kazar inna rammah"
Tana gama maganar tayi Murmushi,kallon mu tayi ta kalli Hajiyah mammah ma kafin ta rufe ido..
Yin hakan keda wuyah ta ta faɗi a wajen kaman matacciyah.
"Mai take aikatawa,harƙeelah badai .......aljanar daji bace"
Zaro ido hajiyah Mammah tayi tareda zare wuƙah zata cakawa Deejah,ganin ta tura mata tsafi amma yaƙi cinta.
Ihu nayi tareda runtse ido na,shikenan zata kasheta shikenan........
Jin shuru ne yasani buɗe ido,Abbah nagani ya riqe hannun hajiyah mamman,idanunsa sun kaɗa sunyi jajur. Bayansa neelah ce,yah Musbahu Ahmad da kuma su Sameer. Iyah Fatee ce kawai babu saisu inna ladiyo da ummi.
Wani daɗine da fatan nasara ya jiyarceni,saidai me.
SADI-SAKHNA ce
09035784150
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
*BOOK 2*
...38...
Fincike hannunta tayi tareda ja da baya tana kallonsu da mamaki,nasan na ganinsu a bazata ne.
"Menene haka Mammah,me nake gani haka da idona ba wanine ya faɗamin ba "
Cikin karayar zuciyah yake maganar.
"Meya kawoka wajennan,karka yadda da abinda ka gani ba gaskiyah bane,duk komai inayine domin ɗauka maka fansa da kuma sama maka ɗaukaka,kaima kasan bazan cutar da kai ba ai"
"Ɗaukar fansa wacce iri da kike shirin kashe wani"
"Ɗaukar fansa irin wacce ta kashemin mijina,Ta kashemin abokiyar zamana,ta kashemin surukaina da mahaifina,ta rabani da ɗana . ina kallon sa amma ban isa amsa sunan mahaifiya a gareshi ba,ta haɗani Da cutar da bansan wacce iri bace,ta tursasamin auren ɗanta saboda barazanar da takemin da rayuwar dangina. Ta so kashemin ɗana da bata samu nasara ba ta sanadiyyar haka ya shiga duniya. Ya dawo da mata da ɗa. Hakan bayyi mata ba kuma tanason kashe matar da kuma ɗanta harma da danginta kaman yanda tayimin. Wannan ne fansar da take iƙirarin faɗa"
Da hajiyah Maryam ta gama bayanin ba iyah wanda basusan mai ya faruba,har wanda suka sani ma ta basu tausayi.
Babu kaman A.M Aliyu wanda jikinsa yake rawa yana jijjiga kai. Ko a mafarki bai taba ganin mai mugunta irin mahaifiyar tasa ba.
"Mai yasa kika aikata hakan,mai suka menene dalili,na taba cemiki inason waɗannan abubuwan?"
"Yimin shuru rufemin baki,nizaka muzanta kuma ka yarda da itah,to ka tabka babban kuskure"
Wani kalamai ta fara faɗa jikinta yana fitar da hayaƙi,yayinda jikin hajiyah Maryam ma yafara bada hayaƙin.
Dukkan mutanen wajen jada baya sukayi, ganin abinda takeyi.
"Dukkan ku babu wanda zai fita daga nan wajen, dolene na ƙareku na........"
"Kece bazaki fita daga nan wajen,miye na amfani da tsafinta tana jikin wani,ki karbeta mana kawai"
Deejah ce take maganar wacce gashin kanta ya tashi yana filluwa a iska,nuna hajiyah maryam tayi da yatsa,take ta fara girgizawa tana wujijjiga.
Baƙin hayaƙi ne yafara fitowa daga ƙirjinta yana haɗuwa.
Kalle kalle hajiya Mammah tafarayi na inda zata shiga,ita kanta tasan idan babu kwalbar a hannunta Harsheelah dama haka takeso.
Shigewa jikinta hayaƙin yayi,lokaci guda kuwa tafara komawa tsohuwarta,jikinta yana yanƙwanewa kamar an zuƙe ruwa a leda.
"Wayyoo banda tsufah banason tsufah bazan tsufa ba,jini jin nakeso Harsheelah zata kasheni inna tsufah haka mukayi da ita.
Wajen da kaltuma take ta nufah tareda kafa hakoranta a wuyanta,ihu tasaka take ta faɗi ƙasa kamar wacce ta mutu.
Jikinta ne yafara dawowa yanda yake. Murmushi tafarayi fusakrta babu alamar nadama a jiki.
Muryar aljanar tata ne yafara amsa kuwwa.
"Ko kiso kokuma kiƙi lokacin ki ya ƙare,koda kin karbi jini dan kiyi ƙarfi toh hakan bazaiyi tasiri akaina ba saboda ba na hannunki,Sannan kwalbar a rufe take bare ki dubani....wannan ƙonawar da akamin a jikin matar nan duk saikin fanshe shi yanzunnan"
Tana gama maganar ta shige jikinta da karfi,wani ihu ta fasa nan da nan jikinta yafara fidda gashi kaman biri.
Durƙushewa tayi a wajen tana wata irin karkarwa da kuka kaman karashiyah.
Bayan komai ya lafa faɗuwa Deejah tayi,da sauri Musbahu ya tareta yana jijjiga ta.
Ahmad ma wajen Sumaimah ya nufah yana ƙoƙarin cire sarƙar da take hannunta.
"Akwai key a jiki,gashinan Sayyid yana miƙa maka"
Sumaimah ta faɗa cikin raunin jiki.
Juyawa yayi indayaron yake miƙomasa key din daya ɗauka a ƙasa.
Tsurawa yaron ido yayi yana kallonsa ko ba'a fadamasa ba yasan jininsa ne.
Karbar key ɗin yayi ya buɗe hannayenta sarƙar tana zubewa ya riƙeta a jikinsa,ganin yanda jikinta yayi laushi.
Kallon kallo suke na kewar juna.
"Habibtee ruwaaaa"
Daga wannan maganar ta sume a hannunsa.
A hankali nake buɗe idona na saukeshi akan farin fentin ɗakin.
Inane nan kuma na faɗa a raina.
Muryar mutane biyu naji,ɗaya babba ɗaya ta yaro.
Waiwayar da kaina nayi na saukeshi akansu.
Ahmad ne shida Sayyid sun saka kaya iri ɗayah. Farar riga da bakin wando design.
Idan nace basuyimin kyau ba to wannan ƙaryane,shin mafarki nake kokuma da gaskene.
Murmushi nakeyi duk da kuwa rashin ƙarfi da jikina yake.
Sayyid ne yafara ganina yace.
"Abbi Unni ta tashi kalli"
Da sauri ya waiwayo inda nake,tasowa yayi zuwa inda nake yazo ya zauna.
"Alhamdulillah nagode Allah da kika tashi"
"Naga ka damu kwanana nawa a haka"
"Kwananki uku hayatee,likita yace an bawa jikinki wahala sosai,kina buƙatar hutu shiyasa baki tashi ba. Ga kuma bake kaɗai bace"
"Uhm zansha ruwa kuma yunwa nakeji"
"Okay barina baki ruwan kafin na ƙira nurse ɗinki ta duba jikinki ta kuma bada wanne abincin da zaki iya ci"
"Amma nan inane naga kaman gida amma kuma nan ɗakin asibitine"
Murmushi yayi tareda kama hannuna.
"Gidanki ne kuma asibitinki ne, kina ɗauke da cikin twin baby,Sannan likita yace jikinki bashida ƙarfi yana buƙatar kulawa. Nikuma banaso ki zauna a asibiti,shiyasa akayi creating ɗaki mai dauke da duk abinda kikeso na asibiti,na ɗauka miki nurse da zata dunga kulada ke har zuwa ki sauka lafiyah"
Farincikine marar misaltuwa ya kamani ganin irin kulawar dayake bani,dama zan samu irin wannan kulawar haka.
Bayan nurse ta dubani porridge aka kawomin na wake yasha kifi. Sosai naci son cina yana nan. Ina cikin ci ne inna larai ta shigo.
"Oh kintashine uwar biyu?"
"Uhm na tashi inna,yaushe kikazo na ganki kaman kin daɗe"
"Lahh hala Amadu bai faɗamiki ba,tare muka dawo ai dan kina kwancene,a can sashen dayake daya vangaren muke,Deejah ma bata nan ta tafi makaranta data shigo"
"Mashaallah dan Allah inna kuna nan, ina ummee,ya jikinta ta warke?"
"To da sauƙi dai,amma wannan ciwon kam tunda dalilinsa ya tafi to babu shi,rashin ƙarfin jikine,jiyama tazo dubaki kina kwance"
"Ayyah amma komai yayi babu wata matsala koh inna"
"Babu komai saidai muce Alhamdulillah,dama abinda nake faɗamiki kenan,mahakurici shi mawadaci ne watarana.
Sumaimah yanzu kinsamu soyayyar mijinki data dangin mijinki saura kuma idan kin ji sauƙi kuje gidan iyayenki su ganki,duk da ga zaman da kukayi amma suɗin naki ne"
"To shikenan inna zanje,nagode da kika tallafeni kika zauna dani a halin ƙuncina inna,keɗin uwace wacce bazan maye mata kurbiba nagode sosai da sosai"
"Matar yallabai ance kin tashi gani nazo yimiki tijara,dama haka abin yake ashe?"
"Ummi ykk"
"Kinga rufemin baki karkice komai"
"Ummi ba haka bane,a lokacin......"
Rugumeni naji tayi tareda cewa..
"Nasani kowa yaji labarin komai Sumaimah,haƙiƙa kinga jarabawa,saidai gashi Allah ya miki sakayyah da mifificin alkhairi. Allah yabaku zaman lafiya ya sauƙeƙi lafiya"
"Ameen ummi nagode"
Wunin ranar baƙi na dungayi,saida Ahmad yatsaya akan zan huta kafin suka tafi gida,sunata mitar waina koresu. Sayyid ma inna yabi da Deejah.
Bayan ya rakasu dawowa ɗakin yayi,a baƙin ƙofa yatsaya yana tsuramin ido,kunya ce ta kamani ganin kallon dayake min.
Takowa yayi zuwa gabana,kafin nace wani abun naji ya hade bakinsa da nawa,ban hanashi ba dannasan dole zai buƙaci hakan sosai.
Sarrafani yakeyi a zafafe har kaina yafara daina ɗaukar darasin.
Cire bakinsa yayi numfashinsa yafara nauyi. Cikin dashashshiyar murya yafara magana.
"Wannan gadon yayi kaɗan,muje ɗaki ina fatan kinada ƙarfin dazaki iya ɗaukar wannan tuzurun koh"
Murmushi nayi tareda ɗaga masa kai.
"Nida na dauki goje waye bazan ɗauka ba?"
Dariyah yayi ganin tsokanarsa nakeyi,ɗagani yayi daga kan gadon zuwa namu ɗakin.
SADI-SAKHNA ce
09035784150
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
*BOOK 2*
...39...
Bayan wata biyu
"Beb ganinan nagama shiryawa ma,hodace kawai ya saura da lip gloss na saka kayan"
"Ohh hayatee awarki biyu kenan kina shirinnan,har inna ta gyara Sayyid sun gama sun shiga mota ke kinanan"
Shagwabe fuska tayi tareda juya masa bayanta.
"Zugemin zip ɗin to nagama shikenan,ga zafi kace saina saka hijabi dogo,motace fah"
"Uhm uhm saka hijabinki kinsan banason gyalennan sosai"
Hijabin ya miƙo mata onion color tasaka kafin yaja hannunta zuwa motah..
Tayi fari ta ƙara kyau ga jiki da cikin ɗan wata shida ya ƙara mata.
Gaban motar tashiga Sayyid da Deejah na baya.
Sai kuma motar da hajiyah Maryam da inna larai suke.
Basuja lokaci sosai ba suka isa garin su Sumaimah Dabagayi,
A baƙin ƙofar gidansu sukayi parking,dan ko gidan su gaji basuje ba,taje can ita tasani aniyarta ta bita.
Sumaimah ce da Deejah suka fara shiga gidan,shaddace a jikinsu iri ɗayah maroon.
Deejah na riƙeda hannun Sayyid saikuma Sumaimah tana riƙeda jakarta.
Tun a bakin ƙofah da sukayi sallama matan gidan suka fara riƙe baki,duk wanda yaganta ya ganeta sai koma ƙofarsa fesawa,kafin wani lokaci gidan ya cika famm da mutane.
Ammi ce tayi ƙarfin halin cewa.
"Sumaimah nake gani ni ƴasu,dama Musbahu yace mana zakizo,amma bai faɗi ranar ba,ashe wai goje ogansu ne a wajen aiki. Ikon Allah Allah mai yadda yaso. Wannan yarinyar fah kaman.....
"Deejah ce baki ganeta bane?"
Turo baki tayi jin yadda suke mata kallon kaman ba ita ba.
"Deejahhh mai cin kazata dai koh"
"Kiji inna rammannan in kazace saina baki kuɗin goma ma"
"Bani kam ko kuɗin koko banida shi ki bani kinji"
Dariyah tayi tana sosa jiki kaman mahaukaciya sabon kamu.
Ganin kallon dasu Sumaimah sukeyi mata yasa ammi yimusu alamar kansu ya kuncene.
Sallama hajiyah maryam itama tayi a cikin gidan. Anan ammi ta shimfiɗamasu tabarma suka zauna.
Yaro aka tura ya ƙira ya ƙira malam uwaisu a bakin masallaci,dan yanxu ba aikin yi nan ya koma zama da dattijan anguwa.
Yana shigowa turus yayi yana kallon su Sumaimah.
"Wannan kamar......."
"Baba nice ya kake ya rayuwa?"
Kuka ya kece dashi tareda zama a ƙasan wajen.
"Sumaimah ki yafeni da abinda nayimiki, na tuba nayi nadama nayi nadama"
"Baba kadaina cewa haka komai ya wuce,sanadin caca yasakani cikin ha'ula'i amma kuma yasaka sanadiyyarsa na gamuda abokin rayuwata,muna fatan masuyi a yanzuma su daina."
"Ina wuni malam uwaisu ya gida?"
"Lafiya kalau ko kece....."
"Nice mahaifiyar goje yanda kuka sanshi kenan"
"Ahah anty Meerah kece koh?"
Shuru tayi tana kallonsa,a tunaninta dai baisan sunan ba kuma wannan sunan?
Zainab ce kawai take ƙiranta dashi.
Tashi yayi daga wajen ya nufi dakinsa,can sai gashi da wani hoto ya miƙawa hajiyah Maryam.
Zaro ido tayi tareda cewa.
"Zainab a ina ka samu hotonta,wanda muka ɗaukane a graduation"
"Itace ai mahaifiyar Sumaimah dama bansan garinta ba da asalinta taƙi faɗamin har ta koma ga mahaliccinta"
Kuka hajiyah maryam ta dungayi tana fadin.
"Rashin riƙe maganata ne yajawo komai,dama duk neman da muka miki kina raye?,Allah ya jiƙanki yamiki rahama. Sumaimah ashe ke ƴata ce bansani ba,ke ƙanwar Neelah ce uwa ɗayah. Wannan zainab ce ƙanwar Muhammad baban Ahmad,kuma mahaifiyar ki"
Lokacin data gama bayanin sai sannan kowa ya fahimceta,Sannan kuma kowa ya gane irin haɗin da Allah yayi wanda bamai iya irinsa saishi.
A ranar an taso da abubuwa da dama da suka wuce,ciki kuwa harda labarin ummah ta da baba ya dunga bayarwa. Ashe ni ƙanwar Neelah ce,ikon Allah.
A sashen yah Musbahu aka sauƙi Ahmad dakuma driver,bayan munci abinci shiga wajennasa nayi. Yana zaune da waya a hannunsa yana dannawa.
Sallama nayi ya ɗago ya kalleni.
"Ummin twins ya gajiyar jiki dai?"
Fadawa nayi jikinsa ya riƙeni kaman jira yakeyi dama.
"Nagaji amma ba sosai ba,idan baka komai inaso muje na nuna maka wani waje"
"Is not fair ma,meyasa ban tuna komai bane har yanxu?"
"Miye kake sauri,likita yace zaka tuna ai muje na nuna maka wani waje,inkuma bakaso toh"
"Inaso muje"
Mota muka shiga mu biyu,nuna masa hanya nake har muka iso anguwar tamu ta da,alama nayi masa ya tsaya kana na fitah.
Wata daba na nufah inda na hangi su yawancin ƴan kungiyarsa ne a wajen,hadda Tunga yanata surutu na siyasa.
A raina nace mai hali baya sanjawa.
Sallama nayi musu,a ciki Tunga ne kawai ya ganeni,bayan mun gaisa alama nayiwa Ahmad akan ya ƙariso.
Kallonsu yake da alama bai sansu ba,yayinda su kuma suke masa kallon mai kama da goje. Ganin hakanne yasa nagane dole nice mai share tantamar nan.
"Tunga kaida sauran ga goje,kaikuma gasu tunga wanda kukayi ta gwagwarmaya tare"
Tun kafin na ƙarisa Tunga ya riƙe hannunsa kaman zayyi kuka.
"Ogah oga ina kashiga mukayi ta nemanka"
Murmushi yayi tareda yimusu takaitaccen bayani. Haƙiƙa yanda aka bashi labarin sudin suwaye a wajensa abune da bazai manta ba.
Kuɗi ya basu tareda address dinsa na abuja kan suzo su sameshi zai Sama musu aiki. Nima naji daɗin abinda yayi sosai,domin sun cancanci hakan a wajensa.
Bayan ya gama dasu hannunsa narike muka nufi hanyar zuwa jeji,da alamar mamaki a fuskarsa amma baice komai ba har muka isa bakin kogon da bazan manta ba.
"Bazan taba manta wannan wajen ba,anannne naji abinda yake cikin zuciyarka gameda ni,ananne muka shirya a matsayinmu na ma'aurata,a nanne nayi jinyarka lokacin da duniya babu wanda yasan hakan saini da Tunga. Kuma shine sanadin shiryuwarka ka fita daga ƙungiyar BC."
Shiga mukayi cikin kogon na tsugunna a inda mukayi ajiyah.
Ganin ina bude wajenne ya tayani muka buɗe.
Akwatin daya sato a daren na fito dashi na bashi.
"Wannan fah"
"Abinda kake tunanin ƙungiyar BC sun sace,kaine kayi rai a tafiyar,Sannan baka kai a ganka ba Neelah ta kawoka nan wajen a ranar tayi maka maganin gaggawa ta tafi. Nice na kulada kai harka warke.
Na rufe sirrin inda abin yake ban faɗawa kowaba,tunda Allah yasa munzo wajen yau gashi na dawo maka dashi,saikayi yanda ya dace dashi"
Buɗewa yayi yaga babu abinda ya sauya a ciki.
Kallon so da ƙauna yakeyimin kowacce tayi aikin jarumta.
"Nikuwa mai zance dake yake wannan baiwar Allah na abinda kika min a rayuwata?"
"Kace Allah ya barmu tare cikin farin ciki,aminci da kuma ƙaunar juna har ƙarshenmu"
"Wannan yana cikin Addu'a ta a kullum"
Rungumeni yayi ina dariya shima yana Murmushi....ohhh ina son mijinah.
Bayan munje naso na kwana biyu amma Ahmad yaƙi,saboda inaso na zaga danginnamu, duk da a baya basu nunamin ƙauna ba,amma badansu zanyi ba ai.
Haka ina gani mukayi kwana ɗaya muka kamo hanyar dawowa, zuwa gidana kuma cikin dangin mahaifiyata,wacce yanzu nasan asalinta.
Bayan shekara biyu da haihuwar ƴan biyuna dukka mata, Maryam da zainab wanda ake ƙiransu Islam da ilham. Dukkansu babu mai kamata,Neelah islam ta iyo,ilham kuma hajiya Maryam har jikin.
Cikin ƙoshin lafiyah na rainesu har na yayesu,lokacin kuma Sayyid yashiga makaranta,wanda yadawo hannuna da zama. Dan so nake nayi masa tarbiyyah yanda ya kamata bata iyayen zamani ba.
Bayan yayennasu makaranta na shiga Jami'a,zan karanci Qur'anic science,dan inada burin sanin ilimi a fannnin,a lokacin ne nayi planing na haihuwa,soyayya kawai muke sha nida mijina Sannan kuma ina samun lokaci na yarana sosai.
****
Ina faka motar dana kasheta shigowa cikin gidan nayi,da islam naci karo ta dawo daga sashen inna larai,wandonta ya jiƙe da fitsari,jijjiga kai nayi dam takaci,magana saita siyarka amma tana fitsari a wando.
"Daga ina kike islam?"
"Gujin inna nake Unni"
"Ina ɗayar taki?"
"Tana bacci gujin inna"
"Kekuma kina yanda kikaga dama koh,yayah fah yana gidan Ummee ko wajen inna "
"Bashu dawoba da abbah"
"Hmm wuce to muje nacire miki wannan wandon"
Saida na gyara mata kafin nashiga kitchen a gurgune,ina cikin yi naji muryar Ahmad a falo shida yaransa.
Jallop ɗin taliya nayi na fita da itah.
Sannu da dawowa nayi masa kafin na juya zan shiga ɗaki..
"Hayatee ke bazaki ci abincin bane zaki tafi yau?"
"Ahah banajin yunwa beb wanka ma nakeson yi,kuci abincinku kada ya huce"
"Ahha baki isa ba dawo ki zauna,banason zama da yunwa,zona baki a baki"
Zaro ido nayi bayan na zauna a gefensa,ganin zai bani kunya a gaban yara na saka hannu mukaci tare.
Kallonsa nake yanda yake sakawa su ilham abincin a baki. A raina nace Alhamdulillah da wannan baiwar da dddaɗar rayuwa.
Nima sainace ALHAMDULILLAH a fili tareda ajiye alƙalaminah. Kuyi haƙuri ta katse littafin a haka,banida zabine exam ta matsoni. Da fatan zaku fahimta. Kowa in bai masa ba yasake maimaita ƙarshen a kundin hasashensa😁.
Godiya ga dukkan makaranta,musamman masu binsa yana da'irar rubutu na gode da kasancewa dani nagode sosai.
Taku a kullum SADI-SAKHNA ke muku sallama da BISSALAM. sai mun haɗu a wani sabon littafin wanda babu rana a yanzu gaskiya. Saboda sabuwar rayuwa na shirin tunkarata ta aure,ina barar addu'ar ku Allah yasa yazomin da sauƙi. Nagode.
THAMMAT BIHAMDULLAH......✍🏼
Showing 60001 words to 62659 words out of 62659 words
Tana gama maganar tayi Murmushi,kallon mu tayi ta kalli Hajiyah mammah ma kafin ta rufe ido..
Yin hakan keda wuyah ta ta faɗi a wajen kaman matacciyah.
"Mai take aikatawa,harƙeelah badai .......aljanar daji bace"
Zaro ido hajiyah Mammah tayi tareda zare wuƙah zata cakawa Deejah,ganin ta tura mata tsafi amma yaƙi cinta.
Ihu nayi tareda runtse ido na,shikenan zata kasheta shikenan........
Jin shuru ne yasani buɗe ido,Abbah nagani ya riqe hannun hajiyah mamman,idanunsa sun kaɗa sunyi jajur. Bayansa neelah ce,yah Musbahu Ahmad da kuma su Sameer. Iyah Fatee ce kawai babu saisu inna ladiyo da ummi.
Wani daɗine da fatan nasara ya jiyarceni,saidai me.
SADI-SAKHNA ce
09035784150
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
*BOOK 2*
...38...
Fincike hannunta tayi tareda ja da baya tana kallonsu da mamaki,nasan na ganinsu a bazata ne.
"Menene haka Mammah,me nake gani haka da idona ba wanine ya faɗamin ba "
Cikin karayar zuciyah yake maganar.
"Meya kawoka wajennan,karka yadda da abinda ka gani ba gaskiyah bane,duk komai inayine domin ɗauka maka fansa da kuma sama maka ɗaukaka,kaima kasan bazan cutar da kai ba ai"
"Ɗaukar fansa wacce iri da kike shirin kashe wani"
"Ɗaukar fansa irin wacce ta kashemin mijina,Ta kashemin abokiyar zamana,ta kashemin surukaina da mahaifina,ta rabani da ɗana . ina kallon sa amma ban isa amsa sunan mahaifiya a gareshi ba,ta haɗani Da cutar da bansan wacce iri bace,ta tursasamin auren ɗanta saboda barazanar da takemin da rayuwar dangina. Ta so kashemin ɗana da bata samu nasara ba ta sanadiyyar haka ya shiga duniya. Ya dawo da mata da ɗa. Hakan bayyi mata ba kuma tanason kashe matar da kuma ɗanta harma da danginta kaman yanda tayimin. Wannan ne fansar da take iƙirarin faɗa"
Da hajiyah Maryam ta gama bayanin ba iyah wanda basusan mai ya faruba,har wanda suka sani ma ta basu tausayi.
Babu kaman A.M Aliyu wanda jikinsa yake rawa yana jijjiga kai. Ko a mafarki bai taba ganin mai mugunta irin mahaifiyar tasa ba.
"Mai yasa kika aikata hakan,mai suka menene dalili,na taba cemiki inason waɗannan abubuwan?"
"Yimin shuru rufemin baki,nizaka muzanta kuma ka yarda da itah,to ka tabka babban kuskure"
Wani kalamai ta fara faɗa jikinta yana fitar da hayaƙi,yayinda jikin hajiyah Maryam ma yafara bada hayaƙin.
Dukkan mutanen wajen jada baya sukayi, ganin abinda takeyi.
"Dukkan ku babu wanda zai fita daga nan wajen, dolene na ƙareku na........"
"Kece bazaki fita daga nan wajen,miye na amfani da tsafinta tana jikin wani,ki karbeta mana kawai"
Deejah ce take maganar wacce gashin kanta ya tashi yana filluwa a iska,nuna hajiyah maryam tayi da yatsa,take ta fara girgizawa tana wujijjiga.
Baƙin hayaƙi ne yafara fitowa daga ƙirjinta yana haɗuwa.
Kalle kalle hajiya Mammah tafarayi na inda zata shiga,ita kanta tasan idan babu kwalbar a hannunta Harsheelah dama haka takeso.
Shigewa jikinta hayaƙin yayi,lokaci guda kuwa tafara komawa tsohuwarta,jikinta yana yanƙwanewa kamar an zuƙe ruwa a leda.
"Wayyoo banda tsufah banason tsufah bazan tsufa ba,jini jin nakeso Harsheelah zata kasheni inna tsufah haka mukayi da ita.
Wajen da kaltuma take ta nufah tareda kafa hakoranta a wuyanta,ihu tasaka take ta faɗi ƙasa kamar wacce ta mutu.
Jikinta ne yafara dawowa yanda yake. Murmushi tafarayi fusakrta babu alamar nadama a jiki.
Muryar aljanar tata ne yafara amsa kuwwa.
"Ko kiso kokuma kiƙi lokacin ki ya ƙare,koda kin karbi jini dan kiyi ƙarfi toh hakan bazaiyi tasiri akaina ba saboda ba na hannunki,Sannan kwalbar a rufe take bare ki dubani....wannan ƙonawar da akamin a jikin matar nan duk saikin fanshe shi yanzunnan"
Tana gama maganar ta shige jikinta da karfi,wani ihu ta fasa nan da nan jikinta yafara fidda gashi kaman biri.
Durƙushewa tayi a wajen tana wata irin karkarwa da kuka kaman karashiyah.
Bayan komai ya lafa faɗuwa Deejah tayi,da sauri Musbahu ya tareta yana jijjiga ta.
Ahmad ma wajen Sumaimah ya nufah yana ƙoƙarin cire sarƙar da take hannunta.
"Akwai key a jiki,gashinan Sayyid yana miƙa maka"
Sumaimah ta faɗa cikin raunin jiki.
Juyawa yayi indayaron yake miƙomasa key din daya ɗauka a ƙasa.
Tsurawa yaron ido yayi yana kallonsa ko ba'a fadamasa ba yasan jininsa ne.
Karbar key ɗin yayi ya buɗe hannayenta sarƙar tana zubewa ya riƙeta a jikinsa,ganin yanda jikinta yayi laushi.
Kallon kallo suke na kewar juna.
"Habibtee ruwaaaa"
Daga wannan maganar ta sume a hannunsa.
A hankali nake buɗe idona na saukeshi akan farin fentin ɗakin.
Inane nan kuma na faɗa a raina.
Muryar mutane biyu naji,ɗaya babba ɗaya ta yaro.
Waiwayar da kaina nayi na saukeshi akansu.
Ahmad ne shida Sayyid sun saka kaya iri ɗayah. Farar riga da bakin wando design.
Idan nace basuyimin kyau ba to wannan ƙaryane,shin mafarki nake kokuma da gaskene.
Murmushi nakeyi duk da kuwa rashin ƙarfi da jikina yake.
Sayyid ne yafara ganina yace.
"Abbi Unni ta tashi kalli"
Da sauri ya waiwayo inda nake,tasowa yayi zuwa inda nake yazo ya zauna.
"Alhamdulillah nagode Allah da kika tashi"
"Naga ka damu kwanana nawa a haka"
"Kwananki uku hayatee,likita yace an bawa jikinki wahala sosai,kina buƙatar hutu shiyasa baki tashi ba. Ga kuma bake kaɗai bace"
"Uhm zansha ruwa kuma yunwa nakeji"
"Okay barina baki ruwan kafin na ƙira nurse ɗinki ta duba jikinki ta kuma bada wanne abincin da zaki iya ci"
"Amma nan inane naga kaman gida amma kuma nan ɗakin asibitine"
Murmushi yayi tareda kama hannuna.
"Gidanki ne kuma asibitinki ne, kina ɗauke da cikin twin baby,Sannan likita yace jikinki bashida ƙarfi yana buƙatar kulawa. Nikuma banaso ki zauna a asibiti,shiyasa akayi creating ɗaki mai dauke da duk abinda kikeso na asibiti,na ɗauka miki nurse da zata dunga kulada ke har zuwa ki sauka lafiyah"
Farincikine marar misaltuwa ya kamani ganin irin kulawar dayake bani,dama zan samu irin wannan kulawar haka.
Bayan nurse ta dubani porridge aka kawomin na wake yasha kifi. Sosai naci son cina yana nan. Ina cikin ci ne inna larai ta shigo.
"Oh kintashine uwar biyu?"
"Uhm na tashi inna,yaushe kikazo na ganki kaman kin daɗe"
"Lahh hala Amadu bai faɗamiki ba,tare muka dawo ai dan kina kwancene,a can sashen dayake daya vangaren muke,Deejah ma bata nan ta tafi makaranta data shigo"
"Mashaallah dan Allah inna kuna nan, ina ummee,ya jikinta ta warke?"
"To da sauƙi dai,amma wannan ciwon kam tunda dalilinsa ya tafi to babu shi,rashin ƙarfin jikine,jiyama tazo dubaki kina kwance"
"Ayyah amma komai yayi babu wata matsala koh inna"
"Babu komai saidai muce Alhamdulillah,dama abinda nake faɗamiki kenan,mahakurici shi mawadaci ne watarana.
Sumaimah yanzu kinsamu soyayyar mijinki data dangin mijinki saura kuma idan kin ji sauƙi kuje gidan iyayenki su ganki,duk da ga zaman da kukayi amma suɗin naki ne"
"To shikenan inna zanje,nagode da kika tallafeni kika zauna dani a halin ƙuncina inna,keɗin uwace wacce bazan maye mata kurbiba nagode sosai da sosai"
"Matar yallabai ance kin tashi gani nazo yimiki tijara,dama haka abin yake ashe?"
"Ummi ykk"
"Kinga rufemin baki karkice komai"
"Ummi ba haka bane,a lokacin......"
Rugumeni naji tayi tareda cewa..
"Nasani kowa yaji labarin komai Sumaimah,haƙiƙa kinga jarabawa,saidai gashi Allah ya miki sakayyah da mifificin alkhairi. Allah yabaku zaman lafiya ya sauƙeƙi lafiya"
"Ameen ummi nagode"
Wunin ranar baƙi na dungayi,saida Ahmad yatsaya akan zan huta kafin suka tafi gida,sunata mitar waina koresu. Sayyid ma inna yabi da Deejah.
Bayan ya rakasu dawowa ɗakin yayi,a baƙin ƙofa yatsaya yana tsuramin ido,kunya ce ta kamani ganin kallon dayake min.
Takowa yayi zuwa gabana,kafin nace wani abun naji ya hade bakinsa da nawa,ban hanashi ba dannasan dole zai buƙaci hakan sosai.
Sarrafani yakeyi a zafafe har kaina yafara daina ɗaukar darasin.
Cire bakinsa yayi numfashinsa yafara nauyi. Cikin dashashshiyar murya yafara magana.
"Wannan gadon yayi kaɗan,muje ɗaki ina fatan kinada ƙarfin dazaki iya ɗaukar wannan tuzurun koh"
Murmushi nayi tareda ɗaga masa kai.
"Nida na dauki goje waye bazan ɗauka ba?"
Dariyah yayi ganin tsokanarsa nakeyi,ɗagani yayi daga kan gadon zuwa namu ɗakin.
SADI-SAKHNA ce
09035784150
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
*BOOK 2*
...39...
Bayan wata biyu
"Beb ganinan nagama shiryawa ma,hodace kawai ya saura da lip gloss na saka kayan"
"Ohh hayatee awarki biyu kenan kina shirinnan,har inna ta gyara Sayyid sun gama sun shiga mota ke kinanan"
Shagwabe fuska tayi tareda juya masa bayanta.
"Zugemin zip ɗin to nagama shikenan,ga zafi kace saina saka hijabi dogo,motace fah"
"Uhm uhm saka hijabinki kinsan banason gyalennan sosai"
Hijabin ya miƙo mata onion color tasaka kafin yaja hannunta zuwa motah..
Tayi fari ta ƙara kyau ga jiki da cikin ɗan wata shida ya ƙara mata.
Gaban motar tashiga Sayyid da Deejah na baya.
Sai kuma motar da hajiyah Maryam da inna larai suke.
Basuja lokaci sosai ba suka isa garin su Sumaimah Dabagayi,
A baƙin ƙofar gidansu sukayi parking,dan ko gidan su gaji basuje ba,taje can ita tasani aniyarta ta bita.
Sumaimah ce da Deejah suka fara shiga gidan,shaddace a jikinsu iri ɗayah maroon.
Deejah na riƙeda hannun Sayyid saikuma Sumaimah tana riƙeda jakarta.
Tun a bakin ƙofah da sukayi sallama matan gidan suka fara riƙe baki,duk wanda yaganta ya ganeta sai koma ƙofarsa fesawa,kafin wani lokaci gidan ya cika famm da mutane.
Ammi ce tayi ƙarfin halin cewa.
"Sumaimah nake gani ni ƴasu,dama Musbahu yace mana zakizo,amma bai faɗi ranar ba,ashe wai goje ogansu ne a wajen aiki. Ikon Allah Allah mai yadda yaso. Wannan yarinyar fah kaman.....
"Deejah ce baki ganeta bane?"
Turo baki tayi jin yadda suke mata kallon kaman ba ita ba.
"Deejahhh mai cin kazata dai koh"
"Kiji inna rammannan in kazace saina baki kuɗin goma ma"
"Bani kam ko kuɗin koko banida shi ki bani kinji"
Dariyah tayi tana sosa jiki kaman mahaukaciya sabon kamu.
Ganin kallon dasu Sumaimah sukeyi mata yasa ammi yimusu alamar kansu ya kuncene.
Sallama hajiyah maryam itama tayi a cikin gidan. Anan ammi ta shimfiɗamasu tabarma suka zauna.
Yaro aka tura ya ƙira ya ƙira malam uwaisu a bakin masallaci,dan yanxu ba aikin yi nan ya koma zama da dattijan anguwa.
Yana shigowa turus yayi yana kallon su Sumaimah.
"Wannan kamar......."
"Baba nice ya kake ya rayuwa?"
Kuka ya kece dashi tareda zama a ƙasan wajen.
"Sumaimah ki yafeni da abinda nayimiki, na tuba nayi nadama nayi nadama"
"Baba kadaina cewa haka komai ya wuce,sanadin caca yasakani cikin ha'ula'i amma kuma yasaka sanadiyyarsa na gamuda abokin rayuwata,muna fatan masuyi a yanzuma su daina."
"Ina wuni malam uwaisu ya gida?"
"Lafiya kalau ko kece....."
"Nice mahaifiyar goje yanda kuka sanshi kenan"
"Ahah anty Meerah kece koh?"
Shuru tayi tana kallonsa,a tunaninta dai baisan sunan ba kuma wannan sunan?
Zainab ce kawai take ƙiranta dashi.
Tashi yayi daga wajen ya nufi dakinsa,can sai gashi da wani hoto ya miƙawa hajiyah Maryam.
Zaro ido tayi tareda cewa.
"Zainab a ina ka samu hotonta,wanda muka ɗaukane a graduation"
"Itace ai mahaifiyar Sumaimah dama bansan garinta ba da asalinta taƙi faɗamin har ta koma ga mahaliccinta"
Kuka hajiyah maryam ta dungayi tana fadin.
"Rashin riƙe maganata ne yajawo komai,dama duk neman da muka miki kina raye?,Allah ya jiƙanki yamiki rahama. Sumaimah ashe ke ƴata ce bansani ba,ke ƙanwar Neelah ce uwa ɗayah. Wannan zainab ce ƙanwar Muhammad baban Ahmad,kuma mahaifiyar ki"
Lokacin data gama bayanin sai sannan kowa ya fahimceta,Sannan kuma kowa ya gane irin haɗin da Allah yayi wanda bamai iya irinsa saishi.
A ranar an taso da abubuwa da dama da suka wuce,ciki kuwa harda labarin ummah ta da baba ya dunga bayarwa. Ashe ni ƙanwar Neelah ce,ikon Allah.
A sashen yah Musbahu aka sauƙi Ahmad dakuma driver,bayan munci abinci shiga wajennasa nayi. Yana zaune da waya a hannunsa yana dannawa.
Sallama nayi ya ɗago ya kalleni.
"Ummin twins ya gajiyar jiki dai?"
Fadawa nayi jikinsa ya riƙeni kaman jira yakeyi dama.
"Nagaji amma ba sosai ba,idan baka komai inaso muje na nuna maka wani waje"
"Is not fair ma,meyasa ban tuna komai bane har yanxu?"
"Miye kake sauri,likita yace zaka tuna ai muje na nuna maka wani waje,inkuma bakaso toh"
"Inaso muje"
Mota muka shiga mu biyu,nuna masa hanya nake har muka iso anguwar tamu ta da,alama nayi masa ya tsaya kana na fitah.
Wata daba na nufah inda na hangi su yawancin ƴan kungiyarsa ne a wajen,hadda Tunga yanata surutu na siyasa.
A raina nace mai hali baya sanjawa.
Sallama nayi musu,a ciki Tunga ne kawai ya ganeni,bayan mun gaisa alama nayiwa Ahmad akan ya ƙariso.
Kallonsu yake da alama bai sansu ba,yayinda su kuma suke masa kallon mai kama da goje. Ganin hakanne yasa nagane dole nice mai share tantamar nan.
"Tunga kaida sauran ga goje,kaikuma gasu tunga wanda kukayi ta gwagwarmaya tare"
Tun kafin na ƙarisa Tunga ya riƙe hannunsa kaman zayyi kuka.
"Ogah oga ina kashiga mukayi ta nemanka"
Murmushi yayi tareda yimusu takaitaccen bayani. Haƙiƙa yanda aka bashi labarin sudin suwaye a wajensa abune da bazai manta ba.
Kuɗi ya basu tareda address dinsa na abuja kan suzo su sameshi zai Sama musu aiki. Nima naji daɗin abinda yayi sosai,domin sun cancanci hakan a wajensa.
Bayan ya gama dasu hannunsa narike muka nufi hanyar zuwa jeji,da alamar mamaki a fuskarsa amma baice komai ba har muka isa bakin kogon da bazan manta ba.
"Bazan taba manta wannan wajen ba,anannne naji abinda yake cikin zuciyarka gameda ni,ananne muka shirya a matsayinmu na ma'aurata,a nanne nayi jinyarka lokacin da duniya babu wanda yasan hakan saini da Tunga. Kuma shine sanadin shiryuwarka ka fita daga ƙungiyar BC."
Shiga mukayi cikin kogon na tsugunna a inda mukayi ajiyah.
Ganin ina bude wajenne ya tayani muka buɗe.
Akwatin daya sato a daren na fito dashi na bashi.
"Wannan fah"
"Abinda kake tunanin ƙungiyar BC sun sace,kaine kayi rai a tafiyar,Sannan baka kai a ganka ba Neelah ta kawoka nan wajen a ranar tayi maka maganin gaggawa ta tafi. Nice na kulada kai harka warke.
Na rufe sirrin inda abin yake ban faɗawa kowaba,tunda Allah yasa munzo wajen yau gashi na dawo maka dashi,saikayi yanda ya dace dashi"
Buɗewa yayi yaga babu abinda ya sauya a ciki.
Kallon so da ƙauna yakeyimin kowacce tayi aikin jarumta.
"Nikuwa mai zance dake yake wannan baiwar Allah na abinda kika min a rayuwata?"
"Kace Allah ya barmu tare cikin farin ciki,aminci da kuma ƙaunar juna har ƙarshenmu"
"Wannan yana cikin Addu'a ta a kullum"
Rungumeni yayi ina dariya shima yana Murmushi....ohhh ina son mijinah.
Bayan munje naso na kwana biyu amma Ahmad yaƙi,saboda inaso na zaga danginnamu, duk da a baya basu nunamin ƙauna ba,amma badansu zanyi ba ai.
Haka ina gani mukayi kwana ɗaya muka kamo hanyar dawowa, zuwa gidana kuma cikin dangin mahaifiyata,wacce yanzu nasan asalinta.
Bayan shekara biyu da haihuwar ƴan biyuna dukka mata, Maryam da zainab wanda ake ƙiransu Islam da ilham. Dukkansu babu mai kamata,Neelah islam ta iyo,ilham kuma hajiya Maryam har jikin.
Cikin ƙoshin lafiyah na rainesu har na yayesu,lokacin kuma Sayyid yashiga makaranta,wanda yadawo hannuna da zama. Dan so nake nayi masa tarbiyyah yanda ya kamata bata iyayen zamani ba.
Bayan yayennasu makaranta na shiga Jami'a,zan karanci Qur'anic science,dan inada burin sanin ilimi a fannnin,a lokacin ne nayi planing na haihuwa,soyayya kawai muke sha nida mijina Sannan kuma ina samun lokaci na yarana sosai.
****
Ina faka motar dana kasheta shigowa cikin gidan nayi,da islam naci karo ta dawo daga sashen inna larai,wandonta ya jiƙe da fitsari,jijjiga kai nayi dam takaci,magana saita siyarka amma tana fitsari a wando.
"Daga ina kike islam?"
"Gujin inna nake Unni"
"Ina ɗayar taki?"
"Tana bacci gujin inna"
"Kekuma kina yanda kikaga dama koh,yayah fah yana gidan Ummee ko wajen inna "
"Bashu dawoba da abbah"
"Hmm wuce to muje nacire miki wannan wandon"
Saida na gyara mata kafin nashiga kitchen a gurgune,ina cikin yi naji muryar Ahmad a falo shida yaransa.
Jallop ɗin taliya nayi na fita da itah.
Sannu da dawowa nayi masa kafin na juya zan shiga ɗaki..
"Hayatee ke bazaki ci abincin bane zaki tafi yau?"
"Ahah banajin yunwa beb wanka ma nakeson yi,kuci abincinku kada ya huce"
"Ahha baki isa ba dawo ki zauna,banason zama da yunwa,zona baki a baki"
Zaro ido nayi bayan na zauna a gefensa,ganin zai bani kunya a gaban yara na saka hannu mukaci tare.
Kallonsa nake yanda yake sakawa su ilham abincin a baki. A raina nace Alhamdulillah da wannan baiwar da dddaɗar rayuwa.
Nima sainace ALHAMDULILLAH a fili tareda ajiye alƙalaminah. Kuyi haƙuri ta katse littafin a haka,banida zabine exam ta matsoni. Da fatan zaku fahimta. Kowa in bai masa ba yasake maimaita ƙarshen a kundin hasashensa😁.
Godiya ga dukkan makaranta,musamman masu binsa yana da'irar rubutu na gode da kasancewa dani nagode sosai.
Taku a kullum SADI-SAKHNA ke muku sallama da BISSALAM. sai mun haɗu a wani sabon littafin wanda babu rana a yanzu gaskiya. Saboda sabuwar rayuwa na shirin tunkarata ta aure,ina barar addu'ar ku Allah yasa yazomin da sauƙi. Nagode.
THAMMAT BIHAMDULLAH......✍🏼
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21