kai wanan shaidar headquater a ranar nayi hatsari,sannan kafin idona ya rufe dukka naga wata mata da baƙaƙen kaya tazo kaina ta ɗauki na'urar a jikina. Daga nan bansake ganin komai ba.
Kafin duk wannan ya faru kuma dama na fara jin sauyi a jikina,sai nayi abu bansan nayi ba,wani lokacin saina dungajin inason na aikata abinda ba daidai ba,har shaye shaye idan naga anayi sainaji ina so nayi. Kokuma yiwa wani rauni ko lahani.
Abinnan ba ƙaramin firgitani yayi ba Sadeeq saidai babu wanda ya sani,sannan idan nace zanyi bacci saina kasa sam. Ina cikin wannan halinne wannan abin ya sameni. Wanda bansan mai ya faru ba sai jiya na dawo hankalina.
Kuma duk kacemin ina cikin wannan halin na zauna na huta?"
Muryar sa tana rawa ya ƙarisa magana,Sadeeq wanda ya zama tamakar gunki sai yanzu ya motsa jin tambayar da Ahmad yayi masa a ƙarshen bayaninnasa.
"Tabbas wannan ba ƙaramin lamari bane,amma duk da haka kayi haƙuri kasake warkewa,kafin sannan ni nayi maka alƙawarin zan taimaka maka da dukkan iyawata akan wannan abun"
"Nagode da kulawarka zan bari na huta ɗin kaman yanda Abbah ya buƙata,amma kafin sannan inason tambayarka.
Shin ƴan team ɗina sunan nan wanda muke aiki dasu kokuwa?"
"Ehh to Eemran yana nan da Bilal shine ma a kan case ɗin saikuma Neelah"
"Yawwa ka ƙira Neelah ka fadamata zanyi magana da itah zuwa gobe ta shirya"
"Uhm to zan bincika itama naji kaman ana cewa za'ayi mata transfer na wajen aikin"
"Zanyi magana da Abbah akan ya barta,dan a halin yanzu daka kai sai ita kawai na yarda dasu akan case ɗinnan. Zan cigaba ne daga inda na tsaya,zama na anan bazaisa na fasa ba"
"Am AA Hamma na manta ban faɗamaka ba,yanzu haka ma akwai wani case da akeyi da su."
"Case wanne iri?"
"Uhhm wata uku kenan da suka sace nuclear da aka kawo,har yanzu ba gantaba,an bi diddigi har an gaji"
"What nuclear,abinnasu har yakai hakane wai,they need to stop now"
Kaɗo ya sace abu amma ya manta,mai yafi haka takaici🤔
SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah 🙏🏼 ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
Ina ƴan mata dakuma Matan aure masu muradin burge mazajensu da ɗinkuna zuƙa zuƙa. *PHEEDY TOILORING DESIGN* ,suna gabatar muku da ɗinkuna kala kala wanda sukayi daidai da zamani.
Zaku samemu a kan wannan layin waya kamar haka
09167130115
Wato a manhajar whatsapp. Domin ganin kalolin samufurin aikinmu kuma ku tuntubemu a INSTAGRAM da kuma TIKTOK a @pheedyxacks_ragtrade
Muna maraba daku a kowanne lokaci🙏🏼🙏🏼🙏🏼🙏🏼🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
*BOOK 2*
...3...
Uhhhh tasake yunƙurin wani aman a karo na ba adadi.
Tun ranar da mijinnata ya bata tamkar wanda aka buɗe sabon babin rashin lafiyarta.
Duk abinda taci saita amarshi,sati ɗayane kacal amma duk ta rame da fita hayyacinta.
A gari kuwa dukka ya ɗauka cewar goje ya gudu ya bar Sumaimah,wasu ma har suna cewa dan ya ƙasa riƙeta ne ya gudu ya barta..
Murna da farincikin hakan har da su inna rammah a ciki.
A bangaren innar goje kuwa tana iya ƙoƙarinta wajen kulada Sumaimah,haka shima Tunga koyaushe yana kan hanyar kawo magani.
Tun inna tana cewa ya huta harta daina.
Gobe monday hutun da makaranta suka bawa Sumaimah ya ƙare zata koma,duk da sunce zata iya ƙarawa,amma yanzun da take tsaka mai wuya itada ɗan cikinnata,tana ganin batada mafita saina tayi karatun.
Koda gojen bai dawo ba kaman yanda mutane suke faɗa mata,a ƙalla yabiya mata kuɗin karatunta har ta ƙarisa.
Tashi tayi daga wajen aman magar magar ta nufi sashen innan,gaba ɗaya jitake duniyar ta fita mata a rai,meyasa duk lokacin data fara mafarkin daɗi saita farkane kam.
Inna tana kallonta ta ajiye tukar tareda binta da ido har tazo ta zauna a kan tabarmar tana fitar da numfashi.
Kallon ta inna tayi cikeda damuwa,tunda suka dawo daga asibiti bayan kwanansu biyu basu ga goje ba,har yanzu Sumaimah bata cewa kowa komai ba,haka gaji zatazo gulma tayi ta magana,amma daga inna har Sumaimah babu wanda yake kulata.
Kallon inna take da zurun zurun idanuwanta kafin tayi magana cikin dishashiyar murya.
"Inna shin da gaskene abinda kuka fada da kawu,cewar dama bakisan waye goje ba,kawai tsintarsa kuka yi uhm"
"Ba dagaske bane Sumaimah,wannan maganar ba haka take ba,kawaidai shi abinda ya sani kenan"
"To in ba haka bane meyasa zai gudu ya barni inna,saida na kamu da sonsa kuma na ɗauki cikinsa kafin zai gudu,meyasa zayyimin haka?"
"Sumaimah goje ba guduwa yayi ya barki ba,kekanki kin sani har cikin ranki bazai yimiki hakan ba,dan haka ki daina yarda da maganganun mutane yana batamiki rai"
"Amma inna......"
"Sumaimah ki daina maganar nan yanzu,domin bashine mai amfani ba,akwai wani aiki gagarumi a gabanki wanda ni kaina bazan iya taimakonki akansa ba,abinda zanyi iya yimiki ɗayane kawai,amma shima bazan miki yanzu ba saikinyimin alƙawari ɗaya"
"Wanne irin alƙawari"
"Cewar zaki fitar da komai a ranki ki maida hankalin ki kan karatu,sannan ki raini cikinki cikin koshin lafiya,idan kikayi hakan har Allah ya kaimu da rai da lafiya,nikuma zan taimaka miki kikaga mijinki,namiki wannan alƙawarin"
Ɗaga kai Sumaimah tayi alamar ta yarda da zancen innan,daga nan ta yunƙura ta koma ɗaki domin ta kwanta. Duk da batasan mai inna tasani gameda gojen ba,sannan kuma taya zata haɗata da mijinnata ba,amma abu ɗaya tasani shine ta yarda da innan ɗari bisa ɗari,kuma zatayi yanda tace ɗin.
Washagari da safe da ɗan ƙarfin jiki Sumaimah ta tashi,ba kaman jiyaba da take tamkar maza wuƙa.
Kuma tasha maganin da aka kawo mata wanda duk yawanci vitaminne da zai ƙara mata ƙarfin jiki.
Shirin makaranta tayi kana ta fito daga sashen gojen,tun ranar da suka dawo inna tace ta koma ɗakinta amma taƙi,dan haka dole ta ƙyaleta.
Murmushi tayiwa inna tareda gaisheta,fara'arta ta dawo kaman da,saidai fuakarta tayi fayau kaman wacce tayi gudawa.
Koko da ƙosan da inna tasiyo taci,taƙara shan magani kafin tafita zuwa makarantar..
A bakin ƙofar gidan ta gamuda Tunga yana jiranta akan mashin ɗin gojen,nan ma gaisawa sukayi kafin ta hau suka tafi.
A hanya babu wanda yacewa kowa komai har suka isa,saidai abu ɗaya da Sumaimah ta kulada shi shine,Tunga yayi aski yasaka manyan kaya,abinda bata taba gani ba sai yanzu..
"Nagode"
Shine abinda ta faɗa kanta a sunkuye,harta juya zata tafi saikuma taji yayi mata magana..
"Kiyi haƙuri da abinda ya faru,nasan hakan babudaɗi amma in kika daure watarana sai labari,Sannan ina mai tabbatar miki goje yana sonki sosai,bazai taba tafiya haka kawai batareda wani ƙwaƙwƙwaran dalili ba"
"Nasani Tunga shiyasa kullum nake masa fatan alkhairi a duk inda yake,Sannan nake addu'ar Allah ya dawomin dashi watarana"
Kuka ne yakusa subce mata,dan haka cikin sauri tashige makarantar tabar Tunga a wajen.
Bayan ta shiga makarantar kai tsaye ajinsu ta nufa,SS 2,suna ma second term yanzu..
Duk inda ta wulga tsit zakaji wajen yayi kamar an ɗauke ruwa,saita wuce kuma a fara gulamarta. Wannan ko kaɗan baya damunta,dan dama tasan zai faru to tashirya tarbarsa.
Harkar gabanta ta cigaba tayi,tareda yin abinda ya kawota wato karatu,wanda suke magana ma da dasu yanzu ta ɗauke kanta daga garesu..
Da aka tashi bata jira Tunga yazo ɗaukarta ba,saboda batayi niyyar zuwa gida ba.
Hanyar kogon da goje yayi jinya ta nufah,dan ma babu nisa daga makarantar su.
Bayan tashiga ta daɗe a bakin ƙofar shigar kana daga baya ta zube wajen tareda yin zaman durshen.Kukanta tayi ta ƙoshi hankalin ta kwance,musamman data san babu mai jinta.
Sai bayan ta gama kafin ta nufi wani waje can ƙarshen cikin kogon.
Buɗe ƙasar wajen tayi har tazo kan akwatin dayake cikin ƙasar,babbane mai matsakaicin girma na ƙarfe.
Buɗe shi tayi inda tayi arba da wata jaka,saikuma akwatin da goje ya taho dashi a ranar da dawo ɗauke da rauninnan.
Ƙurawa akwatin ido tayi,abubuwa barkatai suna mata yawo gameda shi.
Ɗauke kanta tayi akansa tareda ɗaukan jakar da take gefen wajen.
Saita tuna lokacin da goje ya ajiye jakar suna murmushi itada dashi.
Kuɗin saniyarsa ne daya siyar,saikuma kuɗinsa wanda aka bashi na bangar siyasa. Kasancewar Sumaimah tace batason kuɗin fashinsa shiyasa ya ajiye waɗannan kuɗin,a cewarsa tazo ta ɗauka duk lokacin datake buƙatar wani abun.
A lokacin da hakan yafaru Sumaimah bata kawo komai ba,saima shirmansa tada gani na ajiye kuɗin,sai yanzu data wayi gari babu shi tukunna komai ke dawo mata daki daki.
Maida akwatin tayi da kuma ƙasar bayan ta ɗau jakar,a cikin tata jakar ta makaranta ta saka tareda fitowa daga wajen..
Wannan gurin ya tara wani bangare na tarihinta da bazata taba mantawa.
"Mijina meyasa,meyasa sai lokacin da zuciyata ta faɗa tarkon soyayyar ka tukunna zakayimin ƙaura,a ina kake a faɗin wannan duniya,daka gagara dawowa garemu. Nayiwa inna alƙawarin cewar zan kwantar da hankalina nayi karatu Sannan na raini ɗanmu cikin ƙoshin lafiya,nasan kaima bazaka so ganina cikin damuwa ba koh?"
Ita kaɗai take sambatunta na tsawon lokaci kafin ta tafi gida.
Tashi gidan kenan suka haɗa ido da Deejah,wacce take zaune akan tabarma gefen inna.
Jugum suke zaune babu mai cewa komai,kana ganin idon inna kasan tsoron Deejah takeyi..
Dariya abin yabawa Sumaimah ganin yanda suka zauna ɗin.
"Inna na dawo....ke Deejah meyasa kike hararar inna,har yanzu bakiyi hankali ba ko?"
"Uhm ta harareni mana na dafa abinci na bata"
"Ohh gorin abinci zakiyimin,abincin ma da kaɗan kika bani,naga ban ƙoshi ba"
Kallon kallo suke kaman wasu abokan faɗa,hakan ba ƙaramin dariya yabawa Sumaimah ba.
"Ke Deejah zan faɗawa Musbahu fah abinda kikeyi,daga tafiyarsa jiya shine zaki dawo da halinki koh,to inada number sa yanzu saina ƙirashi"
"Nifah tunda nazo ban kulata ba,kawai zama nayi nace jiranki zanyi. Data gama abinci kuma saita sakamin ɗan kaɗan"
Taƙarisa maganar tana turo baki.
"An saka miki kaɗan ɗin,danace ki sayomin kayan miya ai cewa kikayi bazakije ba,Sannan abincin saida na cika miki faranti,lokaci guda kika tashi dashi kega karutu"
"To kinji Deejah laifinki ne,Sannan ki daina yawan cin abinnan,domin hakan ɗabi'ar jakine,ko kin daina son zama mace ƴar gayun"
"Inaso mana,sai ayita cemin banda hankali so nake nazama mai gayu nima,anan ma zan zauna bazan tafi ba,saina zama ƴar gayu tukunna"
Zaro ido inna tayi jin abinda Deejah tace.
"Anan zaki zauna? A ina kenan?"
"A ɗakinki mana,aradu na dawo gidannan kuma bazan tafiba,dama yah Musbahu ne yake siyamin shayi yanzu daya tafi nasan bamai siyamin,dan haka na dawo gidannan wajen Anty Sumaimah."
"Ahah ahah bazaki zauna a gid......"
"Allah saina zauna inna,naga yah Musbahu ne yace na zo nan ɗin,kuma nazo kice bazan zauna ba,kanki zan hau kome,kuma naga har gadone dake shikenan ya zama nawa"
Tafaɗa cikeda tsalle tana shigewa ɗakin,wata ajiyar zuciya inna tayi tareda jijjiga kai..
Ita kuwa Sumaimah abin dariya yabata,haka kawai sai taji zaman Deejah zayyi mata daɗi,koba komai zata koya mata abubuwa Sannan kuma ta tabbatar taje makaranta kaman yanda Musbahu yake fata.
Itama yayi mata abubuwa da yawa a lokacin baya,babu abinda zatayi masa sai tayashi gyaran rayuwar Deejan.
Sallah ta saka ta tayi na azahar,daga nan tasake wankan zuwa islamiyyah,tana dai cije cije ta tafi.
"Inna dagaske bakyason zama da Deejah,ko inyaso ta koma can wajena ɗakin goje da zama kai?"
"Hhhh ba haka bane Sumaima,tsokanar ta nakeyi kawai,nida na zauna da goje ma wacece Deejah. Zamannata ma zayyi amfani,da alama tanada sauƙin dakuma rashin wayo,wanda zaman jejinne ya tabata. Amma idan har tagyaru za'a ji daɗin zama da ita"
"Uhm nima hakan nake tunani kuma da alama tana buƙatar wanda zai tallafi rayuwarta a wannan lokacin. Ta shiga shekara ta shabiyar fah kaman,kawai wautarta ne da jikinta yasa mutum bazai gani ba.
Yawwa bayan wannan ma dama inason muyi wata magana inna"
"Uhm ina jinki magana wacce iri?"
"Kuɗin da goje ya siyar da saniyarsa wancan watan ni ya bawa,to ban taba ba shine nake tunanin ko zamu fara sana'a dashi. Karmuje kuɗin hannunmu ya ƙare"
"Eh to kinyi maganar hankali anan,amma mai kike ganin zamuyi?"
"Uhm sana'a haka tacikin gida wacce bazamu rasa na kashewa ba,ki kuma kina ganin mu raba biyu mu bawa Tunga wani yafara kasuwanci?"
"Duk yanda kike gani zai dace kiyi Sumaimah domin hangen nesan naki abune mai amfani. Ko aune aune saimu farayi a cikin gidan,akwai wani shagon baban gojen a bakin kasuwa,ko za'a ɗaga shi kai a fara sana'a ciki?"
"To shikenan zanyi magana da Tunga gobe,barina kwanta banajin daɗin jikina sosai"
Tashi tayi ta nufi ɗakin gojen,yana nan yanda yake.
Zama tayi a bakin katifar tana ƙarewa ɗakin kallo,duk sanda tashigo ɗakin sai rayuwar da sukayi ta dawo mata akai,ko mantawa batayi.
SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah 🙏🏼 ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
Ina ƴan mata dakuma Matan aure masu muradin burge mazajensu da ɗinkuna zuƙa zuƙa. *PHEEDY TOILORING DESIGN* ,suna gabatar muku da ɗinkuna kala kala wanda sukayi daidai da zamani.
Zaku samemu a kan wannan layin waya kamar haka
09167130115
Wato a manhajar whatsapp. Domin ganin kalolin samufurin aikinmu kuma ku tuntubemu a INSTAGRAM da kuma TIKTOK a @pheedyxacks_ragtrade
Muna maraba daku a kowanne lokaci🙏🏼🙏🏼🙏🏼🙏🏼🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
*BOOK 2*
...4...
.......BAYAN WATA BAKWAI.
A zaune take tasaka tsinin ciki a gaba da kwanon abinci akan cinyarta..
Ta kumbura tayi ƙatuwa,ga wani uban girma da cikinnata yayi kaman an saka babban mutum a ciki.
Hankalinta kwance take cin garin kwakin kaman ance ta cinye kan wasu su shigo.
Tun daga zaure take jiyo hayaniya tsakanin kursiyyah da Deejah,wanda abune da ya kamata ma su saba dashi,duk sanda aka sakasu sharar gida ko ɗiban ruwa sai sunyi faɗa. Kuma duk yawanci Deejah ce take dukan kursiyyah,gaji tayi masifar har abin ya isheta,tunda ta kula Deejah ba rage mata takeba,gashi batajin maganar kowa idan bata Sumaimah ba.
Yanzun ma kaman kullum shigowa sukayi kursiyyah tana kuka da fashashshen botiki a hannunta,sai Deejah wacce tashigo tana ciccije baki,itama da botikin a hannunta amma bai fasheba.
Hanyar ƙofar su kursiyyah tayi,yayinda Deejah kuma ta iyo inda Sumaimah take zaune tasaka kujera a bakin ƙofar goje.
Da kallo ta bita na alamar tambaya,amma sai tayi biris kaman batasan mai take nufi ba.
"Mai kikayi mata naga kun shigo tana kuka,waye yafasa bokitin hannunta"
Tun kafin Deejah ta buɗe baki tayi magana sukaji muryar gaji tana masifah,fitowa sukayi da tana riƙe da hannun kursiyyah.
"Wannan wanne irin iskanci ne,komai aka ga dama sai ayimaka in kayi magana ace kai jarababbene,to wlh bazai yiyu ba,babu wanda yake ban ci ballantana sha. An kawo bare yazo ya kanainaye gida hadda yin aure,saboda bala'in da aka sakashi a gaba ya gudu ana shirin shekara babu shi babu ɗuriyarsa,hakan bai isaba sai itama matar da batada gindin zama a gidan ta kawo wata ɗosun ɗosa nan tana takurawa ƴaƴan gida? To bazai yiyu ba haka sam"
"Kai gaji kai gaji,waini kam yaushe zaki girma ne ki daina waɗannan abubuwan"
"Dakata Mairo dama nasan zakice haka,barni nayi na more,duk tsiyata dai da masifah ta ban kori mijina da baƙin hali ya tsallake ya barni ba"
"To ita wanene yace miki guduwa yayi ya barta,in ma guduwa mai naki na wannan magana"
"Heee to in ba guduwa yayi ba fatalwa ya koma a gidan yake rayuwa idon mu baya ganinsa,wayasani ma ko cikinne ba nasa ba ko kuma lasarsa take da daddare shiyasa ya gudu"
"Gajiiiiiiii!!!!! Duk abinda zaki faɗa ki faɗa,amma ki daina sheganta min ɗa ko kuma yimin sharrin maita,dan bazan yarda da wannan ba,akan hakan zan iya kaiki ƙara"
Hakan da Sumaimah tafaɗa ya razana ta,domin tariga tasani duk lokacin data kai Sumaimah bango bata jin shakkar maida mata martani.
Duk da haka da masifah tana cinta bata yi shuru,ta ɗage gefen zani sai masifa take.
Deejah wacce take tsaye abin yayi mungun isarta,gashi Sumaimah ta hanata idan gaji tana masifa ta tanka,shiyasa babu yanda zatayi tai shuru.
Dafe goshi Sumaimah tayi tana jin gaji wacce take ta bambami akanta,marar ta taji kaman wani abu ya keta mata,hakan yasa ta ajiye kwanon hannunta tareda da dafe wajen.
Muryar inna taji tana magana.
"To ikon Allah Sumaimah ruwa fah kike zubarwa,ko haihuwa ce kai?"
Bin wajen da inna ta kalla tabi ta kallo itama,kaman dama wacce take jira a gane,nishi ta fara tana kama ciki. Komawa ɗaki inna tayi da gudu ta ɗauko kayan da suka shirya na haihuwar..
Tunga ne ya ƙira mota aka sakata zuwa asibiti,dan dama sunce idan zata haihu a kawota asibiti kar a barta a gida. Saboda tun cikin yana ƙarami jininta ya hau,bai sauƙa kuma sosai ba har zuwa lokacin.
Kai tsaye ɗakin labour aka wuce ta ida,harta fara fita daga hayyacinta..
Ƙarbarta nurses sukayi zuwa ciki,ganin yanda numfashinta yaka sama sama.
Inna ban kuka babu abinda takeyi,Tunga ne da Deejah basuyi kuka ba,saidai fuskarsu ta nuna tashin hankali.
Nurse ce tafito daga cikin ɗakin fuskarta ɗauke da murmushi.
"Mashaallah ta sauƙa,saidai jikinta yayi laushi yana buƙatar kulawa."
"To amma mai ta haifa?"
Inna ta tambaya cikin nuna damuwa.
"Ta samu ɗa na miji,amma shima bazaku samu ganinsa yanzu ba,saboda baya motsi sosai"
"To mashaallah Allah ya rayashi bisa sunnah,itama Allah ya bata lafiya. To yanzu kuma me dame za'a buƙata wa ita mai jegon?"
"Eh to a yanzu kam babu,yawwa kada a yi mata wanka da ruwan zafi,za'a rubuta maganin da zatayi amfani dashi"
Har ta tafi dawo tayiwa innan tuni,saboda tasan halin taurin kai irinna mu na mutanen ƙyauye.
"To shikenan Inshaallah zamu kiyaye,mun gode sosai sosai"
Yanzu inna sai murna take kaman ba ita bace take kuka ba ɗazu.
*SUMAIMAH (POV)*
Tashina kenan ban daɗe ba,abin yaban mamaki wai kwana nayi kass ina bacci,duk ma nasan allura ce sanadi..
Tunda na tashi ishirwa take damuna,har na shanye cikin jug nan da nan,dam ma inna ruwan zafi take bani,gashi bana so haka na daurewa na ƙarba.
Shafa cikina nayi,duk da yana nan da girmansa amma ba kaman jiya ba,wai dama duk ƙaton cikinnan dayake jana a hnayar makaranta ɗa ɗayane a cikinsa,kai gaskiya to kato ne inaga..
Nikaɗai nake wannan tunanin a raina,dan bansan ya yaron yake ba,yanzu ne ma wata nurse suka fita itada inna su kawomin shi.
Ikon Allah wai nice na haihu kuma ɗan goje,abinda ban taba kawowa a raina ba kenan,haka wai gojen zai tafi ya barni har tsawon wannan lokacin.
Ƙarar murda ƙofa naji,hakanne yasa na juyo da kaina ina kallon mai shigowa..
Inna ɗauke da yaron a hannunta,sai Deejah wacce take binta a baya.
Tahowa take amma gani nake kaman bata sauri,domin na matsu naganshi.
Hannu nasaka na karbeshi,duk da jikina bashida wani ƙarfi sosai.
Bacci yakeyi abinsa baisan ma mai duniyar take cikiba,yana kamada goje sosai,saidai kuma ban san miye ba amma akwai wani abu irinnawa a fuskar tasa.
"Anty Sumaimah dawa yake kama toh,nidai kama yakemin da wani ɗan jikin calender a ƙofar chemist ɗin anguwarmu"
Kallon bakida hankali har yanzu Sumaimah tayi mata kafin tace.
"To dama dole yayi miki kamada
Showing 3001 words to 6000 words out of 62659 words
Kafin duk wannan ya faru kuma dama na fara jin sauyi a jikina,sai nayi abu bansan nayi ba,wani lokacin saina dungajin inason na aikata abinda ba daidai ba,har shaye shaye idan naga anayi sainaji ina so nayi. Kokuma yiwa wani rauni ko lahani.
Abinnan ba ƙaramin firgitani yayi ba Sadeeq saidai babu wanda ya sani,sannan idan nace zanyi bacci saina kasa sam. Ina cikin wannan halinne wannan abin ya sameni. Wanda bansan mai ya faru ba sai jiya na dawo hankalina.
Kuma duk kacemin ina cikin wannan halin na zauna na huta?"
Muryar sa tana rawa ya ƙarisa magana,Sadeeq wanda ya zama tamakar gunki sai yanzu ya motsa jin tambayar da Ahmad yayi masa a ƙarshen bayaninnasa.
"Tabbas wannan ba ƙaramin lamari bane,amma duk da haka kayi haƙuri kasake warkewa,kafin sannan ni nayi maka alƙawarin zan taimaka maka da dukkan iyawata akan wannan abun"
"Nagode da kulawarka zan bari na huta ɗin kaman yanda Abbah ya buƙata,amma kafin sannan inason tambayarka.
Shin ƴan team ɗina sunan nan wanda muke aiki dasu kokuwa?"
"Ehh to Eemran yana nan da Bilal shine ma a kan case ɗin saikuma Neelah"
"Yawwa ka ƙira Neelah ka fadamata zanyi magana da itah zuwa gobe ta shirya"
"Uhm to zan bincika itama naji kaman ana cewa za'ayi mata transfer na wajen aikin"
"Zanyi magana da Abbah akan ya barta,dan a halin yanzu daka kai sai ita kawai na yarda dasu akan case ɗinnan. Zan cigaba ne daga inda na tsaya,zama na anan bazaisa na fasa ba"
"Am AA Hamma na manta ban faɗamaka ba,yanzu haka ma akwai wani case da akeyi da su."
"Case wanne iri?"
"Uhhm wata uku kenan da suka sace nuclear da aka kawo,har yanzu ba gantaba,an bi diddigi har an gaji"
"What nuclear,abinnasu har yakai hakane wai,they need to stop now"
Kaɗo ya sace abu amma ya manta,mai yafi haka takaici🤔
SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah 🙏🏼 ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
Ina ƴan mata dakuma Matan aure masu muradin burge mazajensu da ɗinkuna zuƙa zuƙa. *PHEEDY TOILORING DESIGN* ,suna gabatar muku da ɗinkuna kala kala wanda sukayi daidai da zamani.
Zaku samemu a kan wannan layin waya kamar haka
09167130115
Wato a manhajar whatsapp. Domin ganin kalolin samufurin aikinmu kuma ku tuntubemu a INSTAGRAM da kuma TIKTOK a @pheedyxacks_ragtrade
Muna maraba daku a kowanne lokaci🙏🏼🙏🏼🙏🏼🙏🏼🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
*BOOK 2*
...3...
Uhhhh tasake yunƙurin wani aman a karo na ba adadi.
Tun ranar da mijinnata ya bata tamkar wanda aka buɗe sabon babin rashin lafiyarta.
Duk abinda taci saita amarshi,sati ɗayane kacal amma duk ta rame da fita hayyacinta.
A gari kuwa dukka ya ɗauka cewar goje ya gudu ya bar Sumaimah,wasu ma har suna cewa dan ya ƙasa riƙeta ne ya gudu ya barta..
Murna da farincikin hakan har da su inna rammah a ciki.
A bangaren innar goje kuwa tana iya ƙoƙarinta wajen kulada Sumaimah,haka shima Tunga koyaushe yana kan hanyar kawo magani.
Tun inna tana cewa ya huta harta daina.
Gobe monday hutun da makaranta suka bawa Sumaimah ya ƙare zata koma,duk da sunce zata iya ƙarawa,amma yanzun da take tsaka mai wuya itada ɗan cikinnata,tana ganin batada mafita saina tayi karatun.
Koda gojen bai dawo ba kaman yanda mutane suke faɗa mata,a ƙalla yabiya mata kuɗin karatunta har ta ƙarisa.
Tashi tayi daga wajen aman magar magar ta nufi sashen innan,gaba ɗaya jitake duniyar ta fita mata a rai,meyasa duk lokacin data fara mafarkin daɗi saita farkane kam.
Inna tana kallonta ta ajiye tukar tareda binta da ido har tazo ta zauna a kan tabarmar tana fitar da numfashi.
Kallon ta inna tayi cikeda damuwa,tunda suka dawo daga asibiti bayan kwanansu biyu basu ga goje ba,har yanzu Sumaimah bata cewa kowa komai ba,haka gaji zatazo gulma tayi ta magana,amma daga inna har Sumaimah babu wanda yake kulata.
Kallon inna take da zurun zurun idanuwanta kafin tayi magana cikin dishashiyar murya.
"Inna shin da gaskene abinda kuka fada da kawu,cewar dama bakisan waye goje ba,kawai tsintarsa kuka yi uhm"
"Ba dagaske bane Sumaimah,wannan maganar ba haka take ba,kawaidai shi abinda ya sani kenan"
"To in ba haka bane meyasa zai gudu ya barni inna,saida na kamu da sonsa kuma na ɗauki cikinsa kafin zai gudu,meyasa zayyimin haka?"
"Sumaimah goje ba guduwa yayi ya barki ba,kekanki kin sani har cikin ranki bazai yimiki hakan ba,dan haka ki daina yarda da maganganun mutane yana batamiki rai"
"Amma inna......"
"Sumaimah ki daina maganar nan yanzu,domin bashine mai amfani ba,akwai wani aiki gagarumi a gabanki wanda ni kaina bazan iya taimakonki akansa ba,abinda zanyi iya yimiki ɗayane kawai,amma shima bazan miki yanzu ba saikinyimin alƙawari ɗaya"
"Wanne irin alƙawari"
"Cewar zaki fitar da komai a ranki ki maida hankalin ki kan karatu,sannan ki raini cikinki cikin koshin lafiya,idan kikayi hakan har Allah ya kaimu da rai da lafiya,nikuma zan taimaka miki kikaga mijinki,namiki wannan alƙawarin"
Ɗaga kai Sumaimah tayi alamar ta yarda da zancen innan,daga nan ta yunƙura ta koma ɗaki domin ta kwanta. Duk da batasan mai inna tasani gameda gojen ba,sannan kuma taya zata haɗata da mijinnata ba,amma abu ɗaya tasani shine ta yarda da innan ɗari bisa ɗari,kuma zatayi yanda tace ɗin.
Washagari da safe da ɗan ƙarfin jiki Sumaimah ta tashi,ba kaman jiyaba da take tamkar maza wuƙa.
Kuma tasha maganin da aka kawo mata wanda duk yawanci vitaminne da zai ƙara mata ƙarfin jiki.
Shirin makaranta tayi kana ta fito daga sashen gojen,tun ranar da suka dawo inna tace ta koma ɗakinta amma taƙi,dan haka dole ta ƙyaleta.
Murmushi tayiwa inna tareda gaisheta,fara'arta ta dawo kaman da,saidai fuakarta tayi fayau kaman wacce tayi gudawa.
Koko da ƙosan da inna tasiyo taci,taƙara shan magani kafin tafita zuwa makarantar..
A bakin ƙofar gidan ta gamuda Tunga yana jiranta akan mashin ɗin gojen,nan ma gaisawa sukayi kafin ta hau suka tafi.
A hanya babu wanda yacewa kowa komai har suka isa,saidai abu ɗaya da Sumaimah ta kulada shi shine,Tunga yayi aski yasaka manyan kaya,abinda bata taba gani ba sai yanzu..
"Nagode"
Shine abinda ta faɗa kanta a sunkuye,harta juya zata tafi saikuma taji yayi mata magana..
"Kiyi haƙuri da abinda ya faru,nasan hakan babudaɗi amma in kika daure watarana sai labari,Sannan ina mai tabbatar miki goje yana sonki sosai,bazai taba tafiya haka kawai batareda wani ƙwaƙwƙwaran dalili ba"
"Nasani Tunga shiyasa kullum nake masa fatan alkhairi a duk inda yake,Sannan nake addu'ar Allah ya dawomin dashi watarana"
Kuka ne yakusa subce mata,dan haka cikin sauri tashige makarantar tabar Tunga a wajen.
Bayan ta shiga makarantar kai tsaye ajinsu ta nufa,SS 2,suna ma second term yanzu..
Duk inda ta wulga tsit zakaji wajen yayi kamar an ɗauke ruwa,saita wuce kuma a fara gulamarta. Wannan ko kaɗan baya damunta,dan dama tasan zai faru to tashirya tarbarsa.
Harkar gabanta ta cigaba tayi,tareda yin abinda ya kawota wato karatu,wanda suke magana ma da dasu yanzu ta ɗauke kanta daga garesu..
Da aka tashi bata jira Tunga yazo ɗaukarta ba,saboda batayi niyyar zuwa gida ba.
Hanyar kogon da goje yayi jinya ta nufah,dan ma babu nisa daga makarantar su.
Bayan tashiga ta daɗe a bakin ƙofar shigar kana daga baya ta zube wajen tareda yin zaman durshen.Kukanta tayi ta ƙoshi hankalin ta kwance,musamman data san babu mai jinta.
Sai bayan ta gama kafin ta nufi wani waje can ƙarshen cikin kogon.
Buɗe ƙasar wajen tayi har tazo kan akwatin dayake cikin ƙasar,babbane mai matsakaicin girma na ƙarfe.
Buɗe shi tayi inda tayi arba da wata jaka,saikuma akwatin da goje ya taho dashi a ranar da dawo ɗauke da rauninnan.
Ƙurawa akwatin ido tayi,abubuwa barkatai suna mata yawo gameda shi.
Ɗauke kanta tayi akansa tareda ɗaukan jakar da take gefen wajen.
Saita tuna lokacin da goje ya ajiye jakar suna murmushi itada dashi.
Kuɗin saniyarsa ne daya siyar,saikuma kuɗinsa wanda aka bashi na bangar siyasa. Kasancewar Sumaimah tace batason kuɗin fashinsa shiyasa ya ajiye waɗannan kuɗin,a cewarsa tazo ta ɗauka duk lokacin datake buƙatar wani abun.
A lokacin da hakan yafaru Sumaimah bata kawo komai ba,saima shirmansa tada gani na ajiye kuɗin,sai yanzu data wayi gari babu shi tukunna komai ke dawo mata daki daki.
Maida akwatin tayi da kuma ƙasar bayan ta ɗau jakar,a cikin tata jakar ta makaranta ta saka tareda fitowa daga wajen..
Wannan gurin ya tara wani bangare na tarihinta da bazata taba mantawa.
"Mijina meyasa,meyasa sai lokacin da zuciyata ta faɗa tarkon soyayyar ka tukunna zakayimin ƙaura,a ina kake a faɗin wannan duniya,daka gagara dawowa garemu. Nayiwa inna alƙawarin cewar zan kwantar da hankalina nayi karatu Sannan na raini ɗanmu cikin ƙoshin lafiya,nasan kaima bazaka so ganina cikin damuwa ba koh?"
Ita kaɗai take sambatunta na tsawon lokaci kafin ta tafi gida.
Tashi gidan kenan suka haɗa ido da Deejah,wacce take zaune akan tabarma gefen inna.
Jugum suke zaune babu mai cewa komai,kana ganin idon inna kasan tsoron Deejah takeyi..
Dariya abin yabawa Sumaimah ganin yanda suka zauna ɗin.
"Inna na dawo....ke Deejah meyasa kike hararar inna,har yanzu bakiyi hankali ba ko?"
"Uhm ta harareni mana na dafa abinci na bata"
"Ohh gorin abinci zakiyimin,abincin ma da kaɗan kika bani,naga ban ƙoshi ba"
Kallon kallo suke kaman wasu abokan faɗa,hakan ba ƙaramin dariya yabawa Sumaimah ba.
"Ke Deejah zan faɗawa Musbahu fah abinda kikeyi,daga tafiyarsa jiya shine zaki dawo da halinki koh,to inada number sa yanzu saina ƙirashi"
"Nifah tunda nazo ban kulata ba,kawai zama nayi nace jiranki zanyi. Data gama abinci kuma saita sakamin ɗan kaɗan"
Taƙarisa maganar tana turo baki.
"An saka miki kaɗan ɗin,danace ki sayomin kayan miya ai cewa kikayi bazakije ba,Sannan abincin saida na cika miki faranti,lokaci guda kika tashi dashi kega karutu"
"To kinji Deejah laifinki ne,Sannan ki daina yawan cin abinnan,domin hakan ɗabi'ar jakine,ko kin daina son zama mace ƴar gayun"
"Inaso mana,sai ayita cemin banda hankali so nake nazama mai gayu nima,anan ma zan zauna bazan tafi ba,saina zama ƴar gayu tukunna"
Zaro ido inna tayi jin abinda Deejah tace.
"Anan zaki zauna? A ina kenan?"
"A ɗakinki mana,aradu na dawo gidannan kuma bazan tafiba,dama yah Musbahu ne yake siyamin shayi yanzu daya tafi nasan bamai siyamin,dan haka na dawo gidannan wajen Anty Sumaimah."
"Ahah ahah bazaki zauna a gid......"
"Allah saina zauna inna,naga yah Musbahu ne yace na zo nan ɗin,kuma nazo kice bazan zauna ba,kanki zan hau kome,kuma naga har gadone dake shikenan ya zama nawa"
Tafaɗa cikeda tsalle tana shigewa ɗakin,wata ajiyar zuciya inna tayi tareda jijjiga kai..
Ita kuwa Sumaimah abin dariya yabata,haka kawai sai taji zaman Deejah zayyi mata daɗi,koba komai zata koya mata abubuwa Sannan kuma ta tabbatar taje makaranta kaman yanda Musbahu yake fata.
Itama yayi mata abubuwa da yawa a lokacin baya,babu abinda zatayi masa sai tayashi gyaran rayuwar Deejan.
Sallah ta saka ta tayi na azahar,daga nan tasake wankan zuwa islamiyyah,tana dai cije cije ta tafi.
"Inna dagaske bakyason zama da Deejah,ko inyaso ta koma can wajena ɗakin goje da zama kai?"
"Hhhh ba haka bane Sumaima,tsokanar ta nakeyi kawai,nida na zauna da goje ma wacece Deejah. Zamannata ma zayyi amfani,da alama tanada sauƙin dakuma rashin wayo,wanda zaman jejinne ya tabata. Amma idan har tagyaru za'a ji daɗin zama da ita"
"Uhm nima hakan nake tunani kuma da alama tana buƙatar wanda zai tallafi rayuwarta a wannan lokacin. Ta shiga shekara ta shabiyar fah kaman,kawai wautarta ne da jikinta yasa mutum bazai gani ba.
Yawwa bayan wannan ma dama inason muyi wata magana inna"
"Uhm ina jinki magana wacce iri?"
"Kuɗin da goje ya siyar da saniyarsa wancan watan ni ya bawa,to ban taba ba shine nake tunanin ko zamu fara sana'a dashi. Karmuje kuɗin hannunmu ya ƙare"
"Eh to kinyi maganar hankali anan,amma mai kike ganin zamuyi?"
"Uhm sana'a haka tacikin gida wacce bazamu rasa na kashewa ba,ki kuma kina ganin mu raba biyu mu bawa Tunga wani yafara kasuwanci?"
"Duk yanda kike gani zai dace kiyi Sumaimah domin hangen nesan naki abune mai amfani. Ko aune aune saimu farayi a cikin gidan,akwai wani shagon baban gojen a bakin kasuwa,ko za'a ɗaga shi kai a fara sana'a ciki?"
"To shikenan zanyi magana da Tunga gobe,barina kwanta banajin daɗin jikina sosai"
Tashi tayi ta nufi ɗakin gojen,yana nan yanda yake.
Zama tayi a bakin katifar tana ƙarewa ɗakin kallo,duk sanda tashigo ɗakin sai rayuwar da sukayi ta dawo mata akai,ko mantawa batayi.
SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah 🙏🏼 ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
Ina ƴan mata dakuma Matan aure masu muradin burge mazajensu da ɗinkuna zuƙa zuƙa. *PHEEDY TOILORING DESIGN* ,suna gabatar muku da ɗinkuna kala kala wanda sukayi daidai da zamani.
Zaku samemu a kan wannan layin waya kamar haka
09167130115
Wato a manhajar whatsapp. Domin ganin kalolin samufurin aikinmu kuma ku tuntubemu a INSTAGRAM da kuma TIKTOK a @pheedyxacks_ragtrade
Muna maraba daku a kowanne lokaci🙏🏼🙏🏼🙏🏼🙏🏼🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
*BOOK 2*
...4...
.......BAYAN WATA BAKWAI.
A zaune take tasaka tsinin ciki a gaba da kwanon abinci akan cinyarta..
Ta kumbura tayi ƙatuwa,ga wani uban girma da cikinnata yayi kaman an saka babban mutum a ciki.
Hankalinta kwance take cin garin kwakin kaman ance ta cinye kan wasu su shigo.
Tun daga zaure take jiyo hayaniya tsakanin kursiyyah da Deejah,wanda abune da ya kamata ma su saba dashi,duk sanda aka sakasu sharar gida ko ɗiban ruwa sai sunyi faɗa. Kuma duk yawanci Deejah ce take dukan kursiyyah,gaji tayi masifar har abin ya isheta,tunda ta kula Deejah ba rage mata takeba,gashi batajin maganar kowa idan bata Sumaimah ba.
Yanzun ma kaman kullum shigowa sukayi kursiyyah tana kuka da fashashshen botiki a hannunta,sai Deejah wacce tashigo tana ciccije baki,itama da botikin a hannunta amma bai fasheba.
Hanyar ƙofar su kursiyyah tayi,yayinda Deejah kuma ta iyo inda Sumaimah take zaune tasaka kujera a bakin ƙofar goje.
Da kallo ta bita na alamar tambaya,amma sai tayi biris kaman batasan mai take nufi ba.
"Mai kikayi mata naga kun shigo tana kuka,waye yafasa bokitin hannunta"
Tun kafin Deejah ta buɗe baki tayi magana sukaji muryar gaji tana masifah,fitowa sukayi da tana riƙe da hannun kursiyyah.
"Wannan wanne irin iskanci ne,komai aka ga dama sai ayimaka in kayi magana ace kai jarababbene,to wlh bazai yiyu ba,babu wanda yake ban ci ballantana sha. An kawo bare yazo ya kanainaye gida hadda yin aure,saboda bala'in da aka sakashi a gaba ya gudu ana shirin shekara babu shi babu ɗuriyarsa,hakan bai isaba sai itama matar da batada gindin zama a gidan ta kawo wata ɗosun ɗosa nan tana takurawa ƴaƴan gida? To bazai yiyu ba haka sam"
"Kai gaji kai gaji,waini kam yaushe zaki girma ne ki daina waɗannan abubuwan"
"Dakata Mairo dama nasan zakice haka,barni nayi na more,duk tsiyata dai da masifah ta ban kori mijina da baƙin hali ya tsallake ya barni ba"
"To ita wanene yace miki guduwa yayi ya barta,in ma guduwa mai naki na wannan magana"
"Heee to in ba guduwa yayi ba fatalwa ya koma a gidan yake rayuwa idon mu baya ganinsa,wayasani ma ko cikinne ba nasa ba ko kuma lasarsa take da daddare shiyasa ya gudu"
"Gajiiiiiiii!!!!! Duk abinda zaki faɗa ki faɗa,amma ki daina sheganta min ɗa ko kuma yimin sharrin maita,dan bazan yarda da wannan ba,akan hakan zan iya kaiki ƙara"
Hakan da Sumaimah tafaɗa ya razana ta,domin tariga tasani duk lokacin data kai Sumaimah bango bata jin shakkar maida mata martani.
Duk da haka da masifah tana cinta bata yi shuru,ta ɗage gefen zani sai masifa take.
Deejah wacce take tsaye abin yayi mungun isarta,gashi Sumaimah ta hanata idan gaji tana masifa ta tanka,shiyasa babu yanda zatayi tai shuru.
Dafe goshi Sumaimah tayi tana jin gaji wacce take ta bambami akanta,marar ta taji kaman wani abu ya keta mata,hakan yasa ta ajiye kwanon hannunta tareda da dafe wajen.
Muryar inna taji tana magana.
"To ikon Allah Sumaimah ruwa fah kike zubarwa,ko haihuwa ce kai?"
Bin wajen da inna ta kalla tabi ta kallo itama,kaman dama wacce take jira a gane,nishi ta fara tana kama ciki. Komawa ɗaki inna tayi da gudu ta ɗauko kayan da suka shirya na haihuwar..
Tunga ne ya ƙira mota aka sakata zuwa asibiti,dan dama sunce idan zata haihu a kawota asibiti kar a barta a gida. Saboda tun cikin yana ƙarami jininta ya hau,bai sauƙa kuma sosai ba har zuwa lokacin.
Kai tsaye ɗakin labour aka wuce ta ida,harta fara fita daga hayyacinta..
Ƙarbarta nurses sukayi zuwa ciki,ganin yanda numfashinta yaka sama sama.
Inna ban kuka babu abinda takeyi,Tunga ne da Deejah basuyi kuka ba,saidai fuskarsu ta nuna tashin hankali.
Nurse ce tafito daga cikin ɗakin fuskarta ɗauke da murmushi.
"Mashaallah ta sauƙa,saidai jikinta yayi laushi yana buƙatar kulawa."
"To amma mai ta haifa?"
Inna ta tambaya cikin nuna damuwa.
"Ta samu ɗa na miji,amma shima bazaku samu ganinsa yanzu ba,saboda baya motsi sosai"
"To mashaallah Allah ya rayashi bisa sunnah,itama Allah ya bata lafiya. To yanzu kuma me dame za'a buƙata wa ita mai jegon?"
"Eh to a yanzu kam babu,yawwa kada a yi mata wanka da ruwan zafi,za'a rubuta maganin da zatayi amfani dashi"
Har ta tafi dawo tayiwa innan tuni,saboda tasan halin taurin kai irinna mu na mutanen ƙyauye.
"To shikenan Inshaallah zamu kiyaye,mun gode sosai sosai"
Yanzu inna sai murna take kaman ba ita bace take kuka ba ɗazu.
*SUMAIMAH (POV)*
Tashina kenan ban daɗe ba,abin yaban mamaki wai kwana nayi kass ina bacci,duk ma nasan allura ce sanadi..
Tunda na tashi ishirwa take damuna,har na shanye cikin jug nan da nan,dam ma inna ruwan zafi take bani,gashi bana so haka na daurewa na ƙarba.
Shafa cikina nayi,duk da yana nan da girmansa amma ba kaman jiya ba,wai dama duk ƙaton cikinnan dayake jana a hnayar makaranta ɗa ɗayane a cikinsa,kai gaskiya to kato ne inaga..
Nikaɗai nake wannan tunanin a raina,dan bansan ya yaron yake ba,yanzu ne ma wata nurse suka fita itada inna su kawomin shi.
Ikon Allah wai nice na haihu kuma ɗan goje,abinda ban taba kawowa a raina ba kenan,haka wai gojen zai tafi ya barni har tsawon wannan lokacin.
Ƙarar murda ƙofa naji,hakanne yasa na juyo da kaina ina kallon mai shigowa..
Inna ɗauke da yaron a hannunta,sai Deejah wacce take binta a baya.
Tahowa take amma gani nake kaman bata sauri,domin na matsu naganshi.
Hannu nasaka na karbeshi,duk da jikina bashida wani ƙarfi sosai.
Bacci yakeyi abinsa baisan ma mai duniyar take cikiba,yana kamada goje sosai,saidai kuma ban san miye ba amma akwai wani abu irinnawa a fuskar tasa.
"Anty Sumaimah dawa yake kama toh,nidai kama yakemin da wani ɗan jikin calender a ƙofar chemist ɗin anguwarmu"
Kallon bakida hankali har yanzu Sumaimah tayi mata kafin tace.
"To dama dole yayi miki kamada
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2 Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21