yanzu kin kasa turani aikatau duk da halin matsi saboda karna halaka,kin zabi kije akaina"
Kallonta nake da mamakin yanda kalaman hankali suke fita daga bakinta,ashedai tana sane da abinda yake faruwa,katseni tayi da maganarta..
"Anty da Sayyid zaki tafi"
"Ahah ba dashi zata tafiba,idan ta tafi dashi bazatayi abinda taje yiba,sannan abin bazai tafi yanda ake so ba"
"Wannan abu kuma inna?"
Na tambaya ta mamaki,ganin yanda take magana kaman an turani wani muhimmin aiki.
"Ohh abu nace? Ina nufin aikin dazaki je yiɗin,anan zaki barshi shima zaifi masa sauƙi"
"Amma ......inna ban yayeshi ba fah"
"To jimin wani zance,ɗan da tun bashida wayo kike guduwa makaranta ki barshi,ana mutuwa a bar yaro ma ya rayu ai?"
"Yawwa shikenan anty karki damu ki barmin shi,zan kula dashi tamkar kinanan"
Deejah ta faɗa cikeda farinciki,sauƙe ajiyar zuciya nayi tareda cewa.
"To shikenan khadija na barmiki shi har naje na dawo"
Daga haka ta fita tana murna,ni tausayima ta bani,ganin yanda muke ta faɗi tashi,idan na tafi zanyi kewarsu sosai.
Wata takarda naji inna ta miƙomin bayan na tafi duniyar nazari,karba nayi na bude,address na gida a abuja.
"Ga wannan gidan shi zaki nema idan kin isa,inkinje ki samu wata mai aiki inna ladiyo,kice mata nina aikoki,idan kika faɗi hakan zata baki aiki"
Ɗaga mata kai nayi,na rasama mai zance,gabaɗaya a rayuwata bana kawo cewar wai zanje neman aikatau wani garin saboda mu samu abinyi.
"Toh inna Inshaallah zanyi hakan,batun kuɗin aikin kuma zan dunga turowa Tunga sai ya baku"
"Karma ki tayar da hankalinki,a nan ma zan samu wata sana'ar kota ɗan tallene na lokaci kaɗan na dungayiwa Deejah,nasan kuma daman ba wai aikinne har a ranki ba,kinasone kiyi nesa da gida saboda abubuwan da suka faru"
Sunkuyar da kaina nayi,gaskiya hadda ma hakan,tunda na rasa mijina gabaɗaya zaman garin ma ya isheni,tun mutum yana toshe kunnuwansa da maganganu har suyi masa yawa.
Na haɗa kayana a ƙaramar jaka duk abinda nake buƙata,Deejah nake jira ta ƙiramin mai mashin ya kaini tasha.
Kallon Sayyid nayi wanda yake tsaye da minti a hannunsa,tun shekaranjiya da nasan ba dashi zan tafi ba na daina bashi nono,dama toh ba dogara yayi gabaɗaya a kai ba.
Amma duk da haka zuciyata saida tayi zafi da barinnasa na shiga duniya,wanda Allah ne kaɗai yasan ranar dawowa ta.
Jiya naje gidanmu nayi musu sallama,muna zancen da ammi inna rammah tajiyo,dama halinta ne yin lab'e idan ana zance,kafi kaceme har zance ya gama ko'ina cewar talauci da baƙin ciki nima zai korani duniya. Wani lokacin abun ma har mamaki yake bani,shin metasa mutane basa ta kansu saita wani ne?
Ko ma dai menene nidai yau zan barmusu garin.
In cikin hakane naji Deejah ta dawo da gudu.."
"Anty ki fito gashinan na ƙiramiki mai mashin ɗin"
"Ohh har an samu mai mashin ɗin?"
Inna tafaɗa wacce ta fito daga kewaye da buta a hannunta,tayi alwalar walaha..
"Ehh inna nasamo,saida ya ɗanani muka taho tare"
Jakata na ɗauko zan fita daga ɗakin,da sauri Sayyid ya jefar da mintin hannunsa yana ɗagamin hannu alamar zai bini,wani kukane ya taho min ya tsaya a maƙogarona.
Inna tana ganin haka ta ɗaukeshi tareda goyonsa,dan ma yau bayyi kukan yayeba da daddare.
Gaba na wuce suna bina a baya zuwa ƙofar gida,har raina banason barinsu,amma kuma nasan zuciyata tana buƙatar zuwa nesa,koba komai hakan zaisa na manta da wasu abubuwan.
Musamman yanzu dana gama karatu banida abinyi.
"Sumaimah Allah ya tsare hanya,ki kulada abubuwan dana faɗamiki jiya da daddare,karki shiga abinda babu ruwanki,amma idan yazamo abu nakine kiyi ƙoƙarin wajen ganin baki takura kanki kin hana kanki ba,ki zama jaruma ta yanda zaki iya tsayawa wanda yke naki. Labarin danace zan baki kiyimin uzuri akai,zakiga abinda zai gigitaki amma kibi komai a sannu. Sannan na miki alƙawarin duk wata tambaya da take ranki ki adana,da zar kin dawo nikuma zan amsa miki su. Idan na faɗamiki yanzu zai iya cutar dake,dan haka ki bi komai a sannu"
Kaina ne ya kulle da maganganun innan,nifa aikatau kawai zanje,shin mai ya haɗani da waɗannan zantukan kuma?
"Inna shin meyasa kike min irin waɗannan zantukan?"
"Da sannu in kika inda zaki je to zaki gane,kije maza Allah ya tsare ya baki NASARA"
Ɗaga mata kai nayi tareda yiwa Deejah da Sayyid kallon ƙarshe kana na ɗale bayan mashin ɗin.
Ina kallon gaji ta fito daga gidan bayan mashin ɗin ya tashi. Nasan ba komai bane banda gulma.
A raina nace kedai kika sani ni yanzu sai sanda kika ganni. Saida ba kama hanyar naji kaman na koma nace na fasa,dan ji nake kaman wani abun zai faru. Amma ya zanyi alƙalami ya riga ya bushe.
Tafiya hausawa suka ce yankin azaba,Musamman da mutum bai taba yiba.
Ba ƙaramar wahala nasha ba kafin mu isa,ga kirjina har yanzu bai daina ciwo ba na yayen da nayi.
Sallahr azahar da la'asar mukayi nida wata mata mai ƴaƴa biyu a tashar bayan mun sauƙa.
Sai surutu take yimin,irin mutananne masu magana,ganin ban bata lokaci sosai ba yasa ta koma yi da ƴaƴan ta.
Ɗari biyu na ɗauka a cikin kuɗina na siya lemo da biredi,wata ƴar ta sai kallona take kaman zata cinyeni,wasu yaran fah dama haka suke da kwaɗayi.
Bayan nasha miƙa musu sauran nayi da sauri suka fizge har suna haɗawa da hannuna..
Tashi nayi na ɗauki kayana na nufi wajen masu taxi,ina ji tana min godiya ko waigawa banyi ba,abin yabani haushi sosai,ƴaƴa kaman goyon gwauro.
Kaman dama jira suke da sauri suka nufoni,kowa ya ƙokarin wajen ganin shi ya karbi kayana,nidai da ido na bisu,kafin na bi wanda yayi nasarar karbar kayannawa.
"Hajiya ina za'a kaiki?"
Shine maganar sa ta farko bayan na shiga motar,ban san me zan ce masa ba,dan haka na miƙamasa takardar da inna ta bani. Ajiyar zuciya na saki ganin ya gane address ɗin jikin takardar.
Kai tsaye kuwa ya kunna motarsa domin ya kaini.
"Hajiya kuɗinki ɗari biyar ne"
"Ehh ɗari Takwas kuma,kaman za'a bar gari dani?"
"Hhhh hala wannan ne zuwanki garin abuja na farko,ai haka abin yake"
"To shikenan nidai ka kainin tukunna"
Dama dubu ɗaya ce ta sauramin ɗaka da waje,dan haka ba musu ba miƙamasa ita ya vani ɗari biyu.
Jingina kaina nayi ta jikin motar tareda lumshe ido,na gaji matuƙa gaskiya yau..
Sama sama naji yana min maganar cewar mun iso,ashe har bacci ya fara ɗaukata ban sani ba..
Fitowa nayi nida jakar kayana,bakina buɗe ina kallon tangamemen gidan da ya ajiyeni a gabansa..
Na dade a tsaye ina kallon gidan,har van lokacin daya ja motarsa ya tafi ba,har na juya zan tambayeshi anya nan ne kuwa,naga wayam babu shi babu labarinsa.
Ohh ni Sumaimah ina na kawo kaina haka?
Nayiwa kaina wannan tambayar.
Kafaɗa a sanyaye na ƙarisa bakin get ɗin naman jikina ta ciki yana rawa.
Na saka hannu zan ƙwanƙwaƙwasa kenan naji muryar wani mutum yana min magana. Sanye yake da wandon sojoji da t-shirt a jikinsa.
"Hey madam what are you looking for?"
(Baiwar Allah wa kike nema?)
Ohh ance ilimi rahama ne kuma babba baiwa ce,koda baka buƙatarsa a sannan kayishi watarana zakaga amfaninsa,cikeda ƙwarin gwiwa na mayar masa a harshen nasarar da yayimin magana dashi.
"Um sir am looking for Inna ladiyo,she is maid in this place"
(Malam ina neman inna ladiyo ne,tana aiki anan)
Ganin na mayar masa amsa yasa ya rage yimin kallon walaƙancin daya faramin daga farko. A haka muka yi ɗan magana dashi har nake cemasa ni ƴar uwarta ce.
Budemin gidan yayi na shiga,abinda banyi zaton zaiyi ba.
Tafiya nake kaman baƙyauye a kano,jinayi na bugi wata mace karaff.
Saurin maido da hankalina nayi jikina,wanda ya tafi da kalle kallen dogon ginin dayake gabana..
Macece matashiya amma tafini daga gani,tana sanye da kayan sojoji itama a jikinta,wai nan gidan sojoji ne ne,na faɗa a raina..
"Sorry am sorry madam,banganki bane"
Hakuri nake bata,amma ko kulani batayiba tayi hanyar wajen da wata tamfatsetsiyar mota take fake a gefe.
Ganin hakan yasa da sauri na shige wata ƙofa da na gani.
Wata mata na gani zata wuce,dattijuwa ce tana ɗauke da wani bokiti a hannunta. Tayimin kamada ƴar aiki,amma kuma kayan jikinta ko wata mai wadatar a garinmu albarka,koda yake wazai haɗa da nan da can.
Saurin isa gabanta nayi ina yimata alamar ta tsaya.
Da mamaki take kallona,ganin bata sanni ba..
Amfani nayi da shurunta na gaisheta,Amsawa tayi a gajarce tana min kallon mai ke tafe dake?
"Uhm dama inna ladiyo nake nema,an aikoni wajenta ne"
"Waye da aikoki?"
"Inna mairo ce daga DABAGAYI,dan Allah kinsanta?"
Ɗan murmushi tayimin na manya tareda cewa.
"Nice ai ladiyon,mairo ce ta aikoki innar goje?"
Jijjiga kai na fara tamkar ƙadangare,tareda jin farinciki ganin yanda kayana ya tsinke a gindin kaba.
Alama tayimin akan na biyota,muna tafiya ina kalle kalle har muka isa inda nayi tunanin muhallin masu aikine.
"Ki ajiye kayanki ki huta,zanje wani waje na dawo,idan hajiya taƙiraki ko wani a gidannan karki kuskura kice masa mairo ce ta aikoki,kicemusu ke ƴar yayana ce daga Zarawa"
To nace mata daga nan ta fice,komai yasa zan boye oho.
SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah 🙏🏼 ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
Ina ƴan mata dakuma Matan aure masu muradin burge mazajensu da ɗinkuna zuƙa zuƙa. *PHEEDY TOILORING DESIGN* ,suna gabatar muku da ɗinkuna kala kala wanda sukayi daidai da zamani.
Zaku samemu a kan wannan layin waya kamar haka
09167130115
Wato a manhajar whatsapp. Domin ganin kalolin samufurin aikinmu kuma ku tuntubemu a INSTAGRAM da kuma TIKTOK a @pheedyxacks_ragtrade
Muna maraba daku a kowanne lokaci🙏🏼🙏🏼🙏🏼🙏🏼🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah 🙏🏼 ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
Ina ƴan mata dakuma Matan aure masu muradin burge mazajensu da ɗinkuna zuƙa zuƙa. *PHEEDY TOILORING DESIGN* ,suna gabatar muku da ɗinkuna kala kala wanda sukayi daidai da zamani.
Zaku samemu a kan wannan layin waya kamar haka
09167130115
Wato a manhajar whatsapp. Domin ganin kalolin samufurin aikinmu kuma ku tuntubemu a INSTAGRAM da kuma TIKTOK a @pheedyxacks_ragtrade
Muna maraba daku a kowanne lokaci🙏🏼🙏🏼🙏🏼🙏🏼🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
*BOOK 2*
...7...
Ina nan zaune a bakin katifa naji alamar shigowar mutum.
Inna ladiyo ce ta dawo hannunta ɗauke da kwanon abinci.
Tashi nayi na karba a hannunta kana na ajiye a tsakar ɗakin.
"Sannu na barki ke kaɗai koh,naje kawo miki abincine,sannan munyi magana da hajiya yanzu.
In kinci abinci kizo zatayi magana dake,ki kula sosai nasan mairo ta fadamiki haka koh?"
Daga mata kai nayi alamar ehh,daga nan ta juya ta fita,zama nayi a gaban kwanon kafin na bude a hankali.
Sakwarace a ciki da miyar ganye,kafin nasaka hannu ma sai ƙamshi takeyi.
Ban bata lokaci ba na saka hannu bayan nayi bismillah na fara zubawa cikina.
Duk yanda naso na cinye malmalar sakwarar guda biyun kasawa nayi,dan ina cin guda ɗaya naji na ƙoshi,ta biyun kada na taba..
Kwanon na tattara wai zan fita dasu,a nan gizo ke saƙar ina zan nufah a wannan tangamemen gidan haka..
Wani mutum na hanga a gefe dani na tambayeshi hanyar kitchen,gyaran wasu fulawowi yakeyi,da alama aikinsa kenan.
"Baiwar Allah ta ina zansan inda hanyar madafa take,wannan ai sai su ladiyo,amma naga sunayin wancan corridor da yayi dama"
Godiya nayi masa daga nan nayi wajen daya faɗamin.
Tafiya nake ina Addu'a a raina har na samu kaina a wajen dana tabbatar madafar ce,duk da bayyimin kama da wanda na saba gani ba. Wannan waje haka ƙato.
Kwanon hannuna na ajiye akan wani tebur dana gani a gabana,har na juya zan fita naji muryar wata matashiya.
"Ke daƙiƙiyar inace dazaki ajiye kwano a wajen da ake yin girki,ko kyauyen cinki bai nuna miki canne wajen wanke wanke ba"
Tafaɗa tana nuna min wani waje mai dan rami da famfo a wajen,wanda ni sai yanzu ma na kulada shi.
Maida kaina nayi kan fuskarta,budurwa ce ko kuma nace ƘARAMAR BAZAWARA(littafin ummu najam amarsisi nayi miki miss).
Domin daga ganinta bazata fini ba.
Wasu kwanuka take jerawa a cikin wardrope,fuskarta a haɗe kaman anyi mata mutuwa.
"Daƙiƙiya? In daƙiƙiya ce ni ashe kekuma kece babbar daƙiƙiyar wacce ta daɗe ma a ciki,domin in ƴan aiki kike ƙira d daƙiƙai to kece babbarsu wacc....."
"Sumaimah ya isa haka,ke kuma Ummi bai kamata kina walaƙanta mutane ba duk sanda kika gansu,ke idan ba mai kuɗi ba to kowa ba kaman ba mutum ba haka yake a wajenki"
Wacce ta ƙira da ummin ta kalla tana yiwa faɗan,ana mata maganar ma tana wani fisfisgewa,wanann daga gani bata da daɗi,in kuwa hakane halinta to batada kirki sam..
"Inna ladiyo wai bakya ganine,ya za'ayi kawai ka kawo kwano ka ajiyeshi a wajen da ake abinci"
"To naji amma dai ai kinsan sabuwar zuwace ko aiki bata fara ba"
"Duk da ai......"
"Kinga ya isa haka,kici gaba da da gyaranki,ke kuma muje na gabatar dake a wajen matar gidan,anyi sa'a ma yau tana gidan"
To nace mata tareda bin bayanta muka fice daga wajen.
Kafaren wani hamshaƙin falo na tsinci kaina a ciki,dama irin wannan gini haka dole mutum yayi tunanin irin kayan alatunnan a cikinsa.
Wata mata ce a zaune akan ɗaya daga cikin kujerun falon,ta saka wani kaya da ban wanne iri bane,amma ko daga gani kasan masu kyaune da tsada.
Abinda yafi bani mamaki shine,meyasa nakejin faɗuwar gaba dana haɗa ido da ita na farko,hmm anya kuwa wannan irin mutanen da mutum zai iya sakewa dasu?.
Tsugunnawa nayi a ƙasa kaman yanda naga inna ladiyo tayi.
"Hajiyah barka da warhaka,g ta nan na kawomiki itah,tazone domin ta samu aiki,da fatan za'a taimaka"
"Hajiyah barka da yamma"
Nima na fada cikin girmamawa,ganin ta kafeni da ido.
Can munyi shuru kaman ruwa ya cinyemu,nida inna ladiyo sai zazzare ido muke.
Jan ajiyar zuciya tayi tareda zare farin glass ɗin dayake idonta.
"Ladiyo banason wani magana yanzunnan,kuma ba kin faɗamin zuwanta ba ɗazu...huhh wancan yaron dama ya dawo gidan,naji waccar tsohuwar nayin mitar kan kan a samu masa wata mai aikin,tunda waccar mun sallameta,kuje ki nuna mata yanda zatayi,in kuma ta kuskure itama ya koreta kaman yanda ya saba toh sai tasan yanda zatayi.
Albashinki dubu ashirin a wata shin yayi miki ko kuwa"
Tun daga ambaton aikin naga ladiyo ta sha ruwan jikinta,koma menene naga da alamar wanda zanyiwa aikin bashida daɗin sha'ani,koma dai menene tunda naji batun dubu ashirin zanyi iya ƙoƙarina wajen ganin nayi nasara.
"Yayimin hajiyah nagode Allah yaƙara buɗi yasa kifi haka"
"Ameen ku tashi ku tafi toh,in wata yayi zanyi miki magana,idan har kina gidan har zuwa lokacin. Sannan kuma karki sake ki nuna masa cewar nina ɗaukeki aiki,kawai kice masa kin fito ne a jerin wacce zatayi masa aiki. Abu na ƙarshe banason ki yaudareni,Sannan ko nan gaba na buƙaci haɗin kanki akan wani abun dole zaki bani"
"Inshaallah hakan bazai gagara ba hajiya,kuma da sannu zanyi yadda kika ce"
____∆∆∆____
Ya yage takardu sunfi guda biyar yana zubarwa,kansa ya kulle ya rasa ma mai zayyi.
Kansa ya riƙe tareda jan gwauron numfashi.
Kwanansa uku kenan da zuwa office amma yagagara yin komai kaman nada,abubuwa da dama sun canja ciki harda tsarin wajen,abun yana cin zuciyarsa ganin duk yanda yakeson aikinsa ya tafi a gaggawa amma abu ya gagara. Duk ƙoƙarin daya dungayi a baya ya tara shaidu duk sun tafi kaman anyi ruwa an ɗauke.
Kansa ya ɗora a kan kujerar yana jinata a hankali idonsa ya rufe.
Yaji alamar buɗe ƙofa wani ya shigo,tun kafin ya bude ido yace.
"Eemran mai Abbah yace,ya bamu izinin binciken wanann gidan?"
"Am sorry sir amma har yanzu ya ƙi saka hannu,a cewarsa wai bai kamata ka fara babban aiki irin wannan ba daga dawowarka"
"Hmmm kaida Neelah ku fara aiki cikin sirri,bazan iya tsayawa da aikinnan ba"
"Amma yallabai akwai hatsari muyi batareda sanin sama ba"
"Hatsari ya wuce wanda nake ciki,kullum hankalina a tashe yake da tunanin a kowanne irin sakanni za'a iya sake farautar rayuwata ba, shin akwai abinda yafi haka hatsari Eemran?"
Duk yanda yake boye damuwarsa tun bayan dawowar tasa,amma kana kallonsa zaka san baƙaramin dauriya yake ba.
"Hakane kam ogah lamarin abin abun a dubane,nida Neelah Inshaallah zamu iya ƙoƙarinmu wajen ganin komai bai sake zuwa da matsala ba.
Wanda suke aikata waɗannan abubuwan da sannu zasu zo hannu.
Hular sa ya ɗauka ya ɗora akan kayan uniform ɗinnasa,wanda suka sake fito da jarumtarsa a fili.
Yau baizo da drivernnasa ba wai mai ɗakinsa ta haihu,dan haka da kansa ya tuƙo bai ɗauki wani drivern ba,domin dukkansu ba yarda yayi dasu ba,yasan duk yaran hajiyah maryam ne.
Buɗe motar yayi zai shiga,tsayawa da shiga motar yayi sanadiyyar wani akwati daya gani a wajen zaman drivern..
Kaishi yayi ɗayan sit ɗin,sai bayan ya zauna kafin ya ɗauko shi ya buɗe..
B'era ne matacce a ciki sai wata wasiƙa da jan ink.
.........kayi hankali da rayuwarka yaro,baka san mai kake shirin tonowa ba,hakan bazai ta'ba kyau ba,domin sakamakon dazaka gani bazai ɗauki ƙwalƙwalrwar ka ba.
Hmmm wato warning ɗin a aka baka a baya bai isheka ba saika sake aikata wani kuskuren?.......
Ninke ta kardar yayi tareda sakata a aljihunsa,yayinda bandir ɗin kuma ya jefashi ta windown motar,ƴar ƙaramar tsuka yaka yana cije ƙasan bakinsa,ganin bata lokacin zayyi yawa yasa yaja motarsa zuwa gida. Wanda baya ganinsa a matsayin gidan kaman yanda wasu ke gani,dan ɗaukar wajen yake tamkar inda duk jagayen dakayi zaka dawo ka kwana da makashinka a ciki..
A hankali yake jan motar yana bin karatun dayake tashi a cikin motar har ya isa gida..
Bai samu kowa a babban falon gidan ba,wanda daman hakan yakeso,in badan Abbah ya hanashi yin amfani da ƙofar bayansa ba da babu wanda zai dunga ganinsa ma saita kama dole.
Buɗe ƙofar shiga sashennasa yayi ya shiga,an sanja masa ajiyar fulawar da take kusa da window,wanda daman yana zuci zucin ya kaita kusada rana ya manta..
Sannan an goge ko ina a falon ƙal ƙal sai ɗaukar ido yakeyi,duk da yanda yaɗebo gajiya da tashin hankali amma gyaan ya burgeshi matuƙa.
Ɗakinnasa ya nufah da hularsa a hannu.
Jefata yayi akan gado,wanda aka sanja zanin gadon ba na ɗazu bane akai.
Rigar jikinsa ya cire harda singlet ɗin,domin dama ya saba duk lokacin daya dawo sai yayi wanka tukunna ya wanke gajiyar jikinsa.
Bai shiga banɗakin ba tukunna sai ya tsaya yana aikinnasa na kullum wato tunani.
.........
Tunda naji batun biyana 20k a wata wani ƙaimi na nayin aiki yanda ya dace ya tashimin.
Bin inna ladiyo na dungayi akan tafaɗamin yanda aikin yake.
Anan nakejin wanda zanyi wa aikin shine ɗa na fari a gidan,mahaifiyar sa bata nan,sannan ance ya mutu a hatsarin mota tsawon shekaru,sai yanzu ya dawo.
Ba wannan na maida hankali akai ba saina halayensa da aka sanar dani.
Bayason mutane sosai, dan haka duk wacce zatayi masa aiki to
Showing 9001 words to 12000 words out of 62659 words
Kallonta nake da mamakin yanda kalaman hankali suke fita daga bakinta,ashedai tana sane da abinda yake faruwa,katseni tayi da maganarta..
"Anty da Sayyid zaki tafi"
"Ahah ba dashi zata tafiba,idan ta tafi dashi bazatayi abinda taje yiba,sannan abin bazai tafi yanda ake so ba"
"Wannan abu kuma inna?"
Na tambaya ta mamaki,ganin yanda take magana kaman an turani wani muhimmin aiki.
"Ohh abu nace? Ina nufin aikin dazaki je yiɗin,anan zaki barshi shima zaifi masa sauƙi"
"Amma ......inna ban yayeshi ba fah"
"To jimin wani zance,ɗan da tun bashida wayo kike guduwa makaranta ki barshi,ana mutuwa a bar yaro ma ya rayu ai?"
"Yawwa shikenan anty karki damu ki barmin shi,zan kula dashi tamkar kinanan"
Deejah ta faɗa cikeda farinciki,sauƙe ajiyar zuciya nayi tareda cewa.
"To shikenan khadija na barmiki shi har naje na dawo"
Daga haka ta fita tana murna,ni tausayima ta bani,ganin yanda muke ta faɗi tashi,idan na tafi zanyi kewarsu sosai.
Wata takarda naji inna ta miƙomin bayan na tafi duniyar nazari,karba nayi na bude,address na gida a abuja.
"Ga wannan gidan shi zaki nema idan kin isa,inkinje ki samu wata mai aiki inna ladiyo,kice mata nina aikoki,idan kika faɗi hakan zata baki aiki"
Ɗaga mata kai nayi,na rasama mai zance,gabaɗaya a rayuwata bana kawo cewar wai zanje neman aikatau wani garin saboda mu samu abinyi.
"Toh inna Inshaallah zanyi hakan,batun kuɗin aikin kuma zan dunga turowa Tunga sai ya baku"
"Karma ki tayar da hankalinki,a nan ma zan samu wata sana'ar kota ɗan tallene na lokaci kaɗan na dungayiwa Deejah,nasan kuma daman ba wai aikinne har a ranki ba,kinasone kiyi nesa da gida saboda abubuwan da suka faru"
Sunkuyar da kaina nayi,gaskiya hadda ma hakan,tunda na rasa mijina gabaɗaya zaman garin ma ya isheni,tun mutum yana toshe kunnuwansa da maganganu har suyi masa yawa.
Na haɗa kayana a ƙaramar jaka duk abinda nake buƙata,Deejah nake jira ta ƙiramin mai mashin ya kaini tasha.
Kallon Sayyid nayi wanda yake tsaye da minti a hannunsa,tun shekaranjiya da nasan ba dashi zan tafi ba na daina bashi nono,dama toh ba dogara yayi gabaɗaya a kai ba.
Amma duk da haka zuciyata saida tayi zafi da barinnasa na shiga duniya,wanda Allah ne kaɗai yasan ranar dawowa ta.
Jiya naje gidanmu nayi musu sallama,muna zancen da ammi inna rammah tajiyo,dama halinta ne yin lab'e idan ana zance,kafi kaceme har zance ya gama ko'ina cewar talauci da baƙin ciki nima zai korani duniya. Wani lokacin abun ma har mamaki yake bani,shin metasa mutane basa ta kansu saita wani ne?
Ko ma dai menene nidai yau zan barmusu garin.
In cikin hakane naji Deejah ta dawo da gudu.."
"Anty ki fito gashinan na ƙiramiki mai mashin ɗin"
"Ohh har an samu mai mashin ɗin?"
Inna tafaɗa wacce ta fito daga kewaye da buta a hannunta,tayi alwalar walaha..
"Ehh inna nasamo,saida ya ɗanani muka taho tare"
Jakata na ɗauko zan fita daga ɗakin,da sauri Sayyid ya jefar da mintin hannunsa yana ɗagamin hannu alamar zai bini,wani kukane ya taho min ya tsaya a maƙogarona.
Inna tana ganin haka ta ɗaukeshi tareda goyonsa,dan ma yau bayyi kukan yayeba da daddare.
Gaba na wuce suna bina a baya zuwa ƙofar gida,har raina banason barinsu,amma kuma nasan zuciyata tana buƙatar zuwa nesa,koba komai hakan zaisa na manta da wasu abubuwan.
Musamman yanzu dana gama karatu banida abinyi.
"Sumaimah Allah ya tsare hanya,ki kulada abubuwan dana faɗamiki jiya da daddare,karki shiga abinda babu ruwanki,amma idan yazamo abu nakine kiyi ƙoƙarin wajen ganin baki takura kanki kin hana kanki ba,ki zama jaruma ta yanda zaki iya tsayawa wanda yke naki. Labarin danace zan baki kiyimin uzuri akai,zakiga abinda zai gigitaki amma kibi komai a sannu. Sannan na miki alƙawarin duk wata tambaya da take ranki ki adana,da zar kin dawo nikuma zan amsa miki su. Idan na faɗamiki yanzu zai iya cutar dake,dan haka ki bi komai a sannu"
Kaina ne ya kulle da maganganun innan,nifa aikatau kawai zanje,shin mai ya haɗani da waɗannan zantukan kuma?
"Inna shin meyasa kike min irin waɗannan zantukan?"
"Da sannu in kika inda zaki je to zaki gane,kije maza Allah ya tsare ya baki NASARA"
Ɗaga mata kai nayi tareda yiwa Deejah da Sayyid kallon ƙarshe kana na ɗale bayan mashin ɗin.
Ina kallon gaji ta fito daga gidan bayan mashin ɗin ya tashi. Nasan ba komai bane banda gulma.
A raina nace kedai kika sani ni yanzu sai sanda kika ganni. Saida ba kama hanyar naji kaman na koma nace na fasa,dan ji nake kaman wani abun zai faru. Amma ya zanyi alƙalami ya riga ya bushe.
Tafiya hausawa suka ce yankin azaba,Musamman da mutum bai taba yiba.
Ba ƙaramar wahala nasha ba kafin mu isa,ga kirjina har yanzu bai daina ciwo ba na yayen da nayi.
Sallahr azahar da la'asar mukayi nida wata mata mai ƴaƴa biyu a tashar bayan mun sauƙa.
Sai surutu take yimin,irin mutananne masu magana,ganin ban bata lokaci sosai ba yasa ta koma yi da ƴaƴan ta.
Ɗari biyu na ɗauka a cikin kuɗina na siya lemo da biredi,wata ƴar ta sai kallona take kaman zata cinyeni,wasu yaran fah dama haka suke da kwaɗayi.
Bayan nasha miƙa musu sauran nayi da sauri suka fizge har suna haɗawa da hannuna..
Tashi nayi na ɗauki kayana na nufi wajen masu taxi,ina ji tana min godiya ko waigawa banyi ba,abin yabani haushi sosai,ƴaƴa kaman goyon gwauro.
Kaman dama jira suke da sauri suka nufoni,kowa ya ƙokarin wajen ganin shi ya karbi kayana,nidai da ido na bisu,kafin na bi wanda yayi nasarar karbar kayannawa.
"Hajiya ina za'a kaiki?"
Shine maganar sa ta farko bayan na shiga motar,ban san me zan ce masa ba,dan haka na miƙamasa takardar da inna ta bani. Ajiyar zuciya na saki ganin ya gane address ɗin jikin takardar.
Kai tsaye kuwa ya kunna motarsa domin ya kaini.
"Hajiya kuɗinki ɗari biyar ne"
"Ehh ɗari Takwas kuma,kaman za'a bar gari dani?"
"Hhhh hala wannan ne zuwanki garin abuja na farko,ai haka abin yake"
"To shikenan nidai ka kainin tukunna"
Dama dubu ɗaya ce ta sauramin ɗaka da waje,dan haka ba musu ba miƙamasa ita ya vani ɗari biyu.
Jingina kaina nayi ta jikin motar tareda lumshe ido,na gaji matuƙa gaskiya yau..
Sama sama naji yana min maganar cewar mun iso,ashe har bacci ya fara ɗaukata ban sani ba..
Fitowa nayi nida jakar kayana,bakina buɗe ina kallon tangamemen gidan da ya ajiyeni a gabansa..
Na dade a tsaye ina kallon gidan,har van lokacin daya ja motarsa ya tafi ba,har na juya zan tambayeshi anya nan ne kuwa,naga wayam babu shi babu labarinsa.
Ohh ni Sumaimah ina na kawo kaina haka?
Nayiwa kaina wannan tambayar.
Kafaɗa a sanyaye na ƙarisa bakin get ɗin naman jikina ta ciki yana rawa.
Na saka hannu zan ƙwanƙwaƙwasa kenan naji muryar wani mutum yana min magana. Sanye yake da wandon sojoji da t-shirt a jikinsa.
"Hey madam what are you looking for?"
(Baiwar Allah wa kike nema?)
Ohh ance ilimi rahama ne kuma babba baiwa ce,koda baka buƙatarsa a sannan kayishi watarana zakaga amfaninsa,cikeda ƙwarin gwiwa na mayar masa a harshen nasarar da yayimin magana dashi.
"Um sir am looking for Inna ladiyo,she is maid in this place"
(Malam ina neman inna ladiyo ne,tana aiki anan)
Ganin na mayar masa amsa yasa ya rage yimin kallon walaƙancin daya faramin daga farko. A haka muka yi ɗan magana dashi har nake cemasa ni ƴar uwarta ce.
Budemin gidan yayi na shiga,abinda banyi zaton zaiyi ba.
Tafiya nake kaman baƙyauye a kano,jinayi na bugi wata mace karaff.
Saurin maido da hankalina nayi jikina,wanda ya tafi da kalle kallen dogon ginin dayake gabana..
Macece matashiya amma tafini daga gani,tana sanye da kayan sojoji itama a jikinta,wai nan gidan sojoji ne ne,na faɗa a raina..
"Sorry am sorry madam,banganki bane"
Hakuri nake bata,amma ko kulani batayiba tayi hanyar wajen da wata tamfatsetsiyar mota take fake a gefe.
Ganin hakan yasa da sauri na shige wata ƙofa da na gani.
Wata mata na gani zata wuce,dattijuwa ce tana ɗauke da wani bokiti a hannunta. Tayimin kamada ƴar aiki,amma kuma kayan jikinta ko wata mai wadatar a garinmu albarka,koda yake wazai haɗa da nan da can.
Saurin isa gabanta nayi ina yimata alamar ta tsaya.
Da mamaki take kallona,ganin bata sanni ba..
Amfani nayi da shurunta na gaisheta,Amsawa tayi a gajarce tana min kallon mai ke tafe dake?
"Uhm dama inna ladiyo nake nema,an aikoni wajenta ne"
"Waye da aikoki?"
"Inna mairo ce daga DABAGAYI,dan Allah kinsanta?"
Ɗan murmushi tayimin na manya tareda cewa.
"Nice ai ladiyon,mairo ce ta aikoki innar goje?"
Jijjiga kai na fara tamkar ƙadangare,tareda jin farinciki ganin yanda kayana ya tsinke a gindin kaba.
Alama tayimin akan na biyota,muna tafiya ina kalle kalle har muka isa inda nayi tunanin muhallin masu aikine.
"Ki ajiye kayanki ki huta,zanje wani waje na dawo,idan hajiya taƙiraki ko wani a gidannan karki kuskura kice masa mairo ce ta aikoki,kicemusu ke ƴar yayana ce daga Zarawa"
To nace mata daga nan ta fice,komai yasa zan boye oho.
SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah 🙏🏼 ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
Ina ƴan mata dakuma Matan aure masu muradin burge mazajensu da ɗinkuna zuƙa zuƙa. *PHEEDY TOILORING DESIGN* ,suna gabatar muku da ɗinkuna kala kala wanda sukayi daidai da zamani.
Zaku samemu a kan wannan layin waya kamar haka
09167130115
Wato a manhajar whatsapp. Domin ganin kalolin samufurin aikinmu kuma ku tuntubemu a INSTAGRAM da kuma TIKTOK a @pheedyxacks_ragtrade
Muna maraba daku a kowanne lokaci🙏🏼🙏🏼🙏🏼🙏🏼🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah 🙏🏼 ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
Ina ƴan mata dakuma Matan aure masu muradin burge mazajensu da ɗinkuna zuƙa zuƙa. *PHEEDY TOILORING DESIGN* ,suna gabatar muku da ɗinkuna kala kala wanda sukayi daidai da zamani.
Zaku samemu a kan wannan layin waya kamar haka
09167130115
Wato a manhajar whatsapp. Domin ganin kalolin samufurin aikinmu kuma ku tuntubemu a INSTAGRAM da kuma TIKTOK a @pheedyxacks_ragtrade
Muna maraba daku a kowanne lokaci🙏🏼🙏🏼🙏🏼🙏🏼🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
*BOOK 2*
...7...
Ina nan zaune a bakin katifa naji alamar shigowar mutum.
Inna ladiyo ce ta dawo hannunta ɗauke da kwanon abinci.
Tashi nayi na karba a hannunta kana na ajiye a tsakar ɗakin.
"Sannu na barki ke kaɗai koh,naje kawo miki abincine,sannan munyi magana da hajiya yanzu.
In kinci abinci kizo zatayi magana dake,ki kula sosai nasan mairo ta fadamiki haka koh?"
Daga mata kai nayi alamar ehh,daga nan ta juya ta fita,zama nayi a gaban kwanon kafin na bude a hankali.
Sakwarace a ciki da miyar ganye,kafin nasaka hannu ma sai ƙamshi takeyi.
Ban bata lokaci ba na saka hannu bayan nayi bismillah na fara zubawa cikina.
Duk yanda naso na cinye malmalar sakwarar guda biyun kasawa nayi,dan ina cin guda ɗaya naji na ƙoshi,ta biyun kada na taba..
Kwanon na tattara wai zan fita dasu,a nan gizo ke saƙar ina zan nufah a wannan tangamemen gidan haka..
Wani mutum na hanga a gefe dani na tambayeshi hanyar kitchen,gyaran wasu fulawowi yakeyi,da alama aikinsa kenan.
"Baiwar Allah ta ina zansan inda hanyar madafa take,wannan ai sai su ladiyo,amma naga sunayin wancan corridor da yayi dama"
Godiya nayi masa daga nan nayi wajen daya faɗamin.
Tafiya nake ina Addu'a a raina har na samu kaina a wajen dana tabbatar madafar ce,duk da bayyimin kama da wanda na saba gani ba. Wannan waje haka ƙato.
Kwanon hannuna na ajiye akan wani tebur dana gani a gabana,har na juya zan fita naji muryar wata matashiya.
"Ke daƙiƙiyar inace dazaki ajiye kwano a wajen da ake yin girki,ko kyauyen cinki bai nuna miki canne wajen wanke wanke ba"
Tafaɗa tana nuna min wani waje mai dan rami da famfo a wajen,wanda ni sai yanzu ma na kulada shi.
Maida kaina nayi kan fuskarta,budurwa ce ko kuma nace ƘARAMAR BAZAWARA(littafin ummu najam amarsisi nayi miki miss).
Domin daga ganinta bazata fini ba.
Wasu kwanuka take jerawa a cikin wardrope,fuskarta a haɗe kaman anyi mata mutuwa.
"Daƙiƙiya? In daƙiƙiya ce ni ashe kekuma kece babbar daƙiƙiyar wacce ta daɗe ma a ciki,domin in ƴan aiki kike ƙira d daƙiƙai to kece babbarsu wacc....."
"Sumaimah ya isa haka,ke kuma Ummi bai kamata kina walaƙanta mutane ba duk sanda kika gansu,ke idan ba mai kuɗi ba to kowa ba kaman ba mutum ba haka yake a wajenki"
Wacce ta ƙira da ummin ta kalla tana yiwa faɗan,ana mata maganar ma tana wani fisfisgewa,wanann daga gani bata da daɗi,in kuwa hakane halinta to batada kirki sam..
"Inna ladiyo wai bakya ganine,ya za'ayi kawai ka kawo kwano ka ajiyeshi a wajen da ake abinci"
"To naji amma dai ai kinsan sabuwar zuwace ko aiki bata fara ba"
"Duk da ai......"
"Kinga ya isa haka,kici gaba da da gyaranki,ke kuma muje na gabatar dake a wajen matar gidan,anyi sa'a ma yau tana gidan"
To nace mata tareda bin bayanta muka fice daga wajen.
Kafaren wani hamshaƙin falo na tsinci kaina a ciki,dama irin wannan gini haka dole mutum yayi tunanin irin kayan alatunnan a cikinsa.
Wata mata ce a zaune akan ɗaya daga cikin kujerun falon,ta saka wani kaya da ban wanne iri bane,amma ko daga gani kasan masu kyaune da tsada.
Abinda yafi bani mamaki shine,meyasa nakejin faɗuwar gaba dana haɗa ido da ita na farko,hmm anya kuwa wannan irin mutanen da mutum zai iya sakewa dasu?.
Tsugunnawa nayi a ƙasa kaman yanda naga inna ladiyo tayi.
"Hajiyah barka da warhaka,g ta nan na kawomiki itah,tazone domin ta samu aiki,da fatan za'a taimaka"
"Hajiyah barka da yamma"
Nima na fada cikin girmamawa,ganin ta kafeni da ido.
Can munyi shuru kaman ruwa ya cinyemu,nida inna ladiyo sai zazzare ido muke.
Jan ajiyar zuciya tayi tareda zare farin glass ɗin dayake idonta.
"Ladiyo banason wani magana yanzunnan,kuma ba kin faɗamin zuwanta ba ɗazu...huhh wancan yaron dama ya dawo gidan,naji waccar tsohuwar nayin mitar kan kan a samu masa wata mai aikin,tunda waccar mun sallameta,kuje ki nuna mata yanda zatayi,in kuma ta kuskure itama ya koreta kaman yanda ya saba toh sai tasan yanda zatayi.
Albashinki dubu ashirin a wata shin yayi miki ko kuwa"
Tun daga ambaton aikin naga ladiyo ta sha ruwan jikinta,koma menene naga da alamar wanda zanyiwa aikin bashida daɗin sha'ani,koma dai menene tunda naji batun dubu ashirin zanyi iya ƙoƙarina wajen ganin nayi nasara.
"Yayimin hajiyah nagode Allah yaƙara buɗi yasa kifi haka"
"Ameen ku tashi ku tafi toh,in wata yayi zanyi miki magana,idan har kina gidan har zuwa lokacin. Sannan kuma karki sake ki nuna masa cewar nina ɗaukeki aiki,kawai kice masa kin fito ne a jerin wacce zatayi masa aiki. Abu na ƙarshe banason ki yaudareni,Sannan ko nan gaba na buƙaci haɗin kanki akan wani abun dole zaki bani"
"Inshaallah hakan bazai gagara ba hajiya,kuma da sannu zanyi yadda kika ce"
____∆∆∆____
Ya yage takardu sunfi guda biyar yana zubarwa,kansa ya kulle ya rasa ma mai zayyi.
Kansa ya riƙe tareda jan gwauron numfashi.
Kwanansa uku kenan da zuwa office amma yagagara yin komai kaman nada,abubuwa da dama sun canja ciki harda tsarin wajen,abun yana cin zuciyarsa ganin duk yanda yakeson aikinsa ya tafi a gaggawa amma abu ya gagara. Duk ƙoƙarin daya dungayi a baya ya tara shaidu duk sun tafi kaman anyi ruwa an ɗauke.
Kansa ya ɗora a kan kujerar yana jinata a hankali idonsa ya rufe.
Yaji alamar buɗe ƙofa wani ya shigo,tun kafin ya bude ido yace.
"Eemran mai Abbah yace,ya bamu izinin binciken wanann gidan?"
"Am sorry sir amma har yanzu ya ƙi saka hannu,a cewarsa wai bai kamata ka fara babban aiki irin wannan ba daga dawowarka"
"Hmmm kaida Neelah ku fara aiki cikin sirri,bazan iya tsayawa da aikinnan ba"
"Amma yallabai akwai hatsari muyi batareda sanin sama ba"
"Hatsari ya wuce wanda nake ciki,kullum hankalina a tashe yake da tunanin a kowanne irin sakanni za'a iya sake farautar rayuwata ba, shin akwai abinda yafi haka hatsari Eemran?"
Duk yanda yake boye damuwarsa tun bayan dawowar tasa,amma kana kallonsa zaka san baƙaramin dauriya yake ba.
"Hakane kam ogah lamarin abin abun a dubane,nida Neelah Inshaallah zamu iya ƙoƙarinmu wajen ganin komai bai sake zuwa da matsala ba.
Wanda suke aikata waɗannan abubuwan da sannu zasu zo hannu.
Hular sa ya ɗauka ya ɗora akan kayan uniform ɗinnasa,wanda suka sake fito da jarumtarsa a fili.
Yau baizo da drivernnasa ba wai mai ɗakinsa ta haihu,dan haka da kansa ya tuƙo bai ɗauki wani drivern ba,domin dukkansu ba yarda yayi dasu ba,yasan duk yaran hajiyah maryam ne.
Buɗe motar yayi zai shiga,tsayawa da shiga motar yayi sanadiyyar wani akwati daya gani a wajen zaman drivern..
Kaishi yayi ɗayan sit ɗin,sai bayan ya zauna kafin ya ɗauko shi ya buɗe..
B'era ne matacce a ciki sai wata wasiƙa da jan ink.
.........kayi hankali da rayuwarka yaro,baka san mai kake shirin tonowa ba,hakan bazai ta'ba kyau ba,domin sakamakon dazaka gani bazai ɗauki ƙwalƙwalrwar ka ba.
Hmmm wato warning ɗin a aka baka a baya bai isheka ba saika sake aikata wani kuskuren?.......
Ninke ta kardar yayi tareda sakata a aljihunsa,yayinda bandir ɗin kuma ya jefashi ta windown motar,ƴar ƙaramar tsuka yaka yana cije ƙasan bakinsa,ganin bata lokacin zayyi yawa yasa yaja motarsa zuwa gida. Wanda baya ganinsa a matsayin gidan kaman yanda wasu ke gani,dan ɗaukar wajen yake tamkar inda duk jagayen dakayi zaka dawo ka kwana da makashinka a ciki..
A hankali yake jan motar yana bin karatun dayake tashi a cikin motar har ya isa gida..
Bai samu kowa a babban falon gidan ba,wanda daman hakan yakeso,in badan Abbah ya hanashi yin amfani da ƙofar bayansa ba da babu wanda zai dunga ganinsa ma saita kama dole.
Buɗe ƙofar shiga sashennasa yayi ya shiga,an sanja masa ajiyar fulawar da take kusa da window,wanda daman yana zuci zucin ya kaita kusada rana ya manta..
Sannan an goge ko ina a falon ƙal ƙal sai ɗaukar ido yakeyi,duk da yanda yaɗebo gajiya da tashin hankali amma gyaan ya burgeshi matuƙa.
Ɗakinnasa ya nufah da hularsa a hannu.
Jefata yayi akan gado,wanda aka sanja zanin gadon ba na ɗazu bane akai.
Rigar jikinsa ya cire harda singlet ɗin,domin dama ya saba duk lokacin daya dawo sai yayi wanka tukunna ya wanke gajiyar jikinsa.
Bai shiga banɗakin ba tukunna sai ya tsaya yana aikinnasa na kullum wato tunani.
.........
Tunda naji batun biyana 20k a wata wani ƙaimi na nayin aiki yanda ya dace ya tashimin.
Bin inna ladiyo na dungayi akan tafaɗamin yanda aikin yake.
Anan nakejin wanda zanyi wa aikin shine ɗa na fari a gidan,mahaifiyar sa bata nan,sannan ance ya mutu a hatsarin mota tsawon shekaru,sai yanzu ya dawo.
Ba wannan na maida hankali akai ba saina halayensa da aka sanar dani.
Bayason mutane sosai, dan haka duk wacce zatayi masa aiki to
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4 Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21