mutanen dake a wajen, mu samman wayan da aka kawo yau, ba wanda ya iya cin abincin dukkansu kowa ya kasa ci da suka farfaɗo kenan, sai dai wayan da suka daɗe a wajen, suma ɗaiɗaiku ne suka iya cin abincin irin su maman Zahrau. Ya Allah ka kawo mana ɗauki, yanzu a naku tunanin ire-iren maman Zahrau da suka sanya zuciyarta ta bushe babu imani babu tausayi me kuke tunani zata iya aikatawa idan aka bata makami? Allah ma ya tsare da yake ba azzaluman bawa bane sai dai bawa zalunci kansa, sai zuciyar tata ta saura da son Allah da Manzonsa, bayan su ba wani abin dake a cikin zuciyar maman Zahra, ya ilahi ya lillillahi😭
Kasan cewar ogan su mai kiran waya baya nan hakan yasa suka wuni a wajen ba wadda aka kira iyayensa, domin duk cikin bandits ɗin mutun biyar kawai ke da damar kiran waya, saura kuma aikinsu kamo jama'a ne kawai, da kuma kula da su, bayan haka ba wani abin.
Jugum-jugum suka zauna ba sallar azahar bare la'asar har karfe shida na yamma sannan suka sanya su a gaba zuwa cikin ɗakunansu, dayawa daga cikin bandits ɗin basa nan, da alama wani abin suka tafi aikatawa acikin gari, domin kusan rabi da kwatansu basu nan a wajen, yan kalilan suka rage, wadda ba su fi yawan mutanen dake a wajen ba.
Haka aka mai da su cikin ɗaki suka cigaba da zama jugum-jugum ita kuma Rufee da alama fa kamar babu rai ajikinta, domin ƙo motsi bata yi, kuma haka suke janta a kasa kamar shanuwa, a wannan dawo da su da suka yi, sun haɗa Aafia da kuma Hanan kanwar Sadiq waje guda, domin dama haka suke yi, idan sun tashi mai da ku, mafiyawancin lukuta suna canza maku ɗaki domin kada kudaɗe a waje guda har ku shirya masu wani abin, shayasa basu barin jama'a su sarara, tsabar rashin yarda da kai.
(To mun ji ɓangaren Aafia bari mu leƙa ɓangaren su Jelly dan jin yadda zata kaya mana.)
Sai murna take yi za su fita yawo da yaya Nawid, abin ba'a magana har wani kin magana take yi ma mutane, sai kauɗi take yi da rawan kai, ita adole za su fita yawo.
Bayan sun yi sallar isha ne suka zauna cin abinci, da sallama Nawid ya shigo palon, zaune ya isko su saman table Ummi na kokarin zuba masu abinci su ci, yau Abbo ba a part nasu yake ba, yana part ɗin maman Afnan hakan yasa Ummi gaba ɗaya bata son fitar da Nawid zai yi da baby, dan kada ya barta cikin kaɗaici.
"Baby ki tashi mu tafi mana, ba sai kinci abinci ba, za mu ci a can, Prof ya sa an shirya mana abinci". Ba tare da ta kalli in da yake ba, ta ce "Yaya Nawid kaza fa Ummi ta soya mani, ni gaskiya babu in da zanje sai na ci wannan kazar". Bin Ummi da ido ya yi, sai yanzu ya gane me matsalar da gangan Ummi ta kawo mata kaza dan bata son su fita saboda Abbo yana part ɗin su Afnan, sanin haka yasa ya samu waje saman chair ɗin tabla ɗin ya zauna yana faɗin shima a zuba mashi abincin kawai ya ci.
Cikin sauri Ummi ta ce "Fitar fa ya zaku yi?" Rai a ɗan ɓace ya ce "Haba Ummi kinsan dai idan Baby ta samu kaza ba'a magana, bata kula kowa, bata kasancewa a duniyar mutane, dan haka a barshi kawai sai wata saan".
Cikin mayen kaza da kuma santi ba tare da ta kalli in da yake ba ta ce "Yaya Nawid ka faɗi gaskiya, aradu kaza tafi duniya daɗi, wai yaya Nawid ka cire wannan abin da aka rufe maka a kasar gadonka kuwa? Sannan na gaya maka wannan Abbon kwarto ne amma kaki yarda, to yanzu kuma ya zama ɗan iska domin yana kallona sosai". Girgiza kai kawai Ummi ta yi babu wanda ya ɗauki zancenta da gaskiya domin suna yi mata kallon mahaukaciya, bare kuma idan ta samu kaza ai shikenan kuma, sai ta kara haukacewa da gasken-gaske.
Ba wanda ya kulata suka zauna suka gama cikin abincinsu, ita kuma har lokacin tana fama da kaza, kamar wata mai aljanun kaza a kai.
A ɓangaren su Rimsha kuwa, kamar yadda Akil ya basu umarnin kawo hadda da karfe 5 haka suka shirya suka yi wanka, suka yi sallah tare da cin abincin rana da suka girka suka shiryawa kansu, a palon Imran suka zauna suna jiransa. Sai 5:10 ya shigo shi da Umaisha, sai murmushi suke yi wa juna, da alama dunuyar tana yi masu daɗi, daga gani kasan sun mace akan juna.
Saman sofa mai zaman mutun 2 ya zauna su kuma suka yi maza suka sauƙa kasa, Akila tana ruƙe da Alkur'ani mai girma, ita kuma Rimsha ta ce zata kawo da kai ba tare da Alkur'ani ba, sai dariya Umaisha take yi wa Akila da alama wani munafurcin suka haɗa, kasa ya ce ita ma Umaisha ta sauƙa, ba musu ta sauƙo kasa, kafin ya fara karɓar haddan nasu ne ya tambayi Akila ina A'afia bata dawo bane, E ta bashi amsa, shiru ya ɗan yi kafin ya ce to su kawo haddansu zai je gida ya same ta.
Da haka suka rufe babyn Aafia suka fara bada haddansu, dukkansu sun kawo daidai, kuma ya jinjina masu, kyautar maki mai girma ya basu, sai ya ce su kara tusawa domin ya zauna a ƙwaƙwalwarsu da kyau, sai zuwa gobe da safe zai kara masu wani shafin. Sai murna suke yi suna zuba mashi godiya, a tare suka miƙe za su tafi.
"Karatun boko da luttatafai fa?" Ya jefo masu tambaya, cikin sauri suka dawo suka zauna, Akila ce ta ɗauko takardunta suka fara koyan karatu, ita kuma Umaisha ta ɗauko masu littafai irin su Nahhu, muɗalaa, malumat, da dai sauran littatafan musulunci, zama suka yi suna ɗaukan karatu da kyau, har da ƙawa'idi, ahlari a ciki, sai karfe 6 kamar yadda ya faɗa suka tashi, cikin hanzari suka faɗa kitchen dan su shiryawa bakon yaya Imran girki kamar yadda ya faɗa.
A tare suka fara aikin, wannan ta kama wannan, wannan ta kama wancan, sai hira suke yi Akila tana bawa Umaisha labarin saurayin Rimsha, wato yaya Ahmad, ɗan anachen Rimsha in ji ita Akilar, shine sunan da ta bashi, sai dariya suke yi, ita kuwa Rimsha ta tsare gida kam, babu alamar dariya ko wasa a tattare da ita, ta yi shiru sai ki rantse da Allah bata a wajen.
Fried rice suka yi ya ji kayan kamshi, su green beans da sauransu, Rimsha ce mai basu command, ita ma wani abin sai ta buɗe takardun girkin sannan take dubawa.
(Manya suna aiki fa.)
"Aunty Akila ke ki haɗa mana ganye, ke kuma Aunty Umaisha ki zuba abincin a kuloli ni kuma bari na haɗa pepper chicken" to suka amsa da shi sannan suka fara aikin da ta basu, abin duk wanda ya gansu sai sun ba shi sha'awa, sosai sun haɗa kansu kaman yan uwan juna, da yake Akila da Umaisha duk basu da matsala sai suka ja Rimsha sosai ajikinsu.
Bayan sun gama tsab, suka fito palo ana kiraye-Kirayen sallar mangariba, bedroom na Rimsha suka wuce, Akila ta ce a nan za ta yi wanka, ita kuma Umaisha ba dan ta so ba ta wuce Part nasu, Akil da Imran kuma sun tafi masallaci.
Rimsha ce ta fara yin wanka tare da ɗauro alwala, bayan ta fito Akila ta shiga.
Zama Rimsha ta yi a gaban mirror ta shafe jikinta da mayukanta masu daɗin kamshi tsab, sannan ta feshe perfume nata masu daɗin kamshi, kafin Akila ta fito har ta gama shafa mayukan da duk wani abin da zata yi a gaban mirror, saura saka kaya, lokacin ita kuma Akila ta fito ɗaure da towel a kirjinta, itakuwa Rimsha lokacin da ta fito, bayan towel da ta ɗaura sai da ta sanya ɗan karamin mayafinta da ta shiga da shi, wato gyalen abayar ta, dan bata son Akila ta ga zanen dake a kan kirjinta, shiyasa ta sanya mayafin a kanta ta rufe har kirjinta.
Riga da wandon da Akila ta ce su yi anko shi, shi ta ɗauko ta sanya, kayan sun karɓeta sosai da sosai, da rigar da wandon dukka masu kama jikine, sannan rigar zuwa gwiwarta ya tsaya mata, an zuba mashi kwalliya a gaba sosai, kai da gani kasan yana da tsada sosai dan ya haɗu over, launin pink color ne da milk, haka ta sanya su, amma kafin ta saka sai da ta sanya vest a ciki, domin wuyar rigar tana da ɗan girma, idan har bata sanya vest ba wannan zane na sunan Lion zai iya bayyana kowa ya gani, dama kuma saboda zanen yasa da suka je shopping ta ɗauki dozen na irin vest ɗin nan masu kama jiki sosai kamar roba, dan bata son kowa ya gani ma bare kuma ya tambayeta me yasa zata rubuta sunansa.
Bayan ta gama shiri sai da ta sake fesa turare sannan ta zura hijabi har kasa ta zauna a bakin gado tana jiran Akila, domin ta tafi sanya nata kayan ita ma.
Jiran minti goma ta yi sai ga Akilar ta dawo shirye cikin nata kayar irin ɗaya suka yi anko, akalla Akila zata bawa Rimsha good 4 years da yan ɗori, amma da yake Rimsha tana da tsawo sai kansu ya yi kusan ɗaya, da kaɗan Akila ta ɗara ta, dan suma ƴaƴan Abba ba baya ba wajen tsawo. Yanzu Rimsha an fara zama ƴan mata tula-tula sun fara girma.
A tare suka yi Sallah, bayan sun idar suka wuce palo dan su ɗan yi kallo. Suna zama saman sofa Rimsha ta ɗauki remote ta shiga News, Rimsha yarinya mai Sa'a duk time da ta shiga News zancen mutumin nata ake yi, yau ma ta yi Sa'a maganarsa ake yi, ga kuma hotonsa nan an kafe kamar kullum yana sanye da face mask.
Kamar ance ta kalli fuskarsa, ai kuwa idanunta suka sauƙa akan nasa, ba abin da ya faɗo mata a ƙwaƙwalwarta irin yadda taga idanuwansa a zahiri cikin mafarkinta, yadda ta gansu muraran, tuna hakan yasa ta runtse idanuwanta, tana tunanin yadda yake a zahiri, wannan idan ka ganshi zaka iya mutuwa.
Ji tayi ba zata iya ganin fuskarsa ba, koda kuwa a hoton ne, mugun razana ta yake yi, hakan yasa ta yi maza ta canja tasha. "A'a Rimsha me yasa zaki kashe mani jarumina ina tsaka da kallo?". Cewar Akila.
Ba tare da tayi magana ba ta miƙe da sauri ta koma cikin ɗaki, daidai lokacin aka kira sallar isha. Saman dadduma ta hau tana hawaye tana Sallah, ta rasa meke damunta, tana bala'in son wannan mutumi, amma kuma duk lokacin da ta kalli even pic nasa da glass ba iya face mask ba, sai ta yi mugun razana, sai ta fi awa uku tana takure waje guda tana razana, kamar wadda taga wani dodon ko wani abin, idan kuwa tana kwayar idonsa a hoton, ma'ana babu glass wunin ranar zata yi shine ba cikin walwala ba, ta rasa menene dalili, tana sallah tana kuka, ko da ta kai sujjada, ya jima sosai tana kuka tana rokan Allah da ya rabata da son wannan mutumi a zuciyarta, ta kuma yi danasanin rubuta sunansa a kirjinta.
A wannan hali Akila ta iskota, bata kawo komai a ranta ba, ganin tana sallama yasa ta yi tunanin kenan dama ƙiran Sallah da akayi ne yasa ta baro palo da gudu ta dawo ɗaki, da farko ta zaci ko wata matsalace, amma ganin tana sallah yasa ita ta tsaya kusa da ita tare da tada kabbara ta fara Sallah.
Rimsha bata bari Akila taga hawayen fuskanta ba, tana idar da sallah ta miƙe ta shiga toilet, lokacin kuma ita Akila tana raka'a na uku ne, tana shiga toilet ta wanke fuskarta sosai, sannan ta fito ta zauna gaban mirror ta ɗan gyara fuskar tata, ta miƙe ta nufi palo.
Bayan Akila ta idar da sallah ta yi addu'a sannan ta bi bayanta, daidai lokacin su Imran suka dawo masallaci, shi da Akil.
A palon suka baje suna hira da dariya, fito da wayarsa Akil ya yi ya kira Umaisha dan ta zo su yi hira a tare, aikuwa ba ɓata lokaci sai ga ta nan ta shigo, haka suka cigaba da hira cikin annashuwa, shi kuma Ahmad sai kiran layin Rimsha yake yi amma wayar na ɗaki ta sanya ta a silent. Sai wuraren karfe 9 da Imran ya samu sakon Nawid akan ba zai samu damar zuwa ba, saboda Jelly ta samu kaza, dariya Imran ya yi sosai ya ce "Ashe kuna da maganinta a gida ma ka tsaya kana wahalar da kanka, ai nan gaba idan ta dameka da ku fita yawo kaza kawai zaka saka Ummi ta soya mata sai ka haɗa ta da shi ka huta". Shima Nawid ɗin dariya ya yi, Imran duk ɗaukansa kanwar Nawid ɗin da ya ce an kawo ta da ga family Abbo ya zaci yarinya ce da bata wuci 8 to 10 years haka ba, shiyasa ma yake yiwa Nawid tsiya irin haka.
Haka suka yi ta hiransu na abokai daga bisani suka yi sallama da juna, Imran ya cewa su Rimsha su kawo masu abinci su ci, saboda Nawid ya ce ba zai samu zuwa ba, cike da murna suka kawo abincin Akil sai mamaki yake yi, yar yarinya kamar Rimshan nan ne ta iya girki, da farko ya ce ba zai ci ba, domin yana ganin kamar jagwalgwalo kawai suka yi, amma daga baya da Imran ya matsa mashi, sai ya ce a sanya mashi kaɗan, ai kuwa yana fara ci ya ce a kara mashi, sai dariya Akila ta ke yi mashi, ta ce "Wai yaya Akil ka manta ka ce duk mace da bata haura shekara talatin ba, ba zaka ci girkinta ba, domin ko masu shekara ashirin da biyar yara ne kamar mu, ba'a gama ya ye mu ba?". Harara ya wurga mata ita kuma Umaisha cewa ta yi "Innalillahi wa inna ilaihir rajiun dama yaya Akil abin da ka faɗa kenan? Lallai ma, to wlh yanzu zan ko yi girki idan ba zaka ci nawa ba, ni ma ba zan ci na restaurant ba".
A kule ya ce "Idan kuma na bada umarnin ki ci dole fa?" Still dai fuskarta ɗauke da murmushi ta ce "E sai na ci mana tun da kai kace, to bama dole na ba" Wani nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke, Akil akwai bala'in son girma, wato tun da idan ya bada umarni zata ci shikenan ai ya huce, shi dai Imran, shi da Rimsha ban da murmushi ba wani abin da suke bin su da shi.
Bayan sun gama cin abincin sun yi komai, sun tattare wajen ne, suka yi wa yaya Imran sallama, Rimsha ta wuce ɗakin ta, Akila da Akil da Umaisha suka wuce cikin gida, shi kuma Imran ya ɗan jima a palon kafin nan ya tashi ya shiga bedroom nasa, ya yi wanka ya shirya cikin kayan barci, sannan ya kwanta.
Itama Rimsha wanka ta yi tare da shiryawa cikin tsadaddun kaya barcinta masu kyau launin pink color riga da wando, dan tana son pink color, sky blue, da kuma fari, sune best color ɗin ta.
Bayan ta gama ne ta sake feshe ɗakinta sa air freshener sannan ta haye gado ta ja bargo tare da jawo wayarta ta fara kiran layin Ayla, amma a kashe sosai ta fara shiga damuwa akan me ya samu Ayla. Haka tana ganin kiran Ahmad amma bata ɗauka ba, saboda bata cikin yanayi mai daɗi, tana tunanin Ayla sosai. A wannan daren dai da kyar barci ya yi awon gaba da ita. Asuba ta gari.
Idan muka koma Washington DC kuma.
Kamar dai yadda suka tsara haka suka yi, sai da suka yi sallah la'asar sannan suka dawo gida, haka da mangariba tun karfe 6 suka fita gida, sai karfe 8 bayan sun yi sallar isha suka dawo gida, a palon Part ɗin Michael suka zauna dan yanzu dama ba su wani cika zuwa palon kasa ba, waya Michael ya yi akan bodyguard su kawo mashi kayan tea part nasa, haka kuwa a kayi ba tare da ɓata lokacin ba, sai ga bodyguard guda biyu, kamar kullun suna cikin dressing nasu na bakaken suit tare da bakaken glasa a kan face nasu, wato no respect.
Saman dining table dake a cikin palon suka ɗaura kayan tea ɗin tare da wani kyakkyawar flaks mai kyan gaske, kayatatcen tea ne wadda aka haɗa shi da ganyayyaki masu kara lafiya a jiki, shine a jikin flaks ɗin, haka suka ajiye suka juya suka bar palon.
Kallon Musharraf Michael ya yi yana faɗin "Uncle ɗin James ka je ka haɗa tea ɗin ni bari na je na yi wanka na duba Lion yau tun safe da muka rabu a gym ba mu sake haɗuwa ba" To Musharraf ya bishi da shi, sannan suka miƙe a tare, Michael ya wuce toilet shi kuma Musharraf ya wuce saman table ɗin dan ya haɗa tea ɗin sa.
A ɓangaren Lion kuwa, lokacin da ya gama zaman shi a lambun sai ya miƙe ba tare da ya sha fruits ɗin ba, maltina kawai ya ɗauka kwara ɗaya da glass cup ɗaya ya fito daga wajen.
Ji kake dip-dip-dip wani jibgegen Bature soja fari tas ya nufishi a guje, yana zuwa ya karɓi maltinan da glass cup dake a hannunsa, cikin girmamawa ya ɗaga hannu ya sara mashi tare da buga kafa, ba musu Lion ya miƙa mashi maltina dan dama dan dole ya ɗauko su, yana jin yunwa amma kuma suna da zama a white house karfe 10 yanzu kuma har 11 ta kai bai je ba, hakan yasa ya fasa shan fruits ɗin dama kuma ba wani niyar sha yake da shi ba, kawai dai bai son cin abincin safe ne yasa ya ce zai sha fruits ɗin.
Kasa kasa ya yi magana kamar mai raɗa "Ku tashi motoci za mu wuce white house" da sauri sojan ya sanarwa da sauran sojojin dake a kusa, kan kace me sun haye saman bayan motoncin, wannan sojan da ya riƙe mashi maltinan shi ya buɗe mashi motarsa
Showing 159001 words to 162000 words out of 344390 words
Kasan cewar ogan su mai kiran waya baya nan hakan yasa suka wuni a wajen ba wadda aka kira iyayensa, domin duk cikin bandits ɗin mutun biyar kawai ke da damar kiran waya, saura kuma aikinsu kamo jama'a ne kawai, da kuma kula da su, bayan haka ba wani abin.
Jugum-jugum suka zauna ba sallar azahar bare la'asar har karfe shida na yamma sannan suka sanya su a gaba zuwa cikin ɗakunansu, dayawa daga cikin bandits ɗin basa nan, da alama wani abin suka tafi aikatawa acikin gari, domin kusan rabi da kwatansu basu nan a wajen, yan kalilan suka rage, wadda ba su fi yawan mutanen dake a wajen ba.
Haka aka mai da su cikin ɗaki suka cigaba da zama jugum-jugum ita kuma Rufee da alama fa kamar babu rai ajikinta, domin ƙo motsi bata yi, kuma haka suke janta a kasa kamar shanuwa, a wannan dawo da su da suka yi, sun haɗa Aafia da kuma Hanan kanwar Sadiq waje guda, domin dama haka suke yi, idan sun tashi mai da ku, mafiyawancin lukuta suna canza maku ɗaki domin kada kudaɗe a waje guda har ku shirya masu wani abin, shayasa basu barin jama'a su sarara, tsabar rashin yarda da kai.
(To mun ji ɓangaren Aafia bari mu leƙa ɓangaren su Jelly dan jin yadda zata kaya mana.)
Sai murna take yi za su fita yawo da yaya Nawid, abin ba'a magana har wani kin magana take yi ma mutane, sai kauɗi take yi da rawan kai, ita adole za su fita yawo.
Bayan sun yi sallar isha ne suka zauna cin abinci, da sallama Nawid ya shigo palon, zaune ya isko su saman table Ummi na kokarin zuba masu abinci su ci, yau Abbo ba a part nasu yake ba, yana part ɗin maman Afnan hakan yasa Ummi gaba ɗaya bata son fitar da Nawid zai yi da baby, dan kada ya barta cikin kaɗaici.
"Baby ki tashi mu tafi mana, ba sai kinci abinci ba, za mu ci a can, Prof ya sa an shirya mana abinci". Ba tare da ta kalli in da yake ba, ta ce "Yaya Nawid kaza fa Ummi ta soya mani, ni gaskiya babu in da zanje sai na ci wannan kazar". Bin Ummi da ido ya yi, sai yanzu ya gane me matsalar da gangan Ummi ta kawo mata kaza dan bata son su fita saboda Abbo yana part ɗin su Afnan, sanin haka yasa ya samu waje saman chair ɗin tabla ɗin ya zauna yana faɗin shima a zuba mashi abincin kawai ya ci.
Cikin sauri Ummi ta ce "Fitar fa ya zaku yi?" Rai a ɗan ɓace ya ce "Haba Ummi kinsan dai idan Baby ta samu kaza ba'a magana, bata kula kowa, bata kasancewa a duniyar mutane, dan haka a barshi kawai sai wata saan".
Cikin mayen kaza da kuma santi ba tare da ta kalli in da yake ba ta ce "Yaya Nawid ka faɗi gaskiya, aradu kaza tafi duniya daɗi, wai yaya Nawid ka cire wannan abin da aka rufe maka a kasar gadonka kuwa? Sannan na gaya maka wannan Abbon kwarto ne amma kaki yarda, to yanzu kuma ya zama ɗan iska domin yana kallona sosai". Girgiza kai kawai Ummi ta yi babu wanda ya ɗauki zancenta da gaskiya domin suna yi mata kallon mahaukaciya, bare kuma idan ta samu kaza ai shikenan kuma, sai ta kara haukacewa da gasken-gaske.
Ba wanda ya kulata suka zauna suka gama cikin abincinsu, ita kuma har lokacin tana fama da kaza, kamar wata mai aljanun kaza a kai.
A ɓangaren su Rimsha kuwa, kamar yadda Akil ya basu umarnin kawo hadda da karfe 5 haka suka shirya suka yi wanka, suka yi sallah tare da cin abincin rana da suka girka suka shiryawa kansu, a palon Imran suka zauna suna jiransa. Sai 5:10 ya shigo shi da Umaisha, sai murmushi suke yi wa juna, da alama dunuyar tana yi masu daɗi, daga gani kasan sun mace akan juna.
Saman sofa mai zaman mutun 2 ya zauna su kuma suka yi maza suka sauƙa kasa, Akila tana ruƙe da Alkur'ani mai girma, ita kuma Rimsha ta ce zata kawo da kai ba tare da Alkur'ani ba, sai dariya Umaisha take yi wa Akila da alama wani munafurcin suka haɗa, kasa ya ce ita ma Umaisha ta sauƙa, ba musu ta sauƙo kasa, kafin ya fara karɓar haddan nasu ne ya tambayi Akila ina A'afia bata dawo bane, E ta bashi amsa, shiru ya ɗan yi kafin ya ce to su kawo haddansu zai je gida ya same ta.
Da haka suka rufe babyn Aafia suka fara bada haddansu, dukkansu sun kawo daidai, kuma ya jinjina masu, kyautar maki mai girma ya basu, sai ya ce su kara tusawa domin ya zauna a ƙwaƙwalwarsu da kyau, sai zuwa gobe da safe zai kara masu wani shafin. Sai murna suke yi suna zuba mashi godiya, a tare suka miƙe za su tafi.
"Karatun boko da luttatafai fa?" Ya jefo masu tambaya, cikin sauri suka dawo suka zauna, Akila ce ta ɗauko takardunta suka fara koyan karatu, ita kuma Umaisha ta ɗauko masu littafai irin su Nahhu, muɗalaa, malumat, da dai sauran littatafan musulunci, zama suka yi suna ɗaukan karatu da kyau, har da ƙawa'idi, ahlari a ciki, sai karfe 6 kamar yadda ya faɗa suka tashi, cikin hanzari suka faɗa kitchen dan su shiryawa bakon yaya Imran girki kamar yadda ya faɗa.
A tare suka fara aikin, wannan ta kama wannan, wannan ta kama wancan, sai hira suke yi Akila tana bawa Umaisha labarin saurayin Rimsha, wato yaya Ahmad, ɗan anachen Rimsha in ji ita Akilar, shine sunan da ta bashi, sai dariya suke yi, ita kuwa Rimsha ta tsare gida kam, babu alamar dariya ko wasa a tattare da ita, ta yi shiru sai ki rantse da Allah bata a wajen.
Fried rice suka yi ya ji kayan kamshi, su green beans da sauransu, Rimsha ce mai basu command, ita ma wani abin sai ta buɗe takardun girkin sannan take dubawa.
(Manya suna aiki fa.)
"Aunty Akila ke ki haɗa mana ganye, ke kuma Aunty Umaisha ki zuba abincin a kuloli ni kuma bari na haɗa pepper chicken" to suka amsa da shi sannan suka fara aikin da ta basu, abin duk wanda ya gansu sai sun ba shi sha'awa, sosai sun haɗa kansu kaman yan uwan juna, da yake Akila da Umaisha duk basu da matsala sai suka ja Rimsha sosai ajikinsu.
Bayan sun gama tsab, suka fito palo ana kiraye-Kirayen sallar mangariba, bedroom na Rimsha suka wuce, Akila ta ce a nan za ta yi wanka, ita kuma Umaisha ba dan ta so ba ta wuce Part nasu, Akil da Imran kuma sun tafi masallaci.
Rimsha ce ta fara yin wanka tare da ɗauro alwala, bayan ta fito Akila ta shiga.
Zama Rimsha ta yi a gaban mirror ta shafe jikinta da mayukanta masu daɗin kamshi tsab, sannan ta feshe perfume nata masu daɗin kamshi, kafin Akila ta fito har ta gama shafa mayukan da duk wani abin da zata yi a gaban mirror, saura saka kaya, lokacin ita kuma Akila ta fito ɗaure da towel a kirjinta, itakuwa Rimsha lokacin da ta fito, bayan towel da ta ɗaura sai da ta sanya ɗan karamin mayafinta da ta shiga da shi, wato gyalen abayar ta, dan bata son Akila ta ga zanen dake a kan kirjinta, shiyasa ta sanya mayafin a kanta ta rufe har kirjinta.
Riga da wandon da Akila ta ce su yi anko shi, shi ta ɗauko ta sanya, kayan sun karɓeta sosai da sosai, da rigar da wandon dukka masu kama jikine, sannan rigar zuwa gwiwarta ya tsaya mata, an zuba mashi kwalliya a gaba sosai, kai da gani kasan yana da tsada sosai dan ya haɗu over, launin pink color ne da milk, haka ta sanya su, amma kafin ta saka sai da ta sanya vest a ciki, domin wuyar rigar tana da ɗan girma, idan har bata sanya vest ba wannan zane na sunan Lion zai iya bayyana kowa ya gani, dama kuma saboda zanen yasa da suka je shopping ta ɗauki dozen na irin vest ɗin nan masu kama jiki sosai kamar roba, dan bata son kowa ya gani ma bare kuma ya tambayeta me yasa zata rubuta sunansa.
Bayan ta gama shiri sai da ta sake fesa turare sannan ta zura hijabi har kasa ta zauna a bakin gado tana jiran Akila, domin ta tafi sanya nata kayan ita ma.
Jiran minti goma ta yi sai ga Akilar ta dawo shirye cikin nata kayar irin ɗaya suka yi anko, akalla Akila zata bawa Rimsha good 4 years da yan ɗori, amma da yake Rimsha tana da tsawo sai kansu ya yi kusan ɗaya, da kaɗan Akila ta ɗara ta, dan suma ƴaƴan Abba ba baya ba wajen tsawo. Yanzu Rimsha an fara zama ƴan mata tula-tula sun fara girma.
A tare suka yi Sallah, bayan sun idar suka wuce palo dan su ɗan yi kallo. Suna zama saman sofa Rimsha ta ɗauki remote ta shiga News, Rimsha yarinya mai Sa'a duk time da ta shiga News zancen mutumin nata ake yi, yau ma ta yi Sa'a maganarsa ake yi, ga kuma hotonsa nan an kafe kamar kullum yana sanye da face mask.
Kamar ance ta kalli fuskarsa, ai kuwa idanunta suka sauƙa akan nasa, ba abin da ya faɗo mata a ƙwaƙwalwarta irin yadda taga idanuwansa a zahiri cikin mafarkinta, yadda ta gansu muraran, tuna hakan yasa ta runtse idanuwanta, tana tunanin yadda yake a zahiri, wannan idan ka ganshi zaka iya mutuwa.
Ji tayi ba zata iya ganin fuskarsa ba, koda kuwa a hoton ne, mugun razana ta yake yi, hakan yasa ta yi maza ta canja tasha. "A'a Rimsha me yasa zaki kashe mani jarumina ina tsaka da kallo?". Cewar Akila.
Ba tare da tayi magana ba ta miƙe da sauri ta koma cikin ɗaki, daidai lokacin aka kira sallar isha. Saman dadduma ta hau tana hawaye tana Sallah, ta rasa meke damunta, tana bala'in son wannan mutumi, amma kuma duk lokacin da ta kalli even pic nasa da glass ba iya face mask ba, sai ta yi mugun razana, sai ta fi awa uku tana takure waje guda tana razana, kamar wadda taga wani dodon ko wani abin, idan kuwa tana kwayar idonsa a hoton, ma'ana babu glass wunin ranar zata yi shine ba cikin walwala ba, ta rasa menene dalili, tana sallah tana kuka, ko da ta kai sujjada, ya jima sosai tana kuka tana rokan Allah da ya rabata da son wannan mutumi a zuciyarta, ta kuma yi danasanin rubuta sunansa a kirjinta.
A wannan hali Akila ta iskota, bata kawo komai a ranta ba, ganin tana sallama yasa ta yi tunanin kenan dama ƙiran Sallah da akayi ne yasa ta baro palo da gudu ta dawo ɗaki, da farko ta zaci ko wata matsalace, amma ganin tana sallah yasa ita ta tsaya kusa da ita tare da tada kabbara ta fara Sallah.
Rimsha bata bari Akila taga hawayen fuskanta ba, tana idar da sallah ta miƙe ta shiga toilet, lokacin kuma ita Akila tana raka'a na uku ne, tana shiga toilet ta wanke fuskarta sosai, sannan ta fito ta zauna gaban mirror ta ɗan gyara fuskar tata, ta miƙe ta nufi palo.
Bayan Akila ta idar da sallah ta yi addu'a sannan ta bi bayanta, daidai lokacin su Imran suka dawo masallaci, shi da Akil.
A palon suka baje suna hira da dariya, fito da wayarsa Akil ya yi ya kira Umaisha dan ta zo su yi hira a tare, aikuwa ba ɓata lokaci sai ga ta nan ta shigo, haka suka cigaba da hira cikin annashuwa, shi kuma Ahmad sai kiran layin Rimsha yake yi amma wayar na ɗaki ta sanya ta a silent. Sai wuraren karfe 9 da Imran ya samu sakon Nawid akan ba zai samu damar zuwa ba, saboda Jelly ta samu kaza, dariya Imran ya yi sosai ya ce "Ashe kuna da maganinta a gida ma ka tsaya kana wahalar da kanka, ai nan gaba idan ta dameka da ku fita yawo kaza kawai zaka saka Ummi ta soya mata sai ka haɗa ta da shi ka huta". Shima Nawid ɗin dariya ya yi, Imran duk ɗaukansa kanwar Nawid ɗin da ya ce an kawo ta da ga family Abbo ya zaci yarinya ce da bata wuci 8 to 10 years haka ba, shiyasa ma yake yiwa Nawid tsiya irin haka.
Haka suka yi ta hiransu na abokai daga bisani suka yi sallama da juna, Imran ya cewa su Rimsha su kawo masu abinci su ci, saboda Nawid ya ce ba zai samu zuwa ba, cike da murna suka kawo abincin Akil sai mamaki yake yi, yar yarinya kamar Rimshan nan ne ta iya girki, da farko ya ce ba zai ci ba, domin yana ganin kamar jagwalgwalo kawai suka yi, amma daga baya da Imran ya matsa mashi, sai ya ce a sanya mashi kaɗan, ai kuwa yana fara ci ya ce a kara mashi, sai dariya Akila ta ke yi mashi, ta ce "Wai yaya Akil ka manta ka ce duk mace da bata haura shekara talatin ba, ba zaka ci girkinta ba, domin ko masu shekara ashirin da biyar yara ne kamar mu, ba'a gama ya ye mu ba?". Harara ya wurga mata ita kuma Umaisha cewa ta yi "Innalillahi wa inna ilaihir rajiun dama yaya Akil abin da ka faɗa kenan? Lallai ma, to wlh yanzu zan ko yi girki idan ba zaka ci nawa ba, ni ma ba zan ci na restaurant ba".
A kule ya ce "Idan kuma na bada umarnin ki ci dole fa?" Still dai fuskarta ɗauke da murmushi ta ce "E sai na ci mana tun da kai kace, to bama dole na ba" Wani nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke, Akil akwai bala'in son girma, wato tun da idan ya bada umarni zata ci shikenan ai ya huce, shi dai Imran, shi da Rimsha ban da murmushi ba wani abin da suke bin su da shi.
Bayan sun gama cin abincin sun yi komai, sun tattare wajen ne, suka yi wa yaya Imran sallama, Rimsha ta wuce ɗakin ta, Akila da Akil da Umaisha suka wuce cikin gida, shi kuma Imran ya ɗan jima a palon kafin nan ya tashi ya shiga bedroom nasa, ya yi wanka ya shirya cikin kayan barci, sannan ya kwanta.
Itama Rimsha wanka ta yi tare da shiryawa cikin tsadaddun kaya barcinta masu kyau launin pink color riga da wando, dan tana son pink color, sky blue, da kuma fari, sune best color ɗin ta.
Bayan ta gama ne ta sake feshe ɗakinta sa air freshener sannan ta haye gado ta ja bargo tare da jawo wayarta ta fara kiran layin Ayla, amma a kashe sosai ta fara shiga damuwa akan me ya samu Ayla. Haka tana ganin kiran Ahmad amma bata ɗauka ba, saboda bata cikin yanayi mai daɗi, tana tunanin Ayla sosai. A wannan daren dai da kyar barci ya yi awon gaba da ita. Asuba ta gari.
Idan muka koma Washington DC kuma.
Kamar dai yadda suka tsara haka suka yi, sai da suka yi sallah la'asar sannan suka dawo gida, haka da mangariba tun karfe 6 suka fita gida, sai karfe 8 bayan sun yi sallar isha suka dawo gida, a palon Part ɗin Michael suka zauna dan yanzu dama ba su wani cika zuwa palon kasa ba, waya Michael ya yi akan bodyguard su kawo mashi kayan tea part nasa, haka kuwa a kayi ba tare da ɓata lokacin ba, sai ga bodyguard guda biyu, kamar kullun suna cikin dressing nasu na bakaken suit tare da bakaken glasa a kan face nasu, wato no respect.
Saman dining table dake a cikin palon suka ɗaura kayan tea ɗin tare da wani kyakkyawar flaks mai kyan gaske, kayatatcen tea ne wadda aka haɗa shi da ganyayyaki masu kara lafiya a jiki, shine a jikin flaks ɗin, haka suka ajiye suka juya suka bar palon.
Kallon Musharraf Michael ya yi yana faɗin "Uncle ɗin James ka je ka haɗa tea ɗin ni bari na je na yi wanka na duba Lion yau tun safe da muka rabu a gym ba mu sake haɗuwa ba" To Musharraf ya bishi da shi, sannan suka miƙe a tare, Michael ya wuce toilet shi kuma Musharraf ya wuce saman table ɗin dan ya haɗa tea ɗin sa.
A ɓangaren Lion kuwa, lokacin da ya gama zaman shi a lambun sai ya miƙe ba tare da ya sha fruits ɗin ba, maltina kawai ya ɗauka kwara ɗaya da glass cup ɗaya ya fito daga wajen.
Ji kake dip-dip-dip wani jibgegen Bature soja fari tas ya nufishi a guje, yana zuwa ya karɓi maltinan da glass cup dake a hannunsa, cikin girmamawa ya ɗaga hannu ya sara mashi tare da buga kafa, ba musu Lion ya miƙa mashi maltina dan dama dan dole ya ɗauko su, yana jin yunwa amma kuma suna da zama a white house karfe 10 yanzu kuma har 11 ta kai bai je ba, hakan yasa ya fasa shan fruits ɗin dama kuma ba wani niyar sha yake da shi ba, kawai dai bai son cin abincin safe ne yasa ya ce zai sha fruits ɗin.
Kasa kasa ya yi magana kamar mai raɗa "Ku tashi motoci za mu wuce white house" da sauri sojan ya sanarwa da sauran sojojin dake a kusa, kan kace me sun haye saman bayan motoncin, wannan sojan da ya riƙe mashi maltinan shi ya buɗe mashi motarsa
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54 Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115