yasamu wannan nasarar.
Yana cikin wasiwasinne Eemran ya shigo office ɗin.
"Eemran kayimin arrenging na zuwa hutu gobe"
"Ogah anya kuwa hakan zayyi wu,don an fitar da aiki daga headquater,kuma naga hadda kai a cikin wanda zayyi supervising"
"Supervising ɗin me"
"Uhmm a cikin trainee ɗin aka dauka masu ƙwaxo zaku tafi dasu Russia na tsawon wata Uku"
Komawa jikin kujerar Ahmad yayi tareda sakin dogon numfashi.
"Yaushene tafiyar?"
"Gobene ogah"
"Ohk"
Abin yabawa Eemran mamaki,yayi tunanin zaice bazai jeba,amma saiyaji sabanin haka,kenan so yake yabar garin kota wacce hanya.
Washagari bayan an gama tsara zaman sojojin a jirgi sun tafi kafin manyan suka bisu a private jet,duk cikinsu Ahmad ne kaɗai ƙarami.
Lokacin dazai taho ko ƴan gidan bai fadamusu zai tafi ba,iya Neelah ce kawai tasani sai Saleem.
Masauƙinsa aka kaimasa kayansa, bayan ya watsa ruwa yasaka riga marar nauyi ta shan iska.
Fitowa yayi wajen cin abinci,amma shi a hadene da sauran ƙananan sojoji.
Bayan ya zauna an saka masa abinci,har zai fara cin abinci yaga wani yazo ya zauna a opposite ɗinsa,mamaki abin yabashi,dan yasandai baizo dasu Eemran ba bare su zauna.
Ɗagowa yayi suka haɗa ido da wani matashi,zaiyyi shi a haife,kallon rashin sani yake masa,amma kuma sai yaji kamar ya taba ganinsa. Shima kallonsa yake ko ƙiftawa bayayi,sai can kafin yace.
"Goje mai kakeyi a nan,bayan batanka kaima soja ka shiga,amma meyasa baka faɗi inda kake ba,kasan kuwa halin da Sumaimah tashiga a sanadiyyar rashinka?"
Maganar da bawan Allahn yayine ta dakeshi da ƙarfi,zaro ido yayi tareda ajiye cokalin yana kallonsa.





SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.



*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)


Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150

Bismillahir-rahmanir-raheem


Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.


*BOOK 2*
...28...




Number dakinsa kawai yabashi tareda yimasa alamar ya sameshi a can ɗin,
Yagane mai yake nufi kuwa,sai yayi shuru da zancen akan zai sameshi a ɗakin.
A zaune yake da labtop akan cinyarsa lokacin da musbahu yayi sallama a ɗakin,bayan ya zauna shuru sukayi babu wanda yace komai,saida suka ɗan ja kaman mutuna kafin Ahmad yayi masa magana.
"Naji kana magana akan goje,ga dukkan alamu kasanni lokacin ina a matsayinsa,kuma kasan inda na zauna"
Kallom mamaki Musbahu yabi Ahmad dashi kafin yace.
"Ya kake magana kaman ba kaine goje ba,shin mai yake faruwane,ka rasa hankalin ka ne a hatsarin dakayi,shiyasa ka manta komai,amma bakayimin kamada wanda ya rasa hankalin sa ba"
"Eh ba hankalina na rasa ba,nayi recovaring hankalina ne,saikuma na manta rayuwar danayi a wanda kake faɗa. Kafin muce komai zanso nasan wanene kai kuma menene alaƙata dakai a rayuwar bayan.
Sunana Ahmad Aliyu,General under Investigation division"
Zaro ido Musbahu yayi jin matsayin da Ahmad ya faɗa.
"Shin mafarki nake kokuma idan har kaine goje yaushene kayi karatu haka,a sanina dai dabanci kakeyi da kuma aiki ma ƴan siyasa. Sannan kana nufin baka ganeni bane,nine fah Musbahu yayan Sumaimah matarka,duk da bakaje wajen ɗaurin aurenba amma ai muna haɗuwa a gari san......."
"Bangane wanne labari kake min ba,kaine yayan matata,kuma banje wajen ɗaurin aure ba,meyasa toh? Barina baka labarin abinda yasa bansan kokai wayeba,sannan inaso ka bani labarin abinda yafaru daga farkon rayuwata a wannan gojen dakake faɗa har ƙarshe,harma da labarin ita matar tawa."

Bayan yabashi labarin abinda yasameshi ya rasa hankalin sa har yayi rayuwa a matsayin goje,ba ƙaramin mamaki yabawa Musbahu ba. Shima labarin rayuwarsa daya sani a matsayin goje ya faɗamasa,da yanayin aurensa da kuma yanda Sumaimah tasha wahalar zaman aurensa harda tafiyar dayayi ya barta.
Abin ba ƙaramin tayarwa Ahmad hankali yayi ba sosai,shin dama haka yake a rayuwar,a ina zai samo wannan baiwar Allah,mai zaice da ita irin wannan abun daya jawo mata.
Kama kai yayi tareda jan numfashi,tsawon lokaci ya ɗauka yana jimamin abinda ya aikata.
"Zan shirya komawa gida gobe,zamu tafi ka nuna min itah"
"Ahah hakan bazai yiyu ba general,duk da nasan kai ogah ne,amma inna bika zan samu matsala a nawa training,nayi ƙoƙari sosai kafin na samu wannan matsayin.
Sannan kuma ita kanta wacce kake son zuwa wajenta bata nan,ta tafi garin abuja aikatau,saboda bayan tafiyarka hatta makarantar daka biyamata kuɗinta had ta gama sun hanata certificate,duk wani abu mutane sun washe ganin an ɗau shekara baka dawo ba,shiyasa ta tafi neman abinda zata rufamusu asiri"
Wani irin sanyin jikin Ahmad ya sake jin wannan batun,gabaɗaya ya rasa mai yake masadaɗi.
Wunin ranar gabaɗaya ƙareshi sukayi Musbahu yana yimasa labarin goje,batun zuwa wajen Sumaimah kuwa sun barshi akan suna komawa zasu nemi inda take yaje.



∆∆∆∆


Sumaimah {POV}

Bayan wata biyu.....

Yau tun safe na tashi da tashin zuciya,abu kaɗan sai naji zanyi amai,da sabuluna nafarayi a banɗaki.
Bayan rana tayi har sannan ban saka komai a cikina ba,saboda banajin son komai.
A zaune muke nida ummi bayan mun gama aikin ranar,inata magana niban kulaba ashe kallona takeyi,ɗaga mata gira nayi da alamar lafiya.
"Lafiya kalau,kawai naga kin sauyaminne kwanannan,duk da ke farace amma ƙin ƙara fari,ga wayan bacci dakikeyi,komai inkin fara saikice kin gaji"
Maganganun da ummi tayi dukka nima na kulada su,amma babban abin tashin hankalin shine abinda na zarga,wanda ban kawo shiba sai yanzun.
Wani zabura nayi nai banɗakinmu da sauri,a gaban madubi na tsaya ina kallon kaina,mamana na kalla wanda naga sun ƙara girma,rabonsu da haka tun inada cikin Sayyid.
Zaro ido nayi tareda shafa cikina,rabona da al'ada wata biyu kenan,wayyo mai nake tunda ban kulaba sai yanzu.
"Innalillahi yanzu ya zanyi kenan,kenan ciki na samu a ranar? Mai yasa dukka biyun suka faru a rashin saninsa,nasan wannan zaisan nasane,amma da wanne zai kalleshi shine tashin hankalina,ahhhhh"
Ƙarar danasaka ne yasa ummi yin magana daga cikin daki.
"Sumaimah lafiyarki kuwa?"
"Ba komai ummi"
Fitowa nayi daga bnaɗakin ina rarraba ido,yanzu wazan tunkara da wannan zancen kenan,nasan hatsarin danake ciki nida wannan cikin Allah ne yasan iyakarsa. Don yanzu su hajiyah Mammah babban burinsu shine gano ni wacece,tunda yanzu babu komai ya ruguje. A bangaren hajiyah Maryam kuwa kullum ƙara rauni takeyi,Neelah kuwa batada lokacin kanta tunda Ahmad ya tafi ya barmata ragamar hidimominsa.
Hanyar sashennasa na nufah,haka kawai na tsinci kaina dayin hakan.
Buɗewa nayi na shiga,alamun rashin mutum duk sun nuna a wajen,har ƙura ta taru a falon.
Ina shiga naji wani ƙamshi a falon,wannan wanne turarene haka dayaƙi washewa tsawon wata biyu.
Ɗakin na bude na shiga,nan kamma har yafi falon,dan ji nayi wata nutsuwa tana sauƙamin.
Duddubawa nakeyi ina neman turaren,saida na shinshina dukka turarensa amma ban jishi a ciki ba.
Wardrobe ɗinsa na buɗe,inda ya lanƙaya kayan daya saka a gefe,a jikinsu turaren yafi yawa,ɗakkosu nayi ina shinshinawa,na daɗe ina abu ɗaya,sai daga baya nagane ina abu tamkar kuliyah. Kuma mai wai tsaya,kenan ba turare hancina yake shinshinowa ba,guminsa ne,yaushe na zama mai iya shinshino yanda gumin mutum yake?.
Ajiye sauran kayan nayi na ɗauki riga ɗaya na boye,kan gadonsa na faɗa,ahhh nan ma jinayi kamar yana kai. Nice nake kewarsa kokuma ɗan cikina duk bai shafen ba,tunda naji daɗin kwanciyar bacci zanyi kawai.
Bacci nayi na ƙoshi sai don kaina natashi,amma duk da haka banji ya wani isheni ba,mitstsike ido nayi,sai sannan na hango gari ta window yafara duhu.
What bacci nayi na kusan tsawon awa shida ko biyar.
Banɗakin sa na faɗa da sauri nayi alwala,mayafin kaina na yaye nayi sallah kafin na fito zuwa kitchen ɗinsa ko zan samu abinda zai iya shiga cikina.
Tundaga lokacin dana gano inada ciki,sai yazama kamar hurashi akeyi,tsorona ɗaya nasan zayyimin girma fiyeda na sayyid,dan daga ganinsa ma.
Nashiga damuwa sosai da lamarin,ga banida waya ta faɗi a ruwa bare na ƙira inna na faɗa mata.
Kullum inna tashi da safe sainayi shiri mai kyau,gashi na tsiri saka hijabi da kuma ɗaurin zani akan cikin. Sati uku da fara laulayin har na rame na yi fayau.
Fitowa nayi daga wanka kware kwaren danayi,to wankane babu sabulu,towel ne a jikina ina gogewa ruwan,kullum a banɗaki nake shiryawa,amma yau dayake naji su ummi suna aiki a babban falo shiyasa ban yi a banɗakin ba.
Motsin tafiya naji,hakan yaa na rarumi hijabina na saka.
"Dama kin ajiye hijabin,wannan boye boyen ya isa haka,nariga nasan cikine dake malama,inna tacemin wai ai mijinki ya kawoki ziyara,shine daga bada tsarabar ciki sai ya tafi,bazai tsaya a gaisa ba?"
Sauƙe ajiyar zuciya nayi bayan naji bayanin ummin,kenan daman sunsan inada ciki,musamman abinda inna ladiyo tafaɗawa ummi,yayi min daɗin matuƙa,kuma ya kareni daga amsa tambayoyi.
"Miye kikayi wani tsaye kamar gunki,kije sashen hajiyah Maryam wai tana nemanki,inna ladiyo ce tace na faɗa miki"
Karisa shiryawa nayi cikin doguwar riga ta atamfa,nasaka hijabina na tafi.
Kafinnan saida nabi ta wajen inna ladiyo tukunna tana kitchen.
"Inna dama kinsan......."
"Haba ƴar nan,muna tare a ɗaki ɗaya har mu kasa gane halinda kike ciki? Abinda zan faɗamiki shine ki daina wannan boye boyen haka,wanda yasani yariga yasani,wanda baisani ba kuma zaki jawo hankalin sa ne yasaka ayar tambaya"
Ɗaga mata kai kawai nayi batareda nace komai ba,kuma maganar tata haka ne.
"Kije hajiyah Maryam tana nemanki a sashenta"
"Toh"
Shine kaɗai amsata kafin na wuce can din,sai a lokacin naji rashin kyautawa ta,don rabona da sashen nayi sati biyu,wasan buya nayi tayi da ƴan gidan,saboda karsu gane inada ciki.
Magana naji sunayi tun kafin na shiga,da waye haka suke surutu.
tura ƙofar nayi na shiga,wani saurayine amma ba zai wuce shekara sha bakwai ba.
Daga yanda suke maganar zaka gano cewar ɗan uwanta ne.
"Wai huzaif yayar babanka nake fah ba kakarka,tashi to ku tafi gatanan ta shigo"
Dukkansu kallona sukayi itada shi,kallo ɗaya mutum zayyi masa ya gano kamar da suke da hajiya maryam,tunda tace yayar banbansa to ɗan Taheer ne kenan,babban dansa.
"Okay ni barina je waje,ki sameni a mota"
Rabawa yayi zai wuce tagaba na hajiyah Maryam tayi masa magana.
"Kai banason sakarci,bata girmeka bane da bazaka gaisheta ba"
Cikin ɗaɗɗagawa irinta masu sabuwar samartaka ya gaisheni,nidai na amsa a taƙaice ya fice. Ƙarisawa nayi muka gaisa da hajiya Maryam,sunkuyar da kaina nayi,don naji kunya sosai.
"Hhhh yau kuma kunyata kikeji,kijr zai kaiki gidansu ne akwai wanda zaki haɗu dasu,bansan ko ki kwana ba ga wannan ki riqe,amma ki tabbatar ki dawo gobe. Kije maza Allah ya tsare,ki kula sosai dan yanzu ba kaman da ba,na fadamasa
kada yayi tuƙin ganganci"
Nidai da toh na amsa mata dakuma godiya. Saikuma kaina a ɗaure shin dawa zan haɗu a gidan da ban taba zuwa ba..
A haka dai na bi bayan wanda taƙira da huzaif ɗin zuwa motarsa. Ina shiga ya tayar da itah ya hau hanya ko magana bayyimin ba.





SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.



*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)


Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150

Bismillahir-rahmanir-raheem


Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.


*BOOK 2*
...29...




Bayan mun shigo gidan fita nayi daga motar ya nufi wajen parcking,ina nan tsaye ina kallon ƙyauye naga ya wuce ta gefena,baicemin na biyoshiba nabi bayansa da sauri,wani falo muka wuce kafin mukazo wani daban. Bai shigaba da hannu ya nunamin na shiga,shikuma yayi wani wajen daban.
Kaman wata baƙuwar kaza haka na kutsa kai ina rarraba ido.
Wazan gani inna ce da deeja dakuma Sayyid.
Suman tsaye nayi ina kallonsu,har deeja ta rungumeni banyi motsi ba,wannan wanne irin bazata ne haka. Nayi kaina tambayar,in suna haka tsaf zasu saka kaina yin kwancewa.
"Innaaa......"
Shine kawai abinda nasamu faɗi,dariya sukayi tare,har matar danake tunanin matar ƙanin hajiyah Maryam ɗince,wacce suke cewa Hajiya Shukurah.
"To anan dasu bazaki iso ba,duk mamaki ne yanaki motsawa"
Da sauri nazo inda inna take na rungumeta da ƙarfi,kukan Sayyid naji yana jan hijabi nah.
Juyawa nayi na tsura masa,kama naga yanayi da hajiyah Maryam,kodan nasan yanzu jikantane,amma idon kam na ubansa ne. Tureni yake yana tiro baki,waina matsa a jikin inna. Dariya abin yabani,wannan kam halin babansa ne.
Hannu nasa na ɗaukeshi,zuciyata cike dason yaron,wai dana riqeshi saina tuno labarin hajiyah Maryam,gaskiya ba ƙaramin azantuwa tayi na sosai.
Kallona yake yaƙi sakin jikinsa dani,deeja tana matsowa ya miƙa mata hannu. Dariya abin yabani,wato har ya mantani kenan. Inna na kalla tareda haɗe rai.
"Inna kiga ya mantani,laifinki ne bakya bashi labarina"
"Ohh jimin,labarinki ma kike cewa,keda kika figeshi a nono kika gudo saboda duniya tamiki zafi,kuma ma dakike can ɗin wani rainonsa kike daya miki zafi. Kinshigo gidan mutane ko gaishesu bakiyi ba kina ta danki koh"
Maganar da tayine yabani kunya,kuma fah ban gaisheda matar gidan ba.
Cikin rusunawa na gaisheta,dariya tayi kafin ta amsa.
"Lahh kada ki damu Sumaimah,ai kinyi kewarsune shiyasa. Dan ma kada ki damu anan zasu zauna"
Kallon inna nayi da sauri,anan zasu zauna kaman yah. Ta gano wanne tunani nake,saita bani amsa.
"Nice nake neman wacce zata tayani aiki,shine Anty Maryam tacemin daman tanason inna ta dawo da aiki,sune suka zauna a sashen hajiyah Mammah suka raini Ahmad itada Inna ladiyo. To bazata manta dasu ba har abada."
Cikeda murna dakuma mamakin dama ashe inna tasan Ahmad tun yana ƙarami na kalleta.
Murmushin manya tayi kafin tace.
"Kiƙara mata godiya har deeja zata saka a makaranta,dama nayi tunanin tafiya da itah zan koma garinmu,to saiga mota wai ƙira daga hajiya,shine muka taho"
Bayan na gama godiyar wani abune ya fadomin.
"Inna meyasa zaki tafi garinku"
"Hmmm wata shida kenan da gaji ta matsawa baba audu kan cewar ya siyar da sashenmu,yanzu haka wanda suka siya sun matsa mu tashi"
Wani takaicine naji yazomin wuya nah menene haka mutanennan suke nufi. Duk kuma wajen bai zama gadon inna ba,ɗanta ya mutu ita tuminin takaba kawai za'a bata,sannna Ahmad ba ɗan ta bane.
Ɗakin da aka bawa inna muka koma,anan sabon hira ya buɗe.
Deeja na kalla tana shirya kayansu,hankalin yarinyar yabani mamaki,dan lokacin dana tafi ba wani har can bane,yanzu ta zama tamkar uwar Sayyid komai wajenta yake zuwa.
Yau jina nake tamkar an tsundumani a aljanna,abu kaɗan saina kallesu na sake kallonsu,jinake kamar na maidasu cikina.
Labari kuwa har raba dare mukayi munayi,nasu gaji da kuma gidanmu.
Bayan mun gama hirar Deejah tayi bacci itada Sayyid tashi nayi na shiga banɗaki.
Bayanna fito rigata na cire nayi sama da zanin,ina shirin kwanciya naji maganar inna.
"Shin kun daidaita ne a tsakaninku?"
"Uhmm ni dawa?"
"Zaki fara wannan juyar da maganar kamar baki gane ba, mijinki mana nake nufi"
"Ahah bamu shirya ba,har yanzu baisanni ba"
"Baisani ba ya akayi kuma naga ciki a jikinki"
Shuru nayi na rasa ma mai zance mata.
"Uhm.....inna uhmm lokacin baya cikin hankalin sa ne,wata tabashi magani sai shine"
Ganin na duburburcene yasa ta juyar da kanta tareda cewa.
"Allah ya kyauta,ya daidaita ku bisa lokacin daya dace"
Ameen nace a hankali daga nan na kwanta.
Da safe bayan mun tashi nice nayi aikace aikacen gidan dukka,bayan mun gama karyawa muna zaune hajiyah Shukurah tashigo da waya a hannunta.
"Sumaimah ga kira nan daga hajiyah Maryam waiki koma driver yazo ɗaukarki"
Zaro ido nayi kaman zanyi kuka,dan har raina gidan ya isheni sosai,don ba yadda zanyi ne. Dan kwana ɗaya danayi dasu inna har naji daɗi,gashi bangama ganinsu ba kuma zan tafi.
"Uhm hajiyah ki bata haƙuri dan Allah na ƙara"
"Ahah ki koma kici gaba da aikinki,bakya tunanin a halin da kike ciki zamanki kusada su ma hadari ne,dan haka ki koma kici gaba da kula Allah yakiyaye,matsalar hajiyah Mammah tariga tasan take a matsayin wacce tasan mai take ciki,zamanki kusan danginki zaisa ta binciko dawa kike tare."
Ɗaga kai nayi alamar na fahimta. Badan naso ba na shirya komawa.
Naso tafiyah da Sayyid amma nasan bazan fara wannan gangancin ba mai suna gani kasheni,dan haka sallama nayi musu na dawo.
Tun a hanya naji kamar banje ba.
Watan su inna ɗaya kenan da dawowa,amma bangansu sosai ba,sai nayi tabi kafin hajiyah Maryam ta barni naje.
I zuwa wannan lokacin cikin jikina ya fito,saboda girman dayakeyi nan da nan,don ya shiga wata na huɗu a satinnan.
Ana Sayyid saida yayi kusan wata bakwai kafin yakai haka,amma shi yanzu haka yakai kusan cikin wata bakwai a matan da basa girman ciki.
Kowa a gidan yanzu yasan inada ciki,saidai ban damu ba,saboda duk a zatonsu na mijina ne daya tafi rani.
Ita kanta hajiyah Mammah har kyauta takemin,tareda cewa mijina bai kyauta ba daya barni da ciki yasake komawa. Nidai saidai nayi murmushi nace uhm.
Bayan nayi sallahr asuba bacci nakoma mai shegen nauyi,gashi nayi wata ƙiba saboda yawan cin abinci kaman gara,cina har ya wuce na cikin Sayyid. Ummi har boye abincinta take inta ganni,inna ladiyo ce da hajiyah Maryam haka hajiyah Mammah suke bani abinci duk sanda suka ganni.
Bayan na miƙe daga kan katifar madubi na ɗauka na kalli fuskata,taƙara fari da ƙiba,haka ma jikina. Ƙafafuna kam ba'a magana.
Wanka na shiga ina fitowa nasaka doguwar riga,daga cikin materials ɗin da hajiyah Maryam ta ɗinkamin saboda goyon ciki,naji daɗinsu kuwa sosai ba kaɗan ba.
Ummi ce tashigo ɗakin ina shafa mai,hijabi ta ɗauka tasaka da kuɗi a hannunta.
"Ke kuma fah ina zuwa haka,nasan baki fiye zuwa aike ba,an fi tura mai gadi shikaɗai"
"Hmmm wai Yallabai ne zai dawo shine inna tayimin lissafin abinda zan siyo,Sannan kuma ki faɗamin mai kike so zaki haɗamasa"
Zaro ido nayi tareda kallonta,wanne yallabaiɗin badai Ahmad ba,gabaɗaya na manta da ashe zai dawo,bana tunashi sainazo kwanciya na rungume rigarsa tukunna.
"Kinga tsaya tsaya basai kinje ba zanje"
"Ke dalla kimin lissafi naga bake kika sakani ba, yanzuma daga sashensa nake na gyara,kina bacci ɗazu na ɗauki key"
Kallonta nake da mamaki,nasan inna ce tasakata,itama kuma tana tausayina nasan.
Rungumeta nayi ina zuba mata godiya,ba ƙaramin daɗi naji ba data gyara ɗin.
"Nagode ummi,barinaje na dudduba sashen,sannan na gyara kitchen ɗin. Kafinnan zan miki lissafin abubuwan"
Lokacin dana shiga sashen tsaf yake ta gyarashi koni zanyi iya haka.
Saidai ɗaki da kuma banɗaki dana ɗan ƙara gyarawa.
Kuɗi da yawa hajiyah Maryam tabawa inna ladiyo na abincinnasa,ni kaina shaidace yanda take ji dashi a cikin ranta.
Hmmm koya zamu kaya nidashi idan ya dawo,shin wacce amsa zan bashi ne idan yayimin tambayar miye a jikina.
Kitchen ɗin na gyara na fitar da abinda zanyi amfani dashi.
Ina cikin haka ummi ta dawo,sosai ta tayani har muka gama aikin wajen daya na rana,lokacin kam nasan anty thing a kowanne time zai iya dawowa,da sauri muka ƙarisa nabar sashen,domin banaso ya dawo ya sameni,ban shirya ganinsa a yau ɗin ba.
Lokacin da muka koma daki nayi sallah waje na samu na zauna ina haki tareda sauke numfashi,don ba ƙaramin gajiya nayi ba,jikina nauyi yakemin kwanannan.
Ruwa mai sanyi ummi ta miƙomin tareda ajiye abincin mu a tsakiyar ɗakin.
Saida na zuqe ruwan naja ajiyar zuciya kafin nace.
"Kai gaskiya ummi a tafawa ruwa,ruwa rahama ce,mai rowar ruwa ya cika marowaci"
Dariya tayi kafin tace.
"Ehh lallai yau gana mai yiwa ruwa santi,haba kema da laifinki,ji yanda kika dage kina yimaza aiki kaman wani mijinki,ko wanda kike aure bakya yimasa bautar da kike masa,Sannan abinda yabani mamaki ban taba ji kince
Showing 45001 words to 48000 words out of 62659 words