nan"
Saida yayi magana nakula ashe ba kayan aikine a jikinsa ba,har yayi wanka ma da alama,tunda ga nan damshin ruwa a jikinsa.
Kawowa abincin nayi na ajiye a gabansa,daidai lokacin da yake sanja tashar tv.
"Yau ka dawo da wuri"
A hankali nayi maganar,banyi zaton ma zaiji ba.
"Uhm"
Naji yabani amsa.
Daga nan shuru ne ya gibta harna gama zuba masa abincin na miƙamasa.
Karba yayi kafin na ajiye yasaka a gabansa. Yanda ba bata lokaci yafara saka abincin a bakinsa har saida yabani dariya,amma a yanzu banida wannan mood ɗin.
"Me yake damunki?"
"Ehh!!"
Bansan lokacin dana bashi wannan amsar ba,tambayar tasa ta razanani,ni yake tambaya wai me yasameni?
"Ehh haka nace mai ya sameki,yau naga yanayinki ya sauya ba kaman kullum ba,bakida lafiya ne?"
"Ahah babu komai,zan iya tafiya idan baka buƙatar komai?"
Jin shuru baiyi magana ba yasa na ɗaga kai na kalleshi,ashe kallona yake tsawon lokacin. Kuma kallone mai ɗauke da alamar kulawa,ban taba ganin ya bini da irin wannan kallon ba sai yau.
Garamm mukaji shigowa cikin falon kaman an jefo bauna.
Ɗaga ido nayi na kalleta cikeda takaici, gabaɗaya wannan kuwa tasan mai ake ƙira da hankali. Barima na tashi na tafi,domin bazan juri wani tension ɗin ba.
"Ka gama da abincinne?"
Na tambayeshi har Sannan fuskata ɗauke da damuwa.
Ɗaga min kai kawai yayi,har sannan bai daina bina da kallon tambaya ba.
Kwanukan na ɗebe na nufi kitchen,ta gefensa na wuce tana tsaye ta naɗe hannaye,batamin magana ba bayan hararar dayayimin,nima kuma dama hakan nake so ai.
Juye sauran abincin nayi na wanke kwanukan,tun daga kitchen ina jiyo maganar Mulaifah,amma dai banajin abinda take cewa sosai.
"Haba D mai yasa kakemin hakane, karka manta fah har an kusa aurenmu wancan abin ya faru,kasan kuwa irin halinda na shiga. Dana jure sai gashi komai ya wuce.
"Wai nikam banaji ance kinyi aure ba,maiyasa kika kashe shi?"
"Saboda bazan iya zama da wani ba idan bakai bane"
"Shine kawai hujjarki"
Ba kunya ta ɗaga masa kai kuwa.
"Hmmm ki tashi ki barmin sashe,karki ga don na amince da aurenki kiyi tunanin cewar domin ke na amince,hakan bazai sauya komai ba daga kallon danake miki"
"Karka ce haka D nasan zaka soni idan muka fara zama tare ina ƙarƙashin ikonka."
Daga haka ta tashi tabar falon,duk da maganganun daya faɗamata amma ko kaɗan basu wani dameta ba,tunda burinta na zama matarsa zai cika.

Da daren ma yau bamu huta ba,ummi sai mita takeyi,gwara suma sunsan ana hakan a gidan,nida bansani ba fah.
Idan akwai abinda za'a tattauna daman ana ƙiran family meeting irin haka. To ranar dukka masu aiki zasu haɗu suyi aikin,ayi dinner tare a babban falo kowa ya tafi bayan an tattauna.
"Mtsww ko akan me za'ayi wannan meeting ɗin kuma oho"
Ummi ta faɗa wacce take zaune a kan kujerar kitchen ɗin..
Kallo ɗaya nayi mata na ɗauke kaina tareda cigaba da zuba fried rice a cikin warmer.
Muryar inna ladiyo mukajiyo tana shigowa.
"Kun shirya komai da komai kuwa,kowa fah ya hallara yakamata akai abinci zuwa yanzu"
Cikin sauri na ƙarisa zuba abincin na ɗauka na fita.
Kaina a ƙasa na ajiye abincin a tsakiyar table ɗin.
Suna zaune a can tsakiyar falon,ban da hayaniya babu abinda sukeyi.
Dama haka sukeda ɗan yawa. Amma duk yawanci ƴan uwan hajiyah Mammah ne,sai ƙanwar babansu wacce take aure a maiduguri da ƴaƴan ta manya haka,Hajiya Aina'u sunata hira itada Maimuna.
Sai Fatee kuma da suke kallon abu a waya itada wacce naji ƴar hajiyah Aina'u ce Muneerah.
Bayan mun gama jejjera komai da ɗaɗɗai da ɗaɗɗai suka fara zama a dinning ɗin.Wajen ya cika har Alhj Aliyu ma yazo da hajiyah Mammah.
Kowa sai gaisheta yake ana mata ya jiki,saboda ƙafarta tana ciwo abinka da jiki ya sha miya.
"Ahh how sweet,ba'a tabayin family meeting da zayyi min daɗi ba sai wannan"
Mulaifah ce ta faɗa wacce take zama a kujerar da babu kowa akai.
Blue material ne a jikinta yanata sheki,kaman wanda aka cemata yaune bikin.
Bayan an zazzauna iya manya masu wayo ne kawai a wajen,ƙananan yara kuma inna ladiyo da mai aikin hajiyah Mammah inna kareema sun tafi dasu.
Shuru wajen yayi naga kowa ya juya yana kallon ƙofah,nima waiwayawa nayi ina zubawa hajiyah Maryam abinci.
Caraf idona ya sauƙa a cikin nasa,don tunda ya shigo wajen idonsa akaina yake.
Inda nake ya nufo kai tsaye,mai kuma zayyimin ya taho wajena.
Kujerar danake gabanta naga yana shirin ja,hakan yasa na jamasa ya zauna kana na matsa. Fuskar mutanen wajen na kalla,dukkansu kowa yayi mamakin zuwan Ahmad wajen da alama,banda Alhaji Aliyu dakuma Mulaifah wacce take ta washe baki kamar gonar auduga.
Plate ɗin gabansa na ɗaga zan saka abinci,wani kallo yayimin nasan na gargaɗi ne,amma sai nayi kamar ban ganshi ba.
Zuba masa nayi na tura gabansa,haɗa ido mukayi amma bansan ya akayi ba na samu kaina nuna masa babu komai da idona.
Sauƙar da kai yayi tareda jan abinci gabansa kamar wanda akayiwa yaro dole.

Duk wajen babu wanda ya kulada abinda ya faru sai hajiyah Maryam,Saleem da kuma Sameer.
A tare nida ummi muka bar wajen,ganin yanzu lokacin sune na tattaunawa.
"Kai nifah masu kuɗi suna bani mamaki,to shi wannan zama a ci abincin menene amfaninsa ne?"
Ƴar dariya nayi kafin nace.
"Uhm kowanne ɗan adam yanada tsarin yanda Allah yayi masa rayuwarsa ummi,su wannan ce hanyar da suke bi wajen haɗuwa da ƴan uwansu,bakya ganin waccar ƙanwar babannasu har daga maiduguri tazo?"
"Uhm ummi dan Allah zoki kai wanann yarinyar tana ta kuka mana"
Lokaci guda ta haɗe fuska,
"Haba inna ladiyo kinsan fah banason shiri da yarannan,ita ɗin menene bazata rike yarinyar nan,su waɗannan masu kuɗin malalata ne"
Kallon yarinyar nayi wacce take ta tsala kuka gata ƙarama. Da kuma ummi wacce take zuba mita.
Kodan nima uwa ce,haka kawai na tsinci kaina da jin tausayin yarinyar.
"Inna kawo ta na kaita,tanata kuka bakinta har ya bushe"
Daidai shigata cikin falon najiyo muryar Alhaji Aliyu.
"Dukka nayi magana dasu kuma sun amince,kuma tunda ba abune na fari ba,kuma akwai halin yin na yanke wani satin za'a ɗaura musu aure"
"Sati ɗaya yayi kaɗan,a matsayina na matar gidannan kuma mai iko da komai to ban yarda ba"
Kowa kallon hajiyah Maryam yayi,jin yadda tayi maganar a dake.
"Meyasa zakice haka,menene dalilinki na ƙin amincewa"
"Maimuna ta yimaka zancen akwai wanda suka daidai ta zaizo wajenka,sai kace sai kayi tunani,haka Fatee kafi kowa sanin soyayyar da suke da Sadeeq amma baka bawa abin hankalin ka. Meyasa sai wannan da bawani damuwa yayi da abinba kake ƙoƙarin saishi zakaga kawai yayi iyalansa?"
Sakin baki Alhaji Aliyu yayi,ya rasa meyasa hajiyah Maryam take masa irin wannan tsanar,yana zure cin zarafinta in suna su kaɗai amma a bainar jama'a abin da cin rai.
Cikin fushi Aina'u ta ajiye cokalinta tareda fuskantar hajiyah Maryam..
"Wai Maryam mai yake damunki,meyasa bakya iya boye zafin kishinki da hassadarki akan rayuwar Ahmad,kodan saboda kinga shine babba ba ƴaƴan ki ba shiyasa?"
Ƴar dariya hajiyah Maryam tayi kafin tace.
"Baƙin ciki da kishi,na me kenan. Inda ɗansa ne shi da saiki cemin zanyi kishi kokuma nayi baƙinciki,amma babu wanann tunda ba ɗansa bane."
"What maryam wannan wane irin shirme kikeyi haka?"
"Shirme haka kike gani shirme nake? Ahmad ba ɗan Alhaji Aliyu bane, Maimuna itace ƴarsa tafari,idan kuma baki yarda ba ga nan uwarki da kuma yayannaki ki tambayesu. Dan haka batun nayi masa baƙinciki ki ajiyeshi a gefe,in kinga yaci gadon Alhaji Aliyu to ƴaƴana ne dukka suka mutu"
Tana gama faɗin hakan ta tashi daga kan kujerarta hankalin ta kwance ta bar wajen.
Idone ya koma kan Ahmad,wanda ya rumtse cokalin dayake hannunsa ƙam kaman zai maidashi cikin hannun,bakinsa yana rawa ya kalli AM Aliyu da jajayen idanuwa.
"Abbb......abba shin dagaskene abinda matarka take faɗa?"
Runtse ido shima AM Aliyu yayi,saboda bashida ƙarfin gwiwar kallon idon Ahmad ɗin ya tabbatar masa da abinda yakeson sanin.
Kuka hajiyah Mammah ta rushe dashi tareda saka gefen zaninta tana sharewa.
Tunda naji abinda hajiyah Maryam ta faɗa na zama tamkar gunki a wajen,shin ni wannan matar wacce iri cene.
Gaba da gaba muka tsaya da taxo zata fita daga falon. Wani shu'umin murmushi tayimin bayan ta dafa kafaɗa kafin tabar wajen.
Juyawa nayi nabi hanyar data bi da kallo.
Bangazata naji mutum yayi yafice daga wajen,iya bayansa kawai na samu gani,tafiya yake kaman zai tashi sama don sauri..
Ohh dagani har shi sai wahala muke sha a bangare mabambamta,shin yaushe komai zaizo da saukine?.
Hankalina yayi gaba ji nayi an fizge yarinyar data ke hannuna tana kuka.
Hanyoyi biyu na kalla wanda suke hannun riga.
Wajenda Ahmad yayi da kuma wajenda hajiyah Maryam tayi.
Shin ita zanbi naji mai yake faruwa,kokuma shi zanbi domin na tausheshi akan halin da yake ciki?
Ku fadamin a comment shin wacce hanya kuke ganin yakamata tabi a ciki?😄😄





SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.



*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)


Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150

Bismillahir-rahmanir-raheem


Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.





Sister's duk wacce batayi anfani da sabulun mg's ba ko kit dinsu inamai shaidamuku anbarku acan baya domin duk wnd yajaraba mg's sai sanbarka duk wani Mai tantama Akan kayan gyaranjiki toh tabbas yacire sabulun mg's domin yahadu bakarya zegyarajiki yafidda dattin fata Dama duk wani matsalan fata duk Wanda kefama da matsalan fata walau pimples ko spot, sunburn acne,stretch mark dama dukkan wani prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari bayan jikinku yy fresh zaisa jikinku yy smooth yadinga glowing,gawanda basa San anfani da Mai zaku iya using mg's batare da kunbukaci wani Mai b🤗nd wnn new soap din💣ne,😯 bama cika Baki kujaraba kugane ma idanku domin ance gani yakoriji Kuma siyan daya maida kudi gida
You can check pic👇for the soap reviews🥰
Soap price:4k
maiso yy mgn
08062991549
07046881166
07067210195
Call 08064532391
Instagram:glow_with_mgs
Facebook: mg's skincare

Masu bukatar cream Shima munadashi harda ma complete set nagyaranjiki
Small 14k
Babba 16k

Munatura Kaya kowani gari dayardar Allah Amma delivery is not free

Be part of the glow team😍karkubari abaku lbr👏





*BOOK 2*
...19...




Hayaniya ake tayi a cikin ɗakin taron,kaf cikinsu babu wanda yayi tunanin a haka abin zai kasance. Kowa yana faɗin albarkacin bakinsa.
Yayinda Sumaimah kuma aka barta a tsaye tamkar gunki a kan mashigar wajen.
Kallon kallo take bawa bangaren guda biyu,da alama ja'inja take da ƙwaƙwalwarta kan wacce hanya zatabi. Hanyar sashen hajiyah Maryam ta nufah,domin a yau kam tanada buƙatar son jin menene maƙasudin faruwar komai,menene ainihin tarihin abinda yake faruwa?.
Har takai daidai shiga sashennata,saikuma wata zuciyar ta tuna mata mijinnata,shin a wanne hali yake a yanzun,gashi bashida kowa a gidan bare ya waiwayi lamarinsa,kuma a wannan yanayin dayake ciki yana buƙatar mai zama a kusada shi.
Juyawa tayi da akalar tafiyar tata zuwa sashennasa. Tafiya take ranta cikeda abubuwa masu dama.
Kai tsaye ɗakinnasa ta wuce,a bakin ƙofar dakin ta tsayah tana kallonsa,yana zaune a tsakiyar gado ya saka gabansa can. Daga bayannasa mutum na iya gano yanda ƙirjinsa yake sama yana ƙasa.
Jan ajiyar zuciya tayi kafin tafara takawa a hankali zuwa inda yake.
Tunda ya tambayi Abbansu yaga yayi shuru,hasalima yakasa haɗa ido dashi,hakan ya tabbatar masa da abinda hajiyah Maryam tafaɗa dagaske takeyi. Wani duhu yagani,yayinda duniyarsa ta tsaya na wasu daƙiƙu,shi ba ɗan Alhaji Aliyu bane,to kenan wanene ubansa,shegene shi ina mahaifiyar sa,an ce ta mutu,waye mijinta kenan,kokuma dawa tayi tarayyah,ko tsintoshi sukayi kai.
Wannan kalaman sune suke ta yawo a ƙwaƙwalwarsa har ikon Allah yakaishi ga sashensa,babu cire takalmi haka ya hau kan gadonnasa, ƙirjinsa ya riƙe gam jin yana yimasa wani hawa da sauƙa kaman ana famfo.
Jinsa yayi tamkar shi kaɗaine a duniyar,bashida kowa ballantana yasamu wanda zai zauna dashi a wannan zazzafan yanayin.
Hawaye ne zafafa suka fara kwaranyowa daga cikin idanunsa. Rayuwarsa kullum cikin karbar baƙuncin sabon abu takeyi,shin yaushe wannan abin zai ƙare?.
Tsayawa yayi da tunanin jin hannu ya daga bayansa,wanene ya tuna dashi yazo wajensa a wannan halin,a saninsa dai Sadeeq bayanan kuma bai san mai yake faruwa ba.
"Lafiya kake? Karka damu komai zai wuce sai labari,hakan jarabawa ce wanda idan ka jure ka cinyeta zakaga sakamako Mai kyau"
Sumaimah ce take yimasa maganar cikin sanyayyiyar zuciya mai cikeda alamar rarrashi,duk da itama tana cikin damuwar amma yanda yakeji tasan yafi nata.
Kanta ta ɗora a bayansa tana cigaba dayimasa maganganun da tun baya fahimta har yafarajin mai take faɗa.
Zogin da zuciyarsa take masa ne yasashi sakin wani wahalallen nishi,jij hakan yasa Sumaimah dawowa gabansa da sauri.
Cikeda damuwa take kallon shanyayyun idanuwansa,masu cike da abubuwa kala kala.
"Ƙirjinahhhh"
Shine abinda ya tsinci kansa da furta mata a hankali.
Hannunta tasaka a saitin ƙirjinnasa kai tsaye bata kawo wani abu a ranta,idon da zare jin yadda take bugawa da matsanancin gudu fiyeda na kowanne lafiyayyayen ɗan adam.
"Tana bugawa da ƙarfi,yakamata na sanarwa Saleem da sauri"
Ƙoƙarin sauƙa take akan gadon yayi saurin riƙo hannunta.
"Karki ƙiramin kowa,banason kallon wani daga cikin ahalinnan kowaye shi a yanzu"
Kallonsa take da alamar tausayi,kaman ƙaramin yaro haka taga ya koma mata a lokacin. Batasan sanda zuciyarta ta ɗebeta da rungumeshi ba. Ga mamakin ta kuma sai taji shima ya maryar mata da martani.
Duk da cewar yasan kusancinta dashi a lokacin ba abune mai kyau ba,amma kuma samunta a gefennasa ya rage kaso mai yawa na damuwarsa,saboda abune da bai fiye samu ba. Shiyasa ya tsinci kansa da kasa hanata,saima sake sakemata da yayi.
Sun daɗe a haka rungume da juna kafin yasaketa tareda cikin sanyin jiki.
Kunyace takamata ta dawo hayyacinta data tuna mai ta aikata,duk da tasan hakan ba laifi amma kuma shi zaiji ya aikata laifin a ransa..
Saurin sauya iskar wajen tayi tareda sauƙa daga kan gadon. Hanyar banɗaki ta nufah da sauri tana magana.
"Uhm barina haɗamaka ruwa kayi wanka gumi kakeyi,kafin ka fito kuma na haɗamaka shayi"
Ƙofar data rufe yabi da kallo tareda jijjiga kai a hankali. Ya rasa meyasa yake idan yana tareda itah sai yarasa nutsuwarsa da taka tsantsansa,he can't imagine wai ya rungume mace kuma ba muharramarsa ba,sannan baiji dana sani sosai a ransa ba. Kodai kai bai warke ba daga halayyar daya gamu da ita a baya? Amma kuma ai bayajin son yin komai banda wannan ɗin.

Bayan ya fito daga wankan ƙaramar riga yasaka da kuma wando 3 quater,ganin bai ganta a ɗakin ba yasa ya fito falon,nan ma batanan,amma yana tsaye yaga ta fito daga kitchen hannunta ɗauke da kofi.
A gaban kujerar dayake zama kullum ta ajiye,itama kuma ta zauna a gefe.
Har tagama komai yana nan tsaye a bakin ƙofar ɗakinsa yana kallonta,shidai yasan wani abu yakeji gameda wannan matar a cikin ransa.
Da hannu ta nuna masa yazo ya zauna,ganin ya tsaya kaman wani soja (ohh dama sojanne ashe).
"Ciwon ƙirjinnaka ya lafa ne kokuma na samomaka maganin?"
Ajiye cup ɗin hannunsa yayi tareda yin ɗan ƙaramin murmushi.
"Idan nace ki nemo min maganin a ina zaki nemo?"
"A inda yake zan nemo"
"Wanne magani zakice a baki?"
"Uhmm maganin ciwon zuciya idan akayi mata abinda ba daidai ba"
Maganar tata ce ta bashi dariya,agogon ɗakin ya kalla.
"Dare yayi yakamata ki tafi"
"Uhm amma zaka iyah........"
"Am not a child Sumaimah,nasaba da irin wannan yanayin zan kulada kaina. Nagode da kulawarki,amma kusancin mu yana yawa,kada ya wuce mizani"
Ɗaga masa kai kawai tayi,domin batada tacewa a yanzun.
Rakata yayi har bakin ƙofa ta fita shikuma ya rufe.
Dare yafara kam,don goma ta wuce,saidai akwai farin wata daya haska gidan.

"Kinƙirani mommy,shin mai yake faruwa?"
Neelah ta tambayi hajiyah Maryam wacce take zaune ta haɗa kai da gwiwa.
Magana neelah tacigaba dayi mata,amma kuma babu wanda ta amsa mata a ciki,hasalima ko ɗagowa batayiba daga tsugunnen.
Zama tayi a bakin gadon kusada itah kana ta sauƙe wani gwauron numfashi.
Sun daɗe a hakan kusan awa guda, hajiyah Maryam batace komai ba,itakuma Neelah ta gaji da tambayarta.
"Sumaimah batazo ba,baki haɗu da ita a hanya ba"
"Uhm banganta ba"
"Ta zabeshi kenan,banyi tunani ba amma tayi zabi mai kyau,takan tsallake duk abinda bana zato"
"Mai ya faru ne a gidan?"
"Duk da a idonta akwai tsananin buƙatar son jin abinda yake faruwa,amma ta zabi kasancewa dashi."
"Wa kike magana akai?"
"Sumaimah"
"Gata nan tashigo fah"
Ɗagowa Hajiyah Maryam tayi daidai shigowar Sumaimah cikin ɗakin,wato ba ɗaya ta zaba ba,ta yanke shawarar zuwa kowanne bangarene.
Takowa tayi har zuwa gaban hajiyah maryam ɗin,fuskarta a dake kaman wata soja a fagen yaƙi.
"Meyasa?"
Shine tambayar data samu ikon furtawa hajiyah Maryam,duk da kuwa a cikin ranta ba iyah hakan taso ta tsayaba.
"Meyasa me?"
"Ba ɗanki bane? Meyasa zaki masa haka,ko meyasa kike masa haka?"
"Saboda shiɗin ɗana ne shiyasa nayi masa hakan,idan ba ɗana bane bazan damu dashi harna bada rayuwata akansa ba"
"Amma abinda kikayi a cikin bainar jama'a hakan kaman ba taimakonsa kikayi ba,saima sakashi a cikin wani tsatstsauran yanayi"
"Taimakonsa nayi Sumaimah,saidai shi taimako kala kala ne da kowacce uwa da irin hanyar da takeyi akan ƴaƴan ta. Ni tawa ƙaddarar kenan taimakonsa a ta hanyar dazai ga kaman cutar dashi nake,kokuma wani daga gefensa"
"Taimako??? Menene dalilin yin wannan maganar toh,shegantashi kikayi fah a gaban kowa,kince shi ba ɗan Alhaji Aliyu bane,to ɗan waye kenan baki faɗaba?"
"Batun ɗan waye karki damu kanki,yanada uba wanda ba kowanne ɗa ne ma yake iya dacen samunsa a uba ba" dalilina nayin hakan kuwa ke baki san komai ba.
Siddabarun da Mulaifah tayi masa,tayine akan Alhaji Aliyu,amma kuma ba iya nan zai tsayaba,shima Ahmad anyi asirin da idan Alhaji Aliyu ya tambayeshi to dole sai ya amince,a matsayinsa na mahaifinsa.
Sai yana ganinsa a matsayin mahaifinsa tukunna asirin zayyi tasiri,wanda bazai karyeba har sai anyi auren.
Hakanne yasa nayi amfani da gaskiya na farfaɗo dasu daga tarkonta. Yanzu da Ahmad ya daina ganin Alhaji Aliyu a matsayin mahaifinsa to asirin ya karye akansa"
"To amma sai kinbi ta wannan hanyar kafin ki karya abin jikinnasa,abinda kika faɗaba i think ya tona abinda bai kamata a tona ba ne na tsawon lokaci,kinaga hakan bayyi yawa ba"
"Yawa?? Hmmmm Sumaimah kenan!! Abinda nayi a yau ɗin shine ya dace ayishi tun shekara talatin baya,dan haka banji wani ɗar ko jin babu daɗi akan abinda nayi,hasalima tsuntsaye biyu na jefah da dutse ɗaya. Shin kinsan mai zai faru idan banyi abinda nayi yau ba?"
Jijjiga kai Sumaimah tayi,harda Neelah wacce ta tsaya ƙyam tana kallonsu su biyun,kuma ta fara ɗago mai yake faruwa.
"Nafarko zan mutu,Mulaifah zata mutu sannan shima Ahmad bazata barshi ba zata kasheshi. Wannan shine kaɗan daga abinda zai faru,to kinga banida zabi face yin hakan,duk da raina dana Ahmad zai sosu akan hakan"
Mutuwa kuma,abin har yakai hakane,to waye mai ƙullah hakan,waye ya hana gidan gabaɗaya zama lafiya,idan har zancen da hajiyah Maryam ta faɗa gaskiya be,cewar ba itace takeyin abubuwannan ba?.
"Hajiyah Maryam shin idan nace na yarda dake har raina,zaki bani labarin abinda yake faruwa?"
"Bazan baki ba,saboda baki yarda dani ɗin ba,saidai zan baki dan wani abun daban"
"Menene?"
"Saboda ke ɗin kin zama ɗaya daga cikin a halinnan,ko ki yarda ko kowa
Showing 30001 words to 33000 words out of 62659 words