*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)


Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150

Bismillahir-rahmanir-raheem


Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah 🙏🏼 ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.



Ina ƴan mata dakuma Matan aure masu muradin burge mazajensu da ɗinkuna zuƙa zuƙa. *PHEEDY TOILORING DESIGN*,suna gabatar muku da ɗinkuna kala kala wanda sukayi daidai da zamani.
Zaku samemu a kan wannan layin waya kamar haka


09167130115
Wato a manhajar whatsapp. Domin ganin kalolin samufurin aikinmu kuma ku tuntubemu a INSTAGRAM da kuma TIKTOK a @pheedyxacks_ragtrade

Muna maraba daku a kowanne lokaci🙏🏼🙏🏼🙏🏼🙏🏼🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻



*BOOK 2*
...1...



Yana shigowa kaman yanda Sadeeq yayi shima haka yayi,ganin wani a akan kujera mai kama da ɗansa,wanda ya fidda saka ran ganinsa tsawon shekara biyar,yau gashi yana kallonsa a gabansa tamkar alamara.
A hankali yake tafiyah har yana dafa hannun kujera saboda kar ƙafafunsa su kasa ɗaukarsa i zuwa ga gudan jinin nasa..
Hannu yakai wanda yake rawa kan kumatun Ahmad ɗin,wanda yayi tafiya cikin duniyar suma bai san mai suke ba.
"Ah......ahhmmad dama kana raye duk tsawon wannan shekarun,toh ina ka shiga hakane bamu sani ba,ya akayi labarinka ya bace ƙasa ko sama babu shi babu alamarsa?"
Ɗagowa idanuwansa yayi ya kalli detective Sadeeq bayan lokaci daya ɗauka yana sambatu ma ɗannasa.
A tsaye yake kyam tun shigowar AM Aliyu yana kallonsu,saidai ya juyo tukunna ya rusuna.
"Sadeeq kacemin daya shigo ƙalau yashigo,to menene ya sakashi yin haka?"
"Am Abbah Nima bansani ba,kawai kafin ka shigo ya riƙe kai,saikuma ya naga ya suma"
"Kuma mai ake jira,kalli fah jikinsa kaman bashiba,maza ka sanar da masu kulada samfuri maza a shirya private jet na fita dashi waje,yana buƙatar a yimasa gwaje gwaje a duba lafiyarsa,a ƙalla ya samu hutun shekara biyu kafin ya dawo""
"To abbah an gama,yanzunnan za'a shirya komai kaman yanda kace"
Yana gama faɗin hakan kuwa a take aka fara shirye shiyen fitada Gen Ahmad ƙasar waje domin a duba lafiyarsa.
Kasancewar abune na masu hannu da shuni,kafin dare an gama komai sun ɗaga Egypt,shikaɗai AM Aliyu ya tura shi,dan dama yawancin rayuwarsa a can yayi,bazaiji wani wahalar zama ba.

Sameer ne a zaune a falo da remote a hannunsa,wani film ɗin sojoji yake gani,gabaɗaya yabada hankalinsa ga wajen. Gefensa kuma Fatee Ce tayi kicin kicin kaman zata fashe dan haushi,sai zabgawa Sameer harara take ta gefen ido,Maimuna ce ta kulada itah,wacce take a zaune a opposite ɗinta tana danna labtop.
"Kai Fatee da wanann hararar kije ɗakinki mana kiyi,kina fah da komai a side ɗinki ba wai bakida shi ba,menene na wannan fushin haka"
Maimuna tayi mata magana cikin sanyin rai,amma ko a jikinta kamam an mintsini kakkausa.
"Haba anty Maimuna ya zakice haka,bakya ganine nice fah na fara ɗaukan remote ɗin amma ya kwace,sai mutum yayi magana ace za'a dakeshi dan anfishi ƙarfi,miye abin kallo a waɗannan gardawan"
Ta faɗa tana nuna tvn,shikuwa Sameer yana jinta amma babu abinda yace,saima ƙara volume da yayi,tafi kowa sanin shuru yayi,ana jimawa idan ta cikashi zai mata duka,saboda zafin zuciya gareshi kaman mahaifiyar tasu.
"Ai wlh ma saina faɗawa Abbah,yana tafiya aiki kake dawowa gida ka damu mutane"
Ajiye remote ɗin yayi tareda sakin ajiyar zuciya yanayimata kallon takaici.
"Ke wai ina wasa dakene,kodan kinga kece ƙarama a gidannan sai akace kiyi yanda kika ga dama,ai ummah bata nan kiyi hankali kona kakkaryaki anan wajen,zakice wani saikin faɗawa Abbah cewar ina dawowa daga wajen aiki,to in kin fasa,ko kinace banda labarin fashin da kike na makaranta. To duk mu faɗamasa mana"
"Ehh naji amma ai bana bin saurayi yawan shaƙatawa dai"
Taƙarisa maganar tana murguɗa baki.
Sakin baki Sameer yayi yana kallonta,ya tashi zai bugeta kenan yaji wayarsa tayi ƙara,tsayawa yayi tareda duba wayar. Wani ɗan wajen aikinsu ne ya ƙirashi dan haka ya ƙyaleta ya ɗaga a zatonsa ko akan akinne.
Su Maimuna da suke falon sai gani sukayi ya samu waje ya zauna,tareda cewa.
"Mai kake cewa ne,yah Ahmad wai ka gani anya kuwa,kuma har abba ma yaje ya ganshi?........"
"Wanne Ahmad ɗin?"
Yaji muryar Hajiya Maryam ta tambayeshi,wanda shigowarta kenan ta dawo daga fitar da tayi da safe,doguwar rigace a jikinta abaya,wacce aka narka kuɗi kafin a fansheta,saikuma gyalenta data yane kanta,jakarta da kuma takalminta suma designer ne masu zaman kansu,wanda ko matan gwamna saisun shirya. Shi kansa AM Aliyu yana mamakin yanda take samun waɗannan kaɗaɗe da take narkawa kanta su,wanda kuma hakanne ya kankaro mata mutunci a wajen mutane da dama.
"Nace maka wanne Ahmad ɗin,ba tambayarka nake bane?"
Ta sake maimaita maganar tana kafe Sameer da kallo,su kansu sunsan dramar da ake sha a gidan da mahaifiyar tasu da kuma yayannasu,idan wani ya shiga harkar wani.
"Uhm ummah dama.....dama....?"
"Dama me.!!!?"
Dafaɗa cikin ɗaga murya,shikansa da yake soja saida ya raxana daganin yanda yanayinnata ya sauya..
"Ummah Ahmad aka gani yau da safe,abba ma yaje wajensa,saidai wai ya suma an fita dashi ma egypt a lokacin"
"Egypt,kawai daga ganinsa sai a fitada shi akan me toh?"
"Ummah ance bashida lafiya ne bayan ya farfaɗo ɗin"
"Uhm"
Tafaɗa tana sauƙe wani numfashi mai nauyi haɗe da dunƙule hannunta,a lokacin inka ganta zaka kasa gane inda yanayinta yake,shin baƙin ciki take ji kokuma tsoro da fargaba.
"Ke Fatee abbanku ya dawo?"
"Ahah baidawo ba ummah"
"Inya dawo ki sanar dani"
Daga faɗin hakan bata sake cewa komai ba tayi hanyar sashenta,dan inda su Sameer suke babban falon gidanne.
Tun a hanyar ɗakinnata ta fito da waya tana dannawa,da alama wani ko wata take nema a wayar cikin gaggawa.
"Hello Neelah? Maza ki bincikamin yanzu,shin da gaskene wanda ya bayyana Ahmad kokuma wani ne daban,ina son bayanai yanzu yanzu,sannan ki tabbatar ba'asan kinyi ba,karki saka ƙungiya ma a ciki"
"To shikenan Ranki ya daɗe yanzu kuwa zan bincika"
"Idan har ya tabbata shine to da akwai gagarumar matsala,don shirin da mukeyi gabaɗaya wargajewa zayyi,dan haka ki taka tsantsan ki ganomin komai. Am har yanzu bakiga wani aikeba?"
"Bangani ba ranki ya dade,amma karki damu Inshaallah babu wata matsala,komai zai tafi daidai,babu wanda zai gano komai"
"Batun akwatin fah?"
"Uhmm shima dai normal tunda babu wani zance kan gwamnati tanada shi,kokuma bayyanar sa a wani wajen,dan haka da sannu komai zai tafi daidai"
"Wai to garin ya haka ta faru a bazata,duk shirin da mukayi na ya bata a duniya saida ya dawo....mtswwww"
Sauƙe wayar hajiyah Maryam tayi,harta buɗe ƙofah zata shiga tajiyo fasa glass a falon data bar su Sameer. Muryar Mulaifah tajiyo,tasan kuma dama babu mai wannan abin sai ita,runtse ido tayi tareda jijjiga kai kana ta koma falon.
Center table ɗin tsakiyar ɗakin ta fasa raga raga,tana kuma tsaye fuska shabe shabe da hawaye.
"Meyasa za'ayimin haka,sanin kowane duk tsawon wadannan shekarun jiran Ahmad nake da yaƙinin dama nasan watarana zai dawo gareni,to yanzu kuma ya dawo ace wai an fita dashi abroad batareda na sani ba?"
"Ke Mulaifah wannne iskanci kika zo kinayi a nan wajen,wanene ya damu da jiransa da kikeyi dazaki zo kin wargazamin gida,kinyi fah ya isheni haka,zanyi mungun maganinki idan baki nutsuba"
Hajiyah Maryam ce take maganar cikin masifah da takaici.
"Ke wacece dazaki yimin masifah iyaee,dan kina matar gida bashine zaisa ki zama matar gidaba,kuma gidannan kokiso kokuma ki ƙi inada iko nima dashi,tunda mahaifiyata ƴar gidance. Nasan wannan masifar da kike dan kinka duk abinda kikeyi bai yi aikiba saida ya dawo shiyasaka,kuma ki zuba ido ki gani,auren da aka fasa ɗaurawa saboda mutuwarsa sai an ɗaura shi yanzu ehe"
"Cabɗijan uban mai zayyi dake,kina bazawara sannan kika sani ko a inda yake yanada mata da ƴaƴa?"
"Ahhhhh aikuwa da saina kasheta na ƙonata,Ahmad nawa ne ni kaɗai,babu wata shegiya a bangon duniyar nan dazata rabe shi,ba'ayita ba kuma babu itah. Ke kuma ni kikecewa bazawara ko,dan ma kema uwar taki a bazawarar aka aureta ai......"
Tass hajiyah maryam ta ɗauke Mulaifah da mari a kuncinta na dama,wanda hakan ya tsaida ta daga masifar da take jajjagawa.
Magana Mulaifah zatayi amma ganin AM Aliyu yasa ta fashe da kuka tareda yin inda yake.
"Abba kalli ka gani koh,yanda shararamin mari dan kawai nace Ahmad ya dawo,dama kowa yasan sun tsaneshi basaso ya dawo,abba ka faɗamin a wace ƙasa yake zanje na ganshi,bazan iya kwana ɗaya va batareda na ganshi ba"
Kuka take tana narkewa kaman ba ita ce ke faɗin maganganu ba a lokacin.
"Shikenan kiyi shuru haka,ke Maryam meyasa kika ........"
Maƙale maganar yayi ganin yanda ta jefeshi da wani arnen kallo mai haɗe da harar.
Juyawa tayi ma tabar wajen ƙwass ƙwass kana jin ƙarar takalminta akan tiles saboda yanda take taka shi da ƙarfi.
Sauƙe a jiyar zuciya yayi tareda kallon Mulaifah.
"Kinga kiyi shuru haka,jeki wajen Mammah nima yanzu ina zuwa"
Daga haka shima ya wuce nasa sashen,su dai Fatee kallo ne nasu kawai a falon,dan inda sabo sun riga sun saba da ganin wannan dramar a da,abin lafawa yayi saboda babu wanda za'ayi rigimar akai,to yanzu da ya dawo za'a cigaba.
Heeho shagali shagali dama wlh nayi missing gidannan ba'a drama,amma yanzu tunda yah Ahmad ya dawo nasan za'a shigaba da gashi"
"Ke Fatee kinada hankali kuwa,tashin hankali da ake a tsakanin iyayenki shine abinda kikeso koh?"
"Ahh to ya zanyi anty Maimuna,in kaji haushima ba fasawa za'ayi ba,dan haka gwanda ka zuba ido kayi kallo ka more....Mulaifah bazata daina haukar nunawa yah Ahmad soyayya ba,shikuma bazai daina nasan dizgata ba kaman da,sannan mommy bazata daina nuna masa ƙiyayya ba,yayinda shima bazai raga mata ba.....kinga kuwa ai za'a sha drama saidai in wani ne ya sanja hali,wanda bana tunanin hakan"
Tana gama faɗin hakan tayi hanyar sashen ta tana waƙa.
A bangaren Mammah kuwa da gudu Mulaifah tashiga kaman an jefata,sakaliyace ta zubawa a taro,duk da cewar akwaita da masifa a tantiranci,mahaifiyar ta ƙanwar AM Aliyu ce,bayan ta rasu Mammah ce ta riƙeta maimakon gidan ubanta,wanda hakan yasa suka shaƙu take ganinta tamkar ƴar ta.
Tun shekara goma baya da Ahmad ya dawo daga Egypt Inda yake zaune ta kamu da sonsa. Tun yana shareta har yafara tsayar mata na shiga rayuwarsa da take,amma hakan duk a banza,daga baya ma sai aka saka zancen manya a ciki. Ahmad yana ji yana gani aka tsaida bikinsu itada shi badan ya so ba.
A na shirin bikinne yayi hatsari ya mutu,bayan haka Mulaifah tayi ta kuka har ƙaramar hauka saida tayi da mutuwar tasa,tayi aure ma baije ko ina ba ta kasheshi ta dawo gidan.
Basa shiri ko kaɗan da hajiyah Maryam saboda nuna ikon da Mulaifah take,da kuma nunawa Ahmad so,a bangaren hajiyah Maryam kuwa kowa yasan bataso taga wani yana baza iko a fadarta,sannan duk wani abu daya shafi Ahmad bata ko buƙatar jinsa ballantana da dunga gani.Dan haka bata kawo Allah a wajen magance matsalarta ballantana mutum,wanda itama Mulaifan haka take a nata bangaren.

Wannan kenan a shafin farko na littafin SANADIN CACA BOOK 2.



SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.



*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)


Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150

Bismillahir-rahmanir-raheem


Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah 🙏🏼 ga number ta nan mai son littafi na ɗaya yayi min magana zan bashi shi kyautane.





Ina ƴan mata dakuma Matan aure masu muradin burge mazajensu da ɗinkuna zuƙa zuƙa. *PHEEDY TOILORING DESIGN* ,suna gabatar muku da ɗinkuna kala kala wanda sukayi daidai da zamani.
Zaku samemu a kan wannan layin waya kamar haka


09167130115
Wato a manhajar whatsapp. Domin ganin kalolin samufurin aikinmu kuma ku tuntubemu a INSTAGRAM da kuma TIKTOK a @pheedyxacks_ragtrade

Muna maraba daku a kowanne lokaci🙏🏼🙏🏼🙏🏼🙏🏼🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻






*BOOK 2*
...2...



"Mammah Mammah kina ina ne?"
Tafaɗa da sauri bayan ta shiga sashen Mammah ɗin.
"Meyafaru haka kike xubamin wannan ƙiran uhm ?"
Mammah tafito daga ɗakinta hannunta ɗauke da carbi da hijabi a jikinta kaman kullum.
Zama tayi akan kujera,wanda daman abinda Mulaifah takeso kenan ta ɗora kanta a cinyarta.
"Mammah bakiji labari ba Ahmad ya dawo ashe bai mutu ba duk tsawon lokacin,Allah yayi zamu kasance tare ashe shiyasa ka aurena ya mutu"
Shuru Mammah tayi kaman mai tunani kafin tacigaba da shafa kan Mulaifah wanda yake kan cinyarta,ganin tayi shuru batace komai bane yasaka Mulaifah juyawa ta kalleta.
"Mammah bakice komai ba,bakiyi mamakin dawowarsa bane?"
Murmushi tayi irinna manya kana ta ɗora da cewar.
"Ahah ba haka bane,waye bazayyi tunanin abin al'jabi irin wannan ba,amma kuma babu abinda yafi larfin Allah,dan haka wannan ba abin mamaki bane dan ya faru,saima na farinciki da Allah yadawo mana dashi garemu. Ina yake yana cikin gidane?"
"Ahah wai fah Abbah ya turashi abroad a duba lafiyarsa"
"Ehh to hakanma yanada kyau,amma ya kamata a a tura wani nasa ya kulada shi,ba a barshi shi kaɗai ba gashi ba cikyakykyiyar lafiya ba,barin abbannaku yashigo muyi maganar,sainaje ganin jikinnasa.."
"Yawwa Mammah in zakije nima zan biki na ganshi,i can't wait to see him"
"Uhmm Mulaifah kenan kefah kike rawarki kike kiɗanki,sanin kanki ne amadu bayason ana haɗashi dake,wancan karon ma abbanku ne yayi masa dole shiyasa ya amince da aurenki,yanzu kuwa kinsan ba lallai ya yarda yasake maimaita wannan hukuncin ba"
Kukan sakarci Mulaifah tafara jin abinda Mammah ta faɗa.
"Wai Mammah haba meyasa kike haka,shima nasan yana sona,ko ba yayi zan sakashi yayi yanzu,sannan nasan zaki roƙi abba ya dawo da maganar aurenmu koh?"
"Ni ban miki wannan alƙawarin ba,so kike ayita shiga haƙƙinsa,yaji da halin dayake cikima na halin waccar matar,yanzu babu wannan zancen,in ya dawo yanaso toh,idan kuma bayaso to ni zan tsaya masa"
Tashi tayi daga cinyarta tana mata kallon mamaki ganin da gaske fah Mammah take akan maganarta,kuma dama tasan hakan zata faru,dan duk zamanta ƴar lele a wajen Mammah to bazata haɗa kanta da Ahmad ba,sanda yana nan idan kaga yana fira da sakin fuska to a sashennata yake.
Tashi tayi cikin fushi ta bar sashen Mammah,nata sashen ta nufah zuciyarta cikeda tunanin shin wanne hanya zata bi na mallakar zabin rannata.

A can kuwa Cairo dake ƙasar Egypt Ahmad a kwance yake akan wani gado,jikinsa sanye da kayan masu jinya,wasu wayoyi aka saka akannasa wanda suke shinshinar lafiyar ƙwaƙwalwartasa.
Buɗe idonsa yayi a karon farko bayan kawoshi ƙasar,wanda kwanansa uku kenan da zuwa..
Yauɗin kuma su Sadeeq sukazo dubashi harda Mammah da Mulaifah saikuma Saleem,dan dama a duk cikin ƴan uwannasa yafi shaƙuwa dashi..
Bayan buɗe idon yana jiyo hayaniya daga ɗan can nesa,amma a ɗakin kam baiji motsin mutum ba,da alama shi kaɗaine..
Tashi yayi a hankali tareda zubawa na'urar da take gabansa ido.
Waishikam duk sanda ya kwanta a asibiti zai farfaɗo ya ganshi,yaushe yazama hakane kaman juji? Ko yaushe yana asibiti?.
Ɗan ƙaramin tsaki yaja tareda fitar da ruwa dayake shiga jikinsa,saƙƙo na ƙafafunsa yagi akan gadon tareda niyyar sauƙa,amma sai ya tsaya jin abu ya riƙe masa kai,suma a wayoyin cikeda bacin rai ya cire su kafin ya nufi banɗaki,wanda yagani a yamma da ɗakin.
Fuskarsa ya wanke tareda kallon kansa a cikin madubi,ɗan razana yayi tareda ja da baya,ganin yanda ya rame yayi baƙi,ya kuma ƙara manyanta ba kaman yanda ya sanshi ba..
Shin dama da gaskene abinda Sadeeq ya faɗa masa,cewar shekararsa biyar da barin gida,to a ina yake tsawon lokacinnan,bacci yake tayi sai ya yanzu ya tashi? Ko kuwa wata rayuwa yayi da bai sani ba kai?.
Zullumine suka cunkushe masa kai,wanda hakan yasa ya fito daga banɗakin.
Cakk ya tsaya a bakin ƙofar banɗakin yana ganin tarin mutanen da suke ɗakin,wanda duk cikinsu babu wanda kallo ɗaya bai ganeshi ba,amma sai ya basar ya nufi gadon daya tashi yanzun..
Mammah ce tafara yimasa magana cikeda kulawa.
"Amadu ka tashi ya jikinnaka,babu inda yake yimaka ciwo,amma ka ganemu kuwa"
Kwanciya yakeson yi,amma ganin yanda take zubo tambayoyi yasaka shi kallonta tareda sakin murmushi ɗan ƙarami.
"Mammah na ganeku mana,ƙalau nake babu abinda ya sameni ciwon kaine shima ya ɗan sauƙa,taya zan manta ki saidai amma kin ƙara tsufa,kinfara cin goro ne"
Dariya Mammah tasaki cikin jin daɗin maganarsa ,kafin tace wani abu Mulaifah ta dawo kusada shi da sauri kaman zata wuce jikinsa..
"Honey ka ganeni nima?"
Wani kallon matsa ki bani waje yayi mata,ganin ta dalleshi da manyan idanuwanta yasa yayi magana cikin ƙosawa.
"Kai Mulaifah wai bazaki sauya bane,gashi a fuska kin ƙara girma amma kinanan yanda kike,saikin shige jikina kafin ki tsaya komai?"
Bataji haushin yanda yayi mata maganar ba,ƙiran sunanta kawai da yayi ma hakan ya wadatar da ita,kuma ya sakata cikin farinciki.
Shareta yayi tareda kallon Saleem wanda yake zaune a waje ɗaya shida Sadeeq.
"Gentle bro kaima ka girma sosai,amma yanzu kam ka zama doctor koh,sanda nasani kana aji ɗaya"
Murmushi yayi shima daya tuna lokacin.
"Ehh nagama yah Ahmad har nafara aiki ma waccar shekarar,Sameer shima yana aiki a barrack ɗinku,sai Maimuna tana karatun law,Fatee kuma tana makaranta"
"Ban tambayeka ya suke ba ai,naka kawai na tambaya"
Yafaɗa yana tsuke fuska,dukkan su kallon juna sukayi,har yanzu yana nan da halinsa,ba dama ayimasa gwaninta.
"Oh AA Hamma ni baka ganni bane komai"
Sadeeq yafaɗa cikin tsokana..
"Banganka ba saida kayi magana"
Yana gama faɗin hakan ya kwanta a gadonnasa,suna ganin haka suka fita,da alama hutu yake so.
Suna fita daga ɗakin ya tashi ya koma banɗakin,dama yayi hakanne saboda su fita,kasancewar bai saba da zama cikin mutane ba tunda,shiyasa yajishi cikin wani irin yanayi.
Alwala ya ɗauro ya dawo ɗakin,domin rama sallolin da ake binsa ,ya daɗe yana yi har saida ƙarfinsa ya ƙare kafin ya dakata.
A wajen Addu'o'i ma ya daɗe nan ma kafin ya dakata.
Jijjiga kai ya fara burinsa kawai ya fitar da tunanin da suke cikin kansa,amma hakan ya faskara.
Ƙarar buɗe ƙofa yaji,har wanda ya shigo ɗin ya zauna bai ɗaga ido yaga wanene ba,har saida yayi magana tukunna ya gane Sadeeq ne.
"AA Hamma nasan tunani kakeyi,koma miye ka barshi ba yanzu ba,saboda a yanzu kana buƙatar hutu sosai"
Bai saurari Sadeeq ɗin ba,saima magana daya farayi.
"Menene haka ya sameni,a ina nake tsawon lokacin nan,wacce irin rayuwa nayi duk bansani ba Sadeeq,ka yi tunanin ya zanji a halin yanzu,sannan rayuwar wa na shiga,cutar dashi nayi kokuma kyautata masa duk bansani ba"
"Hakane kam babu daɗi lamarin,amma babu yanda zakayi saidai haƙuri,a hankali Inshaallah zaka tuno komai,amma yanzu karka saka damuwa a ranka,idan ba haka ba zai dameka sosai.,Saboda hakannne ma yasa yace ka zauna anan kaman na shekara biyu ko ɗaya kafin ka koma gida,saboda ka huta sosai"
Jijjiga kai yayi tareda cewa.
"Bazan iya zama anan ba,bayan nasan wanda ya aikata min hakan yana can hankalinsa kwance,nikuma yasaka rayuwata cikin garari na tsawon shekara biyar"
"Wani mai kake nufi,shin kasan wanda yayi maka hakan"
"Ahah ban tabbatar ba amma nasan najikina ne yayimin,kuma komai yana alaƙa da case ɗin BC da nake a lokacin,Sadeeq abinda zan fadamaka inaso kabarshi anan harsai na tabbatar da hasashena. A binciken danayi harda hannun Hajiya Maryam a wani bangare na ƙungiyar,nagano hakanne bayan na saka na'urar bin diddigi a wayarta da motarta..
Wanda kuma tasan da hakan,amma ga mamakina bata nunamin ta damu ba,hasalima wata hidimarta tacigaba ta daban.
Sannan a ranar dazan
Showing 1 words to 3000 words out of 62659 words