kyar tashi da dabara amma kai ba ruwanka,yanzu an dawo dani dan na huta jiba yadda kake min rigima,kayi hakuri na haihu nayi Arba'in,a fusace yace au harma arba'in Ashe kece mijin ma,to Honey zoka danneni ka kwata,
Murmushi yayi Iklas rigima kenan,zaki ga sanda zan danneki ne ai,dan kawai yanzu kinyi nauyi ne dole a biki sannu amma da sai kinyi bayani,nasan zaka iya ai oya zo muci abinci ka daina rigimar kai kasanni bazan bar mijina cikin Matsala ba dole akwai mafita ka daina bata bakinka,nayi yaji ma na nemoka baka zo biko ba bare yanzu da dole nima su Mama sukayi min,Ummi kakata ce ba wata kunyarta nakeji ba,
Sai yanzu ya dan samu nutsuwa da farin ciki,matsowa yayi tare da zama gabanta murmushi dauke a fuskarsa zama yayi sosai a gaban yana shafa ckinta,daga bisani ya jawo naman yana yankowa ya sa abakinsa sanna ya hade bakinta da nata yasa mata naman ta cinye tana kada kai uhmmmmm kaji dadin bala'i kuwa,
Haka ya dinga ciyar da ita har ta koshi,yau Omar a part dinsa ya kwana gidan Mama ba tare da kowa ya sani ba,Iklas kuwa tayi tunanin dama Omar dakinsa zai kwana,dan haka gaba daya tausayinsa takeji hade da wani sabon sonsa,da sassafe ta shirya kanta cikin doguwar rigar a tamfa,sama ya matse kasa ya bude sosai ya boye cikin ta,fitowa tayi sadaf sadaf zata shiga dakin Omar,suhaila ta gani da suleim zazu tafi schl,Anty ina kwana suka gasheta sukayi gaba da gudu,ita kuma ta fada room din Omar a kan bed ta hangoshi yana ta baccinsa cike da nutsuwa,komawa tayi ta sa key a kofar saboda tsaro.
Tana dawowa ta haura saman bed din tare da rungumeshi kam tana shakar kamshinsa tare da manna masa kiss a goshi,a hankali ya bude idonsa masu matukar kyau,ganin Gomnati a jikinsa ba karamin farin ciki yayi ba.
Ba tare da bata lokaci ba shima ya Kara manneta a kirjinsa wifey I miss u da kyar nayi bacci jiya,baki zo ba har jiranki nayi,miss u more honey nayi niyyar zuwa bacci ya sace ni,cikinta ya Shiga shafawa ya gudan jini na lafiya yake?haushi Iklas taji yace gudan jininsa wato ya kwace mata mijinta,
Shinema gudan jinin naka,ni wlh shi yasa banso haihuwar nan ba,yanzu sai ka dinga daukansa ni kana shareni,dariya Omar yayi me kishi da danta haka akeyin Maman babyn?ta tsani danta? Kece fa zuciyata gaba daya,cike da shagwaba tace to ai jini yafi zuciya muhimmanci shine zaka ce masa gudan jininka ni a bani zuciya,saboda ka samu da,fari tayi da ido Wanda ya susuta Omar lokaci guda tare da cewa dadin abin ai kafin ayi dan ni aka samu,kuma ai da nane.
Dariya Omar yayi kinsan me kike cewa kuwa wifey? Wannan shine ba kano ba birni,ba cinya ba kafar baya, shi yasa tunda ke danki ne kinga shi gudan jinina,ke kuma zuciyata kinga ai kun kwaceni du ke da baby,ni dai Allah ban yarda ba cewar Iklas ,ok to a bashi zuciyar ke gudan jini ko?kafada ta make abinda nafi so zuciyarka shine zaka ce a bashi ita,dariya Omar keyi yace to na bashi liver ta,da Sauri tace tab bai isa ba bazan yarda ba,Kasan kuwa muhimmancin liver da zakace a bashi ita yama fini kenan sosai fa ina laifin ka bashi yar madaciyar jikin hantar taka tunda shi yaro ne,ko ka bashi timbi ko hanji,
Fashewa da dariyar shiriritar Iklas yayi tare da kara kankameta sosai abin dariyar Gomnati da yawa yake, tafin hannunta ya mannawa kiss yana bin hannun da kiss ya gangaro wuyanta nan ya fara lasar wuyanta cike da salon kwarewa tattare da nutsuwa a hankali ya dinga sarrafata tunaninta ya gushe nan fa suka dinga baje harka,bayan sun nutsu wanka sukayi cike da nishadi,Omar na ta zuba mata albarka, Iklas dinsa dabance,tana shagwaba shi sai abinda yake so,gashi tana fahimtar matsalarsa ko bata so sai ta faranta masa,yanda yake bata wahala bata taba nuna gazawarta,
Burinta taga Omar kullum hankalinsa kwance,gaban kowa tana nuna rashin kunyarta dan ta faranta masa.
Har kaya ita ta sawa Omar tare da shiryashi suka fito fes fes dasu,Ummi bataga Iklas ba tunda taga haka to lallai Omar yana gidan,Iklas ta birge Ummi da take kula da mijinta,
Suna hirarsu kasa kasa murmushi dauke a fuskar Iklas suka shiga wajen Ummi suka gaisheta Ummi tana in kaga Zara kaga wata,suna ta murmushi suka je wajen Mama, tana ganinsu haka taji dadi a ranta amma sai ta tamke fuska ta fara yiwa Omar fada Dama nasan baka jin magana Babana saida ka kwana a gidan nan sabo da mun dauko matarka, ka kiyayeni fa,jikinta ya fada haba Mama nifa gwara ki hakura ki kyaleni dan Allah,Iklas ce tayi magana cike da marairaicewa Mama kiyi hakuri ki kyaleshi.ai na kyaleshi Iklas ya zanyi da shi ya fiye rikici,that's my Mum cewar Omar.
Kuje ga breakfast can a dining,Mama ta kara da cewa Iklas yan uwanki na kasar Libya jiya sunyi mana waya ni da Ummi,nayi magana dasu cikin harshen turanci duk da ba wani iya turancin nan nayi ba sosai dama Abdallah ke koya min,sunce zasuzo ganinku nan da 3days sai Ku kirasu kuji komai,number tana wayar Ummi,sosai Iklas take Murna ko ba komai yan uwansu zasu zo dangin mijinta su gansu asan suma suna da gata.
Omar ne ya kira yan uwan Iklas a wayarsa suka tabbatar masa nan da 2days gasu nan ganin yaransu,ai kuwa Saturday na zuwa aka tura driver ya daukosu maza su biyu mata biyu,dayar macen Babba ce sosai ta manyanta,dayar kuma budurwa ce yar gidan best Frnd din Baban Iklas me suna KHAIRAT.
zankadediya itama,part guda Baffa yace a ware musu shima yana nan zuwa next day zaiga yan uwan matar dansa, Iklas ta rasa inda zata sa kanta sabo da murna,su Sadiya ma sunzo sun gaishesu,bangaren Hajiya Rahina ma an rakasu sun gaisa,ba tare da ta nuna musu wani dan hali ba,su Sultan,Raj,yan uwa da abokan arziki duk sun zo sun gaishesu,haka frnds din Iklas suma,Maman saleem,saleem da matarsa duk sun je.
Su Kansu mutan libiya sunji dadi sosai,
Khairat tunda Allah yasa tazo gidan tayi tozali da Omar mijin Gomnati taji duk duniya ba Wanda take so da muradi sai shi,dan haka ta like masa ta manne masa,shi kuma ganin yan uwar abin kaunarsa ce Gomnati Iklas sai yake kulata yana karramata,itama Iklas data ga haka bata damu ba tayi tunanin kawai saboda mijinta ne shi yasa take matukar ji da ya Omar,Wanda ita Khairat balarabiyar kasar libiya Sam ba haka bane a ranta tsabar son Omar ne yayi mata yawa,Wanda tana jin baza ta iya rayuwa ba sai da shi,dole sai dai itama ya aureta tunda musulunci ya bada damar auren mata har hudu,
Shi yasa take Neman hanyar da Omar zai fada tarkon sonta, ita tasan Iklas din Omar ta fita kyau amma dole ne ta sameshi ya aureta.
Shi yasa khairat Sam bata zama a bangaren da Baffa ya basu kullum tana wajen Iklas saboda taga Omar kullum yana manne da matarsa,shi yasa take nacewa kusa da Iklas,Khairat taga Iklas yarinya ce shi yasa take so tayi mata wayo ta kwace mijin,dan burinta ta dauke Omar su koma kasarsu da zama,Khairat shekarunta 28 dan haka ta girmewa Iklas wacce kwanan nan ta cika 17yrs kwata kwata.
Shi fa Omar Khairat ta fara damunsa tana shiga rayuwarsa shi da Iklas, ba dama su kebe waje daya sai tazo ta takura musu,dan dai kawai dangin Gomnati ne da tuni yaci uwarta an wuce wajen,
Amma dannewa kawai yakeyi yana biye mata ganin Iklas bata Nuna damuwarta ba,
Idan sauran bakin sunce time yayi ya kamata su koma kasarsu fafur Khairat ke hanasu wai a bari suga yar uwarsu ta sauka lafiya wato Iklas,Ummi da Mama sun gano take taken Khairat.
Omar yaje gidan Sadiya da Aisha ba tare da ya Sanar da kowa ba,ya musu Sulhu sosai da nasiha sosai sun samu yanci mazan nasu sun fara canjawa inda suma su Sadiya suka kara jajircewa wajen kula da miji,har makaranta ta koyon girki da dabarun zaman aure suka shiga. Har sauran kannansu sun biya musu sun shiga kuma suna ta kula da tarbiyar sauran kannensu tare da yiwa Ummansu Nasiha kuma ta dauka.
Har wajen Baffa suka je gaba dayansu har Umma Rahina suka bashi hakuri kan abubuwan da suka shuka.
Haka Maman Omar ma sun bata hakuri Aisha ta haifi yarta mace me suna Mufida, Sadiya kuwa anayin Hutu tazo ta dauki Suleim da Suhaila Suna gidanta suna jin dadinsu dan Alhaji balarabe kashe musu kudi yakeyi yana shagwaba su.
Mijin Aisha ma Nasihar iyaye data Omar sun jawo ya nutsu ya canja hali,sai kiba da kyau da su Sadiya suka karayi. Kullum sai sun Sawa Omar albarka, har Baffa da Umma Rahina suka fadawa abinda Omar yayi musu,haka Mama har Godiya suka Mata.
Iklas ta shiga damuwa akan Khairat tana shigewa mijinta tayi hakuri tayi kawaici ta gaji haka.musamman da taga Omar na biye mata,shima Omar Haushin Iklas yakeji yaga kamar ta daina sonsa bata kishinsa,tana ganin yanda Khairat ke manne masa amma bata nuna komai,shi kuma kara yake mata kawai,baya ga haka da tuni ya kwadawa Khairat maruka yanda take zama tana goga masa kafardarta a tasa, tana taba jikinsa ko ta rike hannunsa in tana masa magana.ga shi kullum shigar banza takeyi a gidan ko kunyar su Baffa bata ji.
Kamar kullum yau Omar da Iklas suna zaune a palon Mama sun baje suna cin abinci Khairat ta fito taci kwalliya ta matse cikin Riga yar fingila da wando sai kamshi takeyi, wajen Omar ta nufa tare da zama kusa dashi tana gugan jikinsa, ran Gomnati yayi mummunan baci
Kishi ya tashi dama ta gaji da halin Khairat,Iklas wani azababben kishine ke azalzalarta kwakwalwarta ta dau zafi, zuciyarta tafasa kawai takeyi,Omar ya ga halin da Iklas ta shiga amma yace me yasa tun farko bata dakatar da abinba.
Iklas tana so taga Omar ya matsa amma taga cin abincinsa ma kawai yakeyi. Iklas a ranta tace kut inama ina da lafiya da billahillazi sai nayiwa matar nan abinda ko a mafarki baza tayi sha'awar zuwa Nigeria ba,amma zanyi maganinta, maganin shege sai dan banza.
Gani tayi Khairat ta zuba lemo a glass cup za ta kai bakin Omar,cikin Zafin Nama Iklas tasa hannu ta fisge cup din tare da watsawa Khairat lemon a fuska, ta mike tsaye tare da nunata da yatsa a tsawace tace get out before I scatter your skull into peaces, dama ga su da tsoro Da Sauri Khairat ta fice,Omar zaiyi magana Iklas ta daga masa hannu ya Isheka ya Ishe.....bata karasa ba mararta ta mirde,ta kulle tare da zamgewa da cakudewa. Rawa jikinta ya fara Kar kar kar....... Gumi ne kawai yake keto mata,wani azababben ciwo taji Wanda ko a labari,,films,da mafarki bata taba sani ba,mararta ta dafe ta daddage iya karfinta cikin siriyar Muryarta ta tsandara Ihun daya fito dasu Mama da Ummi daga kitchen a guje.
Sulalewa kasa tayi tana kuka wayyo Allah na Ku taimaka min,a kaini asibiti na mutu acan,tuni Omar yana kanta shima hawaye yazo masa yana tunanin idan ya rasa Iklas tasa ta kare.
Iklas ta rike Omar kam yana kiyi addua pls yanzu za a tafi asibiti,tana kuka ta fara La'ila ha illalla la'ilaha ilallah taana rerawa ita kadai yanda zakuru sukeyi kawai kirjinne da bata duka,tuni su Ummi sunyi waje kiran driver,Mama na hada kayan haihuwa,
Suna cikin mota tana cinyar Omar kwance su Mama a gefe,Ummi tace dan Allah Iklas ki rufemana baki haka akanki aka fara haihuwa,Omar shafawa Gomnati marar yakeyi yana lallashi tare da tofa mata addua.
Ciwon ne ya lafa mata suna mota driver na tsala gudu, mikewa zaune Iklas tayi tana goge gumi tana wash naji salama,suna shiga asibitin ciwon ya dawo yafi na da,cije baki Iklas tayi tana Bala'i.....Bala'i....gashi......nan.....Omar sai hawaye yakeyi yanda Iklas ta haukace gaba daya gashin kanta kamar daga bakin kura ya fito,yanzu bata ma San me take cewa ba,kuka takeyi tana nishi tana Ku miko min danwake na kwandala,abani ko dan malelene,haka aka turata a gadon asibiti har dakin da aka kwantar da ita,patients da malaman asibitin kowa dariya sukeyi da tausayin Iklas yanda take fadan abu barkatai.
Ummi ce ta kalleta tace yar bantan Uba taji wahala, Mama tace sannu yanzu Likita zaizo, Iklas ta Kalli Mama ta fara tooooooo.......yayi sauri yazo yamin Allura ta kwandala. Shi kansa Omar ta bashi dariya dannewa yayi.
Ummi ce tsuguna a jikin gadon ai kuwa Iklas Neman abin rikewa takeyi ta tugewa Ummi dan kwali ta jefar,da Sauri Ummi ta matsa ta dauki abinta tana daurawa tace harda ciremin dankwali?Iklas tana cijewa tace idan....dan kwalin na kwandala ne to a bani......lallai.... Nace a bani.
Nurses da likitoci sunzo sunce Kaine mijinta? Da sauri Iklas tace yana ina bakin mugu azzalimi,ta fashe da wani irin kuka me karya zuciya.Omar hankalinsa ya kara tashi gashi kusa da Iklas hannunta cikin nasa amma take nemansa bata ganeba.
AsmaBaffa
Ku kwashe min da tafi readers.
Tnx all nayi delay ban cika alkawari ba, amin afwa nima ko ta kwandala ce.ⓂⓂⓂ
MA'AIKACIYAR
GOMNATI
ⓂⓂⓂ
190-195
By
AsmaBaffa
Ciwon daya taso ne gadan gadan yasa Iklas ta daina kuka sai muzurai da cijewa kawai kuka ya gagara,likitoci sun bazu a kan Iklas yayinda Gomnati ke sambatu karfinta ya kusa karewa a hankali tace doctor kayi min Allurar guba tunda dai haihuwar nan baza ta zo ba,Omar ya rude addua kawai yake tofa mata,
Iklas tace Ku fadawa mijina ya yafemin bazan warke ba,irin wannan ciwon nasan sai dai na tafiya lahira,Omar ne ya rungumeta yana hawaye am sorry wifey insha'allah zaki tashi,kan Omar ta shafa tace kamar Omar dina,nine matata Honey dinki ne,kayiwa Mama biyayya sosai,idan baka bita ba dole kaci wutar jahannama,domin bakusan Haihuwa ba.
Sakinsa tayi,likita yace ya basu waje ga wani sabon ciwon daya taso mata,Ummi tace kiyi fa a Hankali Iklas Maza suna jinki, da karfi tace Maza? Maza basu San Haihuwa ba....wayyo Maza basu San Haihuwa ba.
Likita ne yace su Ummi su fita duka zasuyi Aiki,Omar yace bazai yuwu namiji ya duba masa mata ba,dole suka kawo mace da mata nurses,harda shahararriyar nurse din nan Subby,Maman waleeda ma anyi mata Transfer Hospital din ita ce ta karbi haihuwa da gaggawa,Subby ta Daura drip,Hajiya Jamila,Jamila Sule duk a asibitin suke aiki sai kaiwa da kawowa sukeyi wurin Iklas,
Tun safe ake abu daya Har yamma Iklas bata haihu ba,bakar azaba take sha kawai,Subby tayi gumi sosai,Iklas kuwa da taji shuru sai tace kuji na fada muku bazan Haihu ba kawai kuyi min Allurar guba,Omar ya rasa Inda zai sa kansa,Sallah sai da yayi rafkannuwa da yawa,
Babbar likita King ita ta zo ta kawo wasu dabaru cikin Ikon Allah 5pm kan yaro ya danno kai,Iklass ido yayi jajir yayo waje,ansata nishi ana fush,babu bakin magana ya mutu murus,nishi ake ta sata suna taimakawa,Rabin Rabin jikin Baby yayo waje aka taimaka ya fito du da komai a hannun Subby,
Zukeken Namiji ta santalo me kama da Ubansa,lafiyayye katon gaske, yaro na fitowa Iklas ta sume, sai da tayi 5mnt ta farfado,nan akayi mata Allurai kala kala,nan danan nurses suka gyara yaro tsab,sannan aka fara yiwa Iklas aikin fito da jinin cikinta tas,tare da gyarata ta Huta sosai sannan Ummi ta shigo ta taimaka mata a bayi tayi wanka sosai ta gasa mata ko ina nan ma Gomnati harda kukan ruwan zafi,kafin su fito room din sai kamshine ke tashi,abinka da private hospital me tsadar gaske kai ka rantse Hotel ne,baza kace a asibiti kake ba,Iklas ita kadai ce a room din ba a hada mutane room daya,kowa da nasa.
An canja bedsheet ma sabo,tana fitowa suka fada toilet ma'aikata suka gyara shima,kamshin dadi ne kawai ke ratsa ko ina,
Iklas ta hana a fadawa Omar ta haihu wai sai ta shirya,a cikin jakar kayan haihuwa harda body lotion da su turare,da man gashi da handdrier,wata nurse da tazo domin sauran sun tafi,tace lallai haihuwar fari ce wannan shiri haka.
Aikuwa Iklas ta busar da gashinta da hand drier ta tajeshi tsab ta shafeshi da man gashi me kamshi,da turaren gashi ma aka shafa,tea ta sha me kaurin gaske,sannan taci kaji da sakwara miyar egusi,Omar kuwa tuni Subby ta fada masa ta Haihu lfy amma ance ya jira za a kirashi,ai kudi ya zaro wanda
Showing 90001 words to 93000 words out of 104017 words
Murmushi yayi Iklas rigima kenan,zaki ga sanda zan danneki ne ai,dan kawai yanzu kinyi nauyi ne dole a biki sannu amma da sai kinyi bayani,nasan zaka iya ai oya zo muci abinci ka daina rigimar kai kasanni bazan bar mijina cikin Matsala ba dole akwai mafita ka daina bata bakinka,nayi yaji ma na nemoka baka zo biko ba bare yanzu da dole nima su Mama sukayi min,Ummi kakata ce ba wata kunyarta nakeji ba,
Sai yanzu ya dan samu nutsuwa da farin ciki,matsowa yayi tare da zama gabanta murmushi dauke a fuskarsa zama yayi sosai a gaban yana shafa ckinta,daga bisani ya jawo naman yana yankowa ya sa abakinsa sanna ya hade bakinta da nata yasa mata naman ta cinye tana kada kai uhmmmmm kaji dadin bala'i kuwa,
Haka ya dinga ciyar da ita har ta koshi,yau Omar a part dinsa ya kwana gidan Mama ba tare da kowa ya sani ba,Iklas kuwa tayi tunanin dama Omar dakinsa zai kwana,dan haka gaba daya tausayinsa takeji hade da wani sabon sonsa,da sassafe ta shirya kanta cikin doguwar rigar a tamfa,sama ya matse kasa ya bude sosai ya boye cikin ta,fitowa tayi sadaf sadaf zata shiga dakin Omar,suhaila ta gani da suleim zazu tafi schl,Anty ina kwana suka gasheta sukayi gaba da gudu,ita kuma ta fada room din Omar a kan bed ta hangoshi yana ta baccinsa cike da nutsuwa,komawa tayi ta sa key a kofar saboda tsaro.
Tana dawowa ta haura saman bed din tare da rungumeshi kam tana shakar kamshinsa tare da manna masa kiss a goshi,a hankali ya bude idonsa masu matukar kyau,ganin Gomnati a jikinsa ba karamin farin ciki yayi ba.
Ba tare da bata lokaci ba shima ya Kara manneta a kirjinsa wifey I miss u da kyar nayi bacci jiya,baki zo ba har jiranki nayi,miss u more honey nayi niyyar zuwa bacci ya sace ni,cikinta ya Shiga shafawa ya gudan jini na lafiya yake?haushi Iklas taji yace gudan jininsa wato ya kwace mata mijinta,
Shinema gudan jinin naka,ni wlh shi yasa banso haihuwar nan ba,yanzu sai ka dinga daukansa ni kana shareni,dariya Omar yayi me kishi da danta haka akeyin Maman babyn?ta tsani danta? Kece fa zuciyata gaba daya,cike da shagwaba tace to ai jini yafi zuciya muhimmanci shine zaka ce masa gudan jininka ni a bani zuciya,saboda ka samu da,fari tayi da ido Wanda ya susuta Omar lokaci guda tare da cewa dadin abin ai kafin ayi dan ni aka samu,kuma ai da nane.
Dariya Omar yayi kinsan me kike cewa kuwa wifey? Wannan shine ba kano ba birni,ba cinya ba kafar baya, shi yasa tunda ke danki ne kinga shi gudan jinina,ke kuma zuciyata kinga ai kun kwaceni du ke da baby,ni dai Allah ban yarda ba cewar Iklas ,ok to a bashi zuciyar ke gudan jini ko?kafada ta make abinda nafi so zuciyarka shine zaka ce a bashi ita,dariya Omar keyi yace to na bashi liver ta,da Sauri tace tab bai isa ba bazan yarda ba,Kasan kuwa muhimmancin liver da zakace a bashi ita yama fini kenan sosai fa ina laifin ka bashi yar madaciyar jikin hantar taka tunda shi yaro ne,ko ka bashi timbi ko hanji,
Fashewa da dariyar shiriritar Iklas yayi tare da kara kankameta sosai abin dariyar Gomnati da yawa yake, tafin hannunta ya mannawa kiss yana bin hannun da kiss ya gangaro wuyanta nan ya fara lasar wuyanta cike da salon kwarewa tattare da nutsuwa a hankali ya dinga sarrafata tunaninta ya gushe nan fa suka dinga baje harka,bayan sun nutsu wanka sukayi cike da nishadi,Omar na ta zuba mata albarka, Iklas dinsa dabance,tana shagwaba shi sai abinda yake so,gashi tana fahimtar matsalarsa ko bata so sai ta faranta masa,yanda yake bata wahala bata taba nuna gazawarta,
Burinta taga Omar kullum hankalinsa kwance,gaban kowa tana nuna rashin kunyarta dan ta faranta masa.
Har kaya ita ta sawa Omar tare da shiryashi suka fito fes fes dasu,Ummi bataga Iklas ba tunda taga haka to lallai Omar yana gidan,Iklas ta birge Ummi da take kula da mijinta,
Suna hirarsu kasa kasa murmushi dauke a fuskar Iklas suka shiga wajen Ummi suka gaisheta Ummi tana in kaga Zara kaga wata,suna ta murmushi suka je wajen Mama, tana ganinsu haka taji dadi a ranta amma sai ta tamke fuska ta fara yiwa Omar fada Dama nasan baka jin magana Babana saida ka kwana a gidan nan sabo da mun dauko matarka, ka kiyayeni fa,jikinta ya fada haba Mama nifa gwara ki hakura ki kyaleni dan Allah,Iklas ce tayi magana cike da marairaicewa Mama kiyi hakuri ki kyaleshi.ai na kyaleshi Iklas ya zanyi da shi ya fiye rikici,that's my Mum cewar Omar.
Kuje ga breakfast can a dining,Mama ta kara da cewa Iklas yan uwanki na kasar Libya jiya sunyi mana waya ni da Ummi,nayi magana dasu cikin harshen turanci duk da ba wani iya turancin nan nayi ba sosai dama Abdallah ke koya min,sunce zasuzo ganinku nan da 3days sai Ku kirasu kuji komai,number tana wayar Ummi,sosai Iklas take Murna ko ba komai yan uwansu zasu zo dangin mijinta su gansu asan suma suna da gata.
Omar ne ya kira yan uwan Iklas a wayarsa suka tabbatar masa nan da 2days gasu nan ganin yaransu,ai kuwa Saturday na zuwa aka tura driver ya daukosu maza su biyu mata biyu,dayar macen Babba ce sosai ta manyanta,dayar kuma budurwa ce yar gidan best Frnd din Baban Iklas me suna KHAIRAT.
zankadediya itama,part guda Baffa yace a ware musu shima yana nan zuwa next day zaiga yan uwan matar dansa, Iklas ta rasa inda zata sa kanta sabo da murna,su Sadiya ma sunzo sun gaishesu,bangaren Hajiya Rahina ma an rakasu sun gaisa,ba tare da ta nuna musu wani dan hali ba,su Sultan,Raj,yan uwa da abokan arziki duk sun zo sun gaishesu,haka frnds din Iklas suma,Maman saleem,saleem da matarsa duk sun je.
Su Kansu mutan libiya sunji dadi sosai,
Khairat tunda Allah yasa tazo gidan tayi tozali da Omar mijin Gomnati taji duk duniya ba Wanda take so da muradi sai shi,dan haka ta like masa ta manne masa,shi kuma ganin yan uwar abin kaunarsa ce Gomnati Iklas sai yake kulata yana karramata,itama Iklas data ga haka bata damu ba tayi tunanin kawai saboda mijinta ne shi yasa take matukar ji da ya Omar,Wanda ita Khairat balarabiyar kasar libiya Sam ba haka bane a ranta tsabar son Omar ne yayi mata yawa,Wanda tana jin baza ta iya rayuwa ba sai da shi,dole sai dai itama ya aureta tunda musulunci ya bada damar auren mata har hudu,
Shi yasa take Neman hanyar da Omar zai fada tarkon sonta, ita tasan Iklas din Omar ta fita kyau amma dole ne ta sameshi ya aureta.
Shi yasa khairat Sam bata zama a bangaren da Baffa ya basu kullum tana wajen Iklas saboda taga Omar kullum yana manne da matarsa,shi yasa take nacewa kusa da Iklas,Khairat taga Iklas yarinya ce shi yasa take so tayi mata wayo ta kwace mijin,dan burinta ta dauke Omar su koma kasarsu da zama,Khairat shekarunta 28 dan haka ta girmewa Iklas wacce kwanan nan ta cika 17yrs kwata kwata.
Shi fa Omar Khairat ta fara damunsa tana shiga rayuwarsa shi da Iklas, ba dama su kebe waje daya sai tazo ta takura musu,dan dai kawai dangin Gomnati ne da tuni yaci uwarta an wuce wajen,
Amma dannewa kawai yakeyi yana biye mata ganin Iklas bata Nuna damuwarta ba,
Idan sauran bakin sunce time yayi ya kamata su koma kasarsu fafur Khairat ke hanasu wai a bari suga yar uwarsu ta sauka lafiya wato Iklas,Ummi da Mama sun gano take taken Khairat.
Omar yaje gidan Sadiya da Aisha ba tare da ya Sanar da kowa ba,ya musu Sulhu sosai da nasiha sosai sun samu yanci mazan nasu sun fara canjawa inda suma su Sadiya suka kara jajircewa wajen kula da miji,har makaranta ta koyon girki da dabarun zaman aure suka shiga. Har sauran kannansu sun biya musu sun shiga kuma suna ta kula da tarbiyar sauran kannensu tare da yiwa Ummansu Nasiha kuma ta dauka.
Har wajen Baffa suka je gaba dayansu har Umma Rahina suka bashi hakuri kan abubuwan da suka shuka.
Haka Maman Omar ma sun bata hakuri Aisha ta haifi yarta mace me suna Mufida, Sadiya kuwa anayin Hutu tazo ta dauki Suleim da Suhaila Suna gidanta suna jin dadinsu dan Alhaji balarabe kashe musu kudi yakeyi yana shagwaba su.
Mijin Aisha ma Nasihar iyaye data Omar sun jawo ya nutsu ya canja hali,sai kiba da kyau da su Sadiya suka karayi. Kullum sai sun Sawa Omar albarka, har Baffa da Umma Rahina suka fadawa abinda Omar yayi musu,haka Mama har Godiya suka Mata.
Iklas ta shiga damuwa akan Khairat tana shigewa mijinta tayi hakuri tayi kawaici ta gaji haka.musamman da taga Omar na biye mata,shima Omar Haushin Iklas yakeji yaga kamar ta daina sonsa bata kishinsa,tana ganin yanda Khairat ke manne masa amma bata nuna komai,shi kuma kara yake mata kawai,baya ga haka da tuni ya kwadawa Khairat maruka yanda take zama tana goga masa kafardarta a tasa, tana taba jikinsa ko ta rike hannunsa in tana masa magana.ga shi kullum shigar banza takeyi a gidan ko kunyar su Baffa bata ji.
Kamar kullum yau Omar da Iklas suna zaune a palon Mama sun baje suna cin abinci Khairat ta fito taci kwalliya ta matse cikin Riga yar fingila da wando sai kamshi takeyi, wajen Omar ta nufa tare da zama kusa dashi tana gugan jikinsa, ran Gomnati yayi mummunan baci
Kishi ya tashi dama ta gaji da halin Khairat,Iklas wani azababben kishine ke azalzalarta kwakwalwarta ta dau zafi, zuciyarta tafasa kawai takeyi,Omar ya ga halin da Iklas ta shiga amma yace me yasa tun farko bata dakatar da abinba.
Iklas tana so taga Omar ya matsa amma taga cin abincinsa ma kawai yakeyi. Iklas a ranta tace kut inama ina da lafiya da billahillazi sai nayiwa matar nan abinda ko a mafarki baza tayi sha'awar zuwa Nigeria ba,amma zanyi maganinta, maganin shege sai dan banza.
Gani tayi Khairat ta zuba lemo a glass cup za ta kai bakin Omar,cikin Zafin Nama Iklas tasa hannu ta fisge cup din tare da watsawa Khairat lemon a fuska, ta mike tsaye tare da nunata da yatsa a tsawace tace get out before I scatter your skull into peaces, dama ga su da tsoro Da Sauri Khairat ta fice,Omar zaiyi magana Iklas ta daga masa hannu ya Isheka ya Ishe.....bata karasa ba mararta ta mirde,ta kulle tare da zamgewa da cakudewa. Rawa jikinta ya fara Kar kar kar....... Gumi ne kawai yake keto mata,wani azababben ciwo taji Wanda ko a labari,,films,da mafarki bata taba sani ba,mararta ta dafe ta daddage iya karfinta cikin siriyar Muryarta ta tsandara Ihun daya fito dasu Mama da Ummi daga kitchen a guje.
Sulalewa kasa tayi tana kuka wayyo Allah na Ku taimaka min,a kaini asibiti na mutu acan,tuni Omar yana kanta shima hawaye yazo masa yana tunanin idan ya rasa Iklas tasa ta kare.
Iklas ta rike Omar kam yana kiyi addua pls yanzu za a tafi asibiti,tana kuka ta fara La'ila ha illalla la'ilaha ilallah taana rerawa ita kadai yanda zakuru sukeyi kawai kirjinne da bata duka,tuni su Ummi sunyi waje kiran driver,Mama na hada kayan haihuwa,
Suna cikin mota tana cinyar Omar kwance su Mama a gefe,Ummi tace dan Allah Iklas ki rufemana baki haka akanki aka fara haihuwa,Omar shafawa Gomnati marar yakeyi yana lallashi tare da tofa mata addua.
Ciwon ne ya lafa mata suna mota driver na tsala gudu, mikewa zaune Iklas tayi tana goge gumi tana wash naji salama,suna shiga asibitin ciwon ya dawo yafi na da,cije baki Iklas tayi tana Bala'i.....Bala'i....gashi......nan.....Omar sai hawaye yakeyi yanda Iklas ta haukace gaba daya gashin kanta kamar daga bakin kura ya fito,yanzu bata ma San me take cewa ba,kuka takeyi tana nishi tana Ku miko min danwake na kwandala,abani ko dan malelene,haka aka turata a gadon asibiti har dakin da aka kwantar da ita,patients da malaman asibitin kowa dariya sukeyi da tausayin Iklas yanda take fadan abu barkatai.
Ummi ce ta kalleta tace yar bantan Uba taji wahala, Mama tace sannu yanzu Likita zaizo, Iklas ta Kalli Mama ta fara tooooooo.......yayi sauri yazo yamin Allura ta kwandala. Shi kansa Omar ta bashi dariya dannewa yayi.
Ummi ce tsuguna a jikin gadon ai kuwa Iklas Neman abin rikewa takeyi ta tugewa Ummi dan kwali ta jefar,da Sauri Ummi ta matsa ta dauki abinta tana daurawa tace harda ciremin dankwali?Iklas tana cijewa tace idan....dan kwalin na kwandala ne to a bani......lallai.... Nace a bani.
Nurses da likitoci sunzo sunce Kaine mijinta? Da sauri Iklas tace yana ina bakin mugu azzalimi,ta fashe da wani irin kuka me karya zuciya.Omar hankalinsa ya kara tashi gashi kusa da Iklas hannunta cikin nasa amma take nemansa bata ganeba.
AsmaBaffa
Ku kwashe min da tafi readers.
Tnx all nayi delay ban cika alkawari ba, amin afwa nima ko ta kwandala ce.ⓂⓂⓂ
MA'AIKACIYAR
GOMNATI
ⓂⓂⓂ
190-195
By
AsmaBaffa
Ciwon daya taso ne gadan gadan yasa Iklas ta daina kuka sai muzurai da cijewa kawai kuka ya gagara,likitoci sun bazu a kan Iklas yayinda Gomnati ke sambatu karfinta ya kusa karewa a hankali tace doctor kayi min Allurar guba tunda dai haihuwar nan baza ta zo ba,Omar ya rude addua kawai yake tofa mata,
Iklas tace Ku fadawa mijina ya yafemin bazan warke ba,irin wannan ciwon nasan sai dai na tafiya lahira,Omar ne ya rungumeta yana hawaye am sorry wifey insha'allah zaki tashi,kan Omar ta shafa tace kamar Omar dina,nine matata Honey dinki ne,kayiwa Mama biyayya sosai,idan baka bita ba dole kaci wutar jahannama,domin bakusan Haihuwa ba.
Sakinsa tayi,likita yace ya basu waje ga wani sabon ciwon daya taso mata,Ummi tace kiyi fa a Hankali Iklas Maza suna jinki, da karfi tace Maza? Maza basu San Haihuwa ba....wayyo Maza basu San Haihuwa ba.
Likita ne yace su Ummi su fita duka zasuyi Aiki,Omar yace bazai yuwu namiji ya duba masa mata ba,dole suka kawo mace da mata nurses,harda shahararriyar nurse din nan Subby,Maman waleeda ma anyi mata Transfer Hospital din ita ce ta karbi haihuwa da gaggawa,Subby ta Daura drip,Hajiya Jamila,Jamila Sule duk a asibitin suke aiki sai kaiwa da kawowa sukeyi wurin Iklas,
Tun safe ake abu daya Har yamma Iklas bata haihu ba,bakar azaba take sha kawai,Subby tayi gumi sosai,Iklas kuwa da taji shuru sai tace kuji na fada muku bazan Haihu ba kawai kuyi min Allurar guba,Omar ya rasa Inda zai sa kansa,Sallah sai da yayi rafkannuwa da yawa,
Babbar likita King ita ta zo ta kawo wasu dabaru cikin Ikon Allah 5pm kan yaro ya danno kai,Iklass ido yayi jajir yayo waje,ansata nishi ana fush,babu bakin magana ya mutu murus,nishi ake ta sata suna taimakawa,Rabin Rabin jikin Baby yayo waje aka taimaka ya fito du da komai a hannun Subby,
Zukeken Namiji ta santalo me kama da Ubansa,lafiyayye katon gaske, yaro na fitowa Iklas ta sume, sai da tayi 5mnt ta farfado,nan akayi mata Allurai kala kala,nan danan nurses suka gyara yaro tsab,sannan aka fara yiwa Iklas aikin fito da jinin cikinta tas,tare da gyarata ta Huta sosai sannan Ummi ta shigo ta taimaka mata a bayi tayi wanka sosai ta gasa mata ko ina nan ma Gomnati harda kukan ruwan zafi,kafin su fito room din sai kamshine ke tashi,abinka da private hospital me tsadar gaske kai ka rantse Hotel ne,baza kace a asibiti kake ba,Iklas ita kadai ce a room din ba a hada mutane room daya,kowa da nasa.
An canja bedsheet ma sabo,tana fitowa suka fada toilet ma'aikata suka gyara shima,kamshin dadi ne kawai ke ratsa ko ina,
Iklas ta hana a fadawa Omar ta haihu wai sai ta shirya,a cikin jakar kayan haihuwa harda body lotion da su turare,da man gashi da handdrier,wata nurse da tazo domin sauran sun tafi,tace lallai haihuwar fari ce wannan shiri haka.
Aikuwa Iklas ta busar da gashinta da hand drier ta tajeshi tsab ta shafeshi da man gashi me kamshi,da turaren gashi ma aka shafa,tea ta sha me kaurin gaske,sannan taci kaji da sakwara miyar egusi,Omar kuwa tuni Subby ta fada masa ta Haihu lfy amma ance ya jira za a kirashi,ai kudi ya zaro wanda
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31 Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35