shi mana tunda shima jinjiri ne koh"
"Ehh to hakane,ɗazu da aka shige dake inna tayi ta kuka hhjhhhh dama ashe haka take kuka,waiwai gotal kenan"
Fashewa tayi da dariya tana nuna inna da yatsa,wanda hakan yasa ta kaimata duka tayi waje da gudu.
Dariya mukayi nida innan,wai hakan ma da sauƙi tunda bata dukan yara a makaranta sosai,kuma wata shekarar nakeson sakata a JSS one,tunda nayi magana sunce zasu karbeta indai zata iya karatun. Ban faɗawa inna ba har yanzu,amma kuma kafin na haihunnan nafara koyamata karatun secondry ɗin.
"Allah ka shirya khadija"
"Ameen fah,ai wannnan yarinya sai gyaran Allah"
Inna ta faɗa.
"Uhm inna shin wanne suna za'a saka masa ne?"
Saida nayi maganar ne na tuno ashe bamma san sunan goje ba na ainihi,wannan shi ake ƙira gallo.
A zabure na kalli inna tareda yimata tambayar..
"Tabb inna wai menene sunan gojene na ainihi,koda gaskene sanda aka sameshi babu wanda yasan komai nasa?"
"Uhhh Sumaimah na faɗamiki ki daina wannan zancen,kawo yaronnan nan kigani"
Jin abinda ta faɗa yasa na ɗora mata dan akan cinyarta,cikeda kulawa da ƙauna take kallonsa har ta ɗora bakinta a kunnensa,ta ɗan dau lokaci kafin ta juyo ta kalleni.
"Nayi masa suna da Muhammad. Wato yazama Muhammad Ahmad Hamma kenan"
"Hakane sunan goje na ainihi,Allah ya rayashi,to amma taya kika san laƙaninsa?"
Nafaɗa cikeda mamaki,dan ina cikin duhu diɗim da lamarin rayuwar uban ɗannawa.
"Kinyi min alƙawarin bazaki ɗaga wannan zancen ba sai bayan kin haifi abin cikinki kuma kin gama makaranta,dan haka dan Allah ki bar zancennan ba yanzu ba."
Ba hakan naso ba amma nariga na yarda da hakan tun watannin da suka wuce,Inshaallah zan jira wannan lokacin har yazo.
"Amma zan iya ɗan sakaya masa sunan kaman nace Sayyid"
"Hakan ba matsala Allah ya rayashi bisa imani"
Ahmad na maimaita a raina,suna mai daɗi amma ake ƙiransa da wani goje.

A ranar aka sallamemu muka tafi gida,kasancewar na farfaɗo kuma babu wata matsala.
Tunda mukaje asibitin ammi ce kawai taje,shima ina kwance bansan taje ba.
Ranar daza'ayi dakan yaji dama ban saka a raina za'ayimin komai daga gidan mu ba. Inna ce ta yankamin kaji guda biyu wanda take kiwo a can ƙyauyensu.
Abin suna kuwa dama tun cikina yana ƙarami ta siya ta ajiye a garinnasu,ana gobe suna aka kawoshi,ragone amma ba babba sosai ba,saidai kuma baza'a ce masa ɗan ƙarami ba.
A zaune nake ranar sunan da safe ina bawa sayyid abincinsa,hankalina gabadaya ya karkata kansa,maganar Shareefah naji tamkar a sama,yaushe ta dawo na faɗa a raina,don ita a boarding take makaranta.
"Mashaallah ƙawata da beautiful baby,sauƙata kenan a garin naji wannan labarin."
Murmushi nayi cikeda jin daɗin ganinta.
Gaisawa mukayi na yaushe gamo,miƙa mata yaron nayi sai tubarakallah take cewa,ba yabon kai ba kam kowa yaga yaronnawa sai ya faɗa,kyakykyawa dashi gashi ba rama a jikinsa.
Nima kuma lafiyata ƙalau,iya kula muna samu a wajen inna sosai,dan ranar sunan ma lace ta ɗinkamin ja mai kyau.
Lokacin dana ga abubuwan da tayi mana har kuka saida nayi,domin abun ya bani mamaki sosai,abinda inna takeyimin ko mahaifiya ta iyakaci.
Anyi daɗi anyi ba daɗi dukka a taron sunan,har aka watse kowa yakama gabansa,aka barni dagamu sai halinmu.
Washagari da safe hayaniyar a da ake a cikin gidanne ta tasheni,dan yanzu na dawo ɗakin inna kafin nayi arba'in.
Muryar inna ce da kuma gaji suna sa'insa.
Wai gaji ce ta tashi da sassafe ta ɗauko wuƙa zata fara aikin naman suna,ita kuma inna tace bata yadda ba. Duk aikin da akayi a gidan babu wanda ta taya sai wannan.
"Amma dai gaji bakida kunya,tunda muka dawo daga asibiti ƙafata tana ciwo,amma baki tayani da komai ba na aiki sai yanzu,dayake nama ne zaki fito sassafe kifara gyarawa"
"Ohh kura kika maidani komai,kina nufin kice saboda namane shiyasa nazo nake tayaki?"
"Ahh to da ba haka bane,kinyi wani aikinne bayanshi,dan haka ki barshi zamu gyarashi nida Deejah,tunda na da bai kashemu ba na yanzu ma bazai kashemu ba da ikon Allah"
"To shikenan dama ba'ayi muku gwaninta,saikuje kuyi kayanku gayyar tsiya arna a idi,uban ɗan ma ya gudu ya barku ai ballantana wani"
Ni dariyama abin ya bani danaji maganganunnasu,narasa meyasa gaji bata jin kunyar yin wani abun.
Gidannamu kenan ko yaushe wasu abubuwan zasu zama tarihi oho,ji nake a jikina kaman wasan yanzu ma aka fara.



SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.



*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)


Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150

Bismillahir-rahmanir-raheem


Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah 🙏🏼 ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.



Ina ƴan mata dakuma Matan aure masu muradin burge mazajensu da ɗinkuna zuƙa zuƙa. *PHEEDY TOILORING DESIGN* ,suna gabatar muku da ɗinkuna kala kala wanda sukayi daidai da zamani.
Zaku samemu a kan wannan layin waya kamar haka


09167130115
Wato a manhajar whatsapp. Domin ganin kalolin samufurin aikinmu kuma ku tuntubemu a INSTAGRAM da kuma TIKTOK a @pheedyxacks_ragtrade

Muna maraba daku a kowanne lokaci🙏🏼🙏🏼🙏🏼🙏🏼🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻





*BOOK 2*
...5...


*Bayan Shekara da watanni*......


"Ke maza kiyi abu da jiki,menene haka kaman bakida laka a jikinki,idan har ya iso baku gama komai ba sainayi mungun saba muku"
Cikeda masifa Mulaifah take magana,gabaɗaya duk ta fita daga hayyacinta,bayan wannan tsawon lokacin yaune Ahmad ya yanke shawarar dawowa gidan,dama Abbansune ya damu akan ya zauna jikinsa ya dawo yanda yake.
Kawai dai yana can ɗinne,amma plan ɗinsa gabaɗaya babu wanda ya tsayar dashi,komai yana tafiya normal a tsaikaninnasu shiga abokan aikinnasa,wato Eemran da Neelah.
Yanzu ma buƙatar dawowarsa office ce ta taso shiyasa zai dawo gidan.
Hajiyah Maryam wacce ke zaune a falonta ko gezau batayi ba,tunda AM Aliyu yace mata Ahmad zai dawo daga to bata sake tari ba.
Iya Maimuna ce da Saleem kawai suke murna,saikuma murnar Fatee wanda dan taga yanda abin zai ƙare shiyasa takeso ya dawoɗin. Sameer kuwa an turashi can wajen gyembu wani aiki (Zasuyi bincike akan ƙungiyar BB ta bombi dake cikin dajin)😁😁😁.(uhm mutanen littafin BAƘAR AYAH) munayi musu fatan NASARA littafin na Maman Abdoul. Allah ya bar ƙauna...........

Mammah wacce ta fito daga sashenta zuwa babban sashen gidan,jijjiga kai tayi ganin yanda Mulaifah tun safe ta gagara zaunawa,ta haɗa abincin da ko mutane goma bazasu iya cinyewa ba,duk wai akan mutum ɗaya.
Kowa tausayinta yakeji,yayinda wasu kuma irin Fatee mamaki take basu.
Daidai misalin ƙarfe 1:30 na ranar asabar ɗin jirgin nasu ya sauƙa wanda ya taho daga Egypt ɗin.
Shine mutum na uku daya saƙƙo a jirgin,suit ne a jikinsa baƙaƙe,wanda suka dace da fatar jikinsa wacce tasha hutu mai aji. Ahh dole kam Sadeeq da Abba suce yayi baƙi farkon ganinsa da sukayi,danni ma yanzu na yarda da zancennasu.
Jakace briefcase a hannunsa ba wata babba ba,saikuma ɗaya hannun yana riƙe da trolly mai matsaikacin girma.
Fuskarsa babu murmushi kana kuma babu akasinsa,a takaice dai bazakace ga abinda yake saƙawa ba aransa.
Cikeda taƙama yake tafiyar kana ganinsa kasan babu wasa.
Tun daga nesa ya hango drivernsa na da wanda yake masa aiki,da saurayine amma yanzu ya ƙara girma.
Lallai an ɗau shekaru kam,yafada a ransa.
Yana ƙarisowa ya miƙa masa jakarsa tareda bude bayan motar ya shiga.
Jingunuwa yayi a jikin kujerar tareda sauƙe ajiyar zuciya,ba ƙaramin gajiya yayi ba,tun safe bayyi wani ƙwaƙwƙwaran zama ba,saboda ciku cikun dawowar tasa.
Yayi tunanin ma zaiga su Mulaifah sunzo daukarsa,da alama basu manta yanda ya tsani yaga ana tara masa jama'a ba.
"Ya kke umaru ya bayan lokaci"
"Ahh ogah ka ganeni ne?"
"Ohh meka maidani,saboda bana nan na tsawon wasu shekaru sai akacemuku na rasa hankalina? Bama wannan ba wanne aiki kake bayan bana nan?"
"Uhm ai ogah ina fadamaka bayan tafiyarka da wata shida nayi aure,ga aka koreni daga aiki,na tuka wata kantar ɗiban itace haka haka dai rayuwar ta dunga garamin,kwatsam ina zaune sai Neelah tacemin wai kana nemana na dawo aiki. Jinayi tamkar a mafarki. Nagode nagode ogah"
Da ɗan kukansa ya ƙarisa maganar,a haka har suka isa gidan suna taba hira jefi jefi.
Mulaifah tanajin shigowar motarsa gidan ta fito da gudu,dan dama tun ɗazu take leƙawa,yana fitowa daga motar yaga Fatee a gabansa,a ransa yace yaushe wannan kuma tafara murnar ganina.
"Ke kuma fah?"
"Ohh yah Ahmad murnar dawowarka nake mana,zamu sha kallon shagali a gidannan"
Kafeta yayi da ido kafin ya tureta ya wuce,yana kawar da itah yaga Mulaifah tana tsaye ta haɗe fuska,dariyar Fatee ya jiyo a bayansa,sai a sannan ya gane ashe bawai murnar dawowar tasa bace,tsokanar Mulaifah take. Tun sanda ya santa lokacin tana ƙarama haka take da rigima,ashe girman ma bai saka ta daina ba.
Tahowa yayi zai wuce ta gefenta,tayi saurin tarar sa tareda narke fuska.
"Hubby ya zaka wuce,baka ganni bane,tun ɗazu nake jiran dawowarka fah"
Gaba yayi abinsa tana binsa tana surutu har suka shiga gidan..
Akan dinning ɗin da aka cika da abinci idonsa ya sauƙa,wanda yasan bazai wuce aikin Mulaifah ba,ko cewa yace mata a tsawon lokacinnan babu abinda ya koya sai cin abinci oho.
"Hubby ka tsaya kaci abinci mana"
Ganin yayi hanyar sashensa wanda sai anbi ta wani corridor a isa wajen,domin yana can ƙarshen gidan.
"Hubby ko nazo na tayaka shiryawa naga ka gaji sosai"
Tsayawa yayi tareda wurga mata wani kallo,ganin da gaske take dan sakarci binnasa zata yi,wani kallon ma amsa ce,bata san lokacin data yi burki ba.
Fatee kuwa mai take jira ta tuntsire da dariyah.
Muryar Mammah sukaji a bayansu tana magana.
"Naji ana cewa mai sunan manya ya dawo,ina yayi ne banga ya shigomin ba?"
"Mammah ya wuce sashensa,kaff a gidan ma babu wanda ya kula,har wacce tayi ta hidima har asubar ma bata samu kallon arziƙi ba"
Jimm Mammah tayi tareda cewa.
"Ƙalau yake dai koh,inaga ya gaji ne shiyasa"
Daga haka ta juya sashennata,sauƙe ajiyar zuciya Maimuna tayi tareda cewa.
"Gaskiya yah Ahmad baya kyautawa da irin wannan halinnasa,yana nan dai wato bai sanja ba sam"
Daga haka itama tabar wajen ranta cikeda haushin yayannata.
Banda mutuniyar ita ko a jikinta,yanzu ma zata sake zage dantse wajen ganin ta mallakeshi.
Hannu ya saka a kunkuminsa yana kallon falonnasa,babu komai a ciki sai fararen kujeru da Tv stand sai cerpet a tsakiya.
Ɗakuna biyune a side ɗin kowanne da banɗakinsa sai kitchen.
Ɗakin farkon ya buɗe ya shiga wanda dama shine nasa tun kafin ya tafi..
Shima kaman yanda yake a da hakan yake,kai tsaye banɗaki ya fada ya watso ruwa tareda ɗauro alwala.
Bayan ya idar da sallah yana tun kafin yagama Addu'o'i yaji wayarsa tayi ƙara.
Miƙa hannu yayi ya ɗauka,sunan Eemran ya gani,hakanne yasa ya ɗauka da sauri.
"Hello sir barka da isowa"
"Yawwa naga ƙiranka,shi kun samu wani abinne?"
"Ehh yanzu Neelah ta ƙirani wai ta samo wani underground a nan garin,kuma bashi da nisa da gidan ajiyar muhimman abubuwa na ƙasa,da alama dashi akayi amfani wajen satar da akayi shekara biyu da suka wuce"
"Shikenan gani nan zuwa yanzunnan"
Da sauri ya tashi kaman an tsikareshi ya fita daga ɗakin.
Mulaifah wacce take zaune a wajen dinning sai jin motar sa tayi ya fita daga gidan,da alama taƙofar baya ya fita da take sashensa.
Address ɗin da Neelah ta turo masa ya bi,nan da nan ya isa wajen.
Daga waje mutum zai ɗauka cewar gareji ne a wajen,sai ya shiga yaga ƙofa a wajen wacce zata kai mutum zuwa gidan ƙasan.
Tafiya yake yana nazartar ginin wajen,mutum yana gani ma yasan akwai hannun wani babba akan aikinnan,inba haka ba taya barayi zasu samu damar yin wannan gidan.
Ba wannan ne ya girgizashi ba saida yayi arba da harabar cikin wajen,yaushe aka gidannan wajen toh. Yayiwa kansa wannan tambayar.
Eemran ne da Neelah suke jajjagawa suna kallon abubuwan.
Neelah ce tafara ganin shigowar Ahmad da sauri taƙame tareda sara masa,jin haka yasa shima Eemran ya juyo yayi yanda tayi.
"Sannun ku da aiki,amma Neelah ya akayi kika san wanann wajen,bayan duk binciken da muke babu wani clue daya kawomu nan wajen?"
"Uhm jiyane nashiga napep cikin badda kama,anan yake cemin ya taba ganin wani jirgin sama ya sauƙa a filin waje shekara biyu baya da daddare,Sannan wasu mutane da baƙaƙe kaya sun fito daga ciki sun shigo garejin,hakan yasa nace ya kawoni wajen. Da nayi bincike saina na gano ashe gidan sirrine"
A dake take bada labarin babu gargada,wanda hakan yasa Ahmad jinjina mata,duk da cewar bai daɗe yana aiki ba hatsarin ya sameshi amma yasan itaɗin jajirtacciya ce,wanda ya gwada ta hanyoyi da dama tana tsallakewa,shiyasa ya yarda da ita sosai.
Ɗakunan cikin wajen suka fara duddubawa,anan har suka shigo ɗakin da goje ya zauna.
Wani dumm Ahmad yaji kansa yayi masa,tunda ya shigo gidan yakejin haka,wande Neelah tana kulada shi amma banda Eemran wanda yake ta rubuce rubuce.
"Yallabai lafiya dai naga kaman kana riƙe kai"
"Cikeda kulawa tayi magana,duk da a cikin yanayin aiki tayi tambayar"
"Ahhh bakomai kawai inajin wani yanayine gameda nan wajen,bansan meyasa ba"
A haka dai suka gama dube dubensu kafin suka sanarda headquarter abinda yake faruwa.


___∆∆∆___

Tafiya nake ina sauri na isa gida,dan nasan Sayyid Yana can ya damu inna da rigima, dan ma nasan Deejah ta dawo daga makaranta yanzu.
Ina shawowa kwanar gidannamu naga mutane a ƙofar gidan sunyi zanga zanga,gaba nane ya buga,don a zatona ko mutuwa akayi,saida nazo kusa kafinnaji mai suke cewa.
"Wlh bazamu yarda ba,dolene sai an biyamu kaff asarar da goje ya jawo mana a garinnan,inba haka ba mu koreku daga garinnan"
Hasbunallahu wa ni'imal wakil,yaukuma? Meya taso wannan maganar bayan shekara biyu,wato tunda tsoro suke kar suje ya dawo,yanzu kuma da sukaga an dau lokaci sunsan bazai dawo ba shiyasa zasu tona mana asiri.
Wasu hawayene suka zubomin,shin da wanne mutum zaiji,da rashinsa kokuma da tashin hankalin su.
Kaman bazan ƙarisa ba saboda tsoro da fargaba da suka kamani,amma kuma ina zan gudu naje na bar ɗana gudan jinina,da dattijuwar dana ɗauka tamkar uwata,ko kuma yarinyar dana ɗauka tamkar ƙanwata ta jini?
Hakan yasa nayi shahada na nufi bakin gidan,suna ganina kuwa suka yo kaina kaman nice naci musu kuɗin.
Wasu kamma dan cin mutunci harda jan hijabi,wani baƙin cikine ya isheni,ina juyawa naga wani saurayi ne,ana hayaniya shikuma sai ƙoƙari yake yaga ciremin hijabina,haushine da takaici ya ɗebeni bansan lokacin dana wanka masa mari ba. Faruwar hakanne tasa wajen yayi tsit kaman ruwa ya cinyesu,kowa kallonmu yakeyi a wajen,yayinda shima ya kafamin ido hannunsa riƙeda kumatunsa,da alama yayi mamakin marin danayi masan.
"Bin bashin haukane da kake shirin yimin tsirara a cikin bainar jama'a,ko kuma a gidanku ba'a koyamaka mutunta mata ba musamman matan aure?. Kunzo ƙofar gidan mutane kaman zaku shiga,a bayaninku naji kuna cewa kun yashe shagon da muka buɗe muna ciyar da kanmu. Ina tun ƙahonku goje yayi muku barna,shin labari aka baku mun boyeshi tsawom wannan lokacin,ko ba manya da masu faɗa a ji da kuke mana tujara haka?
Kunata zaginsa cewar ya yimuku ba daidai ba,ai gwanda shima ba a taba cewa yaje ya cutarta marasa ƙarfi ba,kokuma cin mutuncin matar wani ba,amma kufah ku kalli abinda kukeyi mana?.
Duk abinda kuke cewa yacimuku ina a wajen caca ne kokuma in kunshiga harkasa yayi muku,shin to ku faɗamin nina ce me,ban taba yin magana dashi ba sai sanda aka kawoni gidansa,idan ku kuɗinku yaci ni ga nawa iyayen ɗiya ya ɗaukemusu,amma bance komai ba banje wajen wani na roƙeshiba,na tsaya da ƙarfina muna rufawa kanmu asiri kunzo kun wargaza komai"
Kuka ne ya kufcemin na kunci da halin ha'ula'i da suka taru sukayimin waya,yanzu dawowa ta mungama da makaranta kenan akan bazasu bani cartificate ba saina kai dubu hamsin, ina tunanin yanda zanyi kuma ga wannan.
Muna cikin haka inna tafito daga gidan kanta da mayafi ta jani ciki,banda kuka babu abinda mukeyi,abinka da daman cikin ya haɗiya da yawa.


SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.



*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)


Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150

Bismillahir-rahmanir-raheem


Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah 🙏🏼 ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.



Ina ƴan mata dakuma Matan aure masu muradin burge mazajensu da ɗinkuna zuƙa zuƙa. *PHEEDY TOILORING DESIGN* ,suna gabatar muku da ɗinkuna kala kala wanda sukayi daidai da zamani.
Zaku samemu a kan wannan layin waya kamar haka


09167130115
Wato a manhajar whatsapp. Domin ganin kalolin samufurin aikinmu kuma ku tuntubemu a INSTAGRAM da kuma TIKTOK a @pheedyxacks_ragtrade

Muna maraba daku a kowanne lokaci🙏🏼🙏🏼🙏🏼🙏🏼🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻





*BOOK 2*
...6...



"Sumaimah me kikeyi a waje haka,dan kare yana haushi saika biyeshi kayi,ko kin manta da matsayinki ne"
Kuka na rushe dashi tareda tsugunnawa,dan bansan mai zance mata ba,abin ya tarumin sosai.
Tsayawa tayi da faɗan tana rarrashina,saida nayi mai isata kafin na kula da Sayyid wanda yake hannun Deejah yana kuka. Karbarsa nayi na fara bashi abincinsa,da ni naƙi cin nawa ba kamata shi na hanashi ba.
Sai bayan nagama bashi har yayi bacci kafin na tashi nayi alwala.
"Ya takardar gamawar kin ƙarbo ina?"
Jijjiga kai nayi bansan taya zan fara yimata bayani bama,domin maganar akwai nauyi..
"Inna basu bani ba,sunce wai saina bada dubu hamsin tukunna,wai shine kudin da suke bina bashi"
"Bashi bashi kaman yaya,naga yabiyasu kuɗin komai harki gama?"
"Uhm sun sani,kawai yanzu ne suka kawo maganar,ina dawowa kuma na haɗu da waɗancan suma"
"Hmmm ƙaddarace in muka jure watarana sai labari,bari komai ya lafa saimu samu abinda zamuyi"
"Inna inason tafiyah babban birni yin aikatau,naji ina kayi dace da gidan masu hannu da shuni ana samun kuɗi sosai"
Zaro ido inna tayi tana kallona,da alama tayi mamakin furucina.
"A ina kikaji wannan zancen haka?"
"A makarantar islamiyya ne wata take faɗa,wai yanzu hakama wai suna shirin tafiya a satinnan,magana tayimin akan ko zan tura Deejah,tunda yara ake turawa,shine nace mata zan duba nagani"
"To mai yasa kikace ke zakije?"
"Inna bazan iya tura Deejah ba,har yanzu bata mallaki hankalinta ba,ina gudun wani abun ya sameta,sannan bayan hakan nasaka a raina zan sakata tayi karatu kaman yanda yah Musbahu ya sakani. Na yanke shawarar zuwa aikin,idan da rabo goje ya dawo sai ku faɗamasa inda nake. Idan na turo kuɗin aikin inna ku dunga amfani dashi,harda kudin makarantar deejan"
"Naji abinda kikace Sumaimah,irin wannan kyakykyawar niyya da Allah yabaki Allah yabaki mai yi miki,yasa komai ya wuce sao tarihi,dama akwai wani bayani danace miki zanmiki,ita tunanin yanda zan farashi,amma tunda kinkawo wannan zancen a ranki ta kwana gidan sauƙi.
Nayi aiki a garin abuja tsawon shekara talatin,dan haka babu abinda bansani ba gameda aikin,bama saikin bi waɗancan ba akwai adireshin gidan da zan baki,indai kikace nina turoki to za'a vaki aiki,kuma a biyaki mai tsoka"
Daɗi ne yakamani jin furucin innan,duk da zuciyata nasan yimata tambayoyi amma haka nayi shuru.
Tashi tayi ta nufi ƙarƙashin gadonta,da alama wani abun take nema..
Ban ankaraba naji mutum a jikina,ashe Deejah wacce take tsaye tana jin abinda muke faɗa.
"Nagode anty Sumaimah da karamcinki gareni,bazan taba manta yanda kowa ya gujeni amma keda yah Musbahu kuka taimakamin,gashi a
Showing 6001 words to 9000 words out of 62659 words