self please?"
Tajishi sarai amma bata juyo ba,wani kukan tasake fashewa dashi har yafi na ɗaxu.
"Am sorry am sorry please i....i can't..........."
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
*BOOK 2*
...32...
"Am sorry am sorry please i....i can't..........."
Bata gama bayanin ba taji ya rungumeta ta baya.
"Relax"
Shine abinda ya raɗa mata a kunne cikin sanyayyar murya.
Rage sautin muryar kukan tafara tana jan zuciya a hankali.
"Ki daina wannan kukan ya isa haka,tun ɗazu kikeyi zai iya affecting ɗinki, nasan kina tunanin cewa zan takuraki ne saikin faɗamin dalili,bazanyi hakan ba zan baki lokaci daga nan idan kin kwantar da hankalin ki ki faɗamin gaskiya. Yanzu godiya kawai zanyi ga Allah daya warwaremin matsalata a kusa,Alhamdulillah daya kasance kece."
Nagode da fahimtarka da kuma daɗaɗanan kalamanka,Inshaallah zan sanar dakai dalilina nayin hakan,kuma nayi ne saboda lafiyarka tawa da kuma ta ɗana,amma bawai don son rainaba"
"Uhm naji,amma duk da haka bazan gamsu ba sainaji mai nene dalilin. Sannan koba komai ni shaidane na kuladani da kikayi da kuma bin hanya mai hatsari wajen ganin kin karemin mutuncina,duk da nasan hadda kishi a lamarin"
Ƴar dariya tayi kaɗan a cikin kukan tareda ɗora hannunta akan nasa,daidai lokacin kuma cikinta yayi motsi.
Daidai wajen ya ɗora hannunsa tareda sakin ajiya numfashi.
"Am sorry for calling you illegal blood.....ƙanin sayyid koh,inada yaro amma bansani ba"
Ɗaga masa kai tayi tareda murmushi.
"Kayi haƙuri hakan Yazama dolene,nagaji da tsayuwa zan tafi idan na huta in mun sake haɗuwa zan faɗamaka mai yake faruwa,amma kafin sannan dan Allah kada ka faɗawa kowa ni wacece indai ba Neelah ba"
"Taya kikasan Neelah?"
"Labari mai tsayi"
Juyowa yayi da itah tareda share hawayen kan kumatunta.
"Dama haka kike da saurin kuka,shine ya ceceki da kuma tunawa danayi halinda kike ciki,amma da sai raina ya baci sosai"
"Kaima kanada laifi"
Tafaɗa tareda kallon cikin idonsa.
"Wanne laifi nayi,saboda nakasa ganeki?"
"Ahah ba wannan ba,kafin lokacin da hankalin ka yadawo,na daɗe ina zaune a gefenka tareda jiran ka tashi,amma daka tashi baka tasheni ba sai kawai gani nayi baka nan ka tafi ka barni. Kuma nasan ka ganni a wajen gadonnaka"
"Naganki kam,kuma na yarda laifina ne,amma na amshi hukuncina tunda na zauna da matata tsawon lokaci bansan ita bace"
Ɗan yin baya tayi zata faɗi ya riqota tareda tambayar miye.
"Jiri nake ɗanji ne,barinaje na kwanta"
Hannunta take ƙoƙarin cirewa daga nasa,amma yasake riƙota.
"Ina zakije barina kaiki ɗaki ki kwanta,kinci abinci ma kuwa?"
"Naci saidai inna tashi a bacci na ƙara,ahah ka bari na tafi ɗakinmu,inna zauna anan za'a zargi wani abun,nayi maka alƙawarin zan dawo daga na tashi"
"Nikuma banmiki alƙawarin barinki ki tafiba,domin hankalina bazai kwanta ba. Muje ki kwanta kuma anan sashen,bake ba komawa can kin dawo nan. Har sai kin faɗamin dalilin dayasa karna faɗawa kowa ke matata ce"
Yana gama faɗin hakan ya cirata sama zuwa ɗakinsa.
Tun tana mutsu mutsun ya sauƙeta har tayi shuru ta haƙura. (Ku tashi mafarki ne😀😀😀)
_____Tashi tayi daga kan kujerar tareda yin hamma,da Ahmad suka haɗa ido wanda shima itan yake kallo,duk da kafin sannan hankalin sa nakan system ɗin dake gabansa.
Tun lokacin daya raka Musbahu ba direct yashigoba ya tsaya yin waya daga wajen aiki,yana shigowa ya sameta tayi bacci a inda suka barta. Ta gaji amma tasan dole zai tambayeta wani abun saboda baƙon lamari dayaji. Shine a cikin wannan yanayij harta samu damar yin bacci? Harda mafarki? Haba no wonder hakan yake mata kaman bashiba,ashe bada gaske bane.
"Sannu da tashi"
Ya faɗamata yana kallonta.
Kunya ce ta kamata ganin abinda tayi.
"Kayi haƙuri"
Tafaɗa a sanyaye,itama tayi mamakin yin baccinnata yanzu,daga kuka kawai sai bacci.
Tashi tayi ta gyara rigar jikinta tareda ɗaukar hijabinta zata tafi.
Har ta fara tafiyah taji maganar sa.
"Na zauna tsawon awa guda ina jiran ki tashi domin ki faɗamin dalilinki nayin haka,amma daga tashi saiki tafi?"
"Zanyi sallah ne nasan lokaci yayi"
Ba wani sallah kawai don ta samu excuse ɗin fitane.
"Nan sashen baya sallah,ki shiga kiyi sallahr idan kin gama kuma kizo"
"To"
Tace ba musu tareda nufar ɗakinnasa.
Daidai lokacin data idar yashigo ɗakin,a bakin gado ya zauna.
"Uhmm fara bayani ina jinki,kince kinada dalilinki wanne daliline?"
"Uhmm zaka ɗan iyah bani lokaci kafin........."
"Babu wannan maganar,dolene ki faɗamin mai yake faruwa,hajiyah maryam tasan ke matata ce"
Ɗaga masa kai tayi da eh.
"Sannan nasan itace tace kada ki faɗamin,shiyasa kwanaki tayi barazana dake domin hanani yin bincike akan ta. Kuma itace ta hanaki faɗamin ko?"
Tashi yayi a zuciye yana faɗin.
"Barina je wajennata na tabbatar tunda ke ta hanaki magana,kuma kaman yanda bataso kowa sai yasan matsayinki a wajena"
Jin abinda ya faɗa Sumaimah batasan lokacin data tashi tariqoshi ta baya ba.
"Karkaje na roqeqa kada ka rushe abinda muke tsarawa,rayuwar mu na tangal tangal akai. Ba hajiyah maryam bace take aikata abinda kake tunani,hasalima duk duniya idan da wanda bazai cutar dakai ba itace."
Juyowa yayi yana yiwa Sumaimah kallon tana da hankali kuwa.
"Eh inada hankali kuma nasan mai nake,na roqeka kabi komai a sannu,makashinka na tareda kai amma ba hajiyah Maryam bace"
"Taya kike tunanin zan yarda da wannan maganar taki,keda bakisan mai yake faruwa ba"
"Saboda ita ɗin......ita ɗin mahaifiyarka ce wacce ta haifeka. Hajiyah Mammah ita ke ƙulla maka komai Tundaga farko. Shugabar kungiyar BC ma da kake nema itace,inada shaidar hakan domin ni jiyau ce ba ganau ba. Nasan lokacin da kake ƙungiyar a matsayin na ɗaya daga cikinsu dan haka tun ranar dana shigo ɗakinnan na farko naga takaddu akan kungiyar,anan nagano kana bincikene akai.
Sannan a ranar naci karo da hajiyah Mammah itada mai aikinta sun shigo ta jikin bangon gidannan.
Ko lokacin dakuka ci nasara akan BC an ƙira an faɗawa hajiyah Mammah abinda kayi a wajen,wanda yanxu haka babban bincikenta nakan ta gano rayuwar dakayi a bayane. Nasan hakanne saboda aikin baɗɗa kama danake a sashenta. Batun mahaifiyar ka ma hajiyah Maryam duk itace ta rabaku,ta ƙwaceka tun kana jariri a wajenta,Sannan tace idan tafaɗawa duniya kai danta ne saita kasheka........duk wanann bazaka gane ba saina baka labarin mai ya faru.
Ta gargaɗeni da kada na faɗamaka,amma ka riga ka gano wacece ni,dan haka banida zabi daya wuce na faɗamaka mai yake faruwa...."
Labarin abinda tasani tunda ga zuwanta gidan ta sanar masa har zuwa yanzun.
Tun sunayi a tsaye har ta samu waje ta zauna,amma shikam bai zauna ba,ya kafeta da ido tunda tafara har zuwa yanxun,jin abinda take faɗamasa yayi kaman almara,garin ya hakan ya faru amma bai sani ba.......
Ya tafi dogon tunani lokacin data gama bashi labarin tayi shuru,sai bayan taci gaba ne tukunna ya dawo da hankalin sa kanta.
"Wannan shine dalilina na ƙin faɗamaka ni wacece,amma tsawon wannan lokacin ina cutuwa da rashin sanina da bakayi ba,musamman abinda Mulaifah tayi maka,shiyasa na jefa kaina ba tareda tunanin abinda zai faru ba. Haka ma hajiyah Maryam tana cutuwa da nesanta kanta daga gareka tsawon wannan lokacin,bugu da ƙari ga jinyar da take fama da itah tsawon shekara da shekaru,jiya ma saida aka ƙara mata jini. Jikinta yayi tsanani sosai,abinda hajiyah Mammah take ya kamata a dakatar da itah haka.
Takowa yayi a hankali ya zauna a inda take,kana ganinsa kasan jikinsa yayi matuƙar sanyi.
Hannunta ya kama tareda riƙewa a cikin nasa.
"Shin mai zance dake,kwata kwata ma miyasa ban ɗago ba da ya Musbahu yacemin sunanki Sumaimah,ban taba kawo kece matata danake nema ba shiyasa.
Kinyimin abubuwa a rayuwata ta baya,haka ma kinyimin a wannan. Abubuwan da kikayimin bazan taba misaltasu ba,dan haka godiya ma bazata iyah fitowa daga bakina ba,domin tayi kaɗan.
Kuɗin matane da samunsu a cikin al'umma zayyi matuƙar wuyah,nagode da kare min mutuncina da kikayi,nagode da karemin mutuncinki da kikayi,nagode da haifamin ɗana na farko duk da bana tareda ke,Sannan na goɗe da ɗaukamin yaro na biyu duk da bana a cikin hankalina da kuma sani.
Nayi miki alƙwarin nuna miki so da kuma ƴaƴana,zan nuna musu kulawar da ban basu ba a da. Nagode da shigowarki rayuwatah Sumaimah. Har ma da haƙuri dakikayi dani bansan mai zance ba,nasan ba halina da nagartata ce takai ba da har Allah ya hadani dake babu abinda zan.........."
Jijjiga masa kai takeyi ganin maganganunnasa da yawa.
"Karka ce haka,ka wuce duk yanda kake tunani a wajena,kai ɗin na dabanne. Koda kana a lokacin baya kana mutunta inna a matsayin mahaifiya,lokacin da banida lafiyah ka tausayamin ka,ka siyamin magani ka sakani a makaranta dana faɗamaka ina so.
Sannan da muka shirya kamar sauran ma'aurata kai ɗin namijine wanda yasan yadda zai bi da mace. Ko daren mu na farko ma ba.........."
Hannu ta saka a bakinta tareda yin murmushi.
Fitar da hannunnata yayi tareda cewa.
"Mai nayi a ranar faɗamin"
"Ahah bazan faɗaba gaskiya,ka ƙyaleni"
Riqota yayi ganin tana ƙoƙarin guduwa.
"Ina zakije bazaki faɗamin ba wai?"
"To ka sakeni zan faɗamaka"
Yana sakinta ta tashi da gudu,tana dariyah.
"Bazan faɗa maka ba,kayi zuciya ka tuno,abu ɗaya zaka sani shine .......kaƙi ka tashi kayi wanka da kyar na tasheka"
Binta yayi da sauri kafin ya fitah har ta kai bakin ƙofah.
Takalar baƙin ƙofah tayi,cikin zafin nama ya tareda kafin takai ƙasa.
Numfashi take fitarwa sama sama don ta tsorita sosai.
"Habibteee pay attention,kidaina wasa da rayuwarki da kuma na yaron cikinki kinji"
Ɗaga masa kai tayi da toh.
"Rungumeta yayi,sun daɗe a haka kafin ya ɗagota dayaga hankalin ta ya dawo kanta.
Kallon idonta yakeyi cikeda so da kuma kulawa.
Itama shiɗin take kallo cikeda so da burgewa.
"Kayi haƙuriii!!!"
Tafaɗa cikin siririyar murya.
"Okay ya wuce amma ki kula nan gaba sosai,muje ki rakani wajen hajiyah maryam ina so nayi magana da itah"
"Toh"
SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
*BOOK 2*
...33...
Sumaimah ce tafara shiga ɗakin,hajiya Maryam na zaune a bakin gado,hannunta na riqe da ƙirjinta,sai tari take wanda kana gani kasan wahala take sha.
Da gudu ta isa gabanta tareda riqe ɗaya hannunnata,
"Hajiya yadai jikinne ko zamu koma asibitinne"
"Ahah bazan komaba Sumaimah,kozan koma ma yanzu bazayyi ba,jikina yanzu ya daina regulating baƙon jini,is no more lokaci na yayi haka,ki kulada kanki da kuma mijinki Sumaimah,yanzu na maida komai kanki ina miki fatan ki samu nasara ke.
"Ahah dan Allah karki ce haka,zamu samu mafita,nasan abinda yake saka miki wanann matsalar,wannan akwatin nata ne,in muka wargazashi shikenan"
Duk abinda suke Ahmad na tsaye yana kallonsu,inda Sumaimah bata bashi labarin abinda ya faru ba da bazai san mai suke faɗa ba.
Hajiyah maryam ce ta fara ɗaga ido ta ganshi,sai kuma Sumaimah.
A razane da kalleshi,domin tunda take dashi bai taba shigowa ɗakinta ba,maida kallonta tayi ga Sumaimah,tareda alamar biɗar ƙarin bayani..
"Sumaimah mai...,..."
"Eh yariga yasan mai yake faruwa,yasan matsayinki da kuma matsayina a wajensa"
"Meyasa meyasa kin kuwa san kasadar da kikayi, abubuwan suna tafiyah ba yanda muka tsaraba,the more mutane na shigowa the more hatsarin hakan yana ƙaruwa"
Matsowa Ahmad yayi kusada Itah tareda tsugunnawa.
Ɗauke kanta tayi idonta yana zubar da hawaye,tayaya ne zata iyah haɗa ido dashi ita kuwa,bayan abinda tamasa da bazai misaltu ba.
"Um.....mmeee"
Runtse idonta tayi jin kalmar daya kirata da ita,abinda bata taba zato ba a rayuwarta. Ita kanta Sumaimah tayi mamakin furucinnasa sosai.
"Shin bazaki amsa ba,wannan shine sunan danake ambaton mahaifiya ta dashi a cikin Addu'a ta,yanzu kuma tunda ga mai sunan a gabana shiyasa na ƙirayeki dashi,shin bazaki amsa ba?"
Kuka hajiyah Maryam ta rushe dashi.
"Bazan amsa ba bazan iyah ba,bai dace dani ba sam,nagaza nakasa,nayi zaton zan iya amma ashe ba haka bane"
"Ke kuwa kika kai ummeee,abinda kikayi ba kowacce uwace zata iya ba,ko a da dabana ganinki a matsayin mahaifiya ta,amma nasan keɗin jajirtacciyar mata ce. Nine na gaza na kasa,da har ban iya kallo soyayyata a idanunki ba,sai yanzu nagane da kinada niyyar cutata da tuni kin cutar dani ina yaro,saidai kullum ki dunga treating ɗina. Dan Allah ki juyo ki kalleni."
A hankali take juyo da kanta har suka haɗa ido,da alama bataso hakan ba,amma roqon da ɗannata yake yi mata abune da bazata iyah riqewa ba sam.
Kafeshi tayi da ido har sannan bata daina kuka ba,hannayenta takai kan kumatunsa,tamkar tasaka ƙaramin yaro a gabanta.
Shafah kumatunsa takeyi wanda rabonta data taba tun yana jinjiri.
"Ah...ahhmadd kayi haƙuri ka yafemin,shayarwa iyah na wata biyu kawai nayi maka,girman da yaro yake a gaban mahaifiyarsa duk baka samu ba, saboda wani yankyakykyen hukuncina".
Duk kasancewar sa namiji mai dauriya,amma ganinta a gabansa tana roqonsa sai ya tsinci kansa da kasa riqe kansa..
Rungumeta yayi kaman zai shige cikinta inda ya fito,wata soyayyarta ne ke shigarsa Tamkar an jonawa tanki bututun ruwa.
Sun daɗe a haka Sumaimah ta zuba musu ido. Hawayen idonta ta share,data tuna cewar itama bata san tata mahaifiyar ba,kuma tasan bazata taba ganinta ba,tunda ta koma ga mahaliccinta.
Jikinta ne ya shika,hakanne yasakashi ɗagota domin yaga menene,idonta a rufe tamkar bata numfashi..
Jijjiga ta yakeyi amma shuru,waigawa yayi inda Sumaimah take.
"Sumaimah ya zanyi bata motsi fah"
"Jinin jikinta ne ya ƙare,inaga muyi gaggawar kaita asibiti yanzu"
Tashi tayi shikuma ya ɗauketa irin bridal style ɗinnan suka fitah,tashin hankalin daya shiga ya dade baishiga irin sa ba.
A hanyar fita suka haɗu da Maimuna tana magana da Fatee wacce tafito daga motar Saleem sun dawo daga ɗakkota a makaranta.
Ganin Ahmad ɗauke da hajiyah Maryam kaman bata numfashi yasaka su sakin baki suna kallonsa.
Abu ɗayane yazo ransu shine wani abu ya aikata mata.
Saleem ne yasha gabansa cikin bacin rai.
"Yah Ahmad mai kayiwa mommy"
Kallonsa yakeyi da idanunsa wanda ya kaɗa yayi ja. Ya kasa bude bakinsa balle ya bashi amsa.
Ganin hakanne yasa Sumaimah shiga tsakiyar su tace.
"Babu abinda yayi mata dama bata da lafiyah,kaita asibiti zamuyi kubiyomu a baya,amma bayan Sameer kada ku faɗawa kowa mai yake faruwa a gidannan"
Maganar da Sumaimah tayi ne cikin alamar roqo yasaka Saleem matsawa Ahmad ya wuce da hajiyah Maryam a hannunsa.
A gidan baya ya ajiyeta inda Sumaimah tashiga,sai kuma shi ya shiga wajen driver.
Sai bayan sun fita daga gidan kafin su Maimuna suka bi bayansu.
Asibitin gidan marayunta suka nufah,amma a hanya saida suka ƙira babban likita tukunna,wanda suka yayi mata magani na ƙarshe.
Ɗakin karbar mutum na gaggawa aka shiga da itah suna isowa,daidai lokacin kuma su Maimuna suka iso,harda Sameer wanda sukayiwa bayani dama yana kusada wajen.
Babu wanda yake magana a cikinsu,amma kana ganinsu kasan suna buƙatar ƙarin bayani.
Likitanne yafito daga wajen cikin sauri.
"Am duk da jinin ta A+ ne bashida wuyar samun donor,amma kasancewar an daɗe ana bata jini dayawa,yanzu jikinta bazai ƙarba ba sai wanda DNA yayi ɗaya wato jininta"
Yana gama bayanin Sameer da Saleem sukabi bayan sa,Sumaimah tana ganin haka ta kalli Ahmad akan yaje.
"Kaje mana dan Allah,wataƙila sai naka yafi kamancece niya da nata"
Su Maimuna suna jin abinda take faɗa,amma basu fahimce ta ba..
Shiga yayi wajen ɗaukar jinin yabada sample ɗin nasa shima ya fito.
Suna nan tsaye bayan an karbi sample ɗin Sumaimah ta riqe kunkuminta,wani irin kamawa taji yayi mata.
Duk abinda take Ahmad yana kulada itah,cikin wani ɗaki ya shiga ya ɗauko kujera,wajen babu gun zama,yasan kuma in yace taje wajen zama bazata tafi ba.
A gabanta ya ajiye kujerar tareda kama hannayenta ya zaunar da itah.
Da mamaki take kallonsa,kenan yasan ta gaji,hakan yayi mata daɗi sosai,amma taji kunya ganin su Saleem suna kallonta.
"Yah Ahmad matar wani ce fah kake taba jikinta,yanzu kai......"
Wani kallo yayi mata dole ta haɗiye abinda yake bakinta.
Wata nurse ta fito da wata takarda a hannunta.
"Ana ƙiran Ahmad Aliyu,ka shigo wai naka yafi zama iri ɗaya da nata"
"Ohk"
Daga haka ta koma ciki.
Da Murmushi Sumaimah ta kalleshi wanda shima ita ɗin yake kallo.
"Kaga abinda nake faɗamaka koh?"
"Uhm nagani,barina shiga kada ki tashi ki tsaya,ki zauna yanzu zan fito. In kina jin kishirwa Saleem ya nemo miki wani abun uhm?"
"Uhm naji ka shiga Allah ya taimaka yavata lafiya"
Ahmad yana shigewa Fatee ta matso inda Sumaimah take.
"Ke bangane ba mai yake faruwane,shine zai bawa mommy jini a wanne dalilin,wani shirin kuke haɗawa saboda ku kasheta koh? Ke kuma mecece alaƙarki dashi kina matar wani,nake ganin kaman ta Allah ashe........."
"Ke Fatee miye kike hakane,meyasa duk abinda yazo zuciyarki shi kike faɗane. Mahaifiyarki na ciki batada lafiya amma kin gulma"
"To laifinta ka gani,ai dole ta tambaya,nima abin ya ɗauremin kai,miye tsakanin mommy da yah Ahmad da har zai bata jini,wai kuma kuda kuke ƴaƴan ta naku bayyi daidai ba sai nata?"
Maimuna ce tayi maganar cikin kasa gane mai yake faruwa.
Duk abinda sukeyi babu wanda Sumaimah tasaka baki,da abin yayi yawane ma tace musu waƙa a bakin mai ita tafi daɗi.
Bayan an gama jan jinin an ɗaura mata kafin aka barsu suka shiga.
Zuwa lokacin anyi mata allurar bacci.
Fatee ce a zaune a gefen kanta sai su Sameer a tsaye,Sumaimah kuma na gefe a zaune.
Can kaman an ɗan daɗe ta fara juya kanta kaɗan kaɗan.
Fatee da Maimuna ne suka ɗan ɗagota tareda saka mata pillow ganin tana ƙoƙarin tashi.
Idonta akan Ahmad ya sauqa wanda shima ita ɗin yake kallo cikeda soyayya irin ta ɗa da mahaifi.
Sannu sannu su Sameer suka mata,fatee kam rungumeta tayi tana kuka.
"Mommy bakida har haka amma baki faɗamin ba har kwanciya fah kikayi"
"Kin damu ki sani ne,miye ya dameki banda kanki uhm"
Hajiyah Maryam tafaɗa tana dafa kanta..
"Habadai mommy you know i love you"
"Umm naji i love you too,yanxu dai ɗagani bake kaɗai bace a ɗakin koh?"
Ƙin matsawa tayi saida ta tureta tukunna,sai turo baki take kaman zai faɗi.
"Sannu Ummee jikinnaki yanzu"
Ahmad yafaɗa a nutse cikin kulawa.
Murmushi tayi tareda ɗaga masa kai.
"Ummee ya jikin?"
"Alhamdulillah Sumaimah....kinci abinci kuwa?"
"Ahah"
"Tabb Ahmad ka ɗauketa ku tafi gida taci abinci,batayin awa uku ma bataci ba,cikin jikinta mai neman abincine"
"Ahah yau banajin yunwar zan zauna har a sallameki saimu tafi"
Cikeda rigima tayi maganar,wanda hakan yasaka hajiyah Maryam haɗa rai.
"Ahah ku tafi nima yanzu zan tafi idan jininnan yaƙare,uhm yau kuma a wanne bawan Allah aka ɗauka?"
"Mommy yah Ahmad ne yabayar,yaushe kuka shirya dashi da har yabaki jini kuma ya kawoki asibiti,ga waccar mai aikin sai wani kula kike da ita kamar wata mai muhimmanci"
"Buge bakin Fatee hajiyah Maryam tayi tareda cewa.
"Ƙaniyarki da ce mata ƴar aiki,tunda har kunga ya haka yakamata kusan mai yake faruwa.
Ahmad ɗanane na fari kafin na haifi Maimuna,sannan ita kuma matarsa ce wacce ya aureta a lokacin da yayi shekara biyar baya nan. Tanada ɗa mai sunan mahaifin Ahmad kuma yayan babanku wato Muhammad,ana ƙiransa da Sayyid.. (Ta faɗa tana kallon Sumaimah. Wannan suma itan suka kalla cikeda mamaki)
Wannan shine abinda baku sani ba,sauran boyayyun labaran kuma sai daga baya. Sannan wannan maganar banaso tabar wajennan,akwai wanda sanin
Showing 51001 words to 54000 words out of 62659 words
Tajishi sarai amma bata juyo ba,wani kukan tasake fashewa dashi har yafi na ɗaxu.
"Am sorry am sorry please i....i can't..........."
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
*BOOK 2*
...32...
"Am sorry am sorry please i....i can't..........."
Bata gama bayanin ba taji ya rungumeta ta baya.
"Relax"
Shine abinda ya raɗa mata a kunne cikin sanyayyar murya.
Rage sautin muryar kukan tafara tana jan zuciya a hankali.
"Ki daina wannan kukan ya isa haka,tun ɗazu kikeyi zai iya affecting ɗinki, nasan kina tunanin cewa zan takuraki ne saikin faɗamin dalili,bazanyi hakan ba zan baki lokaci daga nan idan kin kwantar da hankalin ki ki faɗamin gaskiya. Yanzu godiya kawai zanyi ga Allah daya warwaremin matsalata a kusa,Alhamdulillah daya kasance kece."
Nagode da fahimtarka da kuma daɗaɗanan kalamanka,Inshaallah zan sanar dakai dalilina nayin hakan,kuma nayi ne saboda lafiyarka tawa da kuma ta ɗana,amma bawai don son rainaba"
"Uhm naji,amma duk da haka bazan gamsu ba sainaji mai nene dalilin. Sannan koba komai ni shaidane na kuladani da kikayi da kuma bin hanya mai hatsari wajen ganin kin karemin mutuncina,duk da nasan hadda kishi a lamarin"
Ƴar dariya tayi kaɗan a cikin kukan tareda ɗora hannunta akan nasa,daidai lokacin kuma cikinta yayi motsi.
Daidai wajen ya ɗora hannunsa tareda sakin ajiya numfashi.
"Am sorry for calling you illegal blood.....ƙanin sayyid koh,inada yaro amma bansani ba"
Ɗaga masa kai tayi tareda murmushi.
"Kayi haƙuri hakan Yazama dolene,nagaji da tsayuwa zan tafi idan na huta in mun sake haɗuwa zan faɗamaka mai yake faruwa,amma kafin sannan dan Allah kada ka faɗawa kowa ni wacece indai ba Neelah ba"
"Taya kikasan Neelah?"
"Labari mai tsayi"
Juyowa yayi da itah tareda share hawayen kan kumatunta.
"Dama haka kike da saurin kuka,shine ya ceceki da kuma tunawa danayi halinda kike ciki,amma da sai raina ya baci sosai"
"Kaima kanada laifi"
Tafaɗa tareda kallon cikin idonsa.
"Wanne laifi nayi,saboda nakasa ganeki?"
"Ahah ba wannan ba,kafin lokacin da hankalin ka yadawo,na daɗe ina zaune a gefenka tareda jiran ka tashi,amma daka tashi baka tasheni ba sai kawai gani nayi baka nan ka tafi ka barni. Kuma nasan ka ganni a wajen gadonnaka"
"Naganki kam,kuma na yarda laifina ne,amma na amshi hukuncina tunda na zauna da matata tsawon lokaci bansan ita bace"
Ɗan yin baya tayi zata faɗi ya riqota tareda tambayar miye.
"Jiri nake ɗanji ne,barinaje na kwanta"
Hannunta take ƙoƙarin cirewa daga nasa,amma yasake riƙota.
"Ina zakije barina kaiki ɗaki ki kwanta,kinci abinci ma kuwa?"
"Naci saidai inna tashi a bacci na ƙara,ahah ka bari na tafi ɗakinmu,inna zauna anan za'a zargi wani abun,nayi maka alƙawarin zan dawo daga na tashi"
"Nikuma banmiki alƙawarin barinki ki tafiba,domin hankalina bazai kwanta ba. Muje ki kwanta kuma anan sashen,bake ba komawa can kin dawo nan. Har sai kin faɗamin dalilin dayasa karna faɗawa kowa ke matata ce"
Yana gama faɗin hakan ya cirata sama zuwa ɗakinsa.
Tun tana mutsu mutsun ya sauƙeta har tayi shuru ta haƙura. (Ku tashi mafarki ne😀😀😀)
_____Tashi tayi daga kan kujerar tareda yin hamma,da Ahmad suka haɗa ido wanda shima itan yake kallo,duk da kafin sannan hankalin sa nakan system ɗin dake gabansa.
Tun lokacin daya raka Musbahu ba direct yashigoba ya tsaya yin waya daga wajen aiki,yana shigowa ya sameta tayi bacci a inda suka barta. Ta gaji amma tasan dole zai tambayeta wani abun saboda baƙon lamari dayaji. Shine a cikin wannan yanayij harta samu damar yin bacci? Harda mafarki? Haba no wonder hakan yake mata kaman bashiba,ashe bada gaske bane.
"Sannu da tashi"
Ya faɗamata yana kallonta.
Kunya ce ta kamata ganin abinda tayi.
"Kayi haƙuri"
Tafaɗa a sanyaye,itama tayi mamakin yin baccinnata yanzu,daga kuka kawai sai bacci.
Tashi tayi ta gyara rigar jikinta tareda ɗaukar hijabinta zata tafi.
Har ta fara tafiyah taji maganar sa.
"Na zauna tsawon awa guda ina jiran ki tashi domin ki faɗamin dalilinki nayin haka,amma daga tashi saiki tafi?"
"Zanyi sallah ne nasan lokaci yayi"
Ba wani sallah kawai don ta samu excuse ɗin fitane.
"Nan sashen baya sallah,ki shiga kiyi sallahr idan kin gama kuma kizo"
"To"
Tace ba musu tareda nufar ɗakinnasa.
Daidai lokacin data idar yashigo ɗakin,a bakin gado ya zauna.
"Uhmm fara bayani ina jinki,kince kinada dalilinki wanne daliline?"
"Uhmm zaka ɗan iyah bani lokaci kafin........."
"Babu wannan maganar,dolene ki faɗamin mai yake faruwa,hajiyah maryam tasan ke matata ce"
Ɗaga masa kai tayi da eh.
"Sannan nasan itace tace kada ki faɗamin,shiyasa kwanaki tayi barazana dake domin hanani yin bincike akan ta. Kuma itace ta hanaki faɗamin ko?"
Tashi yayi a zuciye yana faɗin.
"Barina je wajennata na tabbatar tunda ke ta hanaki magana,kuma kaman yanda bataso kowa sai yasan matsayinki a wajena"
Jin abinda ya faɗa Sumaimah batasan lokacin data tashi tariqoshi ta baya ba.
"Karkaje na roqeqa kada ka rushe abinda muke tsarawa,rayuwar mu na tangal tangal akai. Ba hajiyah maryam bace take aikata abinda kake tunani,hasalima duk duniya idan da wanda bazai cutar dakai ba itace."
Juyowa yayi yana yiwa Sumaimah kallon tana da hankali kuwa.
"Eh inada hankali kuma nasan mai nake,na roqeka kabi komai a sannu,makashinka na tareda kai amma ba hajiyah Maryam bace"
"Taya kike tunanin zan yarda da wannan maganar taki,keda bakisan mai yake faruwa ba"
"Saboda ita ɗin......ita ɗin mahaifiyarka ce wacce ta haifeka. Hajiyah Mammah ita ke ƙulla maka komai Tundaga farko. Shugabar kungiyar BC ma da kake nema itace,inada shaidar hakan domin ni jiyau ce ba ganau ba. Nasan lokacin da kake ƙungiyar a matsayin na ɗaya daga cikinsu dan haka tun ranar dana shigo ɗakinnan na farko naga takaddu akan kungiyar,anan nagano kana bincikene akai.
Sannan a ranar naci karo da hajiyah Mammah itada mai aikinta sun shigo ta jikin bangon gidannan.
Ko lokacin dakuka ci nasara akan BC an ƙira an faɗawa hajiyah Mammah abinda kayi a wajen,wanda yanxu haka babban bincikenta nakan ta gano rayuwar dakayi a bayane. Nasan hakanne saboda aikin baɗɗa kama danake a sashenta. Batun mahaifiyar ka ma hajiyah Maryam duk itace ta rabaku,ta ƙwaceka tun kana jariri a wajenta,Sannan tace idan tafaɗawa duniya kai danta ne saita kasheka........duk wanann bazaka gane ba saina baka labarin mai ya faru.
Ta gargaɗeni da kada na faɗamaka,amma ka riga ka gano wacece ni,dan haka banida zabi daya wuce na faɗamaka mai yake faruwa...."
Labarin abinda tasani tunda ga zuwanta gidan ta sanar masa har zuwa yanzun.
Tun sunayi a tsaye har ta samu waje ta zauna,amma shikam bai zauna ba,ya kafeta da ido tunda tafara har zuwa yanxun,jin abinda take faɗamasa yayi kaman almara,garin ya hakan ya faru amma bai sani ba.......
Ya tafi dogon tunani lokacin data gama bashi labarin tayi shuru,sai bayan taci gaba ne tukunna ya dawo da hankalin sa kanta.
"Wannan shine dalilina na ƙin faɗamaka ni wacece,amma tsawon wannan lokacin ina cutuwa da rashin sanina da bakayi ba,musamman abinda Mulaifah tayi maka,shiyasa na jefa kaina ba tareda tunanin abinda zai faru ba. Haka ma hajiyah Maryam tana cutuwa da nesanta kanta daga gareka tsawon wannan lokacin,bugu da ƙari ga jinyar da take fama da itah tsawon shekara da shekaru,jiya ma saida aka ƙara mata jini. Jikinta yayi tsanani sosai,abinda hajiyah Mammah take ya kamata a dakatar da itah haka.
Takowa yayi a hankali ya zauna a inda take,kana ganinsa kasan jikinsa yayi matuƙar sanyi.
Hannunta ya kama tareda riƙewa a cikin nasa.
"Shin mai zance dake,kwata kwata ma miyasa ban ɗago ba da ya Musbahu yacemin sunanki Sumaimah,ban taba kawo kece matata danake nema ba shiyasa.
Kinyimin abubuwa a rayuwata ta baya,haka ma kinyimin a wannan. Abubuwan da kikayimin bazan taba misaltasu ba,dan haka godiya ma bazata iyah fitowa daga bakina ba,domin tayi kaɗan.
Kuɗin matane da samunsu a cikin al'umma zayyi matuƙar wuyah,nagode da kare min mutuncina da kikayi,nagode da karemin mutuncinki da kikayi,nagode da haifamin ɗana na farko duk da bana tareda ke,Sannan na goɗe da ɗaukamin yaro na biyu duk da bana a cikin hankalina da kuma sani.
Nayi miki alƙwarin nuna miki so da kuma ƴaƴana,zan nuna musu kulawar da ban basu ba a da. Nagode da shigowarki rayuwatah Sumaimah. Har ma da haƙuri dakikayi dani bansan mai zance ba,nasan ba halina da nagartata ce takai ba da har Allah ya hadani dake babu abinda zan.........."
Jijjiga masa kai takeyi ganin maganganunnasa da yawa.
"Karka ce haka,ka wuce duk yanda kake tunani a wajena,kai ɗin na dabanne. Koda kana a lokacin baya kana mutunta inna a matsayin mahaifiya,lokacin da banida lafiyah ka tausayamin ka,ka siyamin magani ka sakani a makaranta dana faɗamaka ina so.
Sannan da muka shirya kamar sauran ma'aurata kai ɗin namijine wanda yasan yadda zai bi da mace. Ko daren mu na farko ma ba.........."
Hannu ta saka a bakinta tareda yin murmushi.
Fitar da hannunnata yayi tareda cewa.
"Mai nayi a ranar faɗamin"
"Ahah bazan faɗaba gaskiya,ka ƙyaleni"
Riqota yayi ganin tana ƙoƙarin guduwa.
"Ina zakije bazaki faɗamin ba wai?"
"To ka sakeni zan faɗamaka"
Yana sakinta ta tashi da gudu,tana dariyah.
"Bazan faɗa maka ba,kayi zuciya ka tuno,abu ɗaya zaka sani shine .......kaƙi ka tashi kayi wanka da kyar na tasheka"
Binta yayi da sauri kafin ya fitah har ta kai bakin ƙofah.
Takalar baƙin ƙofah tayi,cikin zafin nama ya tareda kafin takai ƙasa.
Numfashi take fitarwa sama sama don ta tsorita sosai.
"Habibteee pay attention,kidaina wasa da rayuwarki da kuma na yaron cikinki kinji"
Ɗaga masa kai tayi da toh.
"Rungumeta yayi,sun daɗe a haka kafin ya ɗagota dayaga hankalin ta ya dawo kanta.
Kallon idonta yakeyi cikeda so da kuma kulawa.
Itama shiɗin take kallo cikeda so da burgewa.
"Kayi haƙuriii!!!"
Tafaɗa cikin siririyar murya.
"Okay ya wuce amma ki kula nan gaba sosai,muje ki rakani wajen hajiyah maryam ina so nayi magana da itah"
"Toh"
SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
*BOOK 2*
...33...
Sumaimah ce tafara shiga ɗakin,hajiya Maryam na zaune a bakin gado,hannunta na riqe da ƙirjinta,sai tari take wanda kana gani kasan wahala take sha.
Da gudu ta isa gabanta tareda riqe ɗaya hannunnata,
"Hajiya yadai jikinne ko zamu koma asibitinne"
"Ahah bazan komaba Sumaimah,kozan koma ma yanzu bazayyi ba,jikina yanzu ya daina regulating baƙon jini,is no more lokaci na yayi haka,ki kulada kanki da kuma mijinki Sumaimah,yanzu na maida komai kanki ina miki fatan ki samu nasara ke.
"Ahah dan Allah karki ce haka,zamu samu mafita,nasan abinda yake saka miki wanann matsalar,wannan akwatin nata ne,in muka wargazashi shikenan"
Duk abinda suke Ahmad na tsaye yana kallonsu,inda Sumaimah bata bashi labarin abinda ya faru ba da bazai san mai suke faɗa ba.
Hajiyah maryam ce ta fara ɗaga ido ta ganshi,sai kuma Sumaimah.
A razane da kalleshi,domin tunda take dashi bai taba shigowa ɗakinta ba,maida kallonta tayi ga Sumaimah,tareda alamar biɗar ƙarin bayani..
"Sumaimah mai...,..."
"Eh yariga yasan mai yake faruwa,yasan matsayinki da kuma matsayina a wajensa"
"Meyasa meyasa kin kuwa san kasadar da kikayi, abubuwan suna tafiyah ba yanda muka tsaraba,the more mutane na shigowa the more hatsarin hakan yana ƙaruwa"
Matsowa Ahmad yayi kusada Itah tareda tsugunnawa.
Ɗauke kanta tayi idonta yana zubar da hawaye,tayaya ne zata iyah haɗa ido dashi ita kuwa,bayan abinda tamasa da bazai misaltu ba.
"Um.....mmeee"
Runtse idonta tayi jin kalmar daya kirata da ita,abinda bata taba zato ba a rayuwarta. Ita kanta Sumaimah tayi mamakin furucinnasa sosai.
"Shin bazaki amsa ba,wannan shine sunan danake ambaton mahaifiya ta dashi a cikin Addu'a ta,yanzu kuma tunda ga mai sunan a gabana shiyasa na ƙirayeki dashi,shin bazaki amsa ba?"
Kuka hajiyah Maryam ta rushe dashi.
"Bazan amsa ba bazan iyah ba,bai dace dani ba sam,nagaza nakasa,nayi zaton zan iya amma ashe ba haka bane"
"Ke kuwa kika kai ummeee,abinda kikayi ba kowacce uwace zata iya ba,ko a da dabana ganinki a matsayin mahaifiya ta,amma nasan keɗin jajirtacciyar mata ce. Nine na gaza na kasa,da har ban iya kallo soyayyata a idanunki ba,sai yanzu nagane da kinada niyyar cutata da tuni kin cutar dani ina yaro,saidai kullum ki dunga treating ɗina. Dan Allah ki juyo ki kalleni."
A hankali take juyo da kanta har suka haɗa ido,da alama bataso hakan ba,amma roqon da ɗannata yake yi mata abune da bazata iyah riqewa ba sam.
Kafeshi tayi da ido har sannan bata daina kuka ba,hannayenta takai kan kumatunsa,tamkar tasaka ƙaramin yaro a gabanta.
Shafah kumatunsa takeyi wanda rabonta data taba tun yana jinjiri.
"Ah...ahhmadd kayi haƙuri ka yafemin,shayarwa iyah na wata biyu kawai nayi maka,girman da yaro yake a gaban mahaifiyarsa duk baka samu ba, saboda wani yankyakykyen hukuncina".
Duk kasancewar sa namiji mai dauriya,amma ganinta a gabansa tana roqonsa sai ya tsinci kansa da kasa riqe kansa..
Rungumeta yayi kaman zai shige cikinta inda ya fito,wata soyayyarta ne ke shigarsa Tamkar an jonawa tanki bututun ruwa.
Sun daɗe a haka Sumaimah ta zuba musu ido. Hawayen idonta ta share,data tuna cewar itama bata san tata mahaifiyar ba,kuma tasan bazata taba ganinta ba,tunda ta koma ga mahaliccinta.
Jikinta ne ya shika,hakanne yasakashi ɗagota domin yaga menene,idonta a rufe tamkar bata numfashi..
Jijjiga ta yakeyi amma shuru,waigawa yayi inda Sumaimah take.
"Sumaimah ya zanyi bata motsi fah"
"Jinin jikinta ne ya ƙare,inaga muyi gaggawar kaita asibiti yanzu"
Tashi tayi shikuma ya ɗauketa irin bridal style ɗinnan suka fitah,tashin hankalin daya shiga ya dade baishiga irin sa ba.
A hanyar fita suka haɗu da Maimuna tana magana da Fatee wacce tafito daga motar Saleem sun dawo daga ɗakkota a makaranta.
Ganin Ahmad ɗauke da hajiyah Maryam kaman bata numfashi yasaka su sakin baki suna kallonsa.
Abu ɗayane yazo ransu shine wani abu ya aikata mata.
Saleem ne yasha gabansa cikin bacin rai.
"Yah Ahmad mai kayiwa mommy"
Kallonsa yakeyi da idanunsa wanda ya kaɗa yayi ja. Ya kasa bude bakinsa balle ya bashi amsa.
Ganin hakanne yasa Sumaimah shiga tsakiyar su tace.
"Babu abinda yayi mata dama bata da lafiyah,kaita asibiti zamuyi kubiyomu a baya,amma bayan Sameer kada ku faɗawa kowa mai yake faruwa a gidannan"
Maganar da Sumaimah tayi ne cikin alamar roqo yasaka Saleem matsawa Ahmad ya wuce da hajiyah Maryam a hannunsa.
A gidan baya ya ajiyeta inda Sumaimah tashiga,sai kuma shi ya shiga wajen driver.
Sai bayan sun fita daga gidan kafin su Maimuna suka bi bayansu.
Asibitin gidan marayunta suka nufah,amma a hanya saida suka ƙira babban likita tukunna,wanda suka yayi mata magani na ƙarshe.
Ɗakin karbar mutum na gaggawa aka shiga da itah suna isowa,daidai lokacin kuma su Maimuna suka iso,harda Sameer wanda sukayiwa bayani dama yana kusada wajen.
Babu wanda yake magana a cikinsu,amma kana ganinsu kasan suna buƙatar ƙarin bayani.
Likitanne yafito daga wajen cikin sauri.
"Am duk da jinin ta A+ ne bashida wuyar samun donor,amma kasancewar an daɗe ana bata jini dayawa,yanzu jikinta bazai ƙarba ba sai wanda DNA yayi ɗaya wato jininta"
Yana gama bayanin Sameer da Saleem sukabi bayan sa,Sumaimah tana ganin haka ta kalli Ahmad akan yaje.
"Kaje mana dan Allah,wataƙila sai naka yafi kamancece niya da nata"
Su Maimuna suna jin abinda take faɗa,amma basu fahimce ta ba..
Shiga yayi wajen ɗaukar jinin yabada sample ɗin nasa shima ya fito.
Suna nan tsaye bayan an karbi sample ɗin Sumaimah ta riqe kunkuminta,wani irin kamawa taji yayi mata.
Duk abinda take Ahmad yana kulada itah,cikin wani ɗaki ya shiga ya ɗauko kujera,wajen babu gun zama,yasan kuma in yace taje wajen zama bazata tafi ba.
A gabanta ya ajiye kujerar tareda kama hannayenta ya zaunar da itah.
Da mamaki take kallonsa,kenan yasan ta gaji,hakan yayi mata daɗi sosai,amma taji kunya ganin su Saleem suna kallonta.
"Yah Ahmad matar wani ce fah kake taba jikinta,yanzu kai......"
Wani kallo yayi mata dole ta haɗiye abinda yake bakinta.
Wata nurse ta fito da wata takarda a hannunta.
"Ana ƙiran Ahmad Aliyu,ka shigo wai naka yafi zama iri ɗaya da nata"
"Ohk"
Daga haka ta koma ciki.
Da Murmushi Sumaimah ta kalleshi wanda shima ita ɗin yake kallo.
"Kaga abinda nake faɗamaka koh?"
"Uhm nagani,barina shiga kada ki tashi ki tsaya,ki zauna yanzu zan fito. In kina jin kishirwa Saleem ya nemo miki wani abun uhm?"
"Uhm naji ka shiga Allah ya taimaka yavata lafiya"
Ahmad yana shigewa Fatee ta matso inda Sumaimah take.
"Ke bangane ba mai yake faruwane,shine zai bawa mommy jini a wanne dalilin,wani shirin kuke haɗawa saboda ku kasheta koh? Ke kuma mecece alaƙarki dashi kina matar wani,nake ganin kaman ta Allah ashe........."
"Ke Fatee miye kike hakane,meyasa duk abinda yazo zuciyarki shi kike faɗane. Mahaifiyarki na ciki batada lafiya amma kin gulma"
"To laifinta ka gani,ai dole ta tambaya,nima abin ya ɗauremin kai,miye tsakanin mommy da yah Ahmad da har zai bata jini,wai kuma kuda kuke ƴaƴan ta naku bayyi daidai ba sai nata?"
Maimuna ce tayi maganar cikin kasa gane mai yake faruwa.
Duk abinda sukeyi babu wanda Sumaimah tasaka baki,da abin yayi yawane ma tace musu waƙa a bakin mai ita tafi daɗi.
Bayan an gama jan jinin an ɗaura mata kafin aka barsu suka shiga.
Zuwa lokacin anyi mata allurar bacci.
Fatee ce a zaune a gefen kanta sai su Sameer a tsaye,Sumaimah kuma na gefe a zaune.
Can kaman an ɗan daɗe ta fara juya kanta kaɗan kaɗan.
Fatee da Maimuna ne suka ɗan ɗagota tareda saka mata pillow ganin tana ƙoƙarin tashi.
Idonta akan Ahmad ya sauqa wanda shima ita ɗin yake kallo cikeda soyayya irin ta ɗa da mahaifi.
Sannu sannu su Sameer suka mata,fatee kam rungumeta tayi tana kuka.
"Mommy bakida har haka amma baki faɗamin ba har kwanciya fah kikayi"
"Kin damu ki sani ne,miye ya dameki banda kanki uhm"
Hajiyah Maryam tafaɗa tana dafa kanta..
"Habadai mommy you know i love you"
"Umm naji i love you too,yanxu dai ɗagani bake kaɗai bace a ɗakin koh?"
Ƙin matsawa tayi saida ta tureta tukunna,sai turo baki take kaman zai faɗi.
"Sannu Ummee jikinnaki yanzu"
Ahmad yafaɗa a nutse cikin kulawa.
Murmushi tayi tareda ɗaga masa kai.
"Ummee ya jikin?"
"Alhamdulillah Sumaimah....kinci abinci kuwa?"
"Ahah"
"Tabb Ahmad ka ɗauketa ku tafi gida taci abinci,batayin awa uku ma bataci ba,cikin jikinta mai neman abincine"
"Ahah yau banajin yunwar zan zauna har a sallameki saimu tafi"
Cikeda rigima tayi maganar,wanda hakan yasaka hajiyah Maryam haɗa rai.
"Ahah ku tafi nima yanzu zan tafi idan jininnan yaƙare,uhm yau kuma a wanne bawan Allah aka ɗauka?"
"Mommy yah Ahmad ne yabayar,yaushe kuka shirya dashi da har yabaki jini kuma ya kawoki asibiti,ga waccar mai aikin sai wani kula kike da ita kamar wata mai muhimmanci"
"Buge bakin Fatee hajiyah Maryam tayi tareda cewa.
"Ƙaniyarki da ce mata ƴar aiki,tunda har kunga ya haka yakamata kusan mai yake faruwa.
Ahmad ɗanane na fari kafin na haifi Maimuna,sannan ita kuma matarsa ce wacce ya aureta a lokacin da yayi shekara biyar baya nan. Tanada ɗa mai sunan mahaifin Ahmad kuma yayan babanku wato Muhammad,ana ƙiransa da Sayyid.. (Ta faɗa tana kallon Sumaimah. Wannan suma itan suka kalla cikeda mamaki)
Wannan shine abinda baku sani ba,sauran boyayyun labaran kuma sai daga baya. Sannan wannan maganar banaso tabar wajennan,akwai wanda sanin
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18 Chapter 19Chapter 20Chapter 21