na kasheki,na kuma kashe wanann yaron.
Ko kuma ki amince da ƙudurina,nikuma zan bar ɗanki da rai,amma da sharaɗi duniya bazata shaidashi a matsayin ɗanki ba,saboda bazai yiwu ki auri ɗana zaki haifamin jikoki yazamana kuma wanann yana ranki ba.
Dan haka zai shiga alhalin Hamma ne a matsayin amina,dama already na faɗa musu cewar itace da ciki bake ba"
"Kutt mai kika ce, itace da ciki bani ba?"
"Da mai kike nufi,har abada bazan bada wannan lbarin ba,ke din dan Aliyu aka halittoki ba Muhammad ba,dan haka bazan taba bada albishir na kinada cikinsa ba sam.
Yanzu zabi ya rage ga naki. Zan baki wata biyu ki zauna anan ki gama bawa ɗanki soyayya,daga nan kuma dole tsana zaki dunga nuna masa,ke zaki raineshi amma raino na azaba,duk ranar da soyayyar sa ta ɗarsu a ranki to sunansa matacce,saiki zaba ko ceton jinin Muhammad na ƙarshe dayake muradin gani,kokuma mutuwarsa da taki da kuma ta dukka ƴan uwanki da ubanki?
Wanann shine hukuncinki da butulcin da kikayiwa soyayyar ɗana,kuma haka zaki girbeta har ƙarshen rayuwarki. Sannan kada ki manta,dukkan ahalin gidan suna ƙarƙashin ikona ne,kuskure kaɗan zai kaiki ga yin dana sani marar misali"......




SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.



*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)


Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150

Bismillahir-rahmanir-raheem


Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.


*BOOK 2*
...22...




Hajiyah Maryam tana zuwa nan da labarin muryarta da ƙyar take fita saboda kuka.
Yayinda nikuma a nawa bangaren badan kukan da take ba bazan taba yarda hakan ya faru ba.
Cigaba tayi da maganar wanda zuwa yanzu tana zaune tabas a tsakiyar ɗakin..
"Soyayyar yarona wanda ko zafin haihuwarsa bangama ji ba,ita tasakani amincewa da kuɗurinta,a tunanina idan yana raye ko bana nuna masa so to ba matsala,ashe vansan jure ganin ɗanka yana wahala bakada ikon taimaka masa hakan yafima mutuwar zafi,koba komai Muhammad da Amina su sun huta.
Haka na shafe wata guda ina kulada ɗana wanda nasaka masa suna Ahmad,bayan wata daya ya ƙare nasake roqarta ta ƙaramin wani watan.
A ƙarshen wata na biyunne na miƙa mata yaron,yayinda wata nurse tayimin allura yanda alamun haihuwar danayi zasu gushe.
Ina kuka ina komai haka tasaka wani dattijo data cikashi da kuɗi ya kaini gida,akan wai tsintata yayi a sume a gefen titi inda mukayi accident ,dan cewa tayi wai ƴan uwan Amina ne suka kashe Muhammad ita kuma suka tafi da itah.
Kowa sai tsinemusu yakeyi,harda marigayiya Amina wacce bataji ba bata gani ba.
Kukan mutuwar Muhammad ne ya dawo sabo saboda bayyanata,kowa na cewa ana ta ƙiran number Amina amma bata shiga da gangan dama ta gudu.
Bayan sati biyu da faruwar hakan har sannan ko magana banayi,saboda kewar yarona da kuma mutuwar abokan zamannawa wanda na saba dasu.
A lokacinne kuma wata mata tazo ƙofar gida ta ajiye ahmad ta daddare haɗeda wasiƙa ta tafi.
Wasiƙar tana ɗauke da cewar wai ɗan Amina ne ta mutu su kuma bazasu riƙe jinin Muhammad ba,dan haka ga ɗanmu nan,sunansa Ahmad.
Abinnan yayimin ciwo sosai amma ba yanda zanyi,kowa bayyi na'am da Ahmad ba,saboda baƙin Amina da suke gani,sai hajiyah Mammah wacce ta rungumeshi tamkar jikanta,hakanne kuma yasa tasake fari a idon mutanen gidan,sai a sannan nagane ashe abinda take kenan.
Kwanci tashi bayan yaye har hajiyah Mammah ta yaye Ahmad kowa ya manta abinda ya faru,nikuma saboda bana kula Ahmad yasa aka faramin ganin kaman dan bani na haifeshi bane,haka na toshe kunnuwana badan komai ba saidan kare lafiyar yarona,duk da nasan kularda take bashi na munafurcine amma dai yanamin daɗi.
Ana cikin hakanne Aliyu ya dawo,wanda nasan duk matsawar hajiya Mammah ne,lokacin da aka tada zancen aurenmu kowa ya amince,harshi da dama sona yana zuciyarsa,inaga kumani da daman munyi yarjejeniyah da itah.
Auren bayyi wani armashi,bansan kosu yayi musu ba,amma nikam jinake kaman an ɗauramin mutuwa,kulawar dayake banine ma da zuciyarsa ɗaya,tunda nasan shi bashida laifi shiyasaka ni barin wani abun ya wuce,tunda nasan ƙaddarata ce.
Bayan aurenmu da sati ɗaya zainab tazo gidana ina kuka na faɗamata mai yake faruwa,shima kuma dan ta faramin faɗane akan kiyayyar danake nunawa Ahmad. Bayan na faɗamata saida na gargaɗeta tayi shuru amma sai taƙi.
Lokacin tana goyon Neelah, tazo gida wunin arba'in,wannan magana dana faɗamata nayi dana saninta yafi cikin kwando,domin a daren tana shirin faɗawa hajiya Fatima bakinta ya manne,tayi tayi tai magana abu ya gagara,haka aka bari akan saida safe za'a kaita wajen magani.
A daren aka nemeta sama da ƙasa aka rasa,tun masu magani suna cemana tana gari kaza har muka daina nema muka zubawa sarautar Allah ido.
A sannan ɗin ban daddara ba naso ɗaukar mataki amma banyi nasara ba. Ƙarshe ma wani abu hajiyah Mammah tasakamin a jikina,duk lokacin danayi yunƙurin bata mata shiri sai naji kamar yana zuqar jinina ta ciki.
Haka nacigaba da fama da wannan yanayi babu wanda ya sani har na haifi Maimuna,koshi Aliyu bai san mai yake faruwa.
Tun bana ganin laifin Aliyu da su Aina'u har yazamo ya fara shafarsu,kuma a lokacin ne na nemi aiki na fara saboda ya ɗaukemin hankali.
Shekarar mu biyu da aure muka tare a sabon gidan Aliyu,wanda shine wannan,a sannan ne kuma aka bashi muƙamin general.
Naji daɗin dawowar wani gun kuma banji daɗi ba,saboda ninake kulada Neelah,sannan ina kallon Ahmad duk da bana kulashi,amma kuma koba komai na daina ganin hajiyah Mammah a kusada ni. Dan babu ɗan adam dana tsana a rayuwata kamarta.
A haka rayuwar tacigaba da tafiyah harna haifi su Saleem inada cikin Fatee.
Lokacin na zama babbar lawyer,shikuma Aliyu yazama air marshall a shekarar,wanda duk da saka hannun abba nah,saboda rashin Muhammad yasa yake ganinsa tamkar magajinsa.
Can you imagine wani kisan raini hankali wai su abba Hamma da hajiya Fatima sun dawowa daga umarah tayar motarsu ta kunce motar ta ƙone. Ko qur'ani aka bani na danna nasan aikin hajiya Mammah ne,amma ya zanyi toh shikenan suma ta gama dasu.
Lokacin da abban nah yaji wannan labarin shima ciwon zuciyarsa ya tashi,dama ba lafiyace dashi sosai ba,yamayi retire.
Bayan wani lokaci Aliyu ya damu sai ya dawo da hajiyah Mammah gabansa,saboda ita kaɗaice dukka yaran gidan sunyi aure. Mariya kamma watan haihuwarmu kusan ɗaya,ta haifi Mulaifah tanada cikin na biyu.
Ita a haihuwa ta rasu ɗan shima ya koma,nikuma na haifi Fatee aka sakamata sunan hajiyah Fatima.
Neelah kuma saboda babu hajiyah Fatima saina kaita gidan marayun dana ke kuladashi,lokacim ma ba babba bane,amma tunda bazan iya riƙeta kusada ni ba gudun cutarwar hajiyah Mammah gwanda na kaita inda zata dunga ganin yara sa'anninta,kuma atleast zan dunga ganinta kullum.
Batayi ko wata ɗaya bama Aliyu ya kaisu india itada Ahmad wajen amininsa zasuyi karatu a can.
Kasancewar lafiya suke yasa na kwantar da hankalina na cigaba da kulada wanda suke gabana.
Ana nan har akayi auren Maimuna,itakuma Neelah bayan sun gama makaranta ta dawo gida tana training ɗinta a nan abuja,amma bata zauna a gidan ba saita zauna a barrack,shikuma Ahmad bai dawo ba sai daya gama komai.
A tunanin sa kokuma nace tunanin da aka saka masa kuma yake gani,nafi kowa tsanarsa a duniya,nan kuwa a kaff rayuwata dana tashi na tsinci kai na a uwa,kullum banda lissafi saina suwa yake tareda su,cutar dashi suke kokuma ahah"
Kukane ya kubce mata wanda nima yasakani kukan,dama abinda yake faruwa kenan, tabbb lallai idan kaga mutum ya kabarshi,wato kenan ita kura ce da fatar akuya tazo ta labe anan wajen.
"Kenan matar dana gani da wata ta shige jikin bango ranar danaxo gidannan......."
Ɗago ido hajiyah Maryam tayi tareda ɗaga min kai.
"Ita kika gani ba kowa ba,itada wanann shegiyar Raheenan,wacce ta ɗaukemin yaro lokacin dana haifeshi,su ne kika gani inda sun san kin gansu da tuni bakya numfashi,shiyasa nake cemiki kiyi taka tsantsan kada ki maimaita kuskurena."
"Wannan hoton dana gani shine baban Ahmad,amma kince bai san Ahmad ba,ya na ganshi kuma a hoton?"
"Bada shi akayi hoton,ni kaɗai nayi hoton ranar sunansa,wanda na roqi hajiya Mammah ta barni nayi,shidin bayarwa nayi aka hadamin kamar yana cikin hoton"
Uhm jijjiga kai nayi tareda jajanta lamarin,shin waye zayyi tunanin abinda yake faruwa kenan idan ba gani yayi ba,lallai in kuwa hakane akwai aiki a gaba.
"Akwai wani aikin da zakiyimin Sumaimah"
Hajiyah Maryam ta faɗa tana tafa ƙafaɗa tareda jan majina,wanda tafito saboda yawan kukan data sha.
"Please ki zauna dashi a wannan kwanakin,na ɗago cewar shiba ɗan Aliyu bane,dole za'a faɗamasa waye ubansa,kuma ace shi ɗan tubabbiyane wacce ƴan uwanta suka kashe ubansa,daganan wanda bai sani bama zai sani,dan haka be with him"
"Ammm........amma taya zan zauna dashi bayan baisan ni wacece ba, bayason ina yin kusada shi alhalin yana ganina a matsayin wacce ba muharramarsa,saida nayi miki alƙawarin zan taimaka miki wajen ganin mai yake faruwa,sannan daga gobe zan fara aiki a sashen hajiyah Mammah,saboda gano wani abun"
"Ahah bazan sakaki wannan aikin mai hatsari ba idan tagano wacece ke bazatayi tunani na biyu ba zata kasheki,ta kashe ɗanki. Kinsan ke wacece yanzu haka a wajenta kuwa......?
Matsafanta sun nuna mata wacce zata kawo ƙarshenta matar ɗan data raba da iyayensa ne wato Ahmad. Sannan matar dazatayi sanadiyyarta itace uwar ƴaƴan sa. Abinda bata sani ba ya riga yayi auren,da ta sani bazata hana Mulaifah aurensa ba,hasalima ita zata ƙarfafa hakan. Shiyasa kada ta gano matsayinki ba yanzu ba tukunna"
"Nasan da hakan kuma zan kiyaye,amma ki sani nima rayuwar ɗana data mijina nake dubawa"
"Shikenan kije ki kwanta dare yayi zanyi tunani akai zuwa safiya."

Da haka na bar sashen hajiyah maryam ɗin zuwa namu sashen,duk da banida waya a hannuna amma nasan dare yayi sosai,dan tsitt kakeji babu motsin komai a gidan.
Daidai nazo farfajiyar gidan zan wuce sashenmu naga mata guda da alkyabba,wadanda dai nagani farkon zuwana gidan.
Yanzu kaman wancan lokacin ta jikin katanga suka wuce,daidai inda naga wannan zanen.
Jijjiga kai na nayi tareda cize baki,wannan karon ko ɗar na tsoro banji ba na wuce.
"Aradu kaman yanda kika gama taggunki to sai ya karye,kodan saboda rayuwar mijina dana ɗana bazan saurara miki ba sai asirinki ya tonu,wanda kike tsoron karsu gane kuma kike komai dominsu wato ƴaƴan ki,saisun gane wacece ke"


To fah Sumaimah in action.......let go!!!.




SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.



*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)


Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150

Bismillahir-rahmanir-raheem


Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.


*BOOK 2*
...23...





Gudu gudu sauri sauri tayi parcking motar a ƙofar wani gida,kaman an turata ko gama saita ta batayi ba ta buɗe ƙofar ta faɗa gidan fa gudu.
Hannunta na kan bakinta,kana ganinta kasan kuka take tarewa da hannun.
Kai tsaye wani sashe ta nufah a gidan ba cikin gidan ta shiga ba.
Domin gidan kana kallonsa da alama na haya ne amma na masu aji.
Banke ƙofar tayi ta shiga farlon,ba kowa a ciki dan haka ɗaki ta shige.
Wata matashiya ce mai matsaikacin a jiki a kwance akan gado fanka na seseta tata tana bacci.
Gadon ta hau tareda ɗaga mata duka a hips ɗinta.
Wata zabura mai baccin tayi tareda kallon Mulaifah cikeda mamakin ganinta da tsakar rana a gidanta.
"Ke lafiya na ganki kaman an jefoki iyanzu,daga ina haka?"
Maimakon ta bata amsar maganar ta saima kuka data kece dashi da danasani da kuma takaici.
'Magana nake miki Mulaifah amma kinyi shuru vakicemin komai ba"
"Padush na shiga uku shikenan rayuwata ta ƙare nikam wayyo Allah nah"
"Wai maiya farune?"
Wata takarda da take hannunta ta jefawa padush ɗin,wacce take ɗauke da sunan asibiti.
Da sauri hannunta har yana rawa ta buɗe takardar,zaro ido tayi da alama ta karanta abinda ya saka Mulaifah kuka.
"Ciki..... Omg how,garin ya hakan ta faru mai kike tunani?"
"Nima bansani ba besty,kuma fah ina amfani da magani yanda ya kamata"
"Uhm na waye to a samarinki,nasan bazai wuce useey ba koh"
Ɗaga kai tayi kawai ba tareda ta bata amsa ba.
"Ya sani amma?"
"Yasani dashi ma mukaje asibitin"
"To kuma miyasa kuka dawo ba'a zubarba?"
"Hmmm sunce wai zan iya rasa raina idan natakura saina zubar,saboda mahaifata batada ƙarfi,nayi amfani da magani sosai,ga kuma abortion danayi sau biyu,idan nasake wai zan iya samun bleeding mai tsanani.
Duk da hakan ya takura akan sai an zubarmin shi bai shirya karbar dan shege ba yanzu,wai sunan iyayensa zai baci,musamman da yana neman minister.
Nikuma sai naƙi a zubar ɗin,dan gaskiya ban shirya mutuwa yanzu ba.
To akan hakane mukayi fada dashi ya tafi,yace kuma idan nasake nemansa sai ya batar da rayuwata.
Padush ina cikin tsaka mai wuya,dan Allah ya kikega zanyi yanzu?"
"Uhmm badan badan ba akwai wata shawara,cikin wata nawane"
"Two month ne fah,munje yin gwaji ne na kowanne wata aka ganshi"
Wani juya ido padush tayi tareda gyara zama,
"Badama kince har yanzu baki haƙura da auren Ahmad ba?"
"Eh ban haƙura ba amma yanzu kam kinsan bazai yiyu ba ai,tun bayan da aka ce shiba ɗan abba bane zance ya watse,bama ko magana dashi ma fah yanzu wata biyu kenan,shine ai na koma wajen usseey rage zafi,kinga abinda na jawowa kaina nan"
"To mai zai hana ki maida cikin na Ahmad inyaso,i think kaman zayyi,kinga idan ya san cewa nasane to a gidan za'a saka dole sai ya aureki,shima kuma zai dunga kulawa dake tunda yana tunanin abinda ya aikata miki. Tunda kince cikin two month ne to definatly a wata bakwai nan gaba zaki haihu kenan... Sai mu kasheshi muce ɗan bakwaine batareda kowa ya ganshi ba,kinga ke kuma daga kin warware sai ayi muku aure"
"Wow wannan labarin yayi daɗi,amma taya zai kasance,sanin kanki ne ko karen haukane ya ciji Ahmad to bazai nemi mace ta wannan hanyar ba"
"Tsiyata dake gidadanci,to dama haka kawai zamu je masa,maganin tada ƙarfaffa sha'awa zamu saka masa,wanda ko shi robot ne to bazai iya riƙe kansa ba,saikin tabbatar yasha yafara aiki tukunna saiki je sashennnasa,daga nan ki ɗau wayarsa ki ƙira numberki.
Idan komai ya wakana da safe saikiyi kukan ƙarya,kice masa ƙiranki yayi,to da kika zo bakisan mai yake faruwa ba kawai ya afka miki,gashi da ƙarfi ya farmakeki har kika kasa ƙwatar kanki......haka haka dai nasan dole zaice ki boye abin yazama sirri,daga nan sai ki nuna masa alamar kinada ciki,saiki kai maganar wajen su Abbah.
A lokacin vashida zabi daya wuce ya aureki'"
Tun kafin padush tagama bayanin Mulaifah ta rungumeta saboda tsananin murna,ganin lokaci guda tasamu mafita akan matsalarta.
Daga haka suka cigaba da tsara yanda plan ɗin zai tafi musu a cikin nasara.
Basu tashi ba saida suka ƙira wani doctor saurayin padush ɗin akan a ina zasu samu maganin amma mai ƙarfi sosai.

Sumaimah (POV)


A tsawon wannan watanni biyu da faruwar zancen auren Ahmad da Mulaifah mun samu ɗan kusanci kaɗan fiyeda na da nida Ahmad. Wanda kowa idan ya kalla yasan soyayyata ce tashiga zuciyarsa,kokuma nace zuciyarsa ta ganeni,ƙwaƙwalwarsace dai har yanzu bata ganeni ba.
Ni abinma wani lokacin har dariya yake bani,idanna ga yana hade rai idan ya ganni da Saleem ,bama ya Sameer wanda shima ya dawo daga aikin daya rafi yi,shikamma har kalmar so ya furtamin, a amma lokacin nace masa yayi haƙuri ni matar auece,lokacin dana faɗamsa bai yarda ba saida na rantse masa tukunna.Tundaga lokacin muke mutunci dashi,amma shi Ahmad bai sani ba,gani yake kaman soyayya mukeyi,nikuwa ban taba faɗamasa gaskiya ba,shima ya ɗanɗana yaji yanda naji kokuma nace nake ji. Shima Sameer yanzu nice nake yimasa abinci a gidan, shikuma Saleem in yana nan a sashen Ahmad yake ci. Sameer ma abinda yasa baya zuwa don basa shiri da Ahmad ɗinne,har yanzu yana zarginsa a cewar shiya gani a wajen satar da akayi shekara biyu baya.
A bangaren hajiyah maryam kuwa yanzu har raina nake ɗaukarta tamkar mahaifiya ta,yayinda itama take ji dani tamkar ƴar ta,amma yawanci mukanyi zancene a sashenta inna je yimata aiki,duk da ta hanani ma amma nice na nace akan zan dunga yimata.
Yanxu ma a kitchen nake na dukka gidan ina yin abincin karyawa,Ahmad bayanan yaje Kaduna jiya,da yamma zai dawo.
Dan haka shi yau bashi a abincin safen,iyah Sameer ne kawai da hajiyah maryam,wanda don ita ma na tashi dawurin saboda zata sha magani,jiya a gidan marayunta muka wuni an ƙara mata jini. Duk lokacin danaga tana wahala yanxu haushin hajiyah Mammah nakeji,don nasan itace ummul aba'isin na duk abinda yake faruwa a gidan.
Jallof ɗin taliya nayi mai ruwa ruwa tasha sardine,a warmer na sakawa Sameer nasa,ita kuma a plate na zuba saina kife da wani.
Saida na kai masa nasa kan dining table kafin na wuce sashen hajiyah maryam.
Neelah bata nan tare suka tafi da Ahmad dan haka nice kaɗai mai kulada itah,tunda ni kaɗaice nasan abin dayake faruwa.
Bata ɗakin,amma akan gadon akwai alamun bata daɗe da tashi ba,kenan tana banɗaki.
Ajiye abincin nayi na yaye zanin gadon,ganin alamar jini jini daya bata gadon,wanda nake tunanin inaga daga jikin carnular ta yafito.
Bayan na cire ina shimfiɗa wani tashigo ɗakin jikinta da ruwa,wanka kenan tayi.
Gaisheta nayi tareda yimata ya jiki,ta amsa cikeda fara'ah,ta samu ƙarfin jikinta ba kaman jiya ba.
A bakin gadon ta zauna na miƙo mata abincin,kana na buɗe drawerta na miƙomata magani.
Bayan ta gama ɗan zance mukeyi wayar ta tayi ringing,Neelah ce taƙira taji ya jikinta. Sun fara magana kenan na dauke kwanon na basu waje. Dan yanzu babu wani zance labe na rigada nasan bazata taba cutar da Ahmad ba,kuma bugu da ƙari nariga da nasan wacce take aikata komaiɗin.
Lokacin dana maida plate ɗin ummi harta fara wanke wanke,banyi koƙarin tayata ba dannasan batason hakan.
Ina ajiyewa ma naga wayata tana ƙara.
Yau wace rana nace a raina,yah Musbahu ne yake ƙirana.
Sun fito daga wajen aikin kenan,kai mashaallah dan dama ƙiranmu na ƙarshe dashi tun kafin nazo gidanann,wai an turasu wani waje aikinsu na farko,kuma wajen ba service,harsu gama ba waya.
"Yah Musbahu kaine dagske?"
Dariya yayi kafin yace .
"Nine mana mai kika gani?"
"Wata huɗu fah kenan kona ce biyar"
"Uhm Alhamdulillah mungama ai,jiya na dawo gida da daddare,naje gidanki akace wai bakyanan kin tafi aiki abuja.....Sumaimah meyasa,aikatau fah akace kinayi?"
Shuru nayi na kasa bashi amsa,nasan dama dole sai yaji babu daɗi. Hawayene naji yana shirin zubomin nayi saurin maidashi. Inata garauniya na manta ashe inada wanda suka damu dani.
"Lahh yah Musbahu karka damu ba wani aiki bane fa sosai,bawata matsala. Ina su ammi,kaje gidana kace yasu deeja da Sayyid da inna".
"Duk suna nan ƙalau,banida lokaci gobe zan koma kaduna da nazo na ganki,amma karki damu bayan mungama da kaduna abuja za'a turamu headquarter indai an tabbatar da ƙwazonka,Inshaallah idan na dawo abuja zaki bar wani aikin aikatau"
"Tom Sheeshah Allah ya kaimu yah Musbahu nagode"
"Ameen ya Allah"
Cikin sanyin jiki na sauƙe
Showing 36001 words to 39000 words out of 62659 words