gidan nan,kuma sai na batar dake kamanninki ma sai su shafe a doron kasa,idan uwata ta haifeni da jini sai na tozartaki a idon duniya,mu zuba ni dake.

Iklas tace idan kin fasa bakya kaunar Uwarki da tsohon banza,idan kin fasa Allah tsinewa uwarki,naci uwarki a iskanci kawai tsoron Allah mukeyi saboda lahira,na Fiki daba jahilar banza,Iklas duk kurin da takeyi na ganin Omar na kusa ne wai ita shegiya.
Janta Omar yayi harda kwacewar ka barni da matsiyaciya wai baka bata labarin wace Gomnati ba,ke bafa da iya common hausawa nayi gogayya ba,ki taimakawa kanki ki wuce gidan Ubanki tun kafin na sako wandon ya Omar da rigarsa na fede miki yan hanji,yanzu na yo waje da kwakwalwarki,
Iklas harda matsawa jikin Sahar dan taga Omar na kusa tace honey kawo min aska na cirewa shegiya belin gaba.

Daria Omar keyi sosai ganin yanda Iklas ke kuri Wanda da taga Omar zai yi waje zata rikoshi tana wayancewa,yanzu ma taka kafarsa yayi zai fita carab ta rikoshi dole a gabanka za ayi ita din banza a hankali ba tare da Sahar ta kula ba ta radawa Omar karfa ka tafi Kasan zata iya zaneni.

Sai da Iklas ta gama kurinta sannan suka kyale Sahar na sake saken yanda zatayi maganin Iklas. Kayanta ta hada kaf ta bar gidan Omar, Sahar na zuwa gida ta shirya karya da gaskia,dukan da Iklas tayi mata cewa tayi Omar ne yayi mata shi.
Iyayenta sukace baza su yadda ba,nan take suka kira Baffa suka zazzaga masa masifa tare da sanar masa abinda Omar yayiwa Sahar. da kyar ya basu hakuri yace su jirashi next wk zai taso daga Russia.

Iklas murna kamar ta kashe kanta,daga ita sai Omar dinta,Saida tayi nafeela raka'a biyu tayi musu adduar zaman lfy da karesu daga mahassada etc.
Omar sai dadi yake ji yanda yaga Iklas na kishinsa da kaunarsa, shi kam yayi dace.
Wanka Iklas ta sakeyi kamar yar agwagwa tasa dangalgalar rigarta me dogon hannu da Kadan ta haura mazaunanta,ta baza gashin nan malam,
Yau ba takura main Palo ta rungumo Omar har can,tace zauna oga Honey yau sai ka koshi da rawa, shi dai Omar sai daria Iklas ke bashi,

Manyan speakers Iklas ta jona da phone dinta zafafan wakokin nja sababbi ta kunna kamar zata fasa gidan, su Kansu ma'aikatan gidan tunani sukeyi yau wanne abin farin ciki ne ya faru a gidan oga haka.

Baya Iklas ta juyawa Omar Wanda ke hakimce akan akan daya daga kinkima kinman kujerun dake girke a Palon,Iklas rantsatsiyar rawa take takawa Omar ta birgewa me sa nishadi idan kana kallo, rawar kabilun nan take masa iri iri cikin nutsuwa,

Hip pop dance ta koma yi yanda take karairaya jiki tuni ta kara sacewa Omar tunaninsa gaba daya, kashe kidan yayi ba tare da yace komai ba ya sunkuce abarsa sai bedroom.

AsmaBaffa

Masoyana duk inda kuke wannan shafin nakune. Ga Iklas dinku fa in action.

Readers ayi min afwa idan nayi mistake ko typing error bani da time ne.ⓂⓂⓂ
MA'AIKACIYAR
GOMNATI
ⓂⓂⓂ

165-170



By
AsmaBaffa



Gaskia kuna birgeni masu commenting masoya wannan novel jinjinata gareku da godiya ba adadi





Bedroom ya direta saman bed yana mata chakulkuli sai daria sukeyi,wani mayen kallon Omar ya mata Wanda Iklas da taga irin wannan kallon tasan me yake nufi,Omar yace wifey tallan nan ya lalataki da yawa ko kunyata ba kya ji,murmushinta me kyau ta saki ka godewa Allah ma Da Allah ya kare maka ni iya haka.
Ni da ka ganni ba komai ke bani kunya da yawa ba,kuma ma ai watarana ina jin kunyarka,kasan na saba da kai shi yasa bana boye ma komai,tunda kai nayiwa rashin kunyar ai duk daya,zamu ce ta tadda mujemu kai wacce kunyace da kai?

Ai ban kaika ba ko kafarka ban kamaba,to naji fada min ni wacce rashin kunyar nayi miki ?cewar Omar, kallonsa tayi tare da yin wani fari tana juya idanunta masu rikita Omar,see u kana danne yar mitsilar yarinya a bed kana sambatunka,rannan ma ina jinkafa kyaleka nayi dan kawai naji zafi ne amma wacce kyauta ce baka min ba,gwada masa ta farayi ohhh Baby,my life ahhh na baki garin Abuja ke da kano state ma impact Nigeria du,zan siya miki jirgi,motocina da gidajena,ni darling du nakine sai abinda kika ce.

Dariya Omar keyi sosai karyar da Iklas ta sambado masa yasan yayi sambatu amma bai irgo da cities ba,kiji Tsoron Allah wifey yaushe nace haka?oh to ai lokacin ka bar kasar nan ka Lula dadi world,amma wai
kana zancen wai a kiraka me kunya,
Wanne tabo ne ban sani ba a jikinka? Zaka dinga min pretending, ka fito min a Mutum sak ba wani kwane kwane,

To naji amma ban yarda ba in kin isa zo a karayi aji idan zanyi sambatu wannan lokacin,ai na daina sambatu,ni kuma nace dole sai kayi,musu ne ya kaure tsakaninsu shi yana a karayi bazai Sambatu ba yayiwa Iklas wayo bata gane ba tace duk da ba dadi nake ji ba azaba nake sha a kara yi yau sai an kure Wanda baida gaskia,kasan kuwa irin sambatun da kakemin har kuka kayi a last da kayi,to yau kace baza kayi ba,
Habawa malam dole sai kayi Sambatu,yarinya ai waccen dan ban shirya bane amma wannan ba wani sambatu,a haka ya rinjayi Iklas ta yarda ita dole sai ta kure karya,da suka fara ma jajurcewa tayi iya fasaharta ta nunawa Omar wai duk dan yayi sambatu ta kureshi,sambatu Omar Ke mata sosai tana ta Kara jajircewa,ai kuwa Omar bai San kadan ba sai wajen asuba ya kyaleta,baya gajia da Iklas Sam,iklas kam yau sai murna takeyi tana na kureka Allah sai sambatu kakeyi wooooo,ai dama na fada ma nice fa Gomnati Ikon Allah

Omar murmushi yayi to naji kin kureni ai zan rama ne kema zakiyi fin nawa watarana,suna samun nutsuwa rungume take jikin Omar yana wasa da dukiyar fulaninta,tace honey Kasan me?sai kin fada cewar Omar,
Hmm Allah kaga na yau da kayi min baka ji ba kamar dadi dadi kuma zafi zafi,sai naji kamar kwakwalwata zata buga,daria ta bawa Omar sosai,Iklas ba ayin 1mnt bata bashi daria ba shi yasa yake matukar kaunarta,tana birgeshi ko yaushe nishadi take sashi,shi yasa ko yaje office baya iya aikin sai tunanin matarsa.shi kadai zakaga yana murmushi.

To next idan munyi dadin zaki ji gaba daya na fada miki,tab ai kuwa za ajini a makwafta kai na yau ma fa jurewa kawai nayi,murmushi Omar yayi yana bubbuga mazaunanta kamar jaririya yace bacci kinji maza muyi bacci.
Haka suka kasance cikin jin dadi da kwanciyar hankali har Iklas ta sha fe 2wks gidan Omar.

Baffa ne ya sauka a gida Nigeria kwanan sa daya yace Omar yazo yana son ganinsa,wankan sukari suka dauka shida Iklas tasa atamfa blue riga da skert, yasa shadda light blue,sai kamshi sukeyi kamar ka sace su ka gudu.wata dalleliyar mota ya zaba cikin jerin sababbin motocin da ya sake dal dal dasu bayan mota suka shiga driver na tukasu,hannunsu sakale dana juna Iklas na kwance a kafadar Omar tana lumshe ido Sanyin A.c na ratsasu,
Minti kadan Omar zai juyo ya hade bakinsu wuri daya yana tsotsa,haka har sukaje gida,
Tun daga nesa Iklas ke kwala sallama sai murna takeyi,su Suhaila suka gani Abdallah zai kaisu Islamiyya,da gudu suka rungume Iklas da Omar,Abdallah kuwa a zuciyarsa Yace bari na tsokani ya Omar Iklas ya mikawa hannu wai su gaisa,Omar bige hannun Abdallah yayi yana zazzaga masa bala'i,Mama ce ta fito kai kuma lfy?daga zuwa zaka cika mana gida da fada,Abdallah yana daria kyaleshi Mama wai daga na tsokaneshi,shinefa yake wannan fadan,Dalla malam get lost naga alama baka San me kakeyi ba cewar Omar,
Da sauri cike da ladabi da kunya Iklas ta duka har kasa ta gaishe da Mama, Mama sai dadi takeji tayi suraka yar mutunci me kula da danta,just 2wks amma Omar har yayi kiba ya kara wani fresh da kyau,

Da gudu Suleim ta kira Ummi ta fito tana a'a amarsu ce da angon nawa,Ummi ai munyi fushi cewar Omar,haba dai kai ka isa har kasa Omar ya gaisar da Ummi tana tsokanarsa ango wannan kiba haka kayi wani ja,me Iklas ke baka ne,tsugunawa yayi kusa da Iklas ya rada mata ki fadawa Ummi irin zumar danake sha,hararar wasa Iklas ta yi masa itama a hankali tace Zafa kasa muji kunya,so what?cewar Omar,
Ummi ce tace halina da yaran nan kenan sai ana abin arziki su fara na tsiya ba kunya ba komai,Mama tace zasu koma inda suka fito yanzu ai idan suka sake.

Iklas harda sunkuyar da kai kasa wai kunyar Mama, Omar zama yayi kusa da Iklas ya dan bigi kafarta da tasa kafar jibarki kamar gaske wai kunya sai gulmar tsiya murmushi tayi ta kalleshi da gefen ido tayi masa signa irin a bari sai mun kebe mu biyu.
Wurin Ummi Iklas ta matsa yar tsohuwa ya kk,shine kika manta dani ko? Ke rufe min baki ja'ira kin samu miji kin manta da kowa sai mu zamu biki,hira sukeyi sai ga Baffa ya fito daga sashensa, shima yaji matukar dadi ganin Omar dinsa ya samu nutsuwa,zama yayi a daya Daga cikin kujerun palon, cike da ladabi suka gaidashi yana ta samusu Albarka.

Babana sabo dakai na dawo kasar nan kayi laifi,cewar Baffa yanzu idan banda abinka Babana da hankalinka kayiwa yar mutane duka haka?wannan wacce mugunta ce,ai gwara da saketa ka kyaleta baka daketa ba,ba girmanka bane, iyayanta sun fada min komai nan Baffa ya basu labarin yanda sukayi da iyayen Sahar.
Ummi da Mama tabe baki sukayi sunji dadin sakin da Omar yayiwa Sahar gwara haka.

Omar a hankali yace Baffa kasan duka ba halina bane, ba ni na daketa ba,abubuwan da takemin ne sunyi yawa shi yasa na saketa,Ku kanku kuna da labarin abinda takeyi,
To Omar wa zai daketa idan ba kai ba?ni dan ka saketa bai dameni ba kayi dai dai,babu me iya zama da Sahar tana wannan lalatar.
Iklas cike da ladabi tace Baffa nicefa na zaneta, salati su Ummi suka saki suna mamaki,Iklas tace Allah Baffa ni bazan iya kishi da wata ba musamman Sahar,Kasan inda ta kamani tayi min duka ta farfasa min jikina ta kalli Omar ko ya Omar?kai ya daga yace ae Baffa Iklas ce ta rama dukanta,
Murmushi Baffa yayi to taya kika iya dukan Sahar haka,daria Iklas tayi tace Allah dan Baffa bakusan muguntata bane,a ruwa na sa mata kwaya tasha jikinta ya koma weak ko yatsa bata iya motsawa na cika mata aiki da wayar wuta ta karfe,nan Iklas ta bada labari kowa dariya yakeyi yanda Iklas har gwadawa tayi yanda tayiwa Sahar.amma bata ce ta yanka mata mazaunai ba.
Ci gaba tayi Dama kuma ya Omar yace zai koreta, Baffa ni kuwa na kara zugashi ya saketa, kowanne na dakin mamakin Iklas sukeyi har Omar dan bai San ta sawa Sahar kwaya ba,dama yayi mamakin ya akayi Iklas ta iya yiwa Sahar duka haka,
Ummi ce ta zubawa Iklas rankwashi rufe mana baki shasha sha marar kunya,wato kai Umaru ina ganinka me hankali shine ka biye wata Iklas ka saki Uwar gidanka,murmushi Baffa yayi a'a Ummi ki kyale min 'yata ni tayi min dai dai,gashi mijinta ya samu kwanciyar hankali.

A shagwabe Iklas ta ce Baffa ita Ummi fa ta daina so na amma fa baka ga abinda wannan Sahar din ke wa ya Omar ba,Mama ce tayi dariyar jin dadi Omar fa yayi dacen me sonsa tace kai kulemin 'yata tayi dai dai,ni bana fatan hada zuria dasu Sahar Allah raka taki Gona.
Dadi Iklas taji tana farin ciki tace Allah barmana Mamanmu.
Baffa yace yana daria wato mu a kashemu ko?kanta kasa tace haba dai Baffa ai bamu isa muce haka ba kai gayya ne ai.kai na daban ne.

Ummi ce ta shige room kyaji dashi ja'irar yarinya,hira sukayi sosai da Baffa sannan ya mike yana na fita ni idan na dawo da wuri shikenan idan kuma ban dawo ba Ku gaida gida,Iklas tace zamu iya jiranka ma Baffa ko kwana zamuyi,da sauri Omar yace kwana fa kikace bada ni ba,to ni sai na kwana cewar Iklas, haba yarinya kafata kafarki da gidanmu zamu kwana gidan wasu,Mama ce ta make Omar rufemin baki marar kunya,ni ban San yaushe ka dawo haka ba wlh,nan gidan ne gidan wasu sabo da kai kayi aure ga me gida ko,ka manta yanda ka dawo ka tare mana anan.
Allah kyauta cewar Baffa Babana ka fitsare kafarka ya fice suna masa a dawo lfy.

Saleem Arziki ya bunkasa yayi wata uwar kiba da kyau,sai fantamawa yakeji ya hadu da wata zukekiya chocolate ce me suna JANNAT har an tsai da ranar bikinsu.Ummi sune kan gaba,
Sahar ta warke sosai inda taci gaba da duniyancinta,kamar kullum wani sabon Alhaji ta samu me kudin gaske Hon.Saminu a wani katafaren hotel dake abuja ta je tayashi kwana,suna room dinsu suna aikata masha'a Hon ya faki idon Sahar ya zuba mata wani grain magani a gabanta sannan yaci gaba da shagalinsa,
Bayan ya nutsu wanka yayi yace mata zaije ya dawo,Ashe guduwa yayi,abinda Sahar bata sani ba Hon Saminu hamshakin matsafine,ta hanyar saduwa da mata yake kudin tsafi,
Bai Dade da tafiya ba ta mike itama tayi wanka ta shirya fes ta kwashi kudin daya bata ta sauka ta hau motarta harda bar masa short note kan bed,na wuce wurin aiki ka kirani a waya.
Tun da Sahar ta fara tuki wani kaikayi ya fara damunta a gabanta tun tana Susa a hankali ta koma yi da karfi,da kyar ta kai kanta gida,da gudu ta fada palonsu tana ihu da Susa.

Dakin Ummi Iklas ta shiga suna ta hirarsu Ummi na kara Jan hankalinta kan ladabi da biyayya,da kula da miji Iklas tace tab Ummi kina bata bakinki wlh,ai duk na wuce nan wajen a karatuna,ina sonfa mijina taya bazan kula da abina ba na bashi jin dadi,nifa ko yanzu ji nakeyi nafi karfin nayi Aikin Gomnati indai Allah ya horewa mijinka kuma shi mijin yasan me yakeyi yana sauke hakkokinsa yana ma komai na rayuwa dai dai iya karfinsa me zanyi da wani aikin Gomnati
Kinga Ummi komai tsadar abu yaya Omar yi min yakeyi jin dadin duniya na sameshi shi yasa na sa masa honey zuma zaki Ummi, salati da sallallami Ummi keyi,Iklas ko ajikinta tanawa Ummi daria tace Ummi ni dama sabo daku nake son aikin Gomnati na taimaka mu samu rufin Asiri sai gashi Allah ya rufa mana asiri,komai mun samu,ga karatun Suhaila jibi irin schl din da suhaila ke zuwa me tsada ji sutura ai mu sai godiyar Allah,Ummi tace aikin ma na mata yana da muhimmanci kwarai ta wani bangaren sai dai kawai na wasu bashi da amfani yanda wasu matan ke kauce hanya sabo da Neman kudi.

Iklas tace kuma Ummi abin haushi wasu idan miji yace su zaba ko aiki ko aure sai suce sun zabi aiki,idan suka kashe auren su fada hanyar banza,wasu mazan kuma suna cikin talauci mace tayi karatunta tana aiki suna rufawa juna asiri sai kiga ya sa mata ido a kudin,ba zaman lfy sai in zata bashi kudi,bayan baya iya sauke mata hakkokinta da Allah yace, matsaloli dai gasu nan Sai Allah kyauta.

Omar ne ya bar wajen Mama ya dawo wajen Iklas dake dakin Ummi, kwanciya Omar yayi kan cinyar Iklas rashe rashe Iklas harda sukuyawa tana shafa sumarsa honey ya akayi ne,me kake so,Yunwa cewar Omar,da wuri haka bari to na tashi kaji dan babyna iklas ta furta,Ummi sakin baki tayi ta ciro dankwalinta ta makawa Iklas ta kara makawa Omar dake kwance jikin Iklas sai daria sukewa Ummi.

Marasa kunyar karshen zamani Ku bar min dakina,Iklas tace ba inda zamu bari ma ki gani,mikewa Iklas tayi bari na kawo mana abinci,sai kuyi ai cewar Ummi,abinci Iklas ta kawo musu ita da Omar,sai lallabashi takeyi tana bashi a baki,shi kuwa sai shagwaba yake mata,Ummi na kallonsu tana mamakin rashin kunyar su Omar.

Mamace ta shigo taga abinda su Iklas keyi Ku kuma meye haka,kema Ummi ki korasu waje mana kika kyalesu,Ummi tace kyalesu wannan yar banzarce Mara kunya fitsararriya tace ba Inda zasu.nazo kiransu ne cin abinci shi ma kamar gidansu har sun ebo suna cin abinsu Mama ta furta,Ummi nuna Iklas tayi da dankwalin hannunta kinga wannan tantiriyarce ta je ta zubo masa jibi abinda Umaru keyi kamar shine macen.
Ficewa Mama tayi dan ita kunya suke bata.

Sunayin Sallar azahar Iklas ta koma dakin Mama time din Omar bai dawo daga masallaciba,Mama na ganinta tace wlh fitar min daga daki yanzu zaku zo Ku
Showing 81001 words to 84000 words out of 104017 words