gidannan ta wannan da'rar mai samun nasara akanki idan baki kawarta ba, Sannan kuma itama jinin gidannan ce"
"Me.....me kike faɗi Matiful duluk. ......wacce matar kenan badai matar Ahmad ba danake nema ruwa a jallo,dama tana gidannan ne? Kuma jinin gidannan ce ta yaya kenan?"
"Hhhhhh aiki ya ganki uwar gijiyar Harsheelah,dolene ki dage in kinason cigaba da aiki da dodo,idan ba haka ba ƙarshenki ne kema yazo kamar yanda na wanda suka wanzu kafinki ya wuce"
Ganin sun fara mata dariyar ƙeta ne yasa ta kawar da ƙoƙon ,domin bashine a gabanta ba yanzu.
"Kultum ƙiramin Mulaifah inason in tambayeta,nasan dole tasan wanda ya shigo ɗakina tunda har ya samu makullina"
"Amma hajiyah da alama tayi shaye shaye yauma,ba lallai tah.........."
"Ban tambayeki yin ja'inja dani ba,babu ruwana da shaye shayenta,inta kama zan zaqulo duk abinda ke cikinta ciki kuwa harda shegen ɗan da ya baje koli a mahaifarta idan zan samu amsata. Mtsw matsama kiga naje da kaina"
Bangaje Kultum tayi ta nufi ɗakin Mulaifah,tana kwance tayi ɗaɗɗayah,ko takalminta bata cire ba.
Hajiyah Mammah na zuwa ta nuna hancinta wani hayaƙi ya fita,aikuwa cikin firgici Mulaifah ta tashi ta zauna tana sosa hanci da atishawa.
"Maza faɗamin wa kika faɗawa inda key ɗin ɗakina yake?"
Ganin wacce take gabanta kamar kakar tata amma kuma tafita yarinta yasa ta murza ido.
"Mtsw saida Sport G yacemin dama zanga abinda hankalina bazai ɗauka ba,amma hadda zafi a hanci kaiii"
"Dallah ki ware kokuma namiki abinda yafi na hanci,don tsabar rashin sanin daidai kinada ciki kike shaye shaye koh,in kika mutu ai ke kika sani,na rasa uwarki ma ballantana ke. Ki faɗamin akan shashancinki wa kika bawa bayani ya shiga ɗakina?"
"Uhm na'am ni.....bansani ba iya kawai gyara tace zata miki na kaya shiyasa nace ta shiga amma ni baruwana. Saboda ta gama miki da wuri har na bata fitila. Saboda kullum kina cewa na zama mai kirki"
"Wacece itah baki santa bane?"
"Nasanta mana,wai granny mai ya shiga kankine,na ganki ma kaman wata sa'a ta fahhhh"
Wani wawan hawa hajiyah Mammah tayiwa gadon Mulaifah tareda cafkar wuyanta.
"Faɗamin wacece ita,kokuma na ƙarisaki yanzunnan,matacciyah kawai"
"Wayyo Sumaimah,Sumaimah cefah mai laifina danna barta tashiga ɗakinki,naga dai tanayimiki aiki sosai"
Sakin wuyan Sumaimah hajiyah Mammah tayi tareda daskarewa a wajen,meyasa ma bata taba zarginta ba duk zamanta a gidan. Kenan.......kenan......mijinnata wato Ahmad ne,kenan itace matarsa daya aura a rayuwarsa ta shekara biyar.......jinin mace mai ciki Matiful duluk ya faɗa,kuma tanada ciki.....kenan tasan mai nake ƙulllawa tsawon wannan lokacin,kallon ayaba kawai takeyi mata.
Wata dariyar takaici hajiyah Mammah tasaki lokaci ɗaya kuma ta haɗe rai ƙaman hadarin marka marka mai shirin zubar da ruwa........
SADI-SAKHNA ce
09035784150
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
*BOOK 2*
...36...
Bayan ta dawo daga sashen hajiyah Mammah banɗaki ta wuce,anan taga ciwon dataji da kwalbar data fashe,tafin kafarta ne ta dama ya tsage,
Wankewa tayi ta ɗaure wajen kafin tazo ta kwanta,ɗaya kwalbar kuma dagata tayi tana kallonta.
"Ko itama na fasata kaman yanda ɗayar ta fashe kai?. Ahah idan na fasata kuma wani abun ya shafeni fah?"
Ruwa ta tara a cikin roba ta karanta ayoyin karya sihiri a ciki,bude kwalbar tayi ta juye ruwan a ciki ta rufe.
"Bansani ba kozai karya abinda yake ciki ko ahah,amma Allah ina roqonka Allah yasa yayi aiki"
Ajiyewa kwalbar tayi a cikin kayanta kafin ta kwanta.
Bayan ta kwanta ta daɗe bacci bai ɗauketa ba,shin abinda tayi daidaine kokuma saka kanta tayi a haɗari.
Rufe idonta keda wuyah taji wata iska ta zagayeta,da guguwa ta taho amma ƙarfinta ya ragu kafin ta iso gareta, tana gudu haka ta ɗauketa zuwa wani waje mai duhu.
Buɗe idanunta tayi daga mafarkin,saidai sabanin ɗakinsu a wani waje ta tsinci kanta mai matuƙar duhu,dagane ba ɗakinsu bane saboda jin tana kwancene rairayi.
Hannunta takai kan cikinta,yana nan babu abinda ya sameshi. Tasbihi da fara da salati duk wanda ya samu zuwa bakinta.
A haka tana wannan halin har haske yafara fitowa da gabas. Tunda ta tsinci kanta a wajen take zaune bata motsaba har zuwa wannan lokacin.
Motsin takun mutum tajiyo yana zuwa,ɗauke numfashinta tayi har zuwa lokacin da aka dalleta da wani abu mai haske.
"Hmmm wai dama kece ashe? Kinyi wasanki yanda ya dace,amma bari kiga naki ƙarshen yanzunnan"
Kultum ce take maganar cikeda jin haushin Sumaimah.
Jin wanda yake magana maimakon taji tsoro sai maida martani da tayi.
"Kinyi mamaki ne da kikaganice,zatonku ku kaɗai kuka iya shiri,komin ƙanƙantar allura ƙarfece,dan haka ba abar rainawa bace kuma akan iyalina babu abinda bazanyi ba. Ganin baku kasheni ba duk da kunsan ni wacece to aikin danayi a sashennata ita shugabar taki yayi mata illah sosai koh?"
Wani mari Kultum ta bawa Sumaimah mai ƙarfi.
"Hmmmm zatonki dan kinyi wannan ke wata shegiya ce,jira tazo tasameki kiga yanda zata gama da ahalin da kike komai dominsun. Ke kuma zakiga baƙar wahalar da zaki sha kafin mutuwarki"
Dunƙule hannunta tayi tareda faɗin wata kalma,nan da nan wani tururi ya kunnu a dukkan ilahirin jikin Sumaimah,tana jin zafin kuwa ta fasa wani ihu mai cikeda ban tausayi.
A asibiti kuwa hajiyah Mammah na tafiyah Ahmad ya shigo asibitin.
Anan suka kwana a wajen hajiyah Maryam ɗin har gari ya waye.
Har zuwa lokacin hajiyah Maryam bata tashiba,sai kace matacciyah haka take. Ƙarfin allurar ya ƙare yaci ta tashi amma har yanzu shuru. A.M Aliyu ne ya kwana a kujerar da take gabanta,iyah dare ɗaya amma damuwar da take fuskarsa bazata misaltu ba.
Su Sameer Ahmad da Maimuna suna tsaye a gefe guda,babu mai cewa komai kowa da abinda yake sakawa.
Sallama akayi a ƙofar shigowa ɗakin,Saleem ne ɗauke da kayan karyawa,sai kuma su inna larai itada Hajiya Shukurah.
Gaishe gaishe akayi na kwanan mai jiki.
"Gashi wannan inji inna ladiyo wai na Sumaimah ne,itace mai san ɗanwake"
Ya faɗa yana ajiye wata ƙaramar coolar a gefe.
"Sumaimah kuma,jiya fah yah Ahmad ya maidata gida,ko ba gida ka mayarta ba kai?"
Fatee ta faɗa cikeda mamaki tana kallon Ahmad.
Shima da mamakin yace.
"Gida na mayar ta mana,saida ta shiga ma kafin na wuce"
"Eh ta koma gida,amma inna ladiyo tace wai bayan sun gama fira sun kwanta,data tashi ƙarfe biyun dare bata kanta ba. Tayi zaton ko tana wajenka shiyasa bata nemeta ba"
"Nida ban kwana a gidaba taya za'ace tana wajena,Sannan side ɗina ma a kulle yake,kuma batada key ɗin wajen yanzu. To ina taje kenan?"
Ahmad yayi tambayar a razane.
Kowa hankalin sa ne yadawo kan wannan sabon lamarin,kafin kace me Ahmad yafice da gudu daga ɗakin.
Saleem ne yabi bayansa suke tada mota zuwa gidan.
A ƙanƙanin lokaci suka isa,tareda security na gidan aka shiga nemanta,amma babu ita babu labarin ta a gidan.
Don ba kowa a gidan daga su inna ladiyo itada ummi sai kuma hajiyah Mammah wacce a cewarta ta kwana batada lafiya ciwon zuciyarta ya tashi.
Wasa wasa har dare babu Sumaimah babu alamarta,ga hajiyah Maryam ma har yanxu bata motsi,saidai ta buɗe idonta tana kallon sama kawai,daga haka babu abinda takeyi.
Yanda sukaga rana haka suka dare aka waye,kowa in ka ganshi kaman ya tashi a jinya saboda tashin hankali.
Ganin sun raba kansu a asibiti da kuma gida ga ciwon hajiyah Maryam an tabbatar musu bana asibiti bane,hakan yasa suka dawo da ita gida aka malamin da zai mata na islamic. Suna dawowa gidan da safe sai gashi yazo,yasha manyan kayansa wai hajiyah Mammah ce tayi masa Magana akan zai fara mata magani.
Maimuna ce da Fatee kawai a gidan saisu inna,sauran mazan dukka basanan suna wajen case ɗin neman Sumaimah,wanda aka watsa a media ma amma har yanzu babu takaimaiman labarin ta..
A zaune yake ya zurawa waje ɗaya ido,bai taba sanin haka take a cikin ransa ba sai yanzu,bai san wanne irin so mai zurfi yake mata ba sai yanzun,gaba ɗaya nutsuwarsa bata tareda shi saboda batannata.
Wayarsa ya ɗauka ya danna ƙiran Maimuna,don itace mai kulada hajiyah Maryam ɗin.
"Hello y kuke ya jikinnata,ta farka ne?"
"Ahah bata farka ba har yanxu,mai maganin da aka turo ma yazo ya fara yimata"
"Waye kuma ya turo mai magani?"
"Hajiyah Mammah ce mana,dama tun a asibiti da Likitoci suka ce ayi na gida tace zata nemo mai magani"
"What mai magani daga wajenta,ganinan zuwa yanxunnan,zan taho da mai maganin,munyi magana dama dashi. Ki tabbatar baki bar mutuminnan shikaɗai da ita ba,Sannan kada ki kuskura ki bari ya tabata har sai nazo tukunna"
Cikeda mamaki ta amsa masa da toh.
Yana kashe wayarsa ya ɗau key ɗin motarsa zuwa gidan.
Kaman yanda yace Maimuna jansa tayi da wani abun har ya iso gidan.
Suna zaune an saka masa shayi yana sha,ga babbar riga yasaka ƙatuwa.
Jiran gwashin dayace a kawo yakeyi,wanda Maimuna ta ɗau lokaci da gangan tana kawowa..
Da sauri Ahmad yashigo cikin ɗakin,wanda saida ya razana malamin.
"Kai waye ya aikoka?"
"Uhm ni malamin sayyada ne kakarka,tana ɗaukar karatu a wajena,to har aikin maganin aljanu ma nakanyi sosai,shine tace surukarta batada lafiyah nazo naga abinda zan iya yi akai"
Ya ƙarisa maganar yana Murmushi.
"Kaine malamin,a ina ka zama Zambilu? Garin ya takasa gane mai kake aikatawa har ta kawoka kayi wa wata maganin aljanu?"
Zumbur yayi ya tashi da suka haɗa ido da malam Hadi,wanda Ahmad ya taho dashi. Tsakaninsu kar tasan kar ne,dan zambilu riƙaƙƙen ɗan tsubbune mai aiki da aljanu sosai. Malamai sunsha haɗa ire irensu suyi musu wa'azi amma abu ya faskara.
"A ina kuka haɗu da itah harta aikoka kayiwa wata magani?"
Ahmad ne ya tambayeshi cikin kakkausar muryah.
"Iyee kunga tunda abin yazama haka inaga na manta gidan daya kamata nazo ne,sai anjimanku ni nayi nan"
Yazo da sauri zai wuce ta bakin ƙofah Ahmad ya tareshi.
"Malam zamu tafi dashi headquater,kai kuma ga nan Maimuna zata taimaka maka ku fara aikin"
"To shikenan mashaallah Allah yabamu ikon yin nasara"
Ahmad yana gama magana ya danƙi hannun Zambilu zuwa waje,kana ganin riƙon da yayi masa kasan babu mutunci a lamarin.
Bayan an sakashi a ɗakin duhu ya daku wajen Ahmad kurtun sojojin suka iyo dashi yana makyarkyata,a awa ɗaya har kamanninsa sun sanja daga yanda suke.
Ƙafar Ahmad ya kama yana ƙiƙƙifta ido,ba sakin fuska haka ya buge hannunsa tareda riƙo fuskarsa.
"Maza faramin bayanin ya akayi kasan Sayyadar da kake ambata"
"Iyee kamin rai aradu idan tasan mai zan faɗamuku zata kasheni muss har lahira"
"Sai akace maka nikuma zan ƙyaleka koh,idan kasake shafe wata daƙiƙar baka bani bayani ba saina ballemaka maƙogaro."
Yawu ya haɗiya tareda cewa...
"Nida itah munsan juna tun ba yanzu ba,domin nine nake bata aljanun dazasu kaita wajen ƙungiyarsu,ita kuma tana bani Abubuwa da dama,domin itace wacce shugaban aljanu ya yarada da itah saboda tafi kai mata abinda yake buƙata,hatta manyan ƙasa masu buƙatar nasara sukan shiga ƙungiyarta, mu kuma in an kawo mana bugun ƙasa aljanun dake mata aiki sunfi bada irin waɗannan bayanan..
Yanzu haka ta bani wani aiki na wata yarinya dana ɗauke zuwa tsohon gidanta,idan........"
"Wacce yarinya ce?"
"Bansani ba,kawai tace na ɗauketa daga cikin gidanku ne,daga nan bansan inda ta kaita ba,amma nasan halinta yanzu haka ta kasheta,in kuma bata kasheta ba to tanada wani shiri akanta ne"
"Innalillahi nasan Sumaimah kake nufi,ka faɗamin inda kuka kaita kafin na fasa kanka
yanxunnan"
"Na faɗamaka gaskiya bansan inda take ba har raina,bansani ba,amma mai aikinta ce ta sani haka itama,idan kuka bi ɗaya daga cikinsu zaku sameta"
Ciza baki Ahmad yayi tareda cewa.
"Ku maidashi kuci gaba da ta'bashi yanda kukeso,saina buƙaceshi tukunna"
SADI-SAKHNA ce
09035784150
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
*BOOK 2*
...37...
Duk yanda Ahmad ya matsa amma ya kasa samo wani ƙwaƙwƙwaran bayani akan inda matarsa take.
An fara samun sauƙi daga wajen hajiyah Maryam dan yanzu har tashi take amma bata magana saidai tabi kowa da ido.
Yanxu ma a zaune suke Maimuna tana haɗa mata maganin dazata sha da zuma. Tun jiya da malam hadi yazo ya ganta baice komai ba,sai magani daya bayar na wanka sha dakuma turare,dukka kuma babu wanda ba'ayi mata ba a ciki,gashi har an samu sauƙi.
Fatee bazakije makarantar bane,yakamata ki gyara caurse ɗinnan ki tafi services fah"
Karya kai tayi tareda kallon hajiyah maryam wacce take zaune sun data kanta da pillow.
Kallon Fatee take da alamar itama tanaso ta tafi ɗin.
"Kingani ki shirya ki tafi,karki damu zata samu sauƙi sis ta tashi tacigaba da tambayarki kinci abinci kuwa?"
Ta ƙarisa maganar cikin janta da abin wasa.
Ƴar dariya tayi ta rungumeta kaɗan kafin ta kalli mommy tasu.
"Mommy ki fara magana da wuri,i miss you"
Bayan ta fita zama Maimuna tayi a kusada itah tareda fara bata maganin kaɗan kaɗan.
Tana cikin bata maganinne hajiyah Mammah ta shigo tana daddafawa.
Da Maimuna suka gaisa tana tambayarta ya jiki.
"Da sauƙi maimunatu,ya jikin ummantaku,mai maganin yana kawowa dai koh naga tana samun sauƙi"
"Eh yana kawowa,saidai ba wancan ɗin bane,wani yah Ahmad ya kawo shiyake mata maganin"
"Ahmad kuma ahh gaskiya ya kyauta sosai"
"Ya jikinnaki hajiya da sauƙi dai koh? Naga kema jikin sai a hankali"
"Uhm na samu sauƙi,saina samu labarin wai Sumaimah matar Ahmad ce kuma abin jajantawar daga gano hakan saita bata,ko suwaye suka ɗauketa oho. Allah dai ya bayyanata"
"Ameen ya Allah,ni nafi tunanin koh a garin zata koma asibitine ta rasa hanya,ko ta haɗu da wasu bata gari,amma Inshaallah za'a ganta,koma waye asirinsa zai tonu"
"Hakane kam Allah ya bayyana tah,ni bari zan fitah da driver zamuje likita ya dubamin ƙafafuna."
"To shikenan hajiyah Mammah saikin dawo Allah ya sawwaƙe"
"Ameen Allah yabata lafiyah"
Duk maganar da suke hajiyah Maryam ta tsurawa hajiyah Mammah ido ko ƙoftawa batayi.
Ita kaɗai tasan mai yake faruwa.
Hajiyah Mammah tana fita Maimuna ma ta tashi zata maida kayan abincin da aka kawo.
Riƙo rigarta hajiyah Maryam tayi tareda cewa.
"Maza ki faɗawa yayanku Ahmad cewar yafara aikin,ke kuma kibi hajiyah Mammah a bayah,duk motar data shiga ki faɗamasa wacce ce shiyasan mai zayyi akai. Yi sauri babu lokaci,kada ta tafi baki san waccece ba"
"Mmmmmommy dama ......dama kina maganaaaa wayyo Allah na gode maka amm......."
"Godiya ga Allah yana da daɗi,amma kiyi sauri kiyi abinda naceee"
Cikin saurin jiki Maimuna ta fitah daga ɗakin domin ganin wacce motah hajiyah Mammah zata shiga.
Tana fitah hajiyah Maryam ta tashi daga kan gadon,duk da har yanzu jikinta a riƙe yake ga ciwon da ƙirjinta yakeyi,amma dai da sauƙi sosai.
Wayarta ta ɗauka ta ƙira Neelah,bugu ɗaya ta ɗauka.
"Hello Neelah kina ina,tafita yanzu Ahmad zai turamiki lokacation ɗin da motar takebi ki zama cikin shiri,koda yake ma kizo ki ɗaukeni mutafi zan iya inaga"
"Ahah mommy ko barshi jikinki ba zai iya jurewa ba"
"No dolene naje,ta hakane zan jawo Abbansu zuwa wajen,so nake yau yaga abinda uwarshi take aikatawa,koda kuwa hakan zai zama ƙarshen numfashina,na gaji haka"
Tana haki take maganar tareda saka hijabinta. Ta ƙofar baya ta dafah ta fita inda zasu haɗu da neelan.
∆∆∆∆
Sumaimah (pov)
Yau kwana na uku kenan a wajennan,har yanzu banga hajiyah Mammah ba duk da nasan itace ta bada umarnin a kawoni wajennan,sai wannan mai aikinnata mara imani,jinake da inada dama zan iya yimata komai.
Jikina kaman an jefani cikin ruwan zafi haka nake jinsa,hannuna na saka a kan ɗan cikina,tausayinsa nakeji sosai,yunwar da suke barni da itah abinci sau ɗaya,ga kuma rashin bacci da azaba,nasan dukka sai ya shafeshi..
Hannuna na ɗaga sama ina addu'ar sirri ta Allah ya kawomin mafitah.
Yau har an kai hantsi amma bata zo ba,komai yasa oho. Duk da zata cutar dani amma abincin datake bani shima wani abunne.
Hannuna na kalla wanda aka ɗaureni da sarƙa zuwa jikin ƙaramin gadon dayake ɗakin,to wai tukunna ma nan inane. Gidane mai kyau amma ba kowa a ciki,ko a wanne garine wanne ƙarnine oho.
Jan jiki nake na isa bakin window gidane mai kyau sosai, amma ginin na ɗan dane . babbane sosai kuma bakowa,ko ihu zanyi baza'a gane ba.
Wani hawayene ya zubomin kan kuncinah. Ƙarar buɗe ƙofar naji hakan yasa na juyah da sauri,nasan ma wacece tazo....
Ga mamakina wazan gani ya shigo,hajiyah Mammah ce itada kaltum. Wani murmushi tayimin kaman na matar arziƙi,ja da baya nake harna danganta da bangon ɗakin. Ƙirjina banda bugawa babu abinda yakeyi.
"Ohh kinsanma mai kikayi kenan,tunda daga shigowa har jikinki ya fara karkarwa,bansan ke wacece ba inata nemanki,sai gashi kin nunamin kanki da kanki a ruwan sanyi. Kece makasudin karyewar komai nawa,kama daga rushewar ƙungiyata,yaron dana tsana nake son yabi duniyah,shine kika zauna dashi a matsayin miji harda yaro koh?".
Kujera kaltum ta miƙomata ta zauna tana yiwa Sumaimah kallon ɗan tsako.
"Yanzun zaki faɗamin inda kika saka kwalbar da kika ɗauka kokuma saina miki abinda nayiwa wacce ta gabaceki tukunna"
Kimm Sumaimah tayi da taurin zuciya ga ido a soye tana kallon hajiyah Mammah,vatace komai ba amma kana ganinta kasan batada niyyar yin magana.
Abinda kaltum ta azabtar da itah ta nuna mata,kuka ta saka tana shashshafa jikinta.
"Bazaki samu abinda kike nema ba har abada."
"Nikuwa zan samu,kinsan harda na nuclear information ɗin zaki bani,shi ya manta mai yasameshi a baya,amma keda kike matarsa nasan bazaki gagara sani ba. Zaki ce in inaso na kasheki,amma karki manta nasan raunin mu mu mata......kaltum shigomin dashi"
Tana faɗin hakan Kultum ta fita sai gata da sayyid ta riƙo hannunsa,yaron sai kuka yake yana ƙiran deeja,idonsa cabb da hawaye.
Deejah ce ta shigo wani ƙaton mutum ya hankaɗota ɗakin itada inna larai,dukkansu jikinsu ya baci ka shatar duka.
Zaro ido Sumaimah tayi tareda jan hannunta wanda yake ɗaure,jikinta yana rawa ta kalli hajiyah Mammah tana jijjiga kai.
"Karki tabamin ahalina,kada ki kuskura ki tabamin ahalina,su basumiki komai ba,ki barmin su"
Kuka take tana fincikar hannunta zata isa wajenda su Deejah suke.
Dukkansu sun nuna alamar tausayi banda Deejah wacce ta haɗe rai tana hararar hajiyah Mammah.
"Meyasa kika yiwa Anty Sumaimah haka,mai tayi miki zakiyi mata haka. Uhmmmmmmm(taja numfashi tareda rufe ido).
Baƙin ruhi,ke baƙin ruhi ce,sannan kuma kina amfani da baƙin ruhi......yana kusa ina jiyishi,kin haɗa ruhinki dana Jinsin nas'ass(jinsin aljanune rabi mutum rabi aljani). Mayaudara kana marasa amana"
Bayan ta gama bayanin buɗe idanunta tayi ta kalleni. Nasan mai take shirin yi dan haka nayi mata magana.
"Deejah mai kike haka,kada ki kuskura ki koma gidan jiyah,bayan wahalar da kika sha muma muka sha,ban yadda ki koma wannan rayuwar ba"
"Ba komawa zanyi na,tarayyar danayi dasu na tun ina yarinya ne,duk da mun rabu dasu tunda na zabi mutane akansu,amma hakan bashi ya hanasu yimin alƙawarin taimako daya sashi jinsunsu ba. Karki hanani,bake kaɗai suka taba ba,sun tabamin sayyid wanda bazan iya haƙuri ba,yanzunnan zan dawo,zan arawa Harƙeelah jikina na wani lokaci. Kada ki damu tanada mutunci,itace ta cinye
Showing 57001 words to 60000 words out of 62659 words
"Me.....me kike faɗi Matiful duluk. ......wacce matar kenan badai matar Ahmad ba danake nema ruwa a jallo,dama tana gidannan ne? Kuma jinin gidannan ce ta yaya kenan?"
"Hhhhhh aiki ya ganki uwar gijiyar Harsheelah,dolene ki dage in kinason cigaba da aiki da dodo,idan ba haka ba ƙarshenki ne kema yazo kamar yanda na wanda suka wanzu kafinki ya wuce"
Ganin sun fara mata dariyar ƙeta ne yasa ta kawar da ƙoƙon ,domin bashine a gabanta ba yanzu.
"Kultum ƙiramin Mulaifah inason in tambayeta,nasan dole tasan wanda ya shigo ɗakina tunda har ya samu makullina"
"Amma hajiyah da alama tayi shaye shaye yauma,ba lallai tah.........."
"Ban tambayeki yin ja'inja dani ba,babu ruwana da shaye shayenta,inta kama zan zaqulo duk abinda ke cikinta ciki kuwa harda shegen ɗan da ya baje koli a mahaifarta idan zan samu amsata. Mtsw matsama kiga naje da kaina"
Bangaje Kultum tayi ta nufi ɗakin Mulaifah,tana kwance tayi ɗaɗɗayah,ko takalminta bata cire ba.
Hajiyah Mammah na zuwa ta nuna hancinta wani hayaƙi ya fita,aikuwa cikin firgici Mulaifah ta tashi ta zauna tana sosa hanci da atishawa.
"Maza faɗamin wa kika faɗawa inda key ɗin ɗakina yake?"
Ganin wacce take gabanta kamar kakar tata amma kuma tafita yarinta yasa ta murza ido.
"Mtsw saida Sport G yacemin dama zanga abinda hankalina bazai ɗauka ba,amma hadda zafi a hanci kaiii"
"Dallah ki ware kokuma namiki abinda yafi na hanci,don tsabar rashin sanin daidai kinada ciki kike shaye shaye koh,in kika mutu ai ke kika sani,na rasa uwarki ma ballantana ke. Ki faɗamin akan shashancinki wa kika bawa bayani ya shiga ɗakina?"
"Uhm na'am ni.....bansani ba iya kawai gyara tace zata miki na kaya shiyasa nace ta shiga amma ni baruwana. Saboda ta gama miki da wuri har na bata fitila. Saboda kullum kina cewa na zama mai kirki"
"Wacece itah baki santa bane?"
"Nasanta mana,wai granny mai ya shiga kankine,na ganki ma kaman wata sa'a ta fahhhh"
Wani wawan hawa hajiyah Mammah tayiwa gadon Mulaifah tareda cafkar wuyanta.
"Faɗamin wacece ita,kokuma na ƙarisaki yanzunnan,matacciyah kawai"
"Wayyo Sumaimah,Sumaimah cefah mai laifina danna barta tashiga ɗakinki,naga dai tanayimiki aiki sosai"
Sakin wuyan Sumaimah hajiyah Mammah tayi tareda daskarewa a wajen,meyasa ma bata taba zarginta ba duk zamanta a gidan. Kenan.......kenan......mijinnata wato Ahmad ne,kenan itace matarsa daya aura a rayuwarsa ta shekara biyar.......jinin mace mai ciki Matiful duluk ya faɗa,kuma tanada ciki.....kenan tasan mai nake ƙulllawa tsawon wannan lokacin,kallon ayaba kawai takeyi mata.
Wata dariyar takaici hajiyah Mammah tasaki lokaci ɗaya kuma ta haɗe rai ƙaman hadarin marka marka mai shirin zubar da ruwa........
SADI-SAKHNA ce
09035784150
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
*BOOK 2*
...36...
Bayan ta dawo daga sashen hajiyah Mammah banɗaki ta wuce,anan taga ciwon dataji da kwalbar data fashe,tafin kafarta ne ta dama ya tsage,
Wankewa tayi ta ɗaure wajen kafin tazo ta kwanta,ɗaya kwalbar kuma dagata tayi tana kallonta.
"Ko itama na fasata kaman yanda ɗayar ta fashe kai?. Ahah idan na fasata kuma wani abun ya shafeni fah?"
Ruwa ta tara a cikin roba ta karanta ayoyin karya sihiri a ciki,bude kwalbar tayi ta juye ruwan a ciki ta rufe.
"Bansani ba kozai karya abinda yake ciki ko ahah,amma Allah ina roqonka Allah yasa yayi aiki"
Ajiyewa kwalbar tayi a cikin kayanta kafin ta kwanta.
Bayan ta kwanta ta daɗe bacci bai ɗauketa ba,shin abinda tayi daidaine kokuma saka kanta tayi a haɗari.
Rufe idonta keda wuyah taji wata iska ta zagayeta,da guguwa ta taho amma ƙarfinta ya ragu kafin ta iso gareta, tana gudu haka ta ɗauketa zuwa wani waje mai duhu.
Buɗe idanunta tayi daga mafarkin,saidai sabanin ɗakinsu a wani waje ta tsinci kanta mai matuƙar duhu,dagane ba ɗakinsu bane saboda jin tana kwancene rairayi.
Hannunta takai kan cikinta,yana nan babu abinda ya sameshi. Tasbihi da fara da salati duk wanda ya samu zuwa bakinta.
A haka tana wannan halin har haske yafara fitowa da gabas. Tunda ta tsinci kanta a wajen take zaune bata motsaba har zuwa wannan lokacin.
Motsin takun mutum tajiyo yana zuwa,ɗauke numfashinta tayi har zuwa lokacin da aka dalleta da wani abu mai haske.
"Hmmm wai dama kece ashe? Kinyi wasanki yanda ya dace,amma bari kiga naki ƙarshen yanzunnan"
Kultum ce take maganar cikeda jin haushin Sumaimah.
Jin wanda yake magana maimakon taji tsoro sai maida martani da tayi.
"Kinyi mamaki ne da kikaganice,zatonku ku kaɗai kuka iya shiri,komin ƙanƙantar allura ƙarfece,dan haka ba abar rainawa bace kuma akan iyalina babu abinda bazanyi ba. Ganin baku kasheni ba duk da kunsan ni wacece to aikin danayi a sashennata ita shugabar taki yayi mata illah sosai koh?"
Wani mari Kultum ta bawa Sumaimah mai ƙarfi.
"Hmmmm zatonki dan kinyi wannan ke wata shegiya ce,jira tazo tasameki kiga yanda zata gama da ahalin da kike komai dominsun. Ke kuma zakiga baƙar wahalar da zaki sha kafin mutuwarki"
Dunƙule hannunta tayi tareda faɗin wata kalma,nan da nan wani tururi ya kunnu a dukkan ilahirin jikin Sumaimah,tana jin zafin kuwa ta fasa wani ihu mai cikeda ban tausayi.
A asibiti kuwa hajiyah Mammah na tafiyah Ahmad ya shigo asibitin.
Anan suka kwana a wajen hajiyah Maryam ɗin har gari ya waye.
Har zuwa lokacin hajiyah Maryam bata tashiba,sai kace matacciyah haka take. Ƙarfin allurar ya ƙare yaci ta tashi amma har yanzu shuru. A.M Aliyu ne ya kwana a kujerar da take gabanta,iyah dare ɗaya amma damuwar da take fuskarsa bazata misaltu ba.
Su Sameer Ahmad da Maimuna suna tsaye a gefe guda,babu mai cewa komai kowa da abinda yake sakawa.
Sallama akayi a ƙofar shigowa ɗakin,Saleem ne ɗauke da kayan karyawa,sai kuma su inna larai itada Hajiya Shukurah.
Gaishe gaishe akayi na kwanan mai jiki.
"Gashi wannan inji inna ladiyo wai na Sumaimah ne,itace mai san ɗanwake"
Ya faɗa yana ajiye wata ƙaramar coolar a gefe.
"Sumaimah kuma,jiya fah yah Ahmad ya maidata gida,ko ba gida ka mayarta ba kai?"
Fatee ta faɗa cikeda mamaki tana kallon Ahmad.
Shima da mamakin yace.
"Gida na mayar ta mana,saida ta shiga ma kafin na wuce"
"Eh ta koma gida,amma inna ladiyo tace wai bayan sun gama fira sun kwanta,data tashi ƙarfe biyun dare bata kanta ba. Tayi zaton ko tana wajenka shiyasa bata nemeta ba"
"Nida ban kwana a gidaba taya za'ace tana wajena,Sannan side ɗina ma a kulle yake,kuma batada key ɗin wajen yanzu. To ina taje kenan?"
Ahmad yayi tambayar a razane.
Kowa hankalin sa ne yadawo kan wannan sabon lamarin,kafin kace me Ahmad yafice da gudu daga ɗakin.
Saleem ne yabi bayansa suke tada mota zuwa gidan.
A ƙanƙanin lokaci suka isa,tareda security na gidan aka shiga nemanta,amma babu ita babu labarin ta a gidan.
Don ba kowa a gidan daga su inna ladiyo itada ummi sai kuma hajiyah Mammah wacce a cewarta ta kwana batada lafiya ciwon zuciyarta ya tashi.
Wasa wasa har dare babu Sumaimah babu alamarta,ga hajiyah Maryam ma har yanxu bata motsi,saidai ta buɗe idonta tana kallon sama kawai,daga haka babu abinda takeyi.
Yanda sukaga rana haka suka dare aka waye,kowa in ka ganshi kaman ya tashi a jinya saboda tashin hankali.
Ganin sun raba kansu a asibiti da kuma gida ga ciwon hajiyah Maryam an tabbatar musu bana asibiti bane,hakan yasa suka dawo da ita gida aka malamin da zai mata na islamic. Suna dawowa gidan da safe sai gashi yazo,yasha manyan kayansa wai hajiyah Mammah ce tayi masa Magana akan zai fara mata magani.
Maimuna ce da Fatee kawai a gidan saisu inna,sauran mazan dukka basanan suna wajen case ɗin neman Sumaimah,wanda aka watsa a media ma amma har yanzu babu takaimaiman labarin ta..
A zaune yake ya zurawa waje ɗaya ido,bai taba sanin haka take a cikin ransa ba sai yanzu,bai san wanne irin so mai zurfi yake mata ba sai yanzun,gaba ɗaya nutsuwarsa bata tareda shi saboda batannata.
Wayarsa ya ɗauka ya danna ƙiran Maimuna,don itace mai kulada hajiyah Maryam ɗin.
"Hello y kuke ya jikinnata,ta farka ne?"
"Ahah bata farka ba har yanxu,mai maganin da aka turo ma yazo ya fara yimata"
"Waye kuma ya turo mai magani?"
"Hajiyah Mammah ce mana,dama tun a asibiti da Likitoci suka ce ayi na gida tace zata nemo mai magani"
"What mai magani daga wajenta,ganinan zuwa yanxunnan,zan taho da mai maganin,munyi magana dama dashi. Ki tabbatar baki bar mutuminnan shikaɗai da ita ba,Sannan kada ki kuskura ki bari ya tabata har sai nazo tukunna"
Cikeda mamaki ta amsa masa da toh.
Yana kashe wayarsa ya ɗau key ɗin motarsa zuwa gidan.
Kaman yanda yace Maimuna jansa tayi da wani abun har ya iso gidan.
Suna zaune an saka masa shayi yana sha,ga babbar riga yasaka ƙatuwa.
Jiran gwashin dayace a kawo yakeyi,wanda Maimuna ta ɗau lokaci da gangan tana kawowa..
Da sauri Ahmad yashigo cikin ɗakin,wanda saida ya razana malamin.
"Kai waye ya aikoka?"
"Uhm ni malamin sayyada ne kakarka,tana ɗaukar karatu a wajena,to har aikin maganin aljanu ma nakanyi sosai,shine tace surukarta batada lafiyah nazo naga abinda zan iya yi akai"
Ya ƙarisa maganar yana Murmushi.
"Kaine malamin,a ina ka zama Zambilu? Garin ya takasa gane mai kake aikatawa har ta kawoka kayi wa wata maganin aljanu?"
Zumbur yayi ya tashi da suka haɗa ido da malam Hadi,wanda Ahmad ya taho dashi. Tsakaninsu kar tasan kar ne,dan zambilu riƙaƙƙen ɗan tsubbune mai aiki da aljanu sosai. Malamai sunsha haɗa ire irensu suyi musu wa'azi amma abu ya faskara.
"A ina kuka haɗu da itah harta aikoka kayiwa wata magani?"
Ahmad ne ya tambayeshi cikin kakkausar muryah.
"Iyee kunga tunda abin yazama haka inaga na manta gidan daya kamata nazo ne,sai anjimanku ni nayi nan"
Yazo da sauri zai wuce ta bakin ƙofah Ahmad ya tareshi.
"Malam zamu tafi dashi headquater,kai kuma ga nan Maimuna zata taimaka maka ku fara aikin"
"To shikenan mashaallah Allah yabamu ikon yin nasara"
Ahmad yana gama magana ya danƙi hannun Zambilu zuwa waje,kana ganin riƙon da yayi masa kasan babu mutunci a lamarin.
Bayan an sakashi a ɗakin duhu ya daku wajen Ahmad kurtun sojojin suka iyo dashi yana makyarkyata,a awa ɗaya har kamanninsa sun sanja daga yanda suke.
Ƙafar Ahmad ya kama yana ƙiƙƙifta ido,ba sakin fuska haka ya buge hannunsa tareda riƙo fuskarsa.
"Maza faramin bayanin ya akayi kasan Sayyadar da kake ambata"
"Iyee kamin rai aradu idan tasan mai zan faɗamuku zata kasheni muss har lahira"
"Sai akace maka nikuma zan ƙyaleka koh,idan kasake shafe wata daƙiƙar baka bani bayani ba saina ballemaka maƙogaro."
Yawu ya haɗiya tareda cewa...
"Nida itah munsan juna tun ba yanzu ba,domin nine nake bata aljanun dazasu kaita wajen ƙungiyarsu,ita kuma tana bani Abubuwa da dama,domin itace wacce shugaban aljanu ya yarada da itah saboda tafi kai mata abinda yake buƙata,hatta manyan ƙasa masu buƙatar nasara sukan shiga ƙungiyarta, mu kuma in an kawo mana bugun ƙasa aljanun dake mata aiki sunfi bada irin waɗannan bayanan..
Yanzu haka ta bani wani aiki na wata yarinya dana ɗauke zuwa tsohon gidanta,idan........"
"Wacce yarinya ce?"
"Bansani ba,kawai tace na ɗauketa daga cikin gidanku ne,daga nan bansan inda ta kaita ba,amma nasan halinta yanzu haka ta kasheta,in kuma bata kasheta ba to tanada wani shiri akanta ne"
"Innalillahi nasan Sumaimah kake nufi,ka faɗamin inda kuka kaita kafin na fasa kanka
yanxunnan"
"Na faɗamaka gaskiya bansan inda take ba har raina,bansani ba,amma mai aikinta ce ta sani haka itama,idan kuka bi ɗaya daga cikinsu zaku sameta"
Ciza baki Ahmad yayi tareda cewa.
"Ku maidashi kuci gaba da ta'bashi yanda kukeso,saina buƙaceshi tukunna"
SADI-SAKHNA ce
09035784150
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
*BOOK 2*
...37...
Duk yanda Ahmad ya matsa amma ya kasa samo wani ƙwaƙwƙwaran bayani akan inda matarsa take.
An fara samun sauƙi daga wajen hajiyah Maryam dan yanzu har tashi take amma bata magana saidai tabi kowa da ido.
Yanxu ma a zaune suke Maimuna tana haɗa mata maganin dazata sha da zuma. Tun jiya da malam hadi yazo ya ganta baice komai ba,sai magani daya bayar na wanka sha dakuma turare,dukka kuma babu wanda ba'ayi mata ba a ciki,gashi har an samu sauƙi.
Fatee bazakije makarantar bane,yakamata ki gyara caurse ɗinnan ki tafi services fah"
Karya kai tayi tareda kallon hajiyah maryam wacce take zaune sun data kanta da pillow.
Kallon Fatee take da alamar itama tanaso ta tafi ɗin.
"Kingani ki shirya ki tafi,karki damu zata samu sauƙi sis ta tashi tacigaba da tambayarki kinci abinci kuwa?"
Ta ƙarisa maganar cikin janta da abin wasa.
Ƴar dariya tayi ta rungumeta kaɗan kafin ta kalli mommy tasu.
"Mommy ki fara magana da wuri,i miss you"
Bayan ta fita zama Maimuna tayi a kusada itah tareda fara bata maganin kaɗan kaɗan.
Tana cikin bata maganinne hajiyah Mammah ta shigo tana daddafawa.
Da Maimuna suka gaisa tana tambayarta ya jiki.
"Da sauƙi maimunatu,ya jikin ummantaku,mai maganin yana kawowa dai koh naga tana samun sauƙi"
"Eh yana kawowa,saidai ba wancan ɗin bane,wani yah Ahmad ya kawo shiyake mata maganin"
"Ahmad kuma ahh gaskiya ya kyauta sosai"
"Ya jikinnaki hajiya da sauƙi dai koh? Naga kema jikin sai a hankali"
"Uhm na samu sauƙi,saina samu labarin wai Sumaimah matar Ahmad ce kuma abin jajantawar daga gano hakan saita bata,ko suwaye suka ɗauketa oho. Allah dai ya bayyanata"
"Ameen ya Allah,ni nafi tunanin koh a garin zata koma asibitine ta rasa hanya,ko ta haɗu da wasu bata gari,amma Inshaallah za'a ganta,koma waye asirinsa zai tonu"
"Hakane kam Allah ya bayyana tah,ni bari zan fitah da driver zamuje likita ya dubamin ƙafafuna."
"To shikenan hajiyah Mammah saikin dawo Allah ya sawwaƙe"
"Ameen Allah yabata lafiyah"
Duk maganar da suke hajiyah Maryam ta tsurawa hajiyah Mammah ido ko ƙoftawa batayi.
Ita kaɗai tasan mai yake faruwa.
Hajiyah Mammah tana fita Maimuna ma ta tashi zata maida kayan abincin da aka kawo.
Riƙo rigarta hajiyah Maryam tayi tareda cewa.
"Maza ki faɗawa yayanku Ahmad cewar yafara aikin,ke kuma kibi hajiyah Mammah a bayah,duk motar data shiga ki faɗamasa wacce ce shiyasan mai zayyi akai. Yi sauri babu lokaci,kada ta tafi baki san waccece ba"
"Mmmmmommy dama ......dama kina maganaaaa wayyo Allah na gode maka amm......."
"Godiya ga Allah yana da daɗi,amma kiyi sauri kiyi abinda naceee"
Cikin saurin jiki Maimuna ta fitah daga ɗakin domin ganin wacce motah hajiyah Mammah zata shiga.
Tana fitah hajiyah Maryam ta tashi daga kan gadon,duk da har yanzu jikinta a riƙe yake ga ciwon da ƙirjinta yakeyi,amma dai da sauƙi sosai.
Wayarta ta ɗauka ta ƙira Neelah,bugu ɗaya ta ɗauka.
"Hello Neelah kina ina,tafita yanzu Ahmad zai turamiki lokacation ɗin da motar takebi ki zama cikin shiri,koda yake ma kizo ki ɗaukeni mutafi zan iya inaga"
"Ahah mommy ko barshi jikinki ba zai iya jurewa ba"
"No dolene naje,ta hakane zan jawo Abbansu zuwa wajen,so nake yau yaga abinda uwarshi take aikatawa,koda kuwa hakan zai zama ƙarshen numfashina,na gaji haka"
Tana haki take maganar tareda saka hijabinta. Ta ƙofar baya ta dafah ta fita inda zasu haɗu da neelan.
∆∆∆∆
Sumaimah (pov)
Yau kwana na uku kenan a wajennan,har yanzu banga hajiyah Mammah ba duk da nasan itace ta bada umarnin a kawoni wajennan,sai wannan mai aikinnata mara imani,jinake da inada dama zan iya yimata komai.
Jikina kaman an jefani cikin ruwan zafi haka nake jinsa,hannuna na saka a kan ɗan cikina,tausayinsa nakeji sosai,yunwar da suke barni da itah abinci sau ɗaya,ga kuma rashin bacci da azaba,nasan dukka sai ya shafeshi..
Hannuna na ɗaga sama ina addu'ar sirri ta Allah ya kawomin mafitah.
Yau har an kai hantsi amma bata zo ba,komai yasa oho. Duk da zata cutar dani amma abincin datake bani shima wani abunne.
Hannuna na kalla wanda aka ɗaureni da sarƙa zuwa jikin ƙaramin gadon dayake ɗakin,to wai tukunna ma nan inane. Gidane mai kyau amma ba kowa a ciki,ko a wanne garine wanne ƙarnine oho.
Jan jiki nake na isa bakin window gidane mai kyau sosai, amma ginin na ɗan dane . babbane sosai kuma bakowa,ko ihu zanyi baza'a gane ba.
Wani hawayene ya zubomin kan kuncinah. Ƙarar buɗe ƙofar naji hakan yasa na juyah da sauri,nasan ma wacece tazo....
Ga mamakina wazan gani ya shigo,hajiyah Mammah ce itada kaltum. Wani murmushi tayimin kaman na matar arziƙi,ja da baya nake harna danganta da bangon ɗakin. Ƙirjina banda bugawa babu abinda yakeyi.
"Ohh kinsanma mai kikayi kenan,tunda daga shigowa har jikinki ya fara karkarwa,bansan ke wacece ba inata nemanki,sai gashi kin nunamin kanki da kanki a ruwan sanyi. Kece makasudin karyewar komai nawa,kama daga rushewar ƙungiyata,yaron dana tsana nake son yabi duniyah,shine kika zauna dashi a matsayin miji harda yaro koh?".
Kujera kaltum ta miƙomata ta zauna tana yiwa Sumaimah kallon ɗan tsako.
"Yanzun zaki faɗamin inda kika saka kwalbar da kika ɗauka kokuma saina miki abinda nayiwa wacce ta gabaceki tukunna"
Kimm Sumaimah tayi da taurin zuciya ga ido a soye tana kallon hajiyah Mammah,vatace komai ba amma kana ganinta kasan batada niyyar yin magana.
Abinda kaltum ta azabtar da itah ta nuna mata,kuka ta saka tana shashshafa jikinta.
"Bazaki samu abinda kike nema ba har abada."
"Nikuwa zan samu,kinsan harda na nuclear information ɗin zaki bani,shi ya manta mai yasameshi a baya,amma keda kike matarsa nasan bazaki gagara sani ba. Zaki ce in inaso na kasheki,amma karki manta nasan raunin mu mu mata......kaltum shigomin dashi"
Tana faɗin hakan Kultum ta fita sai gata da sayyid ta riƙo hannunsa,yaron sai kuka yake yana ƙiran deeja,idonsa cabb da hawaye.
Deejah ce ta shigo wani ƙaton mutum ya hankaɗota ɗakin itada inna larai,dukkansu jikinsu ya baci ka shatar duka.
Zaro ido Sumaimah tayi tareda jan hannunta wanda yake ɗaure,jikinta yana rawa ta kalli hajiyah Mammah tana jijjiga kai.
"Karki tabamin ahalina,kada ki kuskura ki tabamin ahalina,su basumiki komai ba,ki barmin su"
Kuka take tana fincikar hannunta zata isa wajenda su Deejah suke.
Dukkansu sun nuna alamar tausayi banda Deejah wacce ta haɗe rai tana hararar hajiyah Mammah.
"Meyasa kika yiwa Anty Sumaimah haka,mai tayi miki zakiyi mata haka. Uhmmmmmmm(taja numfashi tareda rufe ido).
Baƙin ruhi,ke baƙin ruhi ce,sannan kuma kina amfani da baƙin ruhi......yana kusa ina jiyishi,kin haɗa ruhinki dana Jinsin nas'ass(jinsin aljanune rabi mutum rabi aljani). Mayaudara kana marasa amana"
Bayan ta gama bayanin buɗe idanunta tayi ta kalleni. Nasan mai take shirin yi dan haka nayi mata magana.
"Deejah mai kike haka,kada ki kuskura ki koma gidan jiyah,bayan wahalar da kika sha muma muka sha,ban yadda ki koma wannan rayuwar ba"
"Ba komawa zanyi na,tarayyar danayi dasu na tun ina yarinya ne,duk da mun rabu dasu tunda na zabi mutane akansu,amma hakan bashi ya hanasu yimin alƙawarin taimako daya sashi jinsunsu ba. Karki hanani,bake kaɗai suka taba ba,sun tabamin sayyid wanda bazan iya haƙuri ba,yanzunnan zan dawo,zan arawa Harƙeelah jikina na wani lokaci. Kada ki damu tanada mutunci,itace ta cinye
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20 Chapter 21