ga salary ɗin ki ba. Ko yake shima wannan mijinnaki da nice da tuni ai munyi wacce zamuyi,na taho aikatau domin mu rufawa kanmu asiri,amma shine hakan bai isheka ba ka biyoni kayimin ciki ka haɗani da wahala,inama zan ganshi da sai na tsayar masa"
"Hhhhh ummi kinada abin dariyah,zaki iya tsayar masa idan na hadakun?"
"Ehh mana bari ki gani Allah ya kaimu"
Murmushi nayi batareda nasake cewa komai ba na saka hannuna a abinci.
Muna gamawa na kishingiɗa domin na kwanta na huta.




*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)


Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150

Bismillahir-rahmanir-raheem


Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.


*BOOK 2*
...30...



A jirgi ɗaya Musbahu suka taho shida Ahmad,zaibi normal jirgi ya hanashi akan zasu taho tare. Don a dan wannan wata ukun da sukayi sunyi sabo sosai,wanda duk sanadin labarin Matar sa ne.
Bayan sun sauƙa kowa jawo jakarsa yayi suka fito.
"Toh general ni daga nan zan hau motar gida"
"Ahhh habadai,kazo muje gida mana ayi ka huta in yaso gobe saika wuce,sannan ya zancen .......dakace zaka haɗani da itah,gashi numberta tunda ka bani kullum saina gwada amma ban sameta ba"
"Shiyasa nakeson tafiya gida ai general,saboda nasan inna tasan inda take zata bani address ɗinta. Sannan karka damu na gode da dukkan halaccinka,inna dawo nayi maka alƙawarin zanzo har gida,saimu je inda take tare."
"Yaushe zaka dawo,nan da sati biyu za'ayi bikin nasararku"
"Eh kafin lokacin zan dawo Inshaallah"
Sai bayan da Musbahu ya shiga motar garinsu kafin driver yazo ɗaukar Ahmad zuwa gida.
Sashensa ya wuce direct ta ƙofar baya,dan tun abinda ya faru yakejin kamar shida ƴan gidan basu hada wani jini na azo a gani ba. Mahaifinsa ne ɗan uwansu to baya raye,dangin mahaifiyar sa kuma na can wani gari daban,daɗin daɗawa kuma basa Ga maciji da su.
Ɗan tsayawa yayi daga bakin ƙofa yana kallon yanda aka gyara ɗakin,Sumaimah ce ta faɗo masa a rai,yasan babu mai wannan aikin sai itah.
Ɗaki ya wuce ya ajiye jakarsa ya watsa ruwa.
Falon ya fito yana dadanna waya,daga idon da zayyi suka haɗa ido da saleem,wanda yake hakimce akan kujera yana kallon yayannasa.
Hade ido yayi ya kafeshi dasu kaman shine babba,abin ba ƙaramin mamaki yabawa Ahmad ba.
"Kaikuma fah ya haka'
"Dole ka tambaya mana yah Ahmad,yanzu baka gidannan tsawon wata uku ka dawo amma ka wuto sashenka kawai,ƴan cikin gida nacan suna zancen"
"To so what suyi maganar ma,dama sun damu dani ne,kaima in zancen dazakamin kenan to kama hanyarka kayi waje"
Jijjiga kai Saleem yayi tareda jan numfashi,yana son yayannasa kuma wani lokacin baya ganin laifinsa,yanayine yasakashi zama hakan.
Wajen dining ya nufah ya buɗe kulolin,ƙamshin abincine ya bugeshi saida ya lumshe ido.
Zama yayi ya zuba abincin yaci yayi nak,ko ci kanka baicewa Saleem ba,yayinda shikuma ya zuba masa ido yana cin abincin kaman ya samu tv.
"Hmmm kana cewa ba ruwanka da yan aiki gashinan kuma kazo ka ci abincin mai aikin gidan.
Ni inaga ƙoƙarinta ma,da ciki tayi maka wani gyaran sashe da kuma abinci,saikace mijinta"
Yana cikin goge bakinsa ya cakk jin abinda Saleem yafaɗa,ciki ciki kuma wanne iri .
"Saleem mai kake cewa cikine da wa?"
"Sumaimah mana mai aikinka,ohh da kanace budurwace,naga dama ka fara nuna kishi akanta,tun wuri gwanda ka bari,naji an ce cikine da itah,mijinta yazo ganinta sai gata da ciki,lallai wannan miji ya iya bugu sosai"
Wani zimmm kan Ahmad yayi,a ransa yana ta maimaita Allah yasa dagaske na mijinnata ne bashine ba.
Gumin daya keto masa ya goge tareda cewa,
"Cikinnata zaikai kaman ya"
"Oho nina sani,naji dai ana cewa yayi babba kawai"
Duk da abinda Saleem ya faɗamasa hankalin sa bai kwanta ba.
Wayarsa ya ɗauko ta gida wanda takeda layinsa na nigeria..
Ƙiranta ya farayi amma shuru bata shiga,haka har ya Haƙura don kansa.
Faɗawa yayi zurfin tunani Gabaɗaya ya gagara barwa kansa cikin jikinta ba nasane,kai yasan ma nasane.
Hannun Saleem yagani yana yawo akan fuskarsa,hakanne yasakashi firgit ya dawo hankalin sa.
Tashi yayi zaune yayi hanyar ƙofar dazata shigar dashi cikin gidan.
"Ina kuma zakaje ogah ta wannan ƙofar?"
"Zan shiga na gaisar da mutanen gidanne sarkin tambaya"
Sakin baki yayi saida yaga ya shige kafin yabi bayansa,a bangarensa kuwa don ya haɗu da Sumaimah zai shiga.
Ba kowa a babban falon gidan sai Sameer wanda yabada hankalin sa gabaɗaya kan wayar hannunsa..
Jin shigowar mutum yasa ya ɗaga kansa,yana ganin Ahmad ne ya cigaba da harkar gabansa.
"Don kana zargina meyasa bazaka zo gaba da gaba ka tuhumeni akai ba,saika dunga binciken hakan a bayan fage?"
Ajiye wayar Sameer yayi jin topic ɗin da Ahmad ya ɗauko.
"Hmm menene abin zuwa gabanka na faɗamaka,bayan nasan bazaka fadamin gaskiya ba.
"Taya zan faɗamaka gaskiya bayan nima a lokacin bansan ta ba? Zarginka gaskiya ne amma ba yanda kake tunani bane. Nine wanda mukayi faɗa dakai harka cakamin wuƙa"
Yafaɗa yana ƙarisa maganar tareda buɗe masa gefen cikinsa.
Zaro ido Sameer yayi,yayinda fuskarsa ta nuna rashin jin ɗaɗin yanda yayi masa raunin,amma shima ai ya dukashi sosai.
Shuru sukayi babu mai cewa komai,sai can kafin Ahmad yace.
"In kanada kokwanto ka daina kawai gaba,ka tunkareni dashi"
Yana gama faɗin hakan yayi masa ɗan Murmushin kwarewa.
Duk maganar da suke Sumaimah na jinsu,wacce take tsaye cak tayi suman wucin gadi,jikinta rawa yake wanda ta ɗauki tiren,kaddai Ahmad ya tuna rayuwarsa ta goje,in kuwa hakane to zai ganeta tana shiga.
Har ta juya zata koma taji muryar Sameer.
"Yadai naga kin tsaya kuma zaki koma,ko kin manta wani abune,sauri nake fah zan fita"
Shigowa tayi kanta a ƙasa,ta gefen ido tana kallon Ahmad wanda ya tashi zai fita daga falon,da alama bai san zata shigo,saidai tunda ya riga ya tashi kawai ya fice.
Yazo giftawa ta gefenta tayi ƙamshin turaren datake shaƙa kafin tayi bacci a jikinsa,wannan har yafi wancar shigarta,nutsuwa da kasala ya sauƙar mata a lokaci guda,har bata san lokacin data ja dogon numfashi ba.
Sai bayan ya wuce ta dawo hankalin ta kafin ta kulada Sameer wanda yake binta da kallon mamaki.
"Yadai naga kin tsaya ido rufe kaman mai addu'ar kirista,idan bakya jin daɗi waye yace kiyi aiki?"
Bata bashi amsa ba sai ajiye masa abincin da tayi ta fita,gaba ɗaya tunda yanxu sun gane tana aure kuma harda cikin basa yin maganar da sukeyi da,kuma ma cikin ya maidata marar magana,ga yawan gajiya.
Bayan ta fito daga falon har zata wuce taga Ahmad tsaye a bakin shiga sashensa,diriricewa tayi zata yi hanyar kitchen da sauri,sai kuma taji muryasa.
"Kizo yanzu ina son magana dake"
Daga haka ya shige ciki. Ajiyar zuciya tasake tana bin ƙofar da kallon. Banda sunan Allah babu abinda take ambata.
Tiren ta mayar kitchen kafin ta dawo zuwa sashennasa,zuciyarta cikeda zullumin yanda zasu ƙare,tasan dole yaji labarin cikinta kokuma ma yagani da idonsa.
Tura ƙofar falon tayi ta shiga,yana zaune akan kujera yana kallo,amma daga gani kasan hankalin sa baya kan kallon.
Ɗauke idonsa yayi daga kan tv ya mayar kanta,tasan bakomai yake dubawa ba sai yanda ta sauya sosai. Duk da hijabine a jikinta amma dole a gane hakan.
Saida tazo kusada shi kafin ta zauna a tsakiyar falon tana kallon tiles..
Takai minti biyar a haka kafin ta ɗago,desame ita yake kallo har zuwa lokacin. Saida suka haɗa ido kafin yayi magana..
"Shin ban cancanci kimin bayani ba,cikin waye a jikinki. Ni kokuma mijinki? Karki bani amsar daba haka ba,domin idan kika boyemin dole zan gano gaskiya domin zanyi binciken mijinnaki a garinku nagano hakane koba hakane ba. Dan haka ki amsa min *cikin waye?*?"
Shuru Sumaimah tayi bata bashi amsa ba,banda rawa da jikinta yake ba komai..saboda yanda yake kausasa mata murya.
"Na mijinki ne?"
Ɗaga masa kai tayi
"Na wane?"
Nan ma ɗaga masa kai tayi,daka mata tsawa tayi kagin tana bashi amsa guda biyu.
"Ki bani amsa da bakinki cikin waye a jikinki"
A yanzun bude bakinta tayi tareda cewa.
"Cikinka nehhhh"
Runtse ido yayi tareda komawa jikin kujerar ya lafe,shidama hakan yayi tunani,yasan babu wani mijinta,tayi hakanne domin ta boye,kuma hakan yayi domin zai ara masa lokacin mai ya kamata yayi.
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un"
Shine abinda yake ta maimaitawa idonsa rufe..
Kallonsa Sumaimah tayi tareda fara hawaye tana jijjiga kai.
"Cikin shege dashi zan fara ajiye jinina a gidanmu,da wanne ido zan kalli mutane kenan,shin ke kanki mai zancemiki bare mijinki *KAICO NAH* (littafina na huɗu,wanda ya tara ɗumin darasi kenan mai yamin magana).
Da wannan zunubi da kuma ɗanyen aiki dana aikata,shi kanshi ɗan na cuce shi na..........."
"Ya isa haka"
Shine abinda Sumaimah ta faɗa da ƙarfi tareda ƙara sautin kukan ta.
"Kada kasake faɗin hakan akanka da kuma ɗan cikina,domin dukkanku baku cancanci wannan bayaninnaka ba sam,idan laifine ma nice mai laifin kuma na ɗauka,sannan ciki dama ban dangantaka dashi ba,duk da cewa kaine mafi kusantuwar dashi.
Duk abinda kakeji akansa kanada damar kaji,amma na roƙeka kada kasake furtamin wannan kalmar. Ka ɗauka tamkar wannan abin bai faru ba,ta hakanne zaka manta dashi ka koma tamkar yanda kake. Sannan yanda kake daukan abubuwan ba haka suke ba.
Zan dawo aiki gobe,saidai bazan dunga shigowa ba sai ka fita,haka kafin ka dawo bazaka ganni ba,ba'a samu wata mai aikin ba shiyasa,kafin a samu zan dena."
Tana gama faɗin hakan ta miƙe daga zaunen da take tana goge hawayen fuskarta,harta kai bakin ƙofah taji maganar sa a cikin dashashshiyar murya.
"Watansa uku kenan"
"Eh"
"Lafiya kike"
"Eh"
Kici gaba da jira amma dolene zan ɗau mataki akai,zan nemi mijinki akan maganar,dolene na karbi hukuncin abinda na aikata,abin yayi muni dayawa"
Wannan karon Sumaimah bata bashi amsa ba ta fita,tana jin yanda muryarsa ta karye tayi raunin ba ƙaramin tausayinsu take ji ba a wannnan alaƙar,daga itah har shi......
Fatanta Allah ya bata lafiyar cigaba da kulada jaririnnasu,Sannan kuma yabata da sauƙi.
Ɗazun bataso faɗa masa cikinsa bane,gudun kada yayi bincike ya gano komai ne yasa ta amsa masa da eh ɗin.







*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)


Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150

Bismillahir-rahmanir-raheem


Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.


*BOOK 2*
...31...




Anyi sati guda da Ahmad ya gane cewar Sumaimah tanada cikinshi,kuma har zuwa yanzun hankalin sa bai kwanta ba,har mafarki yake mijinta yasaka masa wuƙa a wuyah,abinda yake bashi mamaki kuma mijinnata kamarsu ɗaya dashi,saidai yana zuwa masane a salo na daba.
Yau ma tun Dare abinda ya kwana yanayi kenan,da asuba bai koma bacci ba,karatun qur'ani yayi tareda neman gafarar Allah bisa wannan dumbin zunubi nasa.
Da wuri ya fita daga gidan, gabaɗaya abubuwa sun isheshi.
Lokacin dayaje office babu kowa a headquarter sai masu shara da gyare gyare,aikin dayake kansa ya dauka ya fara,ko zai rage abinda yake cikin ransa.
Wajen misalin ƙarfe sha biyu yaga kira a wayarsa,sunan Musbahu yagani,dama yana expecting kirannasa tun jiyah amma shuru.
Yana ɗagawa sallama sukayi yace masa.
"Yah Musbahu naƙira ka baka ɗaga ba,gobene fah za'ayi bikin baku matsayin"
"Oga wanann yayan da kake ƙirana dashi na kasa sabawa dashi,gani fah a ƙofar headquater bansan office ɗin ka ba"
"Okay ka tsaya ganinan zuwa yanzu"
Ajiye aikin dayake yayi ya fita daga office ɗin,binsa wani squad na ma'aikata sukayi,dama yana ciki,babu wanda yaga ya fito tunda suka zo.
Da sauri sauri ya fita harabar wajen,daga nesa ya hango Musbahu a tsaye wajen da ake parking motoci.
Tun daga nesa daya ganshi ya taho daga wajen suka yi gaisuwar musabaha.
"Barkanka da zuwa muƙarisa"
"Lahh ogah da basai ka shigo bama,in ka yimin kwatance ma zanzo"
"Ahah karka damu ƙarisa,bayan abinda yake tsakaninmu inayi maka kallon aminina ne"
Tafiya suke suna tattaunawa har suka isa,ruwan sanyi yabashi don shine abinda yakeda shi a office ɗin.
"Ga ruwa kasha hanya,barina ƙarisa wannan saimu tafi gida kaci abinci"
"Zan sha ruwan dai abinci kam daka barshi,dan har nayi booking na hotel,muna gaisawa zanje na sauya kaya sai mu haɗu. Har yanzu ina kiran wayar ta ma baya shiga,bansan meyasa ba. Hmmm inaga akwai matsala........."
Jim Musbahu yayi daya faɗi hakan,wanda hakan yasa Ahmad bashi dukkan nutsuwar sa donjin wacce matsala ce.
"Basa garin,daga innan da Deejah dakuma Sayyid,na tambayi matar gidan kuma tana cemin wata baƙar motace tazo ta daukesu wancan watan zuwa nan abuja,bansan waye ba ,amma jikina na bani ko gidan da Sumaimah take aikine"
"Amma kana gani wanne wajene haka,mai ya faru dukka suka tafi gabaɗaya,basusan inda suke ba address ɗinsu?"
Cikeda damuwa Ahmad yake tambayar,gaba ɗaya hankalinsa ya tashi. Ji yake duk laifinsa ne dabai nemeta ba,gashi har ta shiga duniya neman aikatau saboda rashin abinyi.
Rarrashinsa Musbahu ya fara yi ganin yanda hankalin sa ya tashi,don yasan kansa yake ɗorawa duk laifin abinda ya faru. Shikansa ba ƙaramin tausaya masa yayi ba,ace ka yi rayuwa da mata harta haihu amma baka sani ba,to amma meyasa ya kasa tunawa.
Shine wasi wasin da Musbahu yakeyi,wanda shima Ahmad yayi irinnasa.
Sun dade suna zance duk akan matar tasane,saikuma wanda yake damunsa aransa na Sumaimah.
"Bakomai Musbahu karka damu,Inshaallah Allah zai bayyana su. Yanzu dai muje gida tukunna daganan sai mu wuce gidan tv bada information ɗinsu,da kuma radio,maybe idan sunji ko wani yasansu ya ƙira. Ga matsalar babu hotunansu."
A motar Ahmad suka fita daga headquater zuwa gidansu.
Direnct sashensa ya wuce dashi basu shiga cikin gidan ba.
Shidai Musbahu binsa yakeyi a baya,don ya damune ma yabiyoshi,sannan shima yana da buƙatar son ganinsu,musamman Deejah wacce yakejin kaman nauyin kulada itah a kansa yake.
A falo yamasa iso ya zauna,motsin mutum yaji a kitchen,sannan kuma babu abinci a dinning,sai sannan ya tuna ya rage awa guda hadda rabi akan lokacin dawowarsa,ajiyar zuciya yayi yasan abinci take,koba komai zata fiddashi kunya,da har yayi niyyar kuwa hanata yi masa aiki,yanzu ma daga ya samu matarsa sai Yanda zayyi da case ɗinta.
Kitchen ɗin a yashiga ya sameta a kan stool tana wanke kwanukan da tayi amfani dasu,a gefe kuma ta jera kayan abincin a kan tire,da alama tagama gyara wajen take kafin ta tafi.
Aikinta take a hankali ko kuladashi batayi ba,hakanne yabashi damar ƙare mata kallo,tayi fari tayi ƙiba fiyeda da,wanda kuma yasan cikinne ya sakata,don gashinan yafito a jikinta,dayake doguwar rigace a jikinta,kuma ta fara kamata saboda cikin.
Kyau tayi masa a hakan,inaga matarsa take masa wannan hidimar da cikinsa a jikinta. Inama matar dayake ta nema ce. Wani runtse ido yayi tareda jijjiga kai,ahah wannan matar wani ce wanda yaci amana.
Tabon dayake zuciyarsa na abinda ya aikata ne ya dawo sabo.
Jinginar dayayi a jikin ƙofar kitchen ɗinne yasaka ƙofar yin ƙara,wanda kuma ya ankarar da Sumaimah wacce kanta yake sunkuye,kallonsa take da alamar mai ya dawo dashi a lokacin.
Lokaci guda ya tsime tareda yin gyaran murya.
"Nayi baƙo ne mun dawo dashi,zan ɗauki cup ne na shan ruwa,sannan idan kin gama abincin ki kawo shima yanzu"
Yana gama faɗin hakan ya ɗauki cup biyu a inda ta jera ya fita,itadai da kallo kawai tabishi tareda tabe baki.
Gabaɗaya ya dagula mata lissafi da ƙamshin jikinsa,wanda yake rikitata,aman da take ji ɗazu ma yakoma.
Bayan ya fita cigaba tayi da wanke wankenta,saida ta gama kana ta ɗau kwanukan abincin da saka su plate da komai zata kai musu.
Lokacin data shiga da Ahmad suka haɗa ido,saboda shine yake facing kitchen ɗin,shikuma baƙonnasa ya bawa kitchen ɗin baya,magana taji sunayi akan yaɗa labarinta ko za'a sameta,har zuwa taje ta ajiye kayan abincin akan dining table, juyowar da tayi zata tafine idonta ya sauƙa akan Musbahu,yayinda shima itan ya kalla a lokacin daidai yakai gorar ruwa bakinsa.
Dawowa yayi dashi da sauri tareda zare ido.
"Sumaimah!!!!"
"Yah Musbahu"
Itama ta faɗa cikeda mamakin ganinsa a nan ɗin.
Ahmad ne ya kalleshi tareda cewa.
"Kasanta ne?"
"Itace fahh dama kuna tarene tuntuni?"
"Itace wa,muna tareda itah a ina?"
"Mai kake nufi,bakasan wacece ba,ko aljana ce kai ni kaɗai nake ganinta,Sumaimah ce fah matarka wacce ka bari ka tafi. Itace muke nema"
Da wani mungun sauri Ahmad ya kalleta a razane,ganin kallon dayayi matane yasakata sauƙe idonta,wani kuka ne da batasan na menene ba ya kufce mata,dama abinka da yanayinta ya koma na kukan.
Zuba mata ido sukayi dukka ganin yanda take ta kuka kaman an daketa.
Musbahu ne yayi ta mazan yi mata magana.
"Mai aka miki kuma kika fara kuka,zo nan ki faɗamin mai yake faruwa"
Takawa ta farayi kaman wacce ƙwai ya fashewa a ciki,ta gaban Ahmad ta wuce zuwa inda Musbahu yake,shidai binta yayi da kallo kaman ya samu tv. Tun daga tambayar ko kwaƙwƙwaran motsi bai ƙara ba.
"Miye ya faru da wayarki nayi ta ƙiranki bata shiga,ya akayi kike zaune da mijinki amma bai san ke bace,yana can yana nemanki. Ina kuma su inna suke,domin dana koma gida an ce suna garinnan?"
"Uhm uhm wayar ta baci banda wata kuma,su inna kuma suna gidan Hajiyah Shukurah ƙanwar hajiyah Maryam. Ta ɗauki inna ne aiki,kawu audu ne ya koresu bayan tafiyarsa (tafaɗa tana kallon Ahmad kafin ta ɗauke idonta). Tunda wai dama wajen ya zama nasa. Ina baba yake dasu Ammi?"
"Baki ƙarasa bani amsata ba Sumaimah,meyasa dakika haɗu da mijinki baki faɗamasa ke wacece ba,ko rashin ganeki da yayi ne yasa kika ƙullaceshi akan sai sanda ya sani da kansa?"
Jijjiga kai tayi da sauri tareda cewa.
"Ahah ba haka bane,ba a son raina naƙi faɗamasa ba,saidan yazama dolen,mutanen da suka yi sanadiyyar zamansa a goje suna tareda shi,idan suka sanni wacece bazasu ƙyaleni na dakuma shi,shiyasa ban faɗamasa ba"
"Mut......."
"Dan Allah kada ka tambayeni dalili yah Musbahu,inasu baba da ammi baka faɗamin ya suke ba.......baka ga Deejah ba tayi hankali kaman ba itah ba"
Tayi hakane domin ta kawar da maganar ɗazun,duk da tasan hakan bazayyi yu ba.
Ganin kallon da Ahmad yake yiwa Sumaimah mai cikeda abubuwa da dama yasa Musbahu cewa..
"Suna nan ƙalau,yanzu dai bani address ɗin inda su inna suke,ni yanzu zan tafi,kina buƙatar yin magana dashi"
Jimm tayi jin abinda yace,amma haka ta bashi ba yanda zatayi.
Kitchen ta koma tanajin fitarsu shida Ahmad ɗin.
Hannu ta ɗora akan zuciyarta wacce take bugawa fatt fatt.
A bangaren Ahmad kuwa da Musbahu yace zai tafi kasa hanashi yayi,domin a yanzu burinsa ɗaya shine jin bayani daga bakin Sumaimah,na akan me ta ƙi faɗamasa matsayinta a wajensa.
Ganin har suna shirin rabuwa Ahmad baice komai ba yasa Musbahu cewa.
"To ni zan tafi gen. Ga yanda abu ya kasance,amma ni abinda nake gani ka bita a sannu ta faɗamaka mai yake faruwa,ni kaina shaidane akan irin son da take maka a lokacin baya,bata haɗaka da komai,duk da mutane suna jin tsonka amma kaine wanda take burin komawa gareshi idan tayi nisa dashi"
Da kalamai masu dadi cikin hikima ya taushi Ahmad kafin ya tafi ya barshi,yana musu fatan shiryawa mai ɗorewa.
Kaman jira yake yana tafiyah ya koma sashennasa,bai sameta a falon ba,har yaji babu daɗi kaddai tafiya tayi,sai kuma ya gano ƙofar kitchen a buɗe.
A kaban kitchen table ɗin take tsaye tana kallon window,ta bawa ƙofar baya.
"Can you explain your
Showing 48001 words to 51000 words out of 62659 words