gama gyara ko ina ta gama abinci ta kawo masa.
Duk abinda take tanajin idonsa a kanta,komai yake saƙawa a ransa oho.
Bayan ta kawo masa abincin har sannann bai dawo hayyacinsa ba,shurunne yayi yawa hakan yasa Sumaimah yin tafi a daidai fuskarsa,ganin taje ta dawo amma har yanzu bai motsaba.
"Mai yafaru haka?"
"Sumaimah ina son na aureki idan zaki yarda"
Maganar ta daketa sosai,sannan ta bata mamaki a lokaci guda.
"Aure kuma? Shin saboda abinda ya faru a tsakaninmu ne yasa kake wannan tunanin?"
"Eh dashi ɗin ma,amma kuma daman ina son hakan a raina"
"Kayi haƙuri bazai yiyu ka aureni ba a yanzu"
"Meyasa nasan abinda kikemin soyyaya za'a ƙirashi, wanda saboda hakanne nima na fara sonki a cikin raina"
"Ba iya soyayyar bace kaɗai zata wanzar da aure,saida sharaɗi tukunna,sannan cewa nace maka bazayyi yuba,ba wai bazan amince ba."
"Meyasa bazai yiyu ba toh,nariga na keta miki mutuncinki,zuciyata bazata juri ganin abinda namiki ya tafi haka ba,dan haka ki amincemin aurenki ta hakanne zanji na rage wani abun"
"Kona amince maka baya halatta nayi aure guda biyu"
"Aure biyu,mai kike nufi da hakan?"
"Inada aure,harda yaro a garinmu"
"Whattttttt!!!!!!!!!!!!"
Shine abinda Ahmad ya faɗa tareda miƙewa kaman an tsikareshi.....
"Am dama........"
Tun kafin Sumaimah tace wani abun ya toshe kunnensa.
"Shut up,don't say anything,banason jin komai daga bakinki,sannan kuma ki fita daga sashennan,banason ko ido nasake haɗawa dake daga yau"
Taƙarfi ya faɗi hakan har saida ta razana,tashi tayi da sauri ta bar sashen tana hawaye,shikenan komai data dade tana yi ya wargaje a yau ɗin.
SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
*BOOK 2*
...26...
A bangaren Ahmad kuwa da Sumaimah tafita,jiyayi gabaɗaya duniyar tayi masa zafi,kenan daman duk tsawon wannan lokacin matar aure yakeso,wani abu mafi munin ma wai har ya kwanta da itah,wannan lamari har ina.
A daddafe ya shirya cikin kayan aiki ya bar gidan,abincin data haɗamasa ko kallonsa bayyi ba.
Bayan yaje office ɗin ma shuru yayi tareda dafe kai,yarasa ma mai yake masa daɗi.
Eemran ne ya shigo hannunsa ɗauke da file.
Bayan yayi masa gaisuwar sojoji ne ya ajiye masa file ɗin a gabansa.
"Ranka ya daɗe mun samu maboyar inda shigaban ƙungiyar yake,yana garin DABAGAYI ne amma can cikin jeji,mun samu hakanne bayan........."
Bai gama bayanin ba Ahmad ya karbi file ɗin ya fara dubawa,haba no wonder shiyasa suka rasasu,suna can inda ba'a tsammani.
"Eemran ku shirya private jet a yau zamuje wajen,i need to end this case da sauri,nasan koma menene yanada alaƙa da wani nawa,kuma da rayuwar danayi a baya,nagaji da zama cikin wannan duhun,i need to know everything"
Yana gama faɗin hakan suka bar office ɗin zuwa headquater su.
Wajen yamma rana ta kusan faɗuwa suka shiga cikin jejin,a bakin wajen suka tsaya,basuda wani yawa don basu wuce su goma ba,saboda binciken na sirri ne,ko mahaifinsa baisan sun tafi ba.
Saidai sun ɗebi makamai masu hatsarin gaske.
Jejin Ahmad yake ƙarewa kallo,haka kawai ya tsinci kansa dajin kaman yasan wajen. I donsa ya rufe yaja wata iska mai nauyi,haka ido a rufen yafara tafiya a cikin jejin.
Sudai sauran sojojin binsa suke a baya har suka iso bakin wani ɗutse,babu kowa a wajen,amma kuma suna jiyo motsin wasu na tahowa ta bayan dutsen.
Hakanne yasa Ahmad yayiwa tawagarsa alamar suyi baya cikin duhuwar jejin su shirya kai farmaki.
Yana nan tsaye ya saita duk wanda ya zo ya harbeshi,wasu mazajene manyan manya guda huɗu,kana ganinsu kaga shu'umai suka bayyana,suma tasu bingidar tana ɗane,domin da alama kaman yanda su Ahmad suka ji motsinsu suma sun ji nasu motsin.
Na gabanne yafara sauƙe bindigar tareda yiwa na bayan magana.
"Kai ku sauƙe ogah gojene fah ya dawo"
Jin sunan yasakasu sauƙe bindigoginsu tareda matsowa,gaisuwa suka miƙa masa tareda cewa.
"Ogah ya dai sai yanzu ka dawo,ai har anyi taro ganin shuru shuru baku dawo ba yasa akayi tunanin duk cikinku babu wanda ya rayu, Don 2 a ranar na naɗa sabon Don3 amma mu bayyi mana ba,dama muna fatan dawowarka"
Duk maganar da suke Ahmad binsu kawai yake da kallo,sai a sannan maganar wancan barawon da suka kama ta dawo masa,da kuma maganar Sameer shida Abbansu. Kenan dai a rayuwar da yayi baisani ba a wajensu yayi aiki,Allah yasa ma ba kayan sojojine a jikinsa ba da sun ganeshi.
Ɗaya daga cikinsu ne ya dawo dashi daga tunanin daya tafi,ta hanyar jan hannunsa zuwa cikin sansaninnasu.
Suna tafe yana binsu a baya batareda yace komai ba har suka isa Wani ɗaki.
Shiga sukayi ya bisu,ba ɗakin kwana bane,domin hadda kujera da table a ciki.
Don 3 yaji sunce a gaisuwar da sukayiwa wanda yake kan kujerar,shima ƙatone amma bakaman su ba,saidai ya fisu murɗewar jiki.
"To ogah mai guri yazo mai tabarma sai ya naɗe,ogah goje ya dawo,dama matsayinsa ne a ka baka"
Daga yanda suke maganar ya tabbatar kam ba sonsa suke ba a shugabannasu.
"Wanne zancen banza kukeyi haka,kunyi farautar da aka saka kune,nida idona naga goje an soka masa wuƙa,dan haka bai tsira da ransa ba"
Matsawa sukayi daga gaban yayi arba da goje,wanda yake sanye da baƙaƙen kaya da bindiga a hannunsa.
Firgit ya tashi yana rarraba ido,ashe da gaske sukeyi dai.
Ganin yafara kame kame ne yasa Ahmad ƙarisawa gabnasa tareda yin murmushi.
"Lahh ogah kada ka damu fah,ni yanzu ma inada wasu yaran mun kafa tamu ƙungiyar,saboda lokacin da abin yafaru na bugu,na manta komai na rayuwata,iya kawai sunan ƙungiyar ne yazo kaina da kuma inda take shiyasa nazo"
Wani washe baki yayi tareda cewa.
"Ahh toh abu yayi ƙyau sosai,nayi zaton ai kazo ƙarbar matsayinka ne"
"Ahah bashi nazoyi ba,nazone dai wajen Don 2,saboda na tuna zamu haɗu dashi idan muka dawo a raye,sannan kuma nazo nuna masa mutanen dana haɗa,sun ƙware sosai a wajen iya aiki,bansani ba ko zasu samu karbuwa suma a........."
"Ahah mai zai hana,dama munyi rashin mutane sosai a harin da muka kai waccar shekarar,tunda kai ka kawosu to munsan babu matsala.
Kai me kuke jira,ku basu masauki mana shida mutanensa"
Yafaɗa yana bawa wanda suka rako Ahmad ɗin umarni.
"Goje in bazaka damu ba za'a baku masauƙi ku zauna kafin na aikawa da shugaba saƙon cewar kazo"
"To shikenan bakomai,ni barina je nayima mutanennawa magana"
Bayan ya koma wajen daya bar su Eemran bayani yayi musu akan plan ɗin ya sauya,zasu saje da barayinne su san komai nasu kafin su kai farmaki.
Hakan kuwa akayi,dan har kaya suka sanja irin nasu,saidai ba kaman yanda sukayi tunani ba,zasu kai kusan kwana uku kafin wanda suke jira yazo.
Sumaimah (POV)
Bayan Ahmad ya koreni daga sashensa na daɗe a lambu ina tunani,ina ganin fitowarsa ya ɗau mota ya bar gidan.
Tunda yanzu aikin sashensa ya ƙare,lokacine daya kamata dama na farka daga yi masa abu batareda yasan koni wacece ba,yanzu zan fara aikin da hajiyah Maryam tasakani a sashen hajiyah Mammah. Domin itace sanadin dukkan waɗannan abubuwan,da badan itaba da yanzu na faɗamasa cewar nice matarsa,wani lokacin saina kusan subutar baki sai na tuna da rayuwar ɗana,idan tagano shima tarwatsa rayuwarsa zatayi kaman ta mahaifinsa.
Gyara fuskata nayi na nufi sashen hajiyah Mammah.
Tana zaune akan dadduma a tsakiyar falonta,jikinta lullube da babban mayafi kamar kullum.
Sallama nayi da amsa a nutse,tsugunnawa nayi tareda karkatar dakai.
"Hajiya barka da hantsi ya jiki jikin?"
"Lafiya kalau ƴar nan ya haƙuri da rayuwa"
Hawaye na ƙaƙalo yafara zubomin,wanda bakomai na tuna na zubar dashi ba sai korar da Ahmad yayimin ɗazu.
"Hajiyah ki taimakeni kaman yanda Allah ya taimakeki, Yallabai nake yiwa aiki,babu abinda banayi masa,yau da safennan ya koreni wai kada nasake nuna masa fuskata,na tambayeshi mai ya faru yacemin wai kawai ya gaji danine.
Gashi inada ɗa da kanwa da innata a ƙauyenmu wanda nake tallafawa,miji kuma ya tafi nema har yanzu shuru bai dawo ba"
Kuka nake kaman raina zao fice,inaji tana cemin nayi shuru amma banyi niyyar tsayawa haka ba,saina amayar duk abinda na ƙunsa kwanannan.
Saida naji zuciyata tayi sakayau kafin tanafara rage kukan ina jan majina.
Mai akinta Kaltum ta ƙwalawa ƙira,sai gata kuwa tafito daga wani ɗaki.
"Zo kalutume ga wannan yarinyar daga yanzu zata dunga tayaki aiki anan sashen na ɗauketa aiki"
"To shikenan hajiyah za'ayi yadda kika ce"
"Karki damu ki dunga aikin anan sashen,saidai idan zakiyi min aiki banda gulmace gulmace,sannan banda rawar kai,duk da naga bakiyi kamada mai hakan ba dama, ki kwantar da hankalin ki zan biyaki,yanda zaki kulada ƴan uwanki,Allah yaƙara rufamana asiri"
"Ameen ameen hajiya,nagode nagode sosai,kaman yanda kika taimakeni kema Allah yayi miki hakan"
Nadaɗe ina kwararo mata Addu'a godiya,ina cikin hakanne kaltum tasake shigowa tareda raɗawa hajiyah Mammah wani abu a kunne.
Ɗan zaro ido tayi tareda sauya yanayin fuskarta.
"Kin bata maganin amma taƙi sha,mai take nufi kenan,dashi zata zauna har a sani? Kice mata ta sameni a ɗakina yanzunnan"
Daga haka ta sallameni suka shiga ciki. Ko basu fadaba nasan zancene akan cikin Mulaifah,nasan dai bazata taba faɗamusu ba,in kuwa suka gane kenan ya wuce wata biyu.
Ina nan zaune a wajen ina nazari naga Mulaifah tafito daga ɗakinta zata shiga na gaji Mammah ɗin,harara ta bankamin,tayi wata rama ga fari data ƙara kamar wata fatalwa.
Murmushin mugunta nayi kafin na fito daga sashen,hmmmm danma bata san nina lalata mata shirinta ba kenan.
Ban nufi sashen hajiyah Maryam ba saina nufi namu,yanzu dole na rage shiga wajen hajiyah Maryam ɗin,idan har inaso nasha lafiya.
∆∆∆
Su Ahmad har sunyi kwana uku a cikin sansanin barayi,yauɗinne kuma suke saka ran zuwan shugaban kungiyar na biyu wato Don 2.
Abubuwa da dama da suke shirin yi da kuma wanda sukayi babu wanda basu sanar da Ahmad ba,hakan ba ƙaramin dadi yayi masa ba,ganin ya samu dukkan labaran dayake buƙata cikin sauƙi.
Abu ɗayane dai har yanzu bai sani ba shine sanin shugaban ƙungiyar na ɗaya da kuma na biyu.
Wannan kaf cikinsu babu wanda ya sani.
Dare ya fara,kowannne lokaci Za'a iya ƙiran Ahmad su gana da Don 2,a zaune yake shida su Eemran suna plan yanda komai zai kasance.
"Ka gane Eemran ku tabbatar kun saitasu dukka bindiga,sanann gurnet dayake kakkafe yazama cikin ready,so nake mu tashi wajennan a yau bayan munkama shugaban,kada kowa ya tsira da ransa a cikinsu.
"Angama shugaba"
Suna gamawa aka zo ƙiransa ya fita.
Wani ɗaki aka bi dashi,wanda tsawon kwanansu uku na gidan basu taba shigaba.
Yanada matsakaicin girma kuma yasha ado kamar ba'a cikin kogon dutse ba.
Wani mutum ne a zaune yasha suit baƙaƙe,ɗan dattijo ne domin yafara manyanta,magana yake a waya lokacin da suka shigo,sannan fuskarsa da wata baƙar mask tana sheqi.
Bayan ajiye wayar cire mask ɗin yayi tareda juyowa cikin taqama.
"Barka da dawowa jaki na mijin gaske goje,naji daɗin cewar kana raye,domin ko babu komai nasan jakar da muke nema tana hannun ka,sannan........."
Caff ya tsaya da bayanin ganin wanda yake tsaye a gabansa.. Yana zare ido.
Shima Ahmad ɗin a bangarensa tun lokacin daya juyo ɗin kafeshi da ido baya ko motsawa saboda razanar ganinsa a wajen.
"Gen. Buhari Bello wanda suke cewa Uncle BB,Aminin mahaifinsu ne tun suna ƙanana,suma tare suka tashi suka gansu. Komai da AM Aliyu zayyi sai yayi shawara dashi,amma.......what yana ɗaya daga cikin wakilan ƙungiyar datake maƙiyarsu a barikin sojoji??
"General mai kake anan badai kaine goje ba??"
Kafin yagama tantancewa Ahmad ya saitashi da bingida,yayinda ya danna wata makunna a hannunsa,aikuwa wajen ya kaure da ƙarar bindigu da tashin gurneti.
SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
*BOOK 2*
...27...
Duka da naushi Ahmad yake kaiwa Gen Buhari Bello,shima ramawa yakeyi kasancewarsa tsohon soja,ga Don 3 ya buge bindigarsa tun ɗazu.
Ganin faɗan ya ɗauke musu hankaline yasa don 3 ɗauke wayar Gen BB ya fita.
Sun daɗe suna faɗan kafin Ahmad yasamu nasara akansa,ta hanyar ɗaukar bindigar tasa,saita shi yayi da ita yana haki.
"Miye alaƙarka da wannann kungiyar,dama tsawon lokacin nan amanar sojoji kake ci,irinkune kesa a dunga yiwa jami'an tsaron ganin marasa gaskiya koh.......(kwafɗama sa ƙasan bindiga yayi saida ya faɗi)........kaine don 2 to wanene shugaban ƙungiyar,inaso ka faɗamin yanzunnan kokuma na jajjage kanka da bindigar nan"
Cikin ƙaraji da tashin hankali yake maganar.
Wata dariyar baka isa ba gen BB yayi wa Ahmad,cikin sauri yasaka ƙaramar wuƙa ya yanke wuyansa da itah,yana kakarin mutuwa Ahmad ya jefar da bindigarsa ya ƙarisa wajensa da sauri.
Tallafoshi yayi a razane,ga jini yanata zuba a wuyansa,abin har yakai ya kashe kansa akan yafaɗa masa wanene shugaban ƙungiyar nan?
"Yaaa....rrro kenan,mai amfanin na faɗamaka tunda nasan dama mutuwa zanyi idan ta gano kasanni........bazaka taba sanin wacece itttt.......ba"
"Dama macece ka faɗamin, wacece w......"
Shuru yayi tareda sakinsa ya koma gefe,ganin ya riga ya mutu,abin yayi matuƙar razana shi sosai.
Wayarsa ce tayi ƙara,hannunsa yana rawa ya ɗauka ganin Eemran ne.
"Hello sir mungama dasu,saidai wannan shugabannasu mun sameshi yana waya da wani"
"What definitely shugabarsu yake faɗawa mai ya faru"
"Eh nima nayi tunanin haka,na harbeshi a kafaɗarsa da dama"
"Ohh yakamata mu tafi,abin bai tafi yanda ake so ba,amma dai Alhamdulillah hakan ma mukeda nasara"
∆∆∆
"Ina jinka ka faɗamin mai yake faruwa a wajen Gen?"
"Hajiya an samu matsalane ba Ogah bane,Goje ashe sojane yayi mana baɗɗa kama,yanzu haka ya gane ogah kuma ya kamashi,na samu wayarsa ne na ƙiraki"
"Wayeshi ka faɗamin"
"Gen ........"
Kafin yaƙarisa aka katse ƙiran,kuma da alama harbeshi akayi don taji ƙarar bindiga.
"Waye ka faɗamin wayeeeeee......"
Ƙara ta saka tareda yin wurgi da wayar, kaltum ce ta tsugunna ta ɗauke wayar jikinta yana rawa.
Kallon fuskar hajiyah Mammah nakeyi,idan ka ganta zakace bazata wuce shekara talatin ba a duniya,babu wannan sunkuyawar da yamutsewar fuskar.
Mamaki abun ya bani,mai ta shafa haka ta sanja lokaci guda.
Masifa tacigaba dayi tana zuwa tana dawowa,ganin abin bazai mata ba ta jawo wani akwati a ƙarƙashin gadonta,ja ne yana glowing,kana gani kasan abun tsafi ne.
Hannunta ta saka ya buɗe,wani aljana ce ta bayyana a gabanta da baƙaƙen kaya,kamarsu ɗaya da itah,amma kana gani kasan ita ba mutum bace,to wacece kenan.
Jikina rawa ya fara daga inda nake labe da jikin ƙofa ina leƙawa,dan karfin hali bana tsoron ma ta ganni.
"Ruhina inaso kayimin bayani shin mai kasani gameda abinda yake faruwa,ƙungiyar dana kafah wadda da ita nake control na manyan ƙasar nan ta rushe,mai yasa abubuwana suke rushewa"
Muryarta da bibbiyu take fita kamar wata na'urah.
"Hakan dama dole zai faru,tunda dodo ya baki kashedi akai,matar da kike gudun kada ta bayyana harta haifi magajin wannan matakin tariga ta bayyana,kuma itace sanadiyyar karyewar alƙalaminki,indai ba kasheta kikayi ba to bazaki ƙara nasara ba"
"Kaman ya yarinya,ni banga kowa a tareda shi ba,Mulaifah ce itama kuma yanzu sun rabu"
"Hhhhhhhh duk da a zahiri kina kulada yarintarki amma hakan baya aiki a hankalin ki,shiya riga ya tsufah"
"Ruhuuuuuu karki ƙara magana akan tsufah na,bazan tsufah ba bazan taba tsufah ba,wannan fatar tsufan ina nuna ta ne kawai da iyalaina,suma in suka isheni dukka zan gama dasu nayi rayuwar ƴan ci na"
"To inba haka ba mai yasa kika kasa gane cewar Ahmad yayi rayuwa ba'a gabanki ba na tsawon shekara shida,bai kawomiki anan ya gamuda itah ba,sannan kuma yayi rayuwa a cikin ƙungiyar da kike karewa. Sannan ya bar mata da kuma ɗa a rayuwarsa ta baya.......munkasa gane hakanne a da dayake ta Addu'a a lokacin,yanzu dayake kan aikin ruguza ƙungiyarki bayayi sosai shiyasa muka gani......amma duk da haka bamuga hoton madubin rayuwar ba har yanzu"
Jikin hajiya Mammah rawa yafara bakinta yana fitar da wani hayaƙi,ganin Kultum zata fito yasa nayi saurin barin sashen nima nawa jikin yana rawa.
Me suke nufi,kenan nida ɗana mune sanadin karyewarta a yanda ta yarda,in hakane to kuwa muna cikin hatsari,sannan dole kada tasan koni wacece, matar nan ta wuce yanda nake zato.
Ina cikin tafiya ina tunani naji na bangaji mutum,saurin dawowa hankalina nayi tareda kallon Fatee.
"Ke ina kike gani haka, kaman wata sabuwar makahuwa,kije mommy tana nemanki "
Daga haka ta wuceni tana karairaya,nidai binta nayi da ido kafin na wuce sashen hajiya Maryam.
A zaune na gansu itada Neelah suna magana,ita kuma yaushe ta dawo,da alama yaune.
Saida na giashesu kafin na zauna a akan kujerar,Neelah ce ta kalleni tareda cewa.
"Miye ya faru haka Sumaimah naganki kaman wacce taga fatalwa,ko kema kinji labarin nasarar da Ahmad yayi akan ƙungiyar BC?"
"Uhm yayi nasara amma kuma yasake buɗe ƙofar gane shirinmu,domin a yanzu haka hajiya Mammah tasan da labarin yayi rayuwa a cikin ƙungiyar BC,kuma yanada ɗa da mata,duk da batasan sunanmu da fuskarmu ba amma nasan bazata zauna ba saita gano hakan"
Abinda nagani a ɗakin hajiyah Mammah na sanar dasu,duk da basu wani razana ba,amma sunyi mamakin yanda takai har haka a shu'umanci.
Mun daɗe muna tattauna,wanda duk yawanci gargaɗi hajiyah Maryam takemin akan nayi taka tsantsan, lamarin,tunda yanzu yafi nada muni,ga zaman dazan ƙarayi a sashen hajiyah Mammah,domin inkana son kama damisa dole saika shiga sansaninsa.
A ranar Ahmad yadawo daga yankinnamu,anyi murna sosai da nasararsa ciki kuwa harda hajiya Mammah,kaman ba fadarta ya ruguza ba. Musamman A.M Aliyu ba ƙaramin farin ciki yayi ba da nasarar. Ana ta murna amma bandani,domin wajen zamannawa na kullum wato lambu na tafi na zauna. Zuciyata nason ganin Ahmad domin nayi kewarsa sosai,amma kuma ina tuna kashedin da yayimin na cewar kada na kuskura nasake nuna fuskata a gabansa.
∆∆∆
Bayan sati ɗaya da wannan nasarar da gen Ahmad yasamu nutsuwarsa ta ɗan dawo ba kaman da ba,saidai duk da haka yakasa tsintar kansa da jin komai ya ƙare. Koda yake dama yasan akwai sauran rina a kaba,tunda har yanzu bai kama shugabar ƙungiyar ba,amma tunda yasan macece yanzu zarginsa kashi tamanin a cikin ɗari yana kan hajiya Maryam ne,don abinda yake kwanannan kenan saka mata ido na shige da ficenta,domin ya kula tashiga cikin tashin hankali da abinda yafaru,sannan ta tsiri zama cikin busy.
Biron hannunsa yake dannawa yana ɗagoshi,duk da hakan akwai wani abun da babu.
"Ohhh that girl why....meyasa nake missing ɗin matar wani,kaddai na fara son matar da bazata taba zama mallakina ba kai,ahah no ba sonta nake ba,inajin haushi ne da kuma zunubin abinda na aikata mata"
Cije cije yake yace wancan yace wancan shi kaɗai,a iya sati guda daya wuce gabaɗaya yaki ko gidan baya son komawa,domin yana shiga zaiji yana so ya ganta,wanda kuma yasan bazai gantan ba,shida kansa ya bata umarnin kada ya sake ganinta a inda yake.
Kai inaga barin ƙasar zayyi naɗan wasu watanni ko zaiji daɗi,dama abbah yabashi hutu tunda
Showing 42001 words to 45000 words out of 62659 words
Duk abinda take tanajin idonsa a kanta,komai yake saƙawa a ransa oho.
Bayan ta kawo masa abincin har sannann bai dawo hayyacinsa ba,shurunne yayi yawa hakan yasa Sumaimah yin tafi a daidai fuskarsa,ganin taje ta dawo amma har yanzu bai motsaba.
"Mai yafaru haka?"
"Sumaimah ina son na aureki idan zaki yarda"
Maganar ta daketa sosai,sannan ta bata mamaki a lokaci guda.
"Aure kuma? Shin saboda abinda ya faru a tsakaninmu ne yasa kake wannan tunanin?"
"Eh dashi ɗin ma,amma kuma daman ina son hakan a raina"
"Kayi haƙuri bazai yiyu ka aureni ba a yanzu"
"Meyasa nasan abinda kikemin soyyaya za'a ƙirashi, wanda saboda hakanne nima na fara sonki a cikin raina"
"Ba iya soyayyar bace kaɗai zata wanzar da aure,saida sharaɗi tukunna,sannan cewa nace maka bazayyi yuba,ba wai bazan amince ba."
"Meyasa bazai yiyu ba toh,nariga na keta miki mutuncinki,zuciyata bazata juri ganin abinda namiki ya tafi haka ba,dan haka ki amincemin aurenki ta hakanne zanji na rage wani abun"
"Kona amince maka baya halatta nayi aure guda biyu"
"Aure biyu,mai kike nufi da hakan?"
"Inada aure,harda yaro a garinmu"
"Whattttttt!!!!!!!!!!!!"
Shine abinda Ahmad ya faɗa tareda miƙewa kaman an tsikareshi.....
"Am dama........"
Tun kafin Sumaimah tace wani abun ya toshe kunnensa.
"Shut up,don't say anything,banason jin komai daga bakinki,sannan kuma ki fita daga sashennan,banason ko ido nasake haɗawa dake daga yau"
Taƙarfi ya faɗi hakan har saida ta razana,tashi tayi da sauri ta bar sashen tana hawaye,shikenan komai data dade tana yi ya wargaje a yau ɗin.
SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
*BOOK 2*
...26...
A bangaren Ahmad kuwa da Sumaimah tafita,jiyayi gabaɗaya duniyar tayi masa zafi,kenan daman duk tsawon wannan lokacin matar aure yakeso,wani abu mafi munin ma wai har ya kwanta da itah,wannan lamari har ina.
A daddafe ya shirya cikin kayan aiki ya bar gidan,abincin data haɗamasa ko kallonsa bayyi ba.
Bayan yaje office ɗin ma shuru yayi tareda dafe kai,yarasa ma mai yake masa daɗi.
Eemran ne ya shigo hannunsa ɗauke da file.
Bayan yayi masa gaisuwar sojoji ne ya ajiye masa file ɗin a gabansa.
"Ranka ya daɗe mun samu maboyar inda shigaban ƙungiyar yake,yana garin DABAGAYI ne amma can cikin jeji,mun samu hakanne bayan........."
Bai gama bayanin ba Ahmad ya karbi file ɗin ya fara dubawa,haba no wonder shiyasa suka rasasu,suna can inda ba'a tsammani.
"Eemran ku shirya private jet a yau zamuje wajen,i need to end this case da sauri,nasan koma menene yanada alaƙa da wani nawa,kuma da rayuwar danayi a baya,nagaji da zama cikin wannan duhun,i need to know everything"
Yana gama faɗin hakan suka bar office ɗin zuwa headquater su.
Wajen yamma rana ta kusan faɗuwa suka shiga cikin jejin,a bakin wajen suka tsaya,basuda wani yawa don basu wuce su goma ba,saboda binciken na sirri ne,ko mahaifinsa baisan sun tafi ba.
Saidai sun ɗebi makamai masu hatsarin gaske.
Jejin Ahmad yake ƙarewa kallo,haka kawai ya tsinci kansa dajin kaman yasan wajen. I donsa ya rufe yaja wata iska mai nauyi,haka ido a rufen yafara tafiya a cikin jejin.
Sudai sauran sojojin binsa suke a baya har suka iso bakin wani ɗutse,babu kowa a wajen,amma kuma suna jiyo motsin wasu na tahowa ta bayan dutsen.
Hakanne yasa Ahmad yayiwa tawagarsa alamar suyi baya cikin duhuwar jejin su shirya kai farmaki.
Yana nan tsaye ya saita duk wanda ya zo ya harbeshi,wasu mazajene manyan manya guda huɗu,kana ganinsu kaga shu'umai suka bayyana,suma tasu bingidar tana ɗane,domin da alama kaman yanda su Ahmad suka ji motsinsu suma sun ji nasu motsin.
Na gabanne yafara sauƙe bindigar tareda yiwa na bayan magana.
"Kai ku sauƙe ogah gojene fah ya dawo"
Jin sunan yasakasu sauƙe bindigoginsu tareda matsowa,gaisuwa suka miƙa masa tareda cewa.
"Ogah ya dai sai yanzu ka dawo,ai har anyi taro ganin shuru shuru baku dawo ba yasa akayi tunanin duk cikinku babu wanda ya rayu, Don 2 a ranar na naɗa sabon Don3 amma mu bayyi mana ba,dama muna fatan dawowarka"
Duk maganar da suke Ahmad binsu kawai yake da kallo,sai a sannan maganar wancan barawon da suka kama ta dawo masa,da kuma maganar Sameer shida Abbansu. Kenan dai a rayuwar da yayi baisani ba a wajensu yayi aiki,Allah yasa ma ba kayan sojojine a jikinsa ba da sun ganeshi.
Ɗaya daga cikinsu ne ya dawo dashi daga tunanin daya tafi,ta hanyar jan hannunsa zuwa cikin sansaninnasu.
Suna tafe yana binsu a baya batareda yace komai ba har suka isa Wani ɗaki.
Shiga sukayi ya bisu,ba ɗakin kwana bane,domin hadda kujera da table a ciki.
Don 3 yaji sunce a gaisuwar da sukayiwa wanda yake kan kujerar,shima ƙatone amma bakaman su ba,saidai ya fisu murɗewar jiki.
"To ogah mai guri yazo mai tabarma sai ya naɗe,ogah goje ya dawo,dama matsayinsa ne a ka baka"
Daga yanda suke maganar ya tabbatar kam ba sonsa suke ba a shugabannasu.
"Wanne zancen banza kukeyi haka,kunyi farautar da aka saka kune,nida idona naga goje an soka masa wuƙa,dan haka bai tsira da ransa ba"
Matsawa sukayi daga gaban yayi arba da goje,wanda yake sanye da baƙaƙen kaya da bindiga a hannunsa.
Firgit ya tashi yana rarraba ido,ashe da gaske sukeyi dai.
Ganin yafara kame kame ne yasa Ahmad ƙarisawa gabnasa tareda yin murmushi.
"Lahh ogah kada ka damu fah,ni yanzu ma inada wasu yaran mun kafa tamu ƙungiyar,saboda lokacin da abin yafaru na bugu,na manta komai na rayuwata,iya kawai sunan ƙungiyar ne yazo kaina da kuma inda take shiyasa nazo"
Wani washe baki yayi tareda cewa.
"Ahh toh abu yayi ƙyau sosai,nayi zaton ai kazo ƙarbar matsayinka ne"
"Ahah bashi nazoyi ba,nazone dai wajen Don 2,saboda na tuna zamu haɗu dashi idan muka dawo a raye,sannan kuma nazo nuna masa mutanen dana haɗa,sun ƙware sosai a wajen iya aiki,bansani ba ko zasu samu karbuwa suma a........."
"Ahah mai zai hana,dama munyi rashin mutane sosai a harin da muka kai waccar shekarar,tunda kai ka kawosu to munsan babu matsala.
Kai me kuke jira,ku basu masauki mana shida mutanensa"
Yafaɗa yana bawa wanda suka rako Ahmad ɗin umarni.
"Goje in bazaka damu ba za'a baku masauƙi ku zauna kafin na aikawa da shugaba saƙon cewar kazo"
"To shikenan bakomai,ni barina je nayima mutanennawa magana"
Bayan ya koma wajen daya bar su Eemran bayani yayi musu akan plan ɗin ya sauya,zasu saje da barayinne su san komai nasu kafin su kai farmaki.
Hakan kuwa akayi,dan har kaya suka sanja irin nasu,saidai ba kaman yanda sukayi tunani ba,zasu kai kusan kwana uku kafin wanda suke jira yazo.
Sumaimah (POV)
Bayan Ahmad ya koreni daga sashensa na daɗe a lambu ina tunani,ina ganin fitowarsa ya ɗau mota ya bar gidan.
Tunda yanzu aikin sashensa ya ƙare,lokacine daya kamata dama na farka daga yi masa abu batareda yasan koni wacece ba,yanzu zan fara aikin da hajiyah Maryam tasakani a sashen hajiyah Mammah. Domin itace sanadin dukkan waɗannan abubuwan,da badan itaba da yanzu na faɗamasa cewar nice matarsa,wani lokacin saina kusan subutar baki sai na tuna da rayuwar ɗana,idan tagano shima tarwatsa rayuwarsa zatayi kaman ta mahaifinsa.
Gyara fuskata nayi na nufi sashen hajiyah Mammah.
Tana zaune akan dadduma a tsakiyar falonta,jikinta lullube da babban mayafi kamar kullum.
Sallama nayi da amsa a nutse,tsugunnawa nayi tareda karkatar dakai.
"Hajiya barka da hantsi ya jiki jikin?"
"Lafiya kalau ƴar nan ya haƙuri da rayuwa"
Hawaye na ƙaƙalo yafara zubomin,wanda bakomai na tuna na zubar dashi ba sai korar da Ahmad yayimin ɗazu.
"Hajiyah ki taimakeni kaman yanda Allah ya taimakeki, Yallabai nake yiwa aiki,babu abinda banayi masa,yau da safennan ya koreni wai kada nasake nuna masa fuskata,na tambayeshi mai ya faru yacemin wai kawai ya gaji danine.
Gashi inada ɗa da kanwa da innata a ƙauyenmu wanda nake tallafawa,miji kuma ya tafi nema har yanzu shuru bai dawo ba"
Kuka nake kaman raina zao fice,inaji tana cemin nayi shuru amma banyi niyyar tsayawa haka ba,saina amayar duk abinda na ƙunsa kwanannan.
Saida naji zuciyata tayi sakayau kafin tanafara rage kukan ina jan majina.
Mai akinta Kaltum ta ƙwalawa ƙira,sai gata kuwa tafito daga wani ɗaki.
"Zo kalutume ga wannan yarinyar daga yanzu zata dunga tayaki aiki anan sashen na ɗauketa aiki"
"To shikenan hajiyah za'ayi yadda kika ce"
"Karki damu ki dunga aikin anan sashen,saidai idan zakiyi min aiki banda gulmace gulmace,sannan banda rawar kai,duk da naga bakiyi kamada mai hakan ba dama, ki kwantar da hankalin ki zan biyaki,yanda zaki kulada ƴan uwanki,Allah yaƙara rufamana asiri"
"Ameen ameen hajiya,nagode nagode sosai,kaman yanda kika taimakeni kema Allah yayi miki hakan"
Nadaɗe ina kwararo mata Addu'a godiya,ina cikin hakanne kaltum tasake shigowa tareda raɗawa hajiyah Mammah wani abu a kunne.
Ɗan zaro ido tayi tareda sauya yanayin fuskarta.
"Kin bata maganin amma taƙi sha,mai take nufi kenan,dashi zata zauna har a sani? Kice mata ta sameni a ɗakina yanzunnan"
Daga haka ta sallameni suka shiga ciki. Ko basu fadaba nasan zancene akan cikin Mulaifah,nasan dai bazata taba faɗamusu ba,in kuwa suka gane kenan ya wuce wata biyu.
Ina nan zaune a wajen ina nazari naga Mulaifah tafito daga ɗakinta zata shiga na gaji Mammah ɗin,harara ta bankamin,tayi wata rama ga fari data ƙara kamar wata fatalwa.
Murmushin mugunta nayi kafin na fito daga sashen,hmmmm danma bata san nina lalata mata shirinta ba kenan.
Ban nufi sashen hajiyah Maryam ba saina nufi namu,yanzu dole na rage shiga wajen hajiyah Maryam ɗin,idan har inaso nasha lafiya.
∆∆∆
Su Ahmad har sunyi kwana uku a cikin sansanin barayi,yauɗinne kuma suke saka ran zuwan shugaban kungiyar na biyu wato Don 2.
Abubuwa da dama da suke shirin yi da kuma wanda sukayi babu wanda basu sanar da Ahmad ba,hakan ba ƙaramin dadi yayi masa ba,ganin ya samu dukkan labaran dayake buƙata cikin sauƙi.
Abu ɗayane dai har yanzu bai sani ba shine sanin shugaban ƙungiyar na ɗaya da kuma na biyu.
Wannan kaf cikinsu babu wanda ya sani.
Dare ya fara,kowannne lokaci Za'a iya ƙiran Ahmad su gana da Don 2,a zaune yake shida su Eemran suna plan yanda komai zai kasance.
"Ka gane Eemran ku tabbatar kun saitasu dukka bindiga,sanann gurnet dayake kakkafe yazama cikin ready,so nake mu tashi wajennan a yau bayan munkama shugaban,kada kowa ya tsira da ransa a cikinsu.
"Angama shugaba"
Suna gamawa aka zo ƙiransa ya fita.
Wani ɗaki aka bi dashi,wanda tsawon kwanansu uku na gidan basu taba shigaba.
Yanada matsakaicin girma kuma yasha ado kamar ba'a cikin kogon dutse ba.
Wani mutum ne a zaune yasha suit baƙaƙe,ɗan dattijo ne domin yafara manyanta,magana yake a waya lokacin da suka shigo,sannan fuskarsa da wata baƙar mask tana sheqi.
Bayan ajiye wayar cire mask ɗin yayi tareda juyowa cikin taqama.
"Barka da dawowa jaki na mijin gaske goje,naji daɗin cewar kana raye,domin ko babu komai nasan jakar da muke nema tana hannun ka,sannan........."
Caff ya tsaya da bayanin ganin wanda yake tsaye a gabansa.. Yana zare ido.
Shima Ahmad ɗin a bangarensa tun lokacin daya juyo ɗin kafeshi da ido baya ko motsawa saboda razanar ganinsa a wajen.
"Gen. Buhari Bello wanda suke cewa Uncle BB,Aminin mahaifinsu ne tun suna ƙanana,suma tare suka tashi suka gansu. Komai da AM Aliyu zayyi sai yayi shawara dashi,amma.......what yana ɗaya daga cikin wakilan ƙungiyar datake maƙiyarsu a barikin sojoji??
"General mai kake anan badai kaine goje ba??"
Kafin yagama tantancewa Ahmad ya saitashi da bingida,yayinda ya danna wata makunna a hannunsa,aikuwa wajen ya kaure da ƙarar bindigu da tashin gurneti.
SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
*BOOK 2*
...27...
Duka da naushi Ahmad yake kaiwa Gen Buhari Bello,shima ramawa yakeyi kasancewarsa tsohon soja,ga Don 3 ya buge bindigarsa tun ɗazu.
Ganin faɗan ya ɗauke musu hankaline yasa don 3 ɗauke wayar Gen BB ya fita.
Sun daɗe suna faɗan kafin Ahmad yasamu nasara akansa,ta hanyar ɗaukar bindigar tasa,saita shi yayi da ita yana haki.
"Miye alaƙarka da wannann kungiyar,dama tsawon lokacin nan amanar sojoji kake ci,irinkune kesa a dunga yiwa jami'an tsaron ganin marasa gaskiya koh.......(kwafɗama sa ƙasan bindiga yayi saida ya faɗi)........kaine don 2 to wanene shugaban ƙungiyar,inaso ka faɗamin yanzunnan kokuma na jajjage kanka da bindigar nan"
Cikin ƙaraji da tashin hankali yake maganar.
Wata dariyar baka isa ba gen BB yayi wa Ahmad,cikin sauri yasaka ƙaramar wuƙa ya yanke wuyansa da itah,yana kakarin mutuwa Ahmad ya jefar da bindigarsa ya ƙarisa wajensa da sauri.
Tallafoshi yayi a razane,ga jini yanata zuba a wuyansa,abin har yakai ya kashe kansa akan yafaɗa masa wanene shugaban ƙungiyar nan?
"Yaaa....rrro kenan,mai amfanin na faɗamaka tunda nasan dama mutuwa zanyi idan ta gano kasanni........bazaka taba sanin wacece itttt.......ba"
"Dama macece ka faɗamin, wacece w......"
Shuru yayi tareda sakinsa ya koma gefe,ganin ya riga ya mutu,abin yayi matuƙar razana shi sosai.
Wayarsa ce tayi ƙara,hannunsa yana rawa ya ɗauka ganin Eemran ne.
"Hello sir mungama dasu,saidai wannan shugabannasu mun sameshi yana waya da wani"
"What definitely shugabarsu yake faɗawa mai ya faru"
"Eh nima nayi tunanin haka,na harbeshi a kafaɗarsa da dama"
"Ohh yakamata mu tafi,abin bai tafi yanda ake so ba,amma dai Alhamdulillah hakan ma mukeda nasara"
∆∆∆
"Ina jinka ka faɗamin mai yake faruwa a wajen Gen?"
"Hajiya an samu matsalane ba Ogah bane,Goje ashe sojane yayi mana baɗɗa kama,yanzu haka ya gane ogah kuma ya kamashi,na samu wayarsa ne na ƙiraki"
"Wayeshi ka faɗamin"
"Gen ........"
Kafin yaƙarisa aka katse ƙiran,kuma da alama harbeshi akayi don taji ƙarar bindiga.
"Waye ka faɗamin wayeeeeee......"
Ƙara ta saka tareda yin wurgi da wayar, kaltum ce ta tsugunna ta ɗauke wayar jikinta yana rawa.
Kallon fuskar hajiyah Mammah nakeyi,idan ka ganta zakace bazata wuce shekara talatin ba a duniya,babu wannan sunkuyawar da yamutsewar fuskar.
Mamaki abun ya bani,mai ta shafa haka ta sanja lokaci guda.
Masifa tacigaba dayi tana zuwa tana dawowa,ganin abin bazai mata ba ta jawo wani akwati a ƙarƙashin gadonta,ja ne yana glowing,kana gani kasan abun tsafi ne.
Hannunta ta saka ya buɗe,wani aljana ce ta bayyana a gabanta da baƙaƙen kaya,kamarsu ɗaya da itah,amma kana gani kasan ita ba mutum bace,to wacece kenan.
Jikina rawa ya fara daga inda nake labe da jikin ƙofa ina leƙawa,dan karfin hali bana tsoron ma ta ganni.
"Ruhina inaso kayimin bayani shin mai kasani gameda abinda yake faruwa,ƙungiyar dana kafah wadda da ita nake control na manyan ƙasar nan ta rushe,mai yasa abubuwana suke rushewa"
Muryarta da bibbiyu take fita kamar wata na'urah.
"Hakan dama dole zai faru,tunda dodo ya baki kashedi akai,matar da kike gudun kada ta bayyana harta haifi magajin wannan matakin tariga ta bayyana,kuma itace sanadiyyar karyewar alƙalaminki,indai ba kasheta kikayi ba to bazaki ƙara nasara ba"
"Kaman ya yarinya,ni banga kowa a tareda shi ba,Mulaifah ce itama kuma yanzu sun rabu"
"Hhhhhhhh duk da a zahiri kina kulada yarintarki amma hakan baya aiki a hankalin ki,shiya riga ya tsufah"
"Ruhuuuuuu karki ƙara magana akan tsufah na,bazan tsufah ba bazan taba tsufah ba,wannan fatar tsufan ina nuna ta ne kawai da iyalaina,suma in suka isheni dukka zan gama dasu nayi rayuwar ƴan ci na"
"To inba haka ba mai yasa kika kasa gane cewar Ahmad yayi rayuwa ba'a gabanki ba na tsawon shekara shida,bai kawomiki anan ya gamuda itah ba,sannan kuma yayi rayuwa a cikin ƙungiyar da kike karewa. Sannan ya bar mata da kuma ɗa a rayuwarsa ta baya.......munkasa gane hakanne a da dayake ta Addu'a a lokacin,yanzu dayake kan aikin ruguza ƙungiyarki bayayi sosai shiyasa muka gani......amma duk da haka bamuga hoton madubin rayuwar ba har yanzu"
Jikin hajiya Mammah rawa yafara bakinta yana fitar da wani hayaƙi,ganin Kultum zata fito yasa nayi saurin barin sashen nima nawa jikin yana rawa.
Me suke nufi,kenan nida ɗana mune sanadin karyewarta a yanda ta yarda,in hakane to kuwa muna cikin hatsari,sannan dole kada tasan koni wacece, matar nan ta wuce yanda nake zato.
Ina cikin tafiya ina tunani naji na bangaji mutum,saurin dawowa hankalina nayi tareda kallon Fatee.
"Ke ina kike gani haka, kaman wata sabuwar makahuwa,kije mommy tana nemanki "
Daga haka ta wuceni tana karairaya,nidai binta nayi da ido kafin na wuce sashen hajiya Maryam.
A zaune na gansu itada Neelah suna magana,ita kuma yaushe ta dawo,da alama yaune.
Saida na giashesu kafin na zauna a akan kujerar,Neelah ce ta kalleni tareda cewa.
"Miye ya faru haka Sumaimah naganki kaman wacce taga fatalwa,ko kema kinji labarin nasarar da Ahmad yayi akan ƙungiyar BC?"
"Uhm yayi nasara amma kuma yasake buɗe ƙofar gane shirinmu,domin a yanzu haka hajiya Mammah tasan da labarin yayi rayuwa a cikin ƙungiyar BC,kuma yanada ɗa da mata,duk da batasan sunanmu da fuskarmu ba amma nasan bazata zauna ba saita gano hakan"
Abinda nagani a ɗakin hajiyah Mammah na sanar dasu,duk da basu wani razana ba,amma sunyi mamakin yanda takai har haka a shu'umanci.
Mun daɗe muna tattauna,wanda duk yawanci gargaɗi hajiyah Maryam takemin akan nayi taka tsantsan, lamarin,tunda yanzu yafi nada muni,ga zaman dazan ƙarayi a sashen hajiyah Mammah,domin inkana son kama damisa dole saika shiga sansaninsa.
A ranar Ahmad yadawo daga yankinnamu,anyi murna sosai da nasararsa ciki kuwa harda hajiya Mammah,kaman ba fadarta ya ruguza ba. Musamman A.M Aliyu ba ƙaramin farin ciki yayi ba da nasarar. Ana ta murna amma bandani,domin wajen zamannawa na kullum wato lambu na tafi na zauna. Zuciyata nason ganin Ahmad domin nayi kewarsa sosai,amma kuma ina tuna kashedin da yayimin na cewar kada na kuskura nasake nuna fuskata a gabansa.
∆∆∆
Bayan sati ɗaya da wannan nasarar da gen Ahmad yasamu nutsuwarsa ta ɗan dawo ba kaman da ba,saidai duk da haka yakasa tsintar kansa da jin komai ya ƙare. Koda yake dama yasan akwai sauran rina a kaba,tunda har yanzu bai kama shugabar ƙungiyar ba,amma tunda yasan macece yanzu zarginsa kashi tamanin a cikin ɗari yana kan hajiya Maryam ne,don abinda yake kwanannan kenan saka mata ido na shige da ficenta,domin ya kula tashiga cikin tashin hankali da abinda yafaru,sannan ta tsiri zama cikin busy.
Biron hannunsa yake dannawa yana ɗagoshi,duk da hakan akwai wani abun da babu.
"Ohhh that girl why....meyasa nake missing ɗin matar wani,kaddai na fara son matar da bazata taba zama mallakina ba kai,ahah no ba sonta nake ba,inajin haushi ne da kuma zunubin abinda na aikata mata"
Cije cije yake yace wancan yace wancan shi kaɗai,a iya sati guda daya wuce gabaɗaya yaki ko gidan baya son komawa,domin yana shiga zaiji yana so ya ganta,wanda kuma yasan bazai gantan ba,shida kansa ya bata umarnin kada ya sake ganinta a inda yake.
Kai inaga barin ƙasar zayyi naɗan wasu watanni ko zaiji daɗi,dama abbah yabashi hutu tunda
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15 Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21