kyau da tsafta,cikin izza ya karba yasha hade da mikewa tsaye idan ummi ta dawo na wuce ni ki sanar mata
Pls ka bari ta dawo mana ko ka tsaya na kira ta yanzu pls,sallamar ummi sukaji ta shigo palon,yawwa ummi zai tafi wai cewar iklas kuma baici komai ba wlh,hangame baki ummi tayi haba umaru ya zaka Mana haka,mu ka taimakamana mun yarda mun karba duk da bamu sanka ba,ba dangin iya ba na baba amma mun yarda da kai,yanzu dan mun baka abinci shine baza ka ci ba,kamar mun baka guba ko wata cuta.
In dai kana so mu shirya gaskia kaci ko kadan ne idan kuma kyankyami kakeyi bazan ma dole ba.da sauri omar ya koma ya zauna haba ummi ba wani abu kiyi hakuri bari naci.baki ummi ta washe haba ko da kaifa amma ai sai ka sa muji ba dadi ai,iklas zuba masa bari naje na karasa gyara wasu kaya.omar ji yakeyi tsohuwar na birgeshi,kallonta yakeyi kamar mama.
Tana bude flask wani kamshi ya daki hancinsa me dadi,fried rice lafiyayya tasha hadi da su hanta etc,zuba masa tayi ta kara bude wani bowl me kyau na glass kaji ne soyayyu zuba masa tayi a gefe ga hadadden salat,mika masa tayi ta zuba masa lemon kwakwa.
Yatsina fuska ya dauki spoon da kyar ya fara ci,wani arnen dadi yaji kamar kunnensa zai fita,sai santi yakeyi a ransa a fili kuwa yatsina fuska kawai yakeyi,iklas na kallonsa kafafunta sunyi sanyi tun a fuskarsa ta gane baiji dadin abincin ba,kamar zatayi kuka bata San ace girkinta baiyi dadi ba.
Musamman a wajen Omar bata San me yasa take so ya yaba girkinta ba.idonta har ya Tara kwalla kadan,omar yana kallonta ya gama ganota tsab,a ransa sai daria yakeyi,ganin kaka ummi bata kusa yasa yake ta wannan yatsina fuska,tunda yaga yanayin iklas ya kara yatsine fuska dan yanzu har yi yakeyi kamar zaiyi amai,abin mamaki yaci abincin yafi Rabin plate,lemon ma yasha yaji dadi amma harda rike ciki wai a dole yaci guba.can yace kai ummi ta takura naci jagwalgwalo,babu dadi haka akeyin girki,wannan ai sai ki kashe mutane.
Hawaye ne ya digo dis daga idon iklas da sauri ta goge kar sir omar ya gani Wanda ta Riga ta makaro a idonsa tayi komai.kitchen ta shiga sai gata ta fito da wata Leda me kyau a hannunta,mikawa Omar tayi ga wannan ka kaiwa mom dinka,
Tunaninsa ne ya tsaya cak wannan yarinyar akwai mamaki acikin alamarinta,wai tana 15yrs har tasan ta bawa mamansa kyauta yaji dadi kuma ta kara birgeshi.karba yayi hade da cewa tnx kira ummi,sai gani yayi iklas ta tsaya rubutu a jotter bai San me ta rubuta sai da ta gama ta wuce kiran ummi,ita kuwa iklas ta Riga tayi lissafi wannan week din sunyi dambun naman kaza gashi basu ci ba ta bayar kyauta,shi yasa ta canja lissafinta..sallama omar ya musu ummi ma ta bashi sakonta ya ba mama,
Gidansa yaje ya duba lafiyar sahar sabo da amanar aure dake kansa,yar aikinta ya tambaya ina sahar ?ranka Dade tayi tafiya yau tace a fada ma ta tafi kasar ghana akwai wani aiki za suyi..ok kawai yace ya koma gidan mamansa,abinda Omar bai sani ba sahar ta kara lalacewa sai matan manyan alhazawa take kulawa Wanda suke da naira,wata kawarta hajiya talatu matar wani gomnace ita ta bawa sahar shawarar tunda kullum a hanya take ga mijinta ba wani shiri sukeyi ba kuma sahar akwai tsananin sha'awa kawai tunda tana da kudi a hannu ga maza nan samari yara sai ta zaba tunda yanzu matasa sun zama kwadayayyu kudi suke nema ta ko wacce hanya komai kudi,to ta mori dukiyarta ta samu wasu suna biya mata bukatarta tana biyan kudi.amma ta daina zubar da ajinta wurin omar mijinta tunda shi baya taba nemanta itama ta daina kai kanta.wa'iyazu billah mai makon muyi kokari mu gyara halinmu sai mu kara dilmiyewa mu jefa kanmu halaka wacce har ka mutu kana da na sani.Allah shiryamu gaba daya.dan yanzu wannan ya zama ruwan dare wurin wasu matayen musamman masu naira
Mama na room dinta tana shafa magani a kafafunta da suke mata ciwo omar ya shigo da sallama,da fara'a ta amsa masa babanmu ina ka shiga ne haka ban ganka ba,maganin ya karba ya karasa shafa mata,ina gida mama ga office ba sauki,omar kenan na dauka ma ko suruka ta biyu ka samo min,murmushi yayi mama aure tun yanzu zan kara aure,ina zan kai matan dayar ma da za a yagemin ita so nakeyi,daria mama tayi omar sai hakuri dan kawai ba auren so aka maka bane kuma matar taka ba ayi dace ba shi yasa ka fadi haka,
Mama kinji yanzu na dawo gida wai ta bawa yan aiki sako a fada min ta wuce Ghana,duk yawon da takeyi kasar nan bai isheta ba mama.mama ma ranta ya baci da jin abinda sahar tayi,ka bari zanwa baffanku magana a waya sai aje gidansu a sanar da iyayenta tunda ta Gagari kowa,ni ma zan kirata a waya,mama ki kyaleta pls kar tazo tana miki rashin kunya kin San bazan kyale ba.ya isa omar dole a fada mata gaskia.to mama ba matsala.ledar da iklas ta bashi ya mikawa mama,ledar kaka ummi ma ya mika mata gashi mama sunce a baki kuma suna gaisheki,murmushi tayi na gode Allah saka,amma banana wannan su waye suka bani bazan bude ba sai ka fada min,ohh mama wannan red din na kaka ummi ne wannan kuma na jikarta iklas,
Murmushi mama tayi tana jin dadi tana fatan abinda tayi tunani ya zama gaske,a fili tace ban ganesu ba ai...uhm..uhm yana Sosa kai yace aikine ya hadamu gidan gona.kyaleshi mama tayi, tace angode kaga mutanen kirki bari mu gani mene ciki.
Ledar iklas ta fara budewa wata katuwar farar roba ce mai murfi shake take tam da dambun naman kaza iklas yinsa tayi musamman sabo da suhaila na sonsa ganin omar yasa ta canja idea ta juye masa duka me uban yawa ta bawa mamansa.mama taji dadi sosai,ta bude ledar ummi kayan kamshi ne da sauran abubuwan miya busassu.mama sai murna takeyi omar har mamakin murnar mama yayii,babana ya kamata ka kawo min su na gansu ko ka kaini gidansu,ba yanzu ba mama to allah kaimu koma yaushene.kasan bana cin maiko sabo da ulcer ta,kadan zan iba ni da su abdullah.dauki wannan kaje dakinka dashi..da kyar ya karbi na robar wai a dole bayacin girkin yara,amma ya dauke ya wuce room dashi yana bata rai da muzurai.
Sadiya na hango sai masifa take zazzagawa tana dura ashar a compound din gidan,duk wani ma'aikata sunyi luf suna jinta,suleim na hango da uniform jikinta tsugune a gaban sadiya tana faman bata hakuri,anty sadiya kiyi hakuri ban San takadar tana da amfani ba shi yasa Dana gani na yaga na zuba a dustbin,
Wani lafiyayyan mari sadiya ta kwadawa suleim Allah sarki yar yarinya sai ga shatin hannun sadiya radede a fuskarta,kuka ta tsala hade da dafe kumatunta,gashinta sadiya ta ja da karfi dan uwarki baki San darajar takarda ba,gadon tsiya ba laifinki bane uwarku ba ilmi ne da ita ba jahila ce shi yasa Baku San darajar takarda ba,tsabar masifar da sadiya keyi ko kula da motar omar wacce ta shigo har ya parker bata sani ba,hankada suleim tayi ta tintsira ta bige kanta da bakinta,wani gigitaccen kuka ta fasa,omar Wanda yana kallon abinda ke faruwa ransa ya baci,idonsa yayi jajir,zuciya ta tashi,karasowa yayi wajen ya ware hannu ya dinga zubawa sadiya mari,tun tana tsaye sai da takai kasa,belt din wandonsa ya zare ya fara zabgarta gashi ya riketa ram sai daya zaneta tas jikinta duk ya fashe,a hakan ma dan mama ta fito ta rikeshi ne,duk yan gidan suna wurin suna kallo,kafin kace me su Aisha naja sun kama zage zage suma,sannan suka kira baffa da ummansu dake Russia suka fadi karya da gaskia.
Nanfa hajiya rahina ta haukacewa baffan su omar,wlh bazan yarda ko a dauki mataki ko na dauka da kaina,an Dade ana zalinta ni da yarana Sam bazan yarda wlh,akan haka sai dai in ka sakeni amma billahillazi bazan yarda ya kashe min yara ba.tsawa baffa ya daka mata ki saurara min shashashar banza,duka kannensa ne yana da damar hukuntasu,nasan dole omar yana da dalilinsa me karfi,yaran naki bansan halinsu bane an fada miki, marasa tarbiya omar ne wakili na yana da daman yanke komai a gidana.kuma wlh tun kafin na koma ki fada musu dukkansu su fito da miji,na gaji da zubar min da mutunci da sukeyi a unguwa..... Wai wai ai rahina kururuwa ta sa da gunjin kuka,baffa kuwa gidan ya bari.
Asmahbaffa na godiya gareku masoya readers,masu commenting idan nayi posting kunfi kowa birgeni, domin kuna bani kwarin gwiwar typing, na tabbatar kuna jin dadinsa.
[17/03, 21:45] Hadiza Sani Fbk: ⓂⓂⓂ
MA'AIKACIYAR
GOMNATI
ⓂⓂⓂ
10-15
By
Asmabaffa.
Pls readers a dinga kula ana amfani da sakon da muke isarwa me kyau,marar kyau ayi watsi dasu, bukatata kenan,kuskuren da mukayi Allah yafe mana kuma readers ayi mana afwa.Allah tsarkake mana zucuyoyinmu,a dinga rula sakonni nake isarwa ko wanne page lol na gode muku yan readers dina ina ji daku.kunyi male male araina.
Tunda baffa ya fita taki daina kuka sosai take sheka kuka an Zane first daughter dinta me irin halinta sadiya,sai da ta koshi da kuka daga bisani ta jawo wayarta,ta kira haj bilki babbar kawarta tas ta kwashe zance ta fada mata,lallai yaron nan kwai tsinane tambadadde cewar haj bilki,rahina tace shi yasa na fada miki kije min wurin babban malaminki na kasar Mali ayita ta kare,na gaji da tsinannun mutanen nan,akan wannan zan iya dawowa Nigeria muje tare bilki ki rakani,duk wanda na sani nawa malaman ba kudin da ban kasheba abu shuru,nasan naki manyan shegu ne,daga bangaren haj.bilki baki ta tabe daga bisani taji dadi a ranta tana adduar insha'allah bazaiyi aiki ba,yar iska wai ke mijinki me kudi har yanga kike mana kin fimu kudi,ga yaranki masu aikin gomnati,ai sai na miki sanadiyar barin gidan alhaji mohd wlh,hauka nake na yarda ki samu daula ke kadai,Baki San yanda nake miki bakin cikin auren alhaji mohd ba,dan yafi mijina kudi...
Haj rahinace ta katsewa bilki mugun tunanin dake ranta tana ta hello....hello....inajinki network ne wlh rahina,kina jina ki kwantar da hankalinki ni danake babbar kawarki ai dole zanje kasar Mali ko dan ke,ki bar komai hannuna,ammafa sai kin turo isassun kudi,babu matsala wannan cewar rahina,kuma dole sai mun haada da tuggunmu na mata.kin san yanzu sunfi tsafi aiki wajen maza,wasu maganganu haj bilki ta tsarawa haj rahina wanda koni banji me suke cewa ba readers.
Suna katse wayar haj rahina tace shegiya haj bilki tasan takan duniya....banza marar wayo yar matsiyata kina taimakamin na samu abinda nake buri ko kawa nafi karfin nayi dake,jahilar banza yaushe ma inba dole ba zan tsaya ko kusa dani ki raba,iyakarki primary schl.nan umma rahina ta kwashe da daria,a karshe tace har a bada bilki sai dai ki zama baiwata ba kawa ba.haj bilki kuwa tsaki taja tace shashasha naci banza,kudinki zan cinye na Gina kaina,ta zata shawarar Dana bata zata bulle,hhhhh lallai alhaji mohd zai saki dattijuwar banza zaki gane wace bilki.
Kunji fa readers ko wacce cin amanar ko wacce takeyi,kuma wannan cin amanar ya zama ruwan dare tsakanin kawaye musamman mata,kowacce bata son yar uwarta taci gaba hassada,ga mugun nufi wannan ya zama ruwan dare a rayuwarmu ta yanzu,taya zamu ga dai dai wannan ya jefi wannan ,wannan ya jefi wannan.Allah ka tsarkake mana zuciyoyoyinmu.
Bangaren su oga omar kuwa abin nasa yaci tura,da kyar mama ta janyeshi suka dauki suleim,family doctor mama ta kira yawa suleim dressing,abdallah harda kuka an jiwa kanwarsa ciwo,omar kuwa jikinsa sai rawa yake ran maza ya bacifa readers,dama can ya gaji da halin kannen nasa,sharesu kawai yakeyi amma komai da sukewa mama da kannensa ya sani kyalewa yakeyi dan a zauna lfy,amma tunda haka suka zaba zaiyi maganinsu idan basu nutsu ba.sadiya kuwa sai ihu takeyi jiki ya kumbura,sun hadu a kanta su Aisha suna ta Gasa mata jiki yayinda suke ta zage zagensu iri iri,sadiya kuwa jinsu kawai takeyi dan Allah ne kadai yasan irin matakin da zata dauka kan su omar da uwarsa,dan tayi alkawari ko zata mutu,ko zata karar da salary dinta sai ta kulla musu bala'i,yanzu ta fara ta daina jiran ummansu yanzu itama ta zauna da kafafunta daram sai taga karshen omar da wanda ya rabeshi gaba daya...ruwan zafin da Aisha ta danna mata a gefen wuya shi ya dai daita tunaninta ta saki kara da ihu hade da cewa Aisha zanci uwarki kasheni zakiyi.tana ta ciccijewa sabo da azaba..ni kuwa nace heeee..na fece daga wurin,
Omar bakin ciki ya cunkushe masa zucia,haushin gidan yakeji gaba daya,mikewa yayi ya bar gidan gaba daya,har ya dauki hanyar office din sultan ya fasa ya canja hanya,dan yasan idan yaje wurin sultan bacin rai zai kara masa,da gudu na bishi readers na tafi gulma....lol.mayenta layin su iklas na ganshi gheto area yana Jan motar a slow yau 6days rabonsa da gidan,a tsakiyar layin gefen titi ya hangota tana magana da wasu maza igbo su biyu,sanye take cikin uniform 1:30 da alama daga schl take,
Wani bakin ciki ne ya kara mamaye cuciyar oga omar,ya kwaso bakin ciki yaci karo da wani,haka kawai ya tsinci kansa cike da bacin rai ganin iklas da wasu kucakan maza Igbo,tana ta surutunta hankali kwance.omar na karasowa wajen ya danna wani horn da karfi wanda ya janyo hankalin kowa dake wurin suka zubawa shegiyar azababbiyar motarsa na mujiya,cikinsu harda iklas me dafaffen kwai,glass ya sauke sukayi 4 eye da iklas,alama ya mata tazo sallama tayiwa mazan Igbo bye Emma a gwarance suka ce gomnati gomnati murmushi iklas tayi tare da mikawa Emma hannu suka tafa hade da cewa NO BE SMALL THINGS WOOO,Dayan Dennis yace,ur first salary is my share,nanfa gomnati tace,never mind A NO DEY CARRY LAST MY BRO,daria sukayi dukansu sannan ta daga hannu tana WE GO RUNNERM,U ASEY DEY NOOOOW.ta nufi motar omar kafin ta karasa wani bahaushe saleem yace gomnati sai kinci da biro hannu ta daga masa tare da bude gaban motar ta shiga,ta glass ta leko da kanta tace saleem salary na farko da kasonka ciki,fisgar motar omar yayi ji kake gwaf kan iklas ya bigi gaban motar,birki yaci kyaaaaa....ta koma da baya jagwaf...kafin ta nutsu ya kara fincikar motar ta kuma gwaraf da kanta a jikin glass,kuka ta kece dashi yanda zafi ya hadata ta ko ina.cisgar motar omar ya karayi kamar zasu kifa,ina gefe nace Allah tsare na cikinta Dana kan hanya,kuka iklas takeyi musamman da goshinta wani katon kululu ya fito,parking yayi kofar gidansu,da Sauri iklas ta fita dan ta ga mutuwa with her own koro koro eye,tana fita omar ya sauke glass ji mana....juyowa iklas tayi, u hv to be very careful banda sauki ina gargadinki ki tausayawa lafiyarki kiyi abinda ya dace kunnena yaji da wanda idona zai gani,zan dawo next time hukunci yana nan zaki karba dai dai da ke cewar omar tare da figar motarsa ya bar layin gaba daya cike da jin tsananin haushin iklas,shi kadai ya rasa ma ina zaije ya huta,wani katafaren guest house dinsa ya nufa dake gwagwalada,da ma'aikata da komai a gidan so very neat.
Iklas kam ta Dade a tsaye tana tunanin to ita wai me tayi masa,mene hadinta dashi da haka kawai zai tsaneta,ya dauki karan tsana ya Dora mata..tsaki taja tana mulmula ciwonta ta wuce gida tana kunkuni za a kasheta a banza.
Ummi ce ta tsare iklas da tambayar me ya sameta a goshi,fada mukayi a schl ummi Da wata,shine ta buga min kai da chair nima na fasa nata da dutse.kin kyauta iklas Allah taimaka cewar ummi,shashasha matsa ko na makeki wacce bata San ta girma ba,bari Allah ya kawo min yaron albarka umaru na fada masa tunda naga kinfi jin fadan sa.
To wai ummi ni me nake mikine dazaki dinga hadani da wani azzalumi bare can,bamu hada dangi dashi ba amma har kinfi sonsa akanmu...ummi ce ta maketa da gudu ta mike ta wuce toilet,sallah tayi,wanka da cin abinci,mikewa tayi ta kwanta tana tunani kala kala wanda yafi yawa akan omar.tana tunaninsa kuma sai taji ranta yayi fari,ji tayi gwara tayi tunanin oga fiye Dana schl,ita kadai idan tayi tunanin schl sai tace no sai tayi na omar,sai ta saki murmushi tare da cewa kai ni kwai banza,mene abun tunashi,me ma zanyi dashi,ina Sam mijina yafi wancan ogan kyau ma,
Maman omar ce ta kira wayar sahar sai da tayi mata 5 missed calls bata daga ba,after 40min sahar ta kira back tasan Maman mijinta ce tana da number amma sai tace hello who is on the line pls?,who am I speaking with? Shuru mama tayi tana jin sahar na turancinta ta gane me take fada amma baza ta iya mayar mata da turanci ba domin abdallah yana koya mata sosai shi yasa tana ji sai dai baza ta iya mayar da magana da turanci da tsayi ba.
Sahar Maman omar CE...ohh mama ya gida ya aiki,lfy alhmdllh,sahar dama naji tafiyar da kikayi
Showing 15001 words to 18000 words out of 104017 words
Pls ka bari ta dawo mana ko ka tsaya na kira ta yanzu pls,sallamar ummi sukaji ta shigo palon,yawwa ummi zai tafi wai cewar iklas kuma baici komai ba wlh,hangame baki ummi tayi haba umaru ya zaka Mana haka,mu ka taimakamana mun yarda mun karba duk da bamu sanka ba,ba dangin iya ba na baba amma mun yarda da kai,yanzu dan mun baka abinci shine baza ka ci ba,kamar mun baka guba ko wata cuta.
In dai kana so mu shirya gaskia kaci ko kadan ne idan kuma kyankyami kakeyi bazan ma dole ba.da sauri omar ya koma ya zauna haba ummi ba wani abu kiyi hakuri bari naci.baki ummi ta washe haba ko da kaifa amma ai sai ka sa muji ba dadi ai,iklas zuba masa bari naje na karasa gyara wasu kaya.omar ji yakeyi tsohuwar na birgeshi,kallonta yakeyi kamar mama.
Tana bude flask wani kamshi ya daki hancinsa me dadi,fried rice lafiyayya tasha hadi da su hanta etc,zuba masa tayi ta kara bude wani bowl me kyau na glass kaji ne soyayyu zuba masa tayi a gefe ga hadadden salat,mika masa tayi ta zuba masa lemon kwakwa.
Yatsina fuska ya dauki spoon da kyar ya fara ci,wani arnen dadi yaji kamar kunnensa zai fita,sai santi yakeyi a ransa a fili kuwa yatsina fuska kawai yakeyi,iklas na kallonsa kafafunta sunyi sanyi tun a fuskarsa ta gane baiji dadin abincin ba,kamar zatayi kuka bata San ace girkinta baiyi dadi ba.
Musamman a wajen Omar bata San me yasa take so ya yaba girkinta ba.idonta har ya Tara kwalla kadan,omar yana kallonta ya gama ganota tsab,a ransa sai daria yakeyi,ganin kaka ummi bata kusa yasa yake ta wannan yatsina fuska,tunda yaga yanayin iklas ya kara yatsine fuska dan yanzu har yi yakeyi kamar zaiyi amai,abin mamaki yaci abincin yafi Rabin plate,lemon ma yasha yaji dadi amma harda rike ciki wai a dole yaci guba.can yace kai ummi ta takura naci jagwalgwalo,babu dadi haka akeyin girki,wannan ai sai ki kashe mutane.
Hawaye ne ya digo dis daga idon iklas da sauri ta goge kar sir omar ya gani Wanda ta Riga ta makaro a idonsa tayi komai.kitchen ta shiga sai gata ta fito da wata Leda me kyau a hannunta,mikawa Omar tayi ga wannan ka kaiwa mom dinka,
Tunaninsa ne ya tsaya cak wannan yarinyar akwai mamaki acikin alamarinta,wai tana 15yrs har tasan ta bawa mamansa kyauta yaji dadi kuma ta kara birgeshi.karba yayi hade da cewa tnx kira ummi,sai gani yayi iklas ta tsaya rubutu a jotter bai San me ta rubuta sai da ta gama ta wuce kiran ummi,ita kuwa iklas ta Riga tayi lissafi wannan week din sunyi dambun naman kaza gashi basu ci ba ta bayar kyauta,shi yasa ta canja lissafinta..sallama omar ya musu ummi ma ta bashi sakonta ya ba mama,
Gidansa yaje ya duba lafiyar sahar sabo da amanar aure dake kansa,yar aikinta ya tambaya ina sahar ?ranka Dade tayi tafiya yau tace a fada ma ta tafi kasar ghana akwai wani aiki za suyi..ok kawai yace ya koma gidan mamansa,abinda Omar bai sani ba sahar ta kara lalacewa sai matan manyan alhazawa take kulawa Wanda suke da naira,wata kawarta hajiya talatu matar wani gomnace ita ta bawa sahar shawarar tunda kullum a hanya take ga mijinta ba wani shiri sukeyi ba kuma sahar akwai tsananin sha'awa kawai tunda tana da kudi a hannu ga maza nan samari yara sai ta zaba tunda yanzu matasa sun zama kwadayayyu kudi suke nema ta ko wacce hanya komai kudi,to ta mori dukiyarta ta samu wasu suna biya mata bukatarta tana biyan kudi.amma ta daina zubar da ajinta wurin omar mijinta tunda shi baya taba nemanta itama ta daina kai kanta.wa'iyazu billah mai makon muyi kokari mu gyara halinmu sai mu kara dilmiyewa mu jefa kanmu halaka wacce har ka mutu kana da na sani.Allah shiryamu gaba daya.dan yanzu wannan ya zama ruwan dare wurin wasu matayen musamman masu naira
Mama na room dinta tana shafa magani a kafafunta da suke mata ciwo omar ya shigo da sallama,da fara'a ta amsa masa babanmu ina ka shiga ne haka ban ganka ba,maganin ya karba ya karasa shafa mata,ina gida mama ga office ba sauki,omar kenan na dauka ma ko suruka ta biyu ka samo min,murmushi yayi mama aure tun yanzu zan kara aure,ina zan kai matan dayar ma da za a yagemin ita so nakeyi,daria mama tayi omar sai hakuri dan kawai ba auren so aka maka bane kuma matar taka ba ayi dace ba shi yasa ka fadi haka,
Mama kinji yanzu na dawo gida wai ta bawa yan aiki sako a fada min ta wuce Ghana,duk yawon da takeyi kasar nan bai isheta ba mama.mama ma ranta ya baci da jin abinda sahar tayi,ka bari zanwa baffanku magana a waya sai aje gidansu a sanar da iyayenta tunda ta Gagari kowa,ni ma zan kirata a waya,mama ki kyaleta pls kar tazo tana miki rashin kunya kin San bazan kyale ba.ya isa omar dole a fada mata gaskia.to mama ba matsala.ledar da iklas ta bashi ya mikawa mama,ledar kaka ummi ma ya mika mata gashi mama sunce a baki kuma suna gaisheki,murmushi tayi na gode Allah saka,amma banana wannan su waye suka bani bazan bude ba sai ka fada min,ohh mama wannan red din na kaka ummi ne wannan kuma na jikarta iklas,
Murmushi mama tayi tana jin dadi tana fatan abinda tayi tunani ya zama gaske,a fili tace ban ganesu ba ai...uhm..uhm yana Sosa kai yace aikine ya hadamu gidan gona.kyaleshi mama tayi, tace angode kaga mutanen kirki bari mu gani mene ciki.
Ledar iklas ta fara budewa wata katuwar farar roba ce mai murfi shake take tam da dambun naman kaza iklas yinsa tayi musamman sabo da suhaila na sonsa ganin omar yasa ta canja idea ta juye masa duka me uban yawa ta bawa mamansa.mama taji dadi sosai,ta bude ledar ummi kayan kamshi ne da sauran abubuwan miya busassu.mama sai murna takeyi omar har mamakin murnar mama yayii,babana ya kamata ka kawo min su na gansu ko ka kaini gidansu,ba yanzu ba mama to allah kaimu koma yaushene.kasan bana cin maiko sabo da ulcer ta,kadan zan iba ni da su abdullah.dauki wannan kaje dakinka dashi..da kyar ya karbi na robar wai a dole bayacin girkin yara,amma ya dauke ya wuce room dashi yana bata rai da muzurai.
Sadiya na hango sai masifa take zazzagawa tana dura ashar a compound din gidan,duk wani ma'aikata sunyi luf suna jinta,suleim na hango da uniform jikinta tsugune a gaban sadiya tana faman bata hakuri,anty sadiya kiyi hakuri ban San takadar tana da amfani ba shi yasa Dana gani na yaga na zuba a dustbin,
Wani lafiyayyan mari sadiya ta kwadawa suleim Allah sarki yar yarinya sai ga shatin hannun sadiya radede a fuskarta,kuka ta tsala hade da dafe kumatunta,gashinta sadiya ta ja da karfi dan uwarki baki San darajar takarda ba,gadon tsiya ba laifinki bane uwarku ba ilmi ne da ita ba jahila ce shi yasa Baku San darajar takarda ba,tsabar masifar da sadiya keyi ko kula da motar omar wacce ta shigo har ya parker bata sani ba,hankada suleim tayi ta tintsira ta bige kanta da bakinta,wani gigitaccen kuka ta fasa,omar Wanda yana kallon abinda ke faruwa ransa ya baci,idonsa yayi jajir,zuciya ta tashi,karasowa yayi wajen ya ware hannu ya dinga zubawa sadiya mari,tun tana tsaye sai da takai kasa,belt din wandonsa ya zare ya fara zabgarta gashi ya riketa ram sai daya zaneta tas jikinta duk ya fashe,a hakan ma dan mama ta fito ta rikeshi ne,duk yan gidan suna wurin suna kallo,kafin kace me su Aisha naja sun kama zage zage suma,sannan suka kira baffa da ummansu dake Russia suka fadi karya da gaskia.
Nanfa hajiya rahina ta haukacewa baffan su omar,wlh bazan yarda ko a dauki mataki ko na dauka da kaina,an Dade ana zalinta ni da yarana Sam bazan yarda wlh,akan haka sai dai in ka sakeni amma billahillazi bazan yarda ya kashe min yara ba.tsawa baffa ya daka mata ki saurara min shashashar banza,duka kannensa ne yana da damar hukuntasu,nasan dole omar yana da dalilinsa me karfi,yaran naki bansan halinsu bane an fada miki, marasa tarbiya omar ne wakili na yana da daman yanke komai a gidana.kuma wlh tun kafin na koma ki fada musu dukkansu su fito da miji,na gaji da zubar min da mutunci da sukeyi a unguwa..... Wai wai ai rahina kururuwa ta sa da gunjin kuka,baffa kuwa gidan ya bari.
Asmahbaffa na godiya gareku masoya readers,masu commenting idan nayi posting kunfi kowa birgeni, domin kuna bani kwarin gwiwar typing, na tabbatar kuna jin dadinsa.
[17/03, 21:45] Hadiza Sani Fbk: ⓂⓂⓂ
MA'AIKACIYAR
GOMNATI
ⓂⓂⓂ
10-15
By
Asmabaffa.
Pls readers a dinga kula ana amfani da sakon da muke isarwa me kyau,marar kyau ayi watsi dasu, bukatata kenan,kuskuren da mukayi Allah yafe mana kuma readers ayi mana afwa.Allah tsarkake mana zucuyoyinmu,a dinga rula sakonni nake isarwa ko wanne page lol na gode muku yan readers dina ina ji daku.kunyi male male araina.
Tunda baffa ya fita taki daina kuka sosai take sheka kuka an Zane first daughter dinta me irin halinta sadiya,sai da ta koshi da kuka daga bisani ta jawo wayarta,ta kira haj bilki babbar kawarta tas ta kwashe zance ta fada mata,lallai yaron nan kwai tsinane tambadadde cewar haj bilki,rahina tace shi yasa na fada miki kije min wurin babban malaminki na kasar Mali ayita ta kare,na gaji da tsinannun mutanen nan,akan wannan zan iya dawowa Nigeria muje tare bilki ki rakani,duk wanda na sani nawa malaman ba kudin da ban kasheba abu shuru,nasan naki manyan shegu ne,daga bangaren haj.bilki baki ta tabe daga bisani taji dadi a ranta tana adduar insha'allah bazaiyi aiki ba,yar iska wai ke mijinki me kudi har yanga kike mana kin fimu kudi,ga yaranki masu aikin gomnati,ai sai na miki sanadiyar barin gidan alhaji mohd wlh,hauka nake na yarda ki samu daula ke kadai,Baki San yanda nake miki bakin cikin auren alhaji mohd ba,dan yafi mijina kudi...
Haj rahinace ta katsewa bilki mugun tunanin dake ranta tana ta hello....hello....inajinki network ne wlh rahina,kina jina ki kwantar da hankalinki ni danake babbar kawarki ai dole zanje kasar Mali ko dan ke,ki bar komai hannuna,ammafa sai kin turo isassun kudi,babu matsala wannan cewar rahina,kuma dole sai mun haada da tuggunmu na mata.kin san yanzu sunfi tsafi aiki wajen maza,wasu maganganu haj bilki ta tsarawa haj rahina wanda koni banji me suke cewa ba readers.
Suna katse wayar haj rahina tace shegiya haj bilki tasan takan duniya....banza marar wayo yar matsiyata kina taimakamin na samu abinda nake buri ko kawa nafi karfin nayi dake,jahilar banza yaushe ma inba dole ba zan tsaya ko kusa dani ki raba,iyakarki primary schl.nan umma rahina ta kwashe da daria,a karshe tace har a bada bilki sai dai ki zama baiwata ba kawa ba.haj bilki kuwa tsaki taja tace shashasha naci banza,kudinki zan cinye na Gina kaina,ta zata shawarar Dana bata zata bulle,hhhhh lallai alhaji mohd zai saki dattijuwar banza zaki gane wace bilki.
Kunji fa readers ko wacce cin amanar ko wacce takeyi,kuma wannan cin amanar ya zama ruwan dare tsakanin kawaye musamman mata,kowacce bata son yar uwarta taci gaba hassada,ga mugun nufi wannan ya zama ruwan dare a rayuwarmu ta yanzu,taya zamu ga dai dai wannan ya jefi wannan ,wannan ya jefi wannan.Allah ka tsarkake mana zuciyoyoyinmu.
Bangaren su oga omar kuwa abin nasa yaci tura,da kyar mama ta janyeshi suka dauki suleim,family doctor mama ta kira yawa suleim dressing,abdallah harda kuka an jiwa kanwarsa ciwo,omar kuwa jikinsa sai rawa yake ran maza ya bacifa readers,dama can ya gaji da halin kannen nasa,sharesu kawai yakeyi amma komai da sukewa mama da kannensa ya sani kyalewa yakeyi dan a zauna lfy,amma tunda haka suka zaba zaiyi maganinsu idan basu nutsu ba.sadiya kuwa sai ihu takeyi jiki ya kumbura,sun hadu a kanta su Aisha suna ta Gasa mata jiki yayinda suke ta zage zagensu iri iri,sadiya kuwa jinsu kawai takeyi dan Allah ne kadai yasan irin matakin da zata dauka kan su omar da uwarsa,dan tayi alkawari ko zata mutu,ko zata karar da salary dinta sai ta kulla musu bala'i,yanzu ta fara ta daina jiran ummansu yanzu itama ta zauna da kafafunta daram sai taga karshen omar da wanda ya rabeshi gaba daya...ruwan zafin da Aisha ta danna mata a gefen wuya shi ya dai daita tunaninta ta saki kara da ihu hade da cewa Aisha zanci uwarki kasheni zakiyi.tana ta ciccijewa sabo da azaba..ni kuwa nace heeee..na fece daga wurin,
Omar bakin ciki ya cunkushe masa zucia,haushin gidan yakeji gaba daya,mikewa yayi ya bar gidan gaba daya,har ya dauki hanyar office din sultan ya fasa ya canja hanya,dan yasan idan yaje wurin sultan bacin rai zai kara masa,da gudu na bishi readers na tafi gulma....lol.mayenta layin su iklas na ganshi gheto area yana Jan motar a slow yau 6days rabonsa da gidan,a tsakiyar layin gefen titi ya hangota tana magana da wasu maza igbo su biyu,sanye take cikin uniform 1:30 da alama daga schl take,
Wani bakin ciki ne ya kara mamaye cuciyar oga omar,ya kwaso bakin ciki yaci karo da wani,haka kawai ya tsinci kansa cike da bacin rai ganin iklas da wasu kucakan maza Igbo,tana ta surutunta hankali kwance.omar na karasowa wajen ya danna wani horn da karfi wanda ya janyo hankalin kowa dake wurin suka zubawa shegiyar azababbiyar motarsa na mujiya,cikinsu harda iklas me dafaffen kwai,glass ya sauke sukayi 4 eye da iklas,alama ya mata tazo sallama tayiwa mazan Igbo bye Emma a gwarance suka ce gomnati gomnati murmushi iklas tayi tare da mikawa Emma hannu suka tafa hade da cewa NO BE SMALL THINGS WOOO,Dayan Dennis yace,ur first salary is my share,nanfa gomnati tace,never mind A NO DEY CARRY LAST MY BRO,daria sukayi dukansu sannan ta daga hannu tana WE GO RUNNERM,U ASEY DEY NOOOOW.ta nufi motar omar kafin ta karasa wani bahaushe saleem yace gomnati sai kinci da biro hannu ta daga masa tare da bude gaban motar ta shiga,ta glass ta leko da kanta tace saleem salary na farko da kasonka ciki,fisgar motar omar yayi ji kake gwaf kan iklas ya bigi gaban motar,birki yaci kyaaaaa....ta koma da baya jagwaf...kafin ta nutsu ya kara fincikar motar ta kuma gwaraf da kanta a jikin glass,kuka ta kece dashi yanda zafi ya hadata ta ko ina.cisgar motar omar ya karayi kamar zasu kifa,ina gefe nace Allah tsare na cikinta Dana kan hanya,kuka iklas takeyi musamman da goshinta wani katon kululu ya fito,parking yayi kofar gidansu,da Sauri iklas ta fita dan ta ga mutuwa with her own koro koro eye,tana fita omar ya sauke glass ji mana....juyowa iklas tayi, u hv to be very careful banda sauki ina gargadinki ki tausayawa lafiyarki kiyi abinda ya dace kunnena yaji da wanda idona zai gani,zan dawo next time hukunci yana nan zaki karba dai dai da ke cewar omar tare da figar motarsa ya bar layin gaba daya cike da jin tsananin haushin iklas,shi kadai ya rasa ma ina zaije ya huta,wani katafaren guest house dinsa ya nufa dake gwagwalada,da ma'aikata da komai a gidan so very neat.
Iklas kam ta Dade a tsaye tana tunanin to ita wai me tayi masa,mene hadinta dashi da haka kawai zai tsaneta,ya dauki karan tsana ya Dora mata..tsaki taja tana mulmula ciwonta ta wuce gida tana kunkuni za a kasheta a banza.
Ummi ce ta tsare iklas da tambayar me ya sameta a goshi,fada mukayi a schl ummi Da wata,shine ta buga min kai da chair nima na fasa nata da dutse.kin kyauta iklas Allah taimaka cewar ummi,shashasha matsa ko na makeki wacce bata San ta girma ba,bari Allah ya kawo min yaron albarka umaru na fada masa tunda naga kinfi jin fadan sa.
To wai ummi ni me nake mikine dazaki dinga hadani da wani azzalumi bare can,bamu hada dangi dashi ba amma har kinfi sonsa akanmu...ummi ce ta maketa da gudu ta mike ta wuce toilet,sallah tayi,wanka da cin abinci,mikewa tayi ta kwanta tana tunani kala kala wanda yafi yawa akan omar.tana tunaninsa kuma sai taji ranta yayi fari,ji tayi gwara tayi tunanin oga fiye Dana schl,ita kadai idan tayi tunanin schl sai tace no sai tayi na omar,sai ta saki murmushi tare da cewa kai ni kwai banza,mene abun tunashi,me ma zanyi dashi,ina Sam mijina yafi wancan ogan kyau ma,
Maman omar ce ta kira wayar sahar sai da tayi mata 5 missed calls bata daga ba,after 40min sahar ta kira back tasan Maman mijinta ce tana da number amma sai tace hello who is on the line pls?,who am I speaking with? Shuru mama tayi tana jin sahar na turancinta ta gane me take fada amma baza ta iya mayar mata da turanci ba domin abdallah yana koya mata sosai shi yasa tana ji sai dai baza ta iya mayar da magana da turanci da tsayi ba.
Sahar Maman omar CE...ohh mama ya gida ya aiki,lfy alhmdllh,sahar dama naji tafiyar da kikayi
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6 Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35