kuma ya haihu inde kayan aiki na aiki, kefa mace wlhi baki isa ki kai 70yrs bama kina haihuwa, mata iyayenmu kuma yan uwana ku gyara rayuwarku pls, ana bar1n halak dan kunya, koda akace mijinki ya nemeki sanda yaso ba ace ya nemeki a gaban yarankiba, wallahi wani lokaci yara naji wasu kuma ma suna gani tinda ba makafai bane, ku jiba kazanta! Kinga mace in kika haihu Karki sake ki banzatar da yaranki a banza , wallahi yara kmr dukiyane, duk ubangiji ze tambayemu ya mukayi dasu, hisabinnan da kukaji ana cewa wlhi da gaskene akwai hisabi, tsakanin d a da uwa da uba akwai hisabi, danka haifi yara bawai kai ka haliccesuba, most of lalacewar yaran yanzu am sorry to said wlhi akwai sa hannun iyaye mata, shi namiji daman ai ba ruwansa, in yara sukayi kyau sune nasa, in suka lalace nakine ke mace, ya bar miki wallahi, mu nutsu mu gyara rayukanmu, ku kuma yara ku k1yaye bacin ran iyayenku, ubangiji yace abi iyaye koda kafiraine, sannan ubangiji yasake cewa abi iyaye koda fasikaine, aiko a iya haka yaci ku gane girman iyaye, ku kiyaye bacin ran iyayenku sbda ku gama da duniya lafiya, Ubangiji Allah ya raba kowa da iyayensa lafiya Amin, amma kusani ba biyayya cikin sabama ubangiji)



Malam wanzan ya kalli BATOOL wadda kanta ke kasa, ya kalli hassana wadda itama shi take kallo. Yayi gyaran murya hadi dacewa  Duk kubani hankalinku nan,&  cikin ladabi BATOOL tace toh. Hassana ma tace  Toh malam&  malam wanzan ya fara magana ç1k1n nutsuwa.  Inaso kusan cewa komi kukaga ya faru toh daga Allah ne, hatta da motsa d anyasanka wannan in ubangiji beso ba baka isa kayi ba, kuma kome kukaga yasamu bawa insha Allahu Alkhairi ne, ita kaddara da jarrabawa masu kyau ko akasin haka duk na muminine, ubangiji baze tabayin bawa ba tare daya jarabceshi ba, alhamdulillahi wani abu ya faru kuma na Alkhairi ne insha Allahu.. yayi shiru for some seconds, falon ya dauki shiru , duk sun kosa suji me malam wanzan zece, BATOOL kam tinda ya fara maganar kirjinta ke dukan uku-uku, ta kosa taji Ainifin maganar da yaketama wannan shimfidar sharar fagen ta mecece. Malam wanzan yaci gaba da magana idanuwansa nakan BATOOL  ita rayuwa ako wani Hali inka tsinci kanka anaso ne kayima ubangiji godiya,,sannan ke BATOOL ubangiji ya umarceki dakiyima iyayenki biyayya, inhar ba asabama mahalicci bane kinsande bazan cucekiba bazan ha inceki ba, sannan bazan bari a cucekiba , BATOOL kasancewarki dhiyyata tilo aduniya, ina sanki so me tsanani, ina kaunarki kauna irin wadda uba na gari keyima yayansa, ina fatan kmr yadda kika sabam1n biyayya kiyimin awannan karan, ke dhiyyace me tarbiya kin kai kin 0sa ahanaki ki hanu BATOOL, saboda haka na bada Aurenki ga JAROOD d an gidan me martaba Sarkin agadex, Aranar juma ar data gabata aka daura miki Aure, yanzu ke matar aure ce ba budurwa ba& .. ba BATOOL ba hatta hassana seda ta zaro ido waje sbda mamaki, ganin yarinyarta karamace amma a haka malam ze bada Aurenta,ita Sam ba mace bace mesan duniya, Sam bata duba kudinsu ko sarautarauba. Abangaren BATOOL wani irin mummunan yanayi tashiga daga nan datake zaune, daman tini jikinta ya hau bari aiko ya kara daukar bari, nan da nan idanuwanta farare tass dinnan suka kad a sukayi red sosai, ita ko sanin waye JAROOD dinma batayiba, bata taba ganinsaba, a razane ta dago ta kalli mahaifin nata shima ita yake kallo, ta rufe idonta ta bude akansa danta tabbatar, tabbas da gaske ba mafarki take ba mahaifintane agabanta yake gaya mata ya mata Auren dole. Ta maida kanta kasa, rawar da jikinta keyi ya kara yawaita, ji kake Fatt fatt! Heart beat dinta nata bugu kmr zata fito fili, amma sede ba daman magana ko uwarta bata 0sa tay1 musu da abinda malam ya fadi ba balle ita yarshi. Kuka kawai takeso tayi ko zataji sanyi amma ta kasa, khalid ne kawai yake yawo asararin birnin zuciyarta, ji tayi tamkar an rabatane da Khalid, rabata da khalid tamkar rabata ne da ranta.  Daman bazan auri khalid ba? Ta fadi a zuciyarta, nan da nan kawai se hawaye sharrrr saman fuskarta. Mahaifinta ya kula da yanayin data shiga sannan yaga hawayen dake zirya akan kuncinta, har azuciyarsa yakejin zubar hawayen nata amma sede ba yadda za ayi bakin alqalami yariga ya bushe. Har hassana ya kula tashiga yanayi mara dadih sbda harga Allah ita bata da burin yarta tayi aure yanzu, shiyasa ta tsananta tsaro akanta kan karta kula wani. Hasan a taso ace BATOOL takai 18yrs zuwa 20yrs se amata Auren kuma ita asan samunta so takeyi yarta tayi karatun likitanci, batasan a mata aure da wuri, ita in ita keda iko da itama takai 25yrs ma agida badamunta zeyiba, kunsan zuciyar uwa.  Ina me umurtarki dakimin biyayya, insha Allahu baza kiyi nadama ba domin babu wanda yakeyin nadama bayan Yama iyayensa biyayya&  BATOOL na kuka tace  Insha Allahu daadah zan maka biyayya har karshen rayuwata, duk abinda kayi dai-daine akaina saboda ka isa dani, kasameni me biyayya insha Allahu&  ciki kuka da sanyin murya take mgnar. Tausanta ya ratsa zuciyar malam, hassana kam ji takeyi kmr itama tayi kukan ko zata samu sauki, tausan yarta ya rufeta, kallon karama take ma yarta sosai, tayi kankanta da daukar d ana miji a mararta yanzu, Sam batasan JAROOD din bashi d lafiya ba, ko a labari bata tabaji agun mijintaba.  Allah ya miki Albarka, Allah ya baki masu miki biyayya kamar yadda kikamin,,, Cewar malam wanzan BATOOL ta amsa da amin hassana kam sede ta amsa a zuciya, da kyar ta iya cewa.  Allah yasa hakane mafi Alkhairi ya basu zaman lafiya,,, malam wanzan ya amsa da Amin daman yasan hassana bazata masa gaddama ba sbda tanada gudun zuciyar mijinta sannan akwaita da ladabi tafi duk sauran matan daya aura. Har zuwa yanzu kuka kawai BATOOL keyi kasa-kasa tasa hannu ta datse bakinta, Malam wanzan baze jure ganinta a wannan halin ba, dan haka ya tashi ya dauki mukullin motar ya fice agidan zuwa gidan hajiya fatima. Yana fita BATOOL kmr tana jira ta tashi aguje ta 0sa jikin mahaifiyarta ta fada jikinta tana kuka,abinka da shagwababbiya daman surin kuka ne da ita tin tini ita ko fada ka mata se tayi kuka, hawayenta a kusa süke,. Tana fadawa jikin mamanta ta fashe da kuka me tsanani tana fadin  Ammuh, wallahi banasan Aurennan dan Allah ki gayama daadah ya barni inada wanda nakeso khalid Ammuh ni khalid nakeso in aura, ban gaya muku bane amma mun jima muna tare makarantarmu daya, dan Allah Ammuh ki gayama daadah ni Khalid nakeso inma aure yakeso inyi abari muyi aure nida khalid inya gama makaranta, dan Allah Ammuh mutuwa zanyi inna rabu da khalid!!! Seda hassana Tayi hawaye ganin yadda taketa kuka kmr ranta ze fita, se sambatun maganganu takeyi kmr zatayi hauka. Rarrashinta tashiga yi da kalamai masu dadih abinka da Uwa, nan ta dan fara sassauta kukanta amma tay1 1H tana kukan duk tabi ta fice a hayyacinta, idanuwanta sun kumbure süntum. Ganin ta dan fara dawowa hayyacinta yasa hassana tambayar BATOOL din waye khalid, sbda daman tasaba jin BATOOL na kiran sunansa in tana ç1k1n bacci batare da sanintaba, tanataso ta tambayeta waye khalid amma seta dauka ko mafarkine na shirmen yarinta. BATOOL ta bedema mahaifiyarta wuka da wutsiya kan wanene khalid. Mahaifiyarta ta numfasa tace  Toh wallahi tin kuna shaida juna keda mahaifinki karki sake yaji maganarnan abakinki. Yanzu kikace zaki masa biyayya, toh inaso ki masa biyayya, kibarwa ubangiji komi, wlhi inya rubuta sekin Aure khalid toh tabbas seshi d an sarki ya rabu dake kin auri khalid din, karkisa damuwa aranki ki fawwalama ubangiji komi, sallar darennan kici gaba dayinta nima zanta tayaki ina miki Adduah dhiyyata ta gari kinji kou?? Nan de tayita lallaminta da ban baki harta tasamu tasaki ranta azahiri abadinima taji zuciyarta ta mata sanyi amma data Tuna da khalid setayi kwallah, data shiga dakinta ta dauki photon khalid tayita kallo, khalid kyakyawa ne black beauty cikakken buzu ne shima ga kyau ga aji, Gashi matashi a SS3 yake ba babba bane yarone sosai danye sharaf, irin wanda sam iyayensa ko giyar wake sukasha bazasu masa aure yanzu ba. Ranar yini da kwana BATOOL na kallon photon khalid dataji mahaifitarta zata shigo dakin seta boye photon.



Abangaren matan JAROOD bawacce tadamu wai dan benan musamman hajiya zulaikha harkar gabanta kawai takeyi, tinda hajiya aisha tace mata yayi tafiya kawai tace Allah tsare ko kiransa batayiba. Kwara ita hajiya aishar takirasa daukane kawai beyi ba, itama tafijin dadih da baya nan, seda tayi 2days ma bata kwana agidan ba, tana gün d an boy yana gargasa mata duri da Jelah, data dawo ma washe gari takoma ya kuma ci, taciyu a kwanakinnan amma dayake hajira ce Kawai kari take nema kullum setaje d an boy ya gargasa mata duri, ba abinda ya dameta ita bata cikin tension din shaawah, hajiya zulaikha ce ke ciki.



Abangaren JAROOD baccinsa yakesha yanzu sosai, yaci ya koshi ya kwanta , hankalinsa ya d an fara kwanciya ganin amour tabar kiransa kawai yasan ta hakura ne da Aurennan na dole daza amasa, kawai kuma de daa Ubangiji yakejin hankalinsa ya kwanta akasin ada, ya rasa dalilin kwanciyar hankalin nasa. Ranar Tuesday dayaje ganin doctor khamis ya tabbatar masa da jininsa ya fara sauka, saura kadan ya rage, yaji dadih sosai wlhi bayasan hawan jini da sugar Suna bashi tsoro, shida ake nema masa lafiyar jaruma kuma hawan jini da sugar yasamesa aiya banu. Daa asibitin da yayi sallar azahar kawai ya nufa gidan Amour, tinda ya tinkaro kofar gidan yakejin gabansa na dukan uku-uku, daman a hanya ya tsaya ya mata tsaraba irin shi adole daa tafiya ya dawo dinnan. Yana isa get din yaji kamar ya dawo baya, se kawai ya sadakar ya Danna hancin motarsa cikin gidan. Dai-dai malam wanzan na zaune a compound din gidan gefen wata flower suna hira da Abdul aziz me gyaran flower, kawai idanuwansa suka sauka akan motar JAROOD,. Zumbur ya tashi cikin murna ya iso inda JAROOD din yayi packing motar ya fito, yana ganinsa ya sakar mata murmushi hadi dacewa  Nayi missing Dinka ubana&  cikin murnar Ganinsa malam wanzan yace  barka da dawowa uban dakina nima nayi kewarka.. JAROOD yayi wata yar siririyar dariya daya jima beyi irintaba yace  Barkade,,,ina Amour, tagajide ta hakura da mgnr Aurennan aini daman nasan seta gaji ta hakura tinda de ai ba a dole,, ni ba burar gwatso ba inta tara yaran mata suna tsinemin sunajin kmr su kasheni dan takaicina dake rayukansu nawa&  JAROOD ya fadi yana bude Murfin bayan motar yana dakko ledojin daya shigo dasu. Karo na farko da Malam wanzan ya farajin kunyar maganar batsar bakin JAROOD da ada ne shike tayasa maganganunnan, JAROOD besan dadin mace ba amma bakinsa akwai batsa sosai. sede malam wanzan yayi shiru bece da JAROOD komi ba, murmushi yayi kawai. Ya tayasa kwashe ledojin suka nufa hanyar zuwa falon hajiya fatima. Suna shiga falon dai-dai tana fitowa daa bedroom dinta na dakin kasan, idanuwanta sukayi tozali da JAROOD, ta bude ido na mamaki tayi missing danta sosai yau take cewa zata kirasa idan ta tashi daga bacci toh tashinta a baccin kenan tayi sallah ta fito da waya a hannu tana shirin tazauna a falon ta kirasa.  Maraba da yan hijira.. Cewar hajiya fatima data fadi cikin murmushi ta tar1 JAROOD da faraah. Nan da nan farin ciki ya kuma lullube JAROOD domin ganin murmushi mahaifiyarsa. Ta karaso tazauna suka ajiye mata ledojin a kusa da kafafuwanta kana ya tsugunna har kasa ya gaidata, cikin fara ah da zallar farin ciki ya gaidata, ta amsa fuska sake hadi da masa barka da dawowa ya amsa da barkade. malam wanzan ya zauna akan kujera sbda hajiya Fatima tace yazauna amma ada yaso ya fita ne.  saukar ka kenan yanzu? Hajiya Fatima ta tambayi JAROOD, yace  Ehe Amour&   masha Allah, kaje gida kayi sallah ka huta zuwa gobe inka huta ka dawo inada mgna dakai domin Abinda ka guda din be fasuba&  JAROOD yayi shiru yana nazarin maganarta ta karshe, be fahimci me take nufi ba, dan haka cikin kaguwa dasan yaji me takeso ta gaya masa yace  Ai nayi sallah Amour, sannan ban bukatar wani Hutu kawai ki gayamin me kkeso ki gayamin&  hajiya fatima tace  Aah kabari de seka samu nutsuwa kaje gida kaga iyalanka ko zuwa dare ne ka dawo&  Sam ba haka JAROOD yaso ba amma dole ya tafi gidan sbda ta matsa seya tafin. Malam yajasa a car, yaje gida ya kuma wanka yayi la asar ya nufa part din matansa duka ya duba kafiyarsu. Hajiya aisha ta matukar jin bakin ç1k1n dawowarsa, amma ta boye sbda makirci ta nuna azahiri tayi murnar dawowarsa, kasan ranta ji takeyi kamar ta mutu dan bakin ciki in yana gida bason adinga Yawan fita yakeyi ba. Ita kam hajiya zulaiha azahiri ta nuna masa tay1 bakin cikin dawowarsa babu boye-boye ita Sam bata iya makirci da munafunciba komi nata a free takeyi ba tsoro ba gudun zuciya. Daya shiga part din aisha seda yayi 30mnt tana jansa da hira, daya dawo yashiga part din Zulaikha 10mnt yayi ya fito a daddafe, da kyar ma ta iya gaidasa, ita ko miskhala zarratin bata iya makirciba, in kana neman Wacce tafi shedan kisisina da makirci kasamu Aisha magana ta kare, kuma JAROOD be isa ya gano halintaba sbda tasan hannunta.



Bayan yayi isha i, daa masallaci malam wanzan yajashi zuwa gidan hajiya Fatima. A hanya JAROOD se jan malam wanzan yake da hira, amma yayi shiru yanacan yana tunani-tunanin shin ya JAROOD zeji in aka gaya masa yarsa aka aura masa a matsayin matarsa ta aure. Ya zurfafa a tunani har suka iso gidan, JAROOD ya kula da Tuna n1n da Malam wanzan yake ciki dan haka suna isowa gidan ya kallesa yace  me kake tunani babana? Malam wanzan besan sadda bakinsa ya subuceba yace  Na maka lefi&  ya sadda kansa kasa. Ç1k1n mamaki JAROOD yace  Lefin meka min da har zesaka a tunani? Malam wanzan yayi shiru. JAROOD yaci gaba dacewa  Kome kam1n na yafe maka in har ba Amour da Me-martaba ka kashemunba, wlhi na yafe maka&  malam wanzan ya sauke nannauyar numfashi ba tare dayace komi ba. Suka nufa falon hajiya fatima. Bata falon kasa dan haka JAROOD ya kirata a waya batare data dagaba ta sakko daga upstairs tana dakinta na sama ne tana waya dame martaba, taji shigowarsu domin taji karar bude get din gidan kuma tasan sune. JAROOD naganinta ç1k1n nishadi da zolaya yace  Barka da sakkowa Giwa me takun kasaita, Giwar me martaba&   ai yau Kaima ka Ara ka yafa kenan&  ta fadi tana murmushi hadi karasowa ta zauna malam wanzan ya juya ze fita ta dakatar dashi.  karka fita ka zauna ai dakai za ayi mgnr&  JAROOD ya zauna kasan carpet dai-dai yana facing hajiya fatima. Malam wanzan ya dawo ya zauna a kasa shima kusa da uban dakinsa.  Yaya kasamu iyalin lafiya kou? Cewar Amour.  AlhamduLillah amour, ki gayamin wani magana zaki gayamin pls dukna kagu&  JAROOD ya fadi cikin kosawa. Amour ta gyara zama ta sosai azuciyarta se Adduah takeyi Allah yasa d an nata ya aminta domin tasan in be amince ba ba aure, amma inya Amince lafiya lau aurensu yake, daman tinda aka daura Auren taketa Adduah Allah sa inya dawo ya amince da duk abinda tace.  Abinda ka gudane kadawo kaga anyi makashi&  cikin rashin fahimta yace  Amour kinsani a duhu abinda na guda kamar yaya? Wallahi bangane ba&  shi sam ma ya mance da maganar Auren. hajiya fatima taci gaba da magana.  Auren dakayi gudunsa Shi aka maka,,, a razane JAROOD ya kalli amour domin ya tabbatar da abinda tace Akan fuskarta, nan fuskarta ta bashi tabbacin kalamansa.  Innalillahi wa inna ilaihirraju un! Wani irin Aure kuma pls?  JAROOD ya fadi yana dafe kansa, nan da nan zufa ya wankesa Tass. Gaban malam wanzan ya yanke ya fadi ganin yanayin da uban dakinsa ya shiga, yafi yanayin da BATOOL tashiga, dande kawai shi namiji ne. Cikin sassauta harshe dukda an masa abinda bayaso Amma hakan besa ya daga muryarsa sama data mahaifiyarsa ba yace  Dan Allah Amour meyasa kikayi haka? Da gaske kike pls ko wasa amour? Hajiya fatima ta hade rai tace  Nataba wasa dakaine? JAROOD ya kuma dafe kansa wata zufar ta kuma wankesa, ji yakeyi kmr yasaka kuka amma ba dama. yace  Yanzu Amour kuma yar 14yrs din kika auramin saboda kawai kibi maganar malami, haba Amour dan Allah Amour ki duba ki gani 50yrs nike amma a haka akamin Auren dole kamar de bansan ciwon Kaina ba Amour,&  a hasale hajiya fatima tace  Da Anyi magana kashe shekarunka hamsin shin kai ka yankewa kasa cibiya ne wai? Kasani yaro baya girma gaban iyayensa ni yanzu sam bana ganin girmanka, a girman naka in har bakama iyayenka biyayya ba yazama na banza? Da girman naka in kana batawa iyayenka rai baze hana Ubangiji ya saba maka ba wallahi, Ka ganni nan Dani da Mahaifinka me martaba? Duk bamufi karfin iyayenmu su samu abu muyishi adoleba kuma ba tare da Mu_uba, ko rayukanmu sun baci bamu isa mu nuna agabansuba sbda tsantsar ladabinmu agaresu, nida
Showing 33001 words to 36000 words out of 159605 words