kayi abinda nace"
Tana gama faɗin hakan ta kashe wayar,sauƙe wayar yayi a kunnensa tareda runtse ido,abin bai wani bashi mamaki,domin hakan ba shine farau ba. Yarigada yasan bashida wani mutum ɗaya daya yarda dashi wanda ba nata bane.
Ƙofar motar ya buga tareda jingina kansa a jiki.
Yakai aƙallah minti biyu a haka kafin ya buɗe motar ya shiga.
Kai tsaye ma'aikatar data buɗe ya nufah,ransa badan yaso ba saidan bashida zabi.
Get ɗin aka buɗe masa ya shiga,mutane sai zirga zirgarsu sukeyi,a ransa yace hankalin su kwance kaman basu san da wacce suke zaune ba.
Bayan yayi parking kai tsaye makeken office ɗinta ya nufah,babu sallama kawai ya saka kai.
A zaune take a kan kujerar da take gaban makeken wani tebur,magana sukeyi da wata. Ta gefen ido ta kalleshi kafin ta cigaba da maganar ta.
Shikuwa ganin haka yasa yakama wata kujera a gefe ya hakimce akanta. Fuskarsa babu yabo ba fallasa,duk tururin dayake cikin zuciyarsa amma haka ya shanye shi ya bayyana tamkar a nutse yake a zahiri.
Bayan matar ta fita zuyawa hajiyah maryam tayi akan kujerarta tareda ƙare masa kallo daga inda take zaune.
"A tunanina ba ƙirana kikayi domin ki ƙaremin kallo ba,dan haka ki tafi kanki tsaye maganarki,mai kike buƙata?"
"Nima a nawa tunanin ko baka ɗaukeni uwaba,naci darajar na haifi yakai,kokuma na amsa sunan matar ubaka koh.....dan haka ba gaisuwa ne malam Ahmad?".
Ɗauke da murmushi akan fuskarta tayi maganar,inba wanda yasan abinda take aikata masa ba ko shi kansa,mutum zai ɗauka a yanzun ba kallon tsana take aika masa ba sai na ta raina wayonsa,ta guma dariyar yanda ya tsime fuska shi a dole kada ta rainashi.
SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
Sister's duk wacce batayi anfani da sabulun mg's ba ko kit dinsu inamai shaidamuku anbarku acan baya domin duk wnd yajaraba mg's sai sanbarka duk wani Mai tantama Akan kayan gyaranjiki toh tabbas yacire sabulun mg's domin yahadu bakarya zegyarajiki yafidda dattin fata Dama duk wani matsalan fata duk Wanda kefama da matsalan fata walau pimples ko spot, sunburn acne,stretch mark dama dukkan wani prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari bayan jikinku yy fresh zaisa jikinku yy smooth yadinga glowing,gawanda basa San anfani da Mai
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6 Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21