hakan a wajensu daidai yake da shiga hatsari dukkanmu"


∆∆∆

"Sani kuma na nawa Maryam,lallai kin raina wayona da kuma abinda zan iya sosai"
Hajiya Mammah ta faɗa wacce take zaune gabanta dauke da ƙwaryah wacce take ganin abinda yake faruwa a ɗakin asibitin.

Muje zuwa..........









SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.







*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)


Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150

Bismillahir-rahmanir-raheem


Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.


*BOOK 2*
...34...


Ciza yatsa tayi tareda jan hannunta a iska ƙwaryar ta bace.
"Ba abinda ta faɗamusu daya danganceni,ita kuma waccar matar Ahmad wacce na daɗe ina nema naganta amma ya ƙi nuna fusakarta har yanzu,saidai neman ta daga baxayyi wahala ba,tunda nagano tana tareda su"
Kaltum ce ta kalli hajiyah Mammah tareda cewa.
"Meyasa to ba'a ganin fuskarta,da alama wajen da muryar ta ɗaukema sunan ta aka ambata,ko wata shu'umar ce kai itama?"
"Ahah ruhinane yayi rauni,kullum hakan zai cigaba d kasancewa idan ba ban kawar da waɗannan mutanen ba"
"Ki shirya yau inada meeting,zan ɗora wani a kujerar bello"
"Toh amma shugaba ya za'ayi da neman matar shi ........."
Wani dariya tayi tareda cewa.
"Ki ƙaddara na sameta,tunda har duk yaran gidan da kuma ita kanta Maryam tasan wacece,to samun bazai mun wuyaba,samota kamar nayine"
"Gobe zamu koma gida, sannan ina so darennan na kafe ruhin Maryam,ƴaƴan ta su zaba,ko rayuwarta kokuma su rufe wacece matar Ahmad"
Wata ƴar tsana ta ɗauko a gefenta, an caccaka allurai a tsakiyar ƙirjinta,ga kuma zarruka an ɗaureta dasu. Zaren tafara ja tana wasu kalamai,lokaci ɗaya ɗakin ya turnuƙe da duhu. Kultum na ganin haka ta fita daga ɗakin da gudu,saboda tasan idan wannan ruhinnata ya fito daga akwatin suka haɗa ido,kwana zatayi tana mafarkin sa.
Zagaya ta yakeyi yana wani ƙugi,yayinda itakuma idonta ya rufe tana ta karanto wasu surkulle.
Can kaman wani lokaci ta tsaya da abinda take tareda da fara tari har jini yana zuba.
Wani rishi ruhinnata tayi wacce kamarsu ɗaya da itah.
"Hahahhaha nace miki kin tsufah ki musamu,banda kina aiki da jini domin maida ƙuruciyarki da tuni bazaki kai wannan shekarun kina aiki damuba. Kuma kinsan dokar aiki,duk ranarda kika kasa iyah damu to jininki mallakinmu ne.......uhmmm zayyi daɗi kuwa,munasan gubataccen jini ahhhhhhhh"
Tana cikin maganganunnata mai kamada raɗa hajiyah Mammah ta daka mata tsawa.
"Ƙarya kike,banga ranar da zaki fi ƙarfina ba,ke baiwata ce kaman yanda dodo ya bani saboda ki yimin aiki. Dolene saina gama cika burina,sai na gama ɗaukar dukkan fansana tassss"
Tana faɗin hakan ta ɗakko wata kwalba a cikin akwatin,ja ce wani abu yana juyawa a cikin ta yana walwali.
Baki ta saka ta zuqo abun zuwa cikinta.
Lumshe ido tayi jin ƙarfin dayabi jikinta. Buɗe ido tayi jajaye dasu suna fesar da wani jan haske.
"Yanzu na umarceki daki je ki riƙemin Maryam,ruhinta nake so yakasa sukuni a jikinta sam"
"Ahhhhhh ruhinki ya amshi buƙatarki kuma zai cika"
Tana gama faɗin hakan ta bace a iska,
Sauƙe ajiyar zuciya hajiyah Mammah tayi tana kallon kwalbar da take hannunta.
"Ina so na kasheki,amma saina samu wanda zan cigaba da zuqar jininsa tukunna. Yanzu dolene ki kasance a wannan halin har sai nagama da wannan yarinyar tukunna."
Maida kwalbar tayi cikin akwatin kana ta maidashi cikin ƙarƙashin gadonta ba tareda ta rufe ba,saboda wanda take rufewa a cikin akwatin baya ciki.


∆∆∆

Bayan gama bayanin tashi Ahmad yayi akan zai mayar Fatee da Sumaimah gida,in yaso gobe saisu dawo.
Sun fita kenan sukaji hajiyah Maryam tafara jijjiga kamar zata karya gadon da take kai..
A rikice dukka suka juyah kanta tareda da daddane sassan jikinta..
Sukam su Fatee kuka suka fashe dashi ganin abinda takeyi.
Jini ne yake fita ta hancinta,yayin idonta kuma ya koma fari soll kamar ba'a taba halittar ƙwaya daga cikinsa ba.
Ahmad ne yayi ƙarfin halin yin magana a wajen, sauran daga mai kuka sai wanda yayi suman tsaye.
"Saleem maza ƙira likita yanzunnan"
To yace cikin karyayyiyar murya ya fita.
Tun kusan magriba suke abu ɗaya har dare ya fara.
Mazanne sukaje sallah,matan kuma anan gidan marayun sukayi sallah,an basu abinci ma amma babu bakin ci.
Bayan sun dawo daga masallacin wata mota suka gani ta shigo wajen baƙa.
A.M Aliyu ne ya fito daga cikin motar a razane zuwa cikin asibitin.
Ahmad ne ya kalli su Sameer.
"Waye ya sanar dashi,yaushe ya dawo garin?"
"Bansan yaushe ya dawo ba,amma ai dole dama zai san mai yake faruwa ba,abin yayi zafi sosai wanda da alama sai an fita da itah wata ƙasar"
"Uhm uhm ba abinda ya shafi wata ƙasar bane,da sannu zamu samu mafita"
Karisawa sukayi inda yake,yana ganinsu yazo inda suke da sauri,in mutum ya ganshi bazaice shine dakyakykyen sojan nan ba,lallai ba ƙaramin so yakewa hajiyah maryam ɗin ba.
Hannun Saleem ya kama tareda cewa.
"A ina aka kwantar da itan,ya jikinnata. Fatee tace wai ta daɗe batada lafiya ana ƙaramata jini,yaune yayi tsanani sosai"
Ganin yanda yake maganar a gigice ne yasa Ahmad jijjiga kai,wato Fatee ce ta faɗamasa mai yake faruwa,duk da an hanata,this thing is no more secret,dolene su ɗau matakinsa da wuri. Abin tsoronsa ɗaya wacce ake tsoron da sani tariga ta sani,abin sauƙin ɗaya batasan sunsan wacece ita ba.
"Eh batada lafiyah Abbah,ɗazu kam da sauƙi har tayi magana,daga baya abin ya rikice sosai,amma dai likitoci suna kanta domin yin nasu ƙoƙarin"
"Tun ɗazun jikin ya rikice amma ba'a sanja asibiti ba,mai yasama aka kawota wannnan wajen,yakama ta in fitane ma an fara shirye shirye zuwa yanzun"
"Itace batason zuwa wani asibitin,saboda batason asan batada lafiyah,Sannan da alama jinyarta kaman bai shafi asibiti kaɗai ba,hadda na musulunci za'a haɗa,wato islamic medicine"
"Eh to sai ayi ai dukka,yanzu dai barinaje naga jikinnata"
Yana gama faɗin hakan ya nufi cikin asibitin,waya ya ɗauko daga cikin aljihunsa,jin ya ambaci sunan Mammah yasa Ahmad runtse ido tareda barin wajen.
Shikenan is no more sceret,duk da yasan tasan dama mai yake faruwa.
"Salam Mammah muna asibiti ashe maryam ce badata lafiyah,nima dawowata garin kenan nasani......eh ba lallai ki sani ba wai bataso a sanine........ya kawoki wannan gidan marayun data gina anan aka kwantar da itan. Eh shi to shikenan Allah ya kawoki lafiyah"
Daidai ya isa wajen da su Fatee suke ya kashe wayar,duk sunji abinda ya faɗa.
Zaro ido Sumaimah tayi tareda haɗiyar yawu,batason ko yaya hajiyah Mammah tazo ta sameta a wajennan.
Tashi tayi ta gyara mayafinta kana ta kalli su Fatee.
"Anty Maimuna ni zan koma gida naji cikina yana........."
"Ahh dama yakamata ki koma gida,kar hakan zaman ya miki illah gaki bake ɗaya ba,kije gida kici abinci ki hutah"
"Tom barina leƙata kafin na tafi,dan Allah idan hajiyah Mammah tazo karkuyi mata zance nah please"
Murmushi Fatee tayi tareda cewa.
"Karki damu matar bro bazamu ce komai ba,dama mai kamata kowa ya saniba sai mommy ta warke muyi miki official introduction,kina kirki kin dace da yah Ahmad,Allah ya barku tare"
"Ameen ya Allah nagode,Allah ya bawa ummee lafiya ya tashi kafaɗunta"
"Ameen ya Allah"
Fatee tafaɗa cikin rawar murya tana shirin kuka.
Tashi tayi zuwa wajen windown da take ciki.
An bar A.M Aliyu ya shiga inda taken,har sannan jijjiga takeyi,kodaga nesa ka gani kasan tana jin jiki sosai.
Hawayen idonta tashare tareda cewa.
"You are not deserve this,Allah ya baki lafiyah ya saka miki. Da sannu sai taga sakayya akan abinda takeyimiki......ina miki fatan samun sauƙi"
Sakin ƙarfen windown tayi tabar wajen.
Inda su Sameer suke ta nufah,Ahmad baya wajen.
"Saleem ina Ahmad yayi?"
Ta tambaya cikin ƙaramar muryah.
"Yaje yin wayah ne yanzu,gashi can"
Ya nuna mata ɗan gefensu kaɗan.
Ɗaga kai tayi tareda nufar inda yake,daidai lokacin ya gama wayar,kansa ya ɗora akan saman motarsa yayi shuru.
Cikeda tausayawa take kallonsa, a yau yagane matsayinta a wajensa,a yau kuma yake ganin kamar zai rasata,ganinta cikin wannan hali ma abune da duk wani ɗa sai yayi da gaske ya daure.
Takawa tayi a hankali zuwa bayansa,hannunta tasaka ta saqalo ta bayansa kana ta ɗora kanta a bayannasa.
Shuru sukayi na wasu mintunan kafin ya ɗaro nasa hannun akan nata.
"Lafiyah kike,kin gaji koh,ko yunwa kikeji,yanzu nake shirin tafiya neme muku wani abun"
"Ahah ba wannan bane,inason tafiya ne kafin hajiya Mammah ta tarar ni a nan wajen.....bayan haka ƙalau nake,kaifah ykk nasan kana cikin damuwa,amma ka daure ka jure. Kowanne tsanani yana tareda sauƙi. Sannan bawa bazai zama mai miƙa lamuransa ga Allah ba face ya jarrabeshi da gurare da dama. Idan ka jure kaci sai komai yazo da sauƙi"
"Uhm naji bayaninki,nagode da samunki. da Sannu zan cigaba da yimata addu'ar samun lafiyah,itakuma da take ba daidai ba Allah ya yi maganinta."
"Ameen ya Allah"
"Muje na saukeki a gida"
Hannayenta ya kama ya buɗe mata motar ta shiga kafin ya zagaya ɗaya bangaren.
Tafiyah suke babu wanda yake cewa komai,kawai hannun ta yakama yana tuƙin,ɗan Murmushi tayi,dan ya kula yanason kama hannunnata.

Sun barin wajen driver ya kawo hajiyah Mammah itada Kultum,lokacin tara na dare yayi.
Ta ɗau wani glass tasaka,tana tattakawa a hankali.
Hannun A.M Aliyu yakama suka shiga inda take. Tana ganin halinda hajiyah Maryam take ta fashe da kuka tana gogewa da gefen zaninta.
"Allah sarki baiwar Allah,wannan wacce irin wahala ce haka kika gamu da itah ƴar nan?"
"Wlh nima Mammah bansani ba sai yanzu,a she ciwon yaci ya yacinyeta. Naso ma fita da itah,amma su yaran sun ce yakamata ayi na islamic ma,saboda abin yana kama da kamun aljanu"
"Eh to hakane kam kace wani abun,amma kasan fah akwai wani lokacin da ciwukan zamani sai kaga kaman na aljanu,sai anke asibiti kaga ashe zallan kamen ciwone"
"Wasu kam suna zuwa da haka,abinda yasa na yarda da maganar su likitocin munyi magana dasu,sunce wai basuga komai ba a jikinta,ko ɗagawar da kirjinta yake sunce basuga komai ba."
"Hasbunallah,shikenan sai a yi na musuluncin,akwai wani malami zanyi masa magana akan matsalar"
"Hakan ma yayi,Allah ya bata lafiyan ya tashi kafaɗunta"
A.M Aliyu ya faɗa cikin damuwa.
Kallonsa hajiyah Mammah tayi tareda cewa ameen cikin ƙasan maƙoshinta.

∆∆∆

A bakin get Ahmad ya sauƙe Sumaimah,bayan yabata nata abincin,yaso rakata har sashensa,dan shi a son ransa yafison ta kwana a can, amma taƙi yarda,haka yayi mata sallama ya juyah.
Sashensu ta nufah,ummi da inna ladiyo sunata hira sun kunna fitila kasancewar sannan aka ɗauke wutah,ba a kunna generator ba.
Sallama tayi tashiga ɗakin,shuru sukayi suna kallonta,ganin yadda take tafiyah kaman an yi mata mutuwa.
"Ke kuma daga ina haka tun rana,kikaje kika ɗebo damuwa?"
Zama tayi tareda ɗora kanta a kan cinyar inna ladiyo.
"Inna ciwon hajiyah Maryam ya tashi,wannan karon har yafi nada,inna bakiga ba kaman bazata waye safiyar gobe ba,duk da rai da mutuwa na hannun Allah"
Hannunta ta ɗora akan Sumaimah tareda jan numfashi.
"Tana ganin jarabawa kam a gun matar can,amma in Allah yasa da sauran kwananta sai kiga komai yazo da sauƙi. Ki kwantar da hankalin ki,Inshaallah zata samu sauƙi"
Da haka inna ladiyo ta lallami Sumaimah taci abincin ta tazo dashi,hankalin ta kuma ya ɗan kwanta ba kaman nada ba..
Dare ya fara kowa ya kwanta,amma Sumaimah gabaɗaya ta kasa bacci,sai juye juye take,tunowa da wani abu tayi. Zumbur ta tashi Zaune tareda saka mayafinta.
Lallabawa tayi a hankali ta bude ɗakinnasu saboda karsu ummi su jita.
Ko tsoro bataji ba haka ta nufi sashen hajiyah Mammah ga duhu.
Tafiyah take kaman wata mai shiga ɗakin fatalwa jikinta yana rawa,amma taurin kai ya hanata juyawa da baya.


SADI-SAKHNA ce
09035784150




*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)


Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150

Bismillahir-rahmanir-raheem


Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.


*BOOK 2*
...35...


Motsi kaɗan taji saita haska,kuma dayake tasaka hakan a ranta har muryoyi takeji suna amsa mata kuwwa.
Key ɗin falon ta ɗakko,dan dama tana dashi saboda tana yi mata aiki.
Abinda zai bata cikas shiga ɗakin hajiya Mammah ne,wanda batasan yana buɗe ba kokuma a rufe.
Murɗa ƙofar tayi,amma wannan kam babu zancen zai buɗe a lokacin.
Hankalin ta ya tafi wajen buɗe ƙofar,bata tsammata ba sai muryar Mulaifah taji a bayanta.
"Ke kuma mai kike anan wajen da wannan daren"
Cikin alamar maye take maganar tana tangaɗi,kana ganinta kasan ta hau air.
Ganin hakanne yasa Sumaimah wata dabarar ta faɗo mata.
Gyara fuskarta tayi alamar damuwa kafin tace.
"Am dama hajiyah Mammah ce tace na gyara mata ɗaki,to kuma na manta ne sai yanzu nazo,gashi bata nan banaso tazo taga ban gyaraba"
"To kuma gyaranne zakiyi shi yanzu,ina Mamman taje ta?"
"Dare bayyi bafah sosai bakya ganine,ita kuma taje asibitine hajiyah Maryam batada lafiyah. Dan Allah kozaki buɗemin na gyara mata,yanzunnan zan gama"
Shuru tayi kaman mai tafiyah tunani kafin ta gyara tsayuwarta.
"Uhm banida key ɗinta,amma nasan tana ajiyewa a Drawer tv stand dinta,amma fah ba ruwana in kika ɗauka,don ta hana"
Tafaɗa tana saka hannun ta a baki,kana ganinta kaga marar hankali.
Murmushi Sumaimah tayi jin barin zancen da Mulaifah take,kai dole ace giya haramunce,Sannan tana saka mutum yin komai da aka hana.
Bayan ta shige ɗakinta wajen data kwantanta mata ta nufah. Cikin sa'a kuwa saiga key ɗin,guda uku ne saida ta gwada dukkansu kafin ta samu wanda ya shiga.
Ɗakin duhune ƙirin,baka ganin komai,ga batada wayah bare ta haska.
"Kince zaki gyara ɗaki amma bakida haske a hannunki,ga fitila ki gyara mata kizo ki fitah,dan bawani sonki nake ba kinsani. Ohhh"
Tana cikin maganar tasaki amai a ɗakin.
Matsawa gefe Sumaimah tayi tana kallonta,itah harta manta tana gidan ma,rabonta data shigo gidan ta kusa wata uku,yau mai ya dawo da itah oho. Ga nan cikin jikinta ya fito sosai.
Miƙowa Sumaimah fitilar tayi tareda yin Murmushin masu shaye shaye.
"Ahhh abinka da mai ciki tana shaye shaye,so nake ba ya mutu kar yazo da rai,banason haifarsa ko kaɗan"
Taƙarisa maganar tana jijjiga hannunta alamar ahah.
Karbar fitilar Sumaimah tayi ta koma gefe tana kallonta,duk rayuwar data tsinci kanta taji tausayin kanta,amma wannan ta damata ta cinye akan wacce za'a tausayawa.
Bayan ta gama magangunun ta fita jan ajiyar zuciya Sumaimah tayi tareda rufe ƙofar.
Dube dube takeyi ko zata samu wani abu daya sabawa hankalin ta a ɗakin,amma bata gani ba har ta shafe wasu mintuna.
"Wayyo Allah nah shin ina take ajiye abubuwan ta ne? Ohh ƙarƙashin gado,anan naga wannan fatalwar ta fito"
Tsugunnawa tayi ta leƙa ƙarshin gadon,har nishi take saboda girman da cikinta ya fara.
Ido biyu tayi da akwatin,batayi wani tunanin ba ta jawoshi waje.
A buɗe yake sai wasu kwalabe guda biyu a ciki. Ɗayar a bude take ba komai a ciki,sai kuma ɗayar da wani jan abu a ciki.
Ɗaga su tayi a hannunta tana kallo.
"Wannan kuma mai nene,ya nagansu a buɗe,ina abin cikin?"
Motsin mutum taji,ga fitilar da Mulaifah ta bata tana ta rawa,itama kuma jikinta yana rawa.
Dan muryar kaltum babu makawa taji,mai ya dawo da itah yanzu.
Bakin ƙofar tazo a garin tafiyah tayi tuntube kwalbar hannunta guda ɗaya ta faɗi,taji fashewarta kuma a lokaci guda ta taka bata saniba.
Zafine ya ziyarci ƙafartata har cikin kanta,bata tsaya duba ciwon ba ta fito daga ɗakin,daidai lokacin da kaltum tashige ɗakinta,hakanne yabawa Sumaimah damar ficewa daga sashen.
Muryar Kultum taji tana fadin.
"Waye anan,Mulaifah kece?"
Gudu Sumaimah ta fara jin Kultum ta biyo bayanta,wani lungu ta shiga da wasu fulawowi a wajen. Ban nishi babu abinda takeyi,tana cikin wannan halin aka kawo wuta wajen ya ɗau haske,Allah ya taimaketa Kultum ɗin ta wuce.
Kwalbar da take hannunta da kallah,sai yanzu ta gane ainihin kalarta,baƙace samanta a tsuke. Wani baƙin zarene a cikinta an cika shi tamm.
Zarewa takeyi tana zubarwa har saida ta cireshi tass tukunna ta mayar kwalbar ta rufe ta nufi sashensu.

___A bangaren Kultum kuwa ganin tabiyo sawu bataga komai yasa ta koma,a hanyar juyawar tata aka kawo haske.
Jini tagani ya tako tun daga cikin ɗakin hajiyah Mammah zuwa waje,zaro ido tayi tareda shiga ɗakin da gudu.
"Yau waye ya shigo sashennan?"
Shine abinda ta faɗa a razane,musamman da taga akwatin da yafi rayuwar hajiyah Mammah kanta daraja a ƙasa a buɗe,hannu ta ɗora a ƙirjinta ta dafe.
"Nashiga uku waye ya shigo cikin ɗakinnan haka"
Waya ta ɗauka hannunta har rawa yakeyi ta ƙira hajiyah Mammah.
"Hajiyah hajiyah akwai babbar matsala fah,wani ya shigo ɗakinki ya buɗe akwatinki na ƙarƙashin gado"
"Akwati kuma dama a bude na barshi,waye yasamu key ɗin dakina,babu wanda ya sani banda Mulaifah,ita kuma batasan inda na saka akwatin ba"
"Hajiyah babu komai a cikin akwatin,sai wata fashashshiyar kwalbar an takata ɗakin duk jini"
"What jini kuma? Ganin nan dawowa yanzunnan,akwai kwalba biyu a ciki ina suke?"
"Ga ɗaya mai zan abu ta fashe,ɗaya kuma bata nan"
"Wayyo nashiga uku,ganin nan dawowa yanzunnan driver zai dawo dani a darennan,amma ba Mulaifah bace tayi?"
"Ba ita bace,tana bacci a ɗakinta, wani ne fah ya shigo,na bishi ma yagudu ɗazu"
"Kuma mai kike da kika daina binsa,koma waye sai ya karbi hukuncin lalatamin shirina na tsawon shekara da shakeru,ganin zuwa idan wanda ya ɗauka ya lalata kwalbar ko wanne lokaci hajiyah maryam zata iyah tashi"
"Mammah keda waye kike magana haka naji hankalin ki a tashe?"
Maimuna ta tambayeta ganin yanda take haɗa gumi,itah mai sunan tazo wajen jinya amma gabaɗaya hankalin ta na wani wajen daban..
"Inason komawa gidane yanzunnan ƴar nan,an samu matsala,ciwon zuciya na ya tashi,dama yakan yimin idan naga mai jinya. Ko zaku kulada itah kafin......."
Lahh karki damu Mammah kije gidan kawai,sha ɗaya tayi bazan iya tuƙin dare ba,amma bari na faɗawa Saleem ya maidaki gida"
Godiya ta dungayiwa Maimuna har tagama ƙiran Saleem ya kaita gidan.
Shiga tayi wajen hajiyah Maryam wacce akayi wa allurar bacci tana kwance tamkar gawa,kuka tayi a gunnata da kuma wasu surutai kafin ta fito suka tafi..
Sai sannu suke jeramata tana saiƙe nishi ɗaɗɗaya..
Har bakin sashenta Saleem ya rakota kafin ya wuce nasu part ɗin,dama jini ya bata masa kaya daya taimakawa likita wajen sakama hajiya Maryam na'urar iska.
Tana ganin yabar wajen ta jefar da gyalen jikinta tareda miƙewa tsaye.
Kultum wacce ke falon a tsaye sai ganin tayi kamar an jefo ta ciki.
Hancinta ta ɗaga sama ta shaƙi iskar ɗakin kafin ta buɗe ido..
"Koma wacece zata gane kuranta,abinda ta ɗauka yafi ƙarfin sata"
"To amma hajiyah wannan data fasa babu komai,Sannan wacce ta tafi da itah inta fasata fah itama"
"Wacce ta fashe aikin dana yiwa Maryam ne,a yanzu bazan ƙara amfani da jininta na dawo da ƙuruciyata ba,Sannan ina buƙatar ƙarin ƙarfi da gaggawa,domin idan wani abu yafaru da kwalbar Harsheelah nasan kaina zata dawo,domin kullum burinta shine taga raunina"
Buɗe hannunta tayi a iska saiga wani ƙoƙo a cikeda jini ya bayyana.
Jinin da Sumaimah ta yanku a tsakiyar ɗakin ta dandala kana ta ɗiga a cikin na ƙoƙon.
Cikin ƙanƙanin lokaci aka fara zaro mata bayi kamar rediyo..
"Macee macecee da ciki a jikinta,itaceeee wacce ta kasance masomin alƙadarinki,surukar
Showing 54001 words to 57000 words out of 62659 words