ba wannan da tana prison yanzu, duk abin da ya faru a gidan bayan tafiyar mu ranar Akila ta gaya mani a waya, wlh Allah zan iya cewa Ommu kin zama mace mai saa ta farko da Akil ya ɗagawa kafa, ina mai tabbatar maki badan Irfan ba da babu abin da zai hana Akil ya sharara maki maruka wadda za su sanya ki manta hanyar da ki ka nufa, su sanya ki gani taurari, su sanya kunnuwarki doɗewa, ni ki bani account number bari na cireki daga kangin tsiya da kuma talaucin nan ko zamu samu sake a gidan bappanmu idan muka zo!!". Ya kai karshen maganar rai a matukar ɓace, dama an ce mai hakuri bai iya fushi ba.
Sakin Jelly daddy ya yi yana faɗin "Rimsha ku je sama wajen Hanan ko, babyn daddy ta shi ku je ko?".
To suka amsa da shi, da kyar Ayla ta miƙe, da sauri Aunty ta zo ta dafa mata suka wuce sama, domin ita ma Aunty bata son tsayawa a wajen dan bata ma son jin hayaniyar tasu.
Dawo da kallonsa a kanta daddy ya yi tare da ɗaure fuska nan yau shima ransa ya yi mugun ɓaci, yau karo na biyu kenan da take cin mutuncin su a gaban ƴaƴansu to gaskiyar Imran ne yana da kyau su taka mata birki domin iskancin nata ya fara wuce misali.
"Hadiza ina ganin mutunci ki ne nima dan saboda Irfan, yaron kirki, Allah ya rufa mishi asiri ba ke kika raine shi ba, wlh nasan da ke kika ba su tarbiya ƴaran nan da sai sun zama kannen sheɗanu, yanzu ke ba abin kunya bane ma ki ɗauko kafar ki da sunan wai kin dawo gidan nan? Wlh ta bakin Imran kin yi babbar sa'ar Akil aure ta sauya shi, ba dan haka ba ko yaya suke da Irfan sai ya dalla maki mari, idan ma baki yi sa'a ba sai kin wuce gadon asibiti, yanzu tsabar rashin kunya ƴaƴan yaya babban ne talakawa? Ke kin sani a gaba ɗaya cikin mu a tsabar kuɗi dai daga Hosain sai Yaya babba wato Abban su Imran, ko dai dama baki san su Imran ƴaƴan yaya babba bane? To idan baki sani ba yanzu ki sani Akil kawai zai iya sayan Familynku baki ɗaya, sannan bugu da kari ƴaƴan Umaiya ce wadda ta ma fi yaya babba kuɗi, kuma ke kin sani ko ada baya da yaya ki ka kwaci kanki a hannun Umaiya? To ki sani barewa ba zata yi gudu ɗan ta ya yi rarrafe ba, tun wuri ki fita har karmu idan ba haka ba zaki yi dana sani, yadda ki ka san Umaiya a da to yanzu Akil ne photo copyn ta, shiyasa ki ka ji munce maki kin ciri tuta tun da har Akil ya iya danne zuciya ya kyaleki!!!".
Cikin sauri Ommu ta ce "Yanzu kenan Umaisha ɗan gidan Yaya babban ta aura?".
Ba wanda ya tanka mata a cikinsu, cikin zumuɗi ta ce "Kai amma Alhadulillah da ya kasance ba ƴaƴan Matsiyata ƴar cikina ta aura ba, kai abin ya min daɗi". Tana gama magana ta juyawa ta nufi sama, sai daɗi take ji.
Girgiza kai daddy ya yi tare da komawa ya zauna a saman sofa, shima Abbi zama ya yi a saman sofa yana mamakin hali irin na Aunty, Baiwar Allah mace mai sanin Yakamata, bata son hayaniya, mafi yawancin mata suna son su ga ana ci wa kishiyarsu mutunci amma ban da Aunty, da zarar sun fara faɗa zata wuce ɗakinta dan ma kada ta ga abin da yake faruwa, bata son hayaniya kuma bata son abin haushi, tana da zuciya mai kyau sosai, har cikin ransa yau Abbi ya ji wani irin mugun daɗi abin da Aunty ta aikata, ta san abin da take yi.
Shi kuma Imran sama ya haura domin ya je ya kira su jelly.
Jim kaɗan sai ga Ommu ta fito riƙe da wayarta ta canza shiga zuwa doguwar riga, da alama ya fasa fitan kenan.
Kusa da Abbi ta zo ta tsaya tare da miƙa mashi wayarta tana faɗin "Saka Mani number Umaisha ko kuma na mijinta a nan bari na kira shi ya kawo mani ita yanzun nan zan yi magana da ita".
Kallon daddyn Jelly Abbi ya yi, mamaki ya hana su magana, tun da ta dawo bata nemi yaran ba sai da ta ji Umaisha na auren Akil sannan ne zata ne me su dan ta ji ruwan kuɗi.
Sosai daddy yake addu'ar kada ta lalatawa yaran nan aurensu, dan yasan halinta sarai, zata iya kai Umaisha ta barota, kuma kun san tsakanin uwa da ƴa, sannan Ommu ba ruwanta da wai ƴar cikinta ce, idan bukatar ta ya biya shikenan ai.
Ƙin saka mata number Abbi ya yi, ya ce bashi da shi, ba dan ta so ba ta hakura ta koma sama tana tunanin yadda zata yi.
Tana komawa ba jimawa sai ga su Imran sun sauƙo kasa, jelly ta canza kaya zuwa doguwar riga ash color, shi kuma Imran yana manne da waya a kunne yana magana da Akil akan su zo gidan Abbi yanzu an gane Jelly.
Aunty na rungume da Ayla suka sauƙo kasa. Jikin daddy jelly ta je ta haye tana zuba mashi shagwaɓa akan tana kewarsa, da hannu ya yi wa Ayla alama akan ta zo ita ma, ba musu ta je dan dama bata taɓa yin musu da shi ba.
Ta gefen jikinsa ya jawota yana faɗin "Babyn daddy wannan ita ce Jelly" jin abin da daddy ya ce yasa Jelly ta yi saurin ɗago kai tana maimaita sunnan da daddy ya kira Ayla da shi.
Kamar wadda aka yi wa allura haka Jelly ta diro kasa ta yi zaman ƴan bori a tsakiyar carpet ɗin tare da fara wuwwurga kafafu a kasa tana ihu kamar ba lafiya ba, daddy ya san me take yi wa ihu, wato dan ya kira Ayla da babyn daddy shi ne take kuka, sunan babyn daddy sunan Jelly ɗin ne da yake kiranta da shi lokacin suna Kano.
Imran ne ya yi saurin marisowa wajenta tare da riƙota yana faɗin "Jelly menene?".
Cikin kuka ta ce "Yaya Imran daddy fa yanzu ya daina so na, kana ganin wata babyn ya samu". Babbar magana wai ɗan sanda ya ga gawar soja, dama shi daddy already yasan za'ayi hakan, yasan ba zata taɓa yarda da Ayla ba, shiyasa ya ce tana dawowa za'a ɗaura mata aure da Imran kowa ma ya huta.
Cikin sigar rarrashi Imran ya ce "Jelly wannan fa mummynki ce ba wai wata ba, mummy zaki ce mata".
Cak ta tsaya da kukan nata tare da ɗago idanu da sauri ta sauƙe akan Ayla ɗin. Kallon minti ɗaya ta yi mata kafin kuma ta kwashe da dariya kamar wata zautatciya, daddy kam ko ajikinsa dan ya san halin kayarsa, in dai jelly ce to fin hakan ma zata yi, sai ta sa ka ka yi tunanin ko kaine mahaukaci, wlh tsab jelly zata sanya ka fara tunanin anya kana lafiya kuwa? Anya kai ba mahaukaci bane kuwa?.
Shi kuwa Imran da yake har yanzu yana da sauran karatu akanta sai ya ce "Jelly lafiya kike dariya kuma?" Kara sautin dariyar tata ta yi har da rike ciki, kamar ba ita ba ce mai yin kuka yanzun nan.
Sai da ta yi dariyarta mai isarta sannan ta ce "Amma yaya Imran a sanina dai kafin mu zo nan lafiya lou kake, ya akayi kuma yanzu ka canza kamar mara lafiya?" Ɗan kallon kansa ya yi dan ko zai ga abin da ta gani a tattare da shi da ta ce mashi ba shi da lafiya.
Shikam daddy a zuciyarsa cewa ya yi kaɗan ka gani Imran ba dai jelly ba, wata rana sai ta sanya ka tuɓe wando a cikin jama'a, Abbi kuwa ban da murmushi ba abin da yake yi, ita kuwa Aunty yau ta ga duniya a wajen jelly, ta ga abin mamaki, Rimsha kam ko a jikinta, Hanan ce ma ta ɗan tsorata da ganin abin da jellyn take yi.
"Jelly wai me yake faruwa ne?" Cewar Imran, cikin dariya ta ce "Yaya Imran wannan ƴar karamar yarinyar da bata wuce na kamata na haɗiyeta na kora ruwa bace mummyna? Wai ka manta mummyna ta rasu ne? To idan ka manta na tuna maka, mummyna bata nan wannan kuma ai ko mai....." Bata karasa ba ta ja birki sakamakon karewa fuskar Ayla kallo da take yi.
Zubur ta miƙe tana faɗin "Ya na kalli tana kama da mumnyn kuma?" Da yake ta san fuskar mumnynta a hoto, da sauri ta koma jikin daddy tana tambayarsa ya akayi take kama da mummynta kuma.
Daddy bai san time ɗin da ya ce mata "kanwar mummyn ki ce ai". Imran yana ƙoƙarin gaya mata ita ce matar daddy, daddy ya yi saurin dakatar da shi domin kuwa yasan a yanzu dai jelly ba zata taɓa yarda da Ayla matarsa ba, for now dai a barta a kanwar mummyn kawai zai fi, sai ta kara hankali idan ta je gidan mijinta, idan ba haka ba yanzu zata yi masu karamin hauka.
Suna a haka wayar Imran ta fara kara, hannu yasa a aljihun nasa ya ciro wayar, Nawid ne yake kiransa, picking ya yi tare da manna wayar a kunnensa.
Maganar minti 5 suka yi, sannan Imran ya ce sai kun zo, daga nan suka yi sallama, hakan kuma ya yi daidai da danno hancin motar Akil cikin gidan.
Zama Imran ya koma ya yi a saman sofa, ita kuma Jelly tuni ta rungumi Ayla sun fara hira a matsayin kanwar mummynta, dama ta jima tana cewa daddy ya kai ta wajen ƴan uwan mumnynta ko kuma ya kawo mata su gida ta gansu, amma kullun sai ya rinƙa ce mata zai yi zai yi amma bai taɓa yi ɗin ba, sai ga shi yau ta ga kanwar mummyn nata ai farinciki ba'a magana, har da rungumar Ayla ta yi suna ta hira.
A haka Akil ya shigo ya same su, tare da Akila, Umaisha da kuma A'afia suke tafe, duk ya haɗo kansu dan su zo su sake kulla zumunci.
Sai murna suke yi kamar me, daddy ne ya ce da Akila ta tashi ta je ta ɗauko mashi kuɗi a cikin drawer mirror a ɗakinsa ta kawo mashi, to ta amsa mashi da shi tare da miƙe wa da sauri ta nufi waje.
Tana shiga palon suka ci karo da Irfan zai fito, cikin sauri ta yi baya zata faɗi, yana ƙoƙarin riƙota ta kauce mashi ta faɗi kasa, bata son ya taɓa ta dan kada ɓoyayyen masoyi ya ɓata rai.
Yadda ta kauce mashin ba ƙaramin mamaki ta ba shi ba, amma kuma bai kawo komai a ransa ba ya duka yana son ɗagota tare da yi mata sannu, kin yarda ya ɗagota ta yi, nan ta ce mashi a'a ya bari zata tashi, bai damu ba dan shima dama ba wani son cika taɓa jikinta ya yi ba, dan tsaro.
Bayan ta miƙe suka gaisa ya tambayeta yaushe suka zo, nan ta gaya mashi yanzun nan kuma daddy ne ya aiketa su Imran suna palo, da Muryarsa ya ce to ta ɗauko saƙon daddyn sai su wuce zuwa cikin gidan tare, to ta amsa da shi sannan ta wuce zuwa bedroom ɗin na daddy tare da taimakonsa wajen nuna mata bedroom ɗin.
Kuɗi ta ɗauko mashi wadda a kalla zasu iya kai 500k, Irfan na tsaye har ta fito suka jera zuwa cikkn gida.
Kamar yadda ta barsu haka ta shigo ta same su, sai hira ake zubawa kamar ba gobe, miƙawa daddy kuɗin ta zo ta yi tana faɗin "ga shi nan bappa".
Karɓa daddy ya yi tare da miƙawa Abbi ya ce ga sadakin Jelly, a matsayinsa na waliyin Imran, yana neman alfarmar da a ɗaura auren nan yanzu, Allah sarki kuruci dangin hauka, jin hakan yasa jelly ta rungume shi tana dariya tana faɗin zata zama matar yaya Imran, zata zama matar yaya Imran, shi kuwa Imran kasa da kansa ya yi duk kunya ta rufe shi, nan take Akil da Irfan suka fara tsokanarsa, aunty ce ta ce da Jelly ta ta so ta zo su ɗan yi magana.
To jelly ta amsa da shi tare da tashi ta je, har ga Allah duk wanda ya zauna da Aunty dole zata shiga ransa domin tana da halayya masu kyau, kowa ya zo gidan ita yake so ba Ommu ba, tana da tarin masoya ciki kuma har da ƴaƴan Ommu ɗin, domin Irfan yana kaunarta sosai saboda kirkinta, haka su Aafia ma, suna sonta, kowa nata ne bata da mugunta ko kaɗan.
Miƙewa Abbi ya yi ya ce su je waje bari ya kira makwabtansa sai a ɗaura auren. A tare gaba ɗaya mazan suka fita, su kuma matan suka cigaba da hira Aunty tana yiwa Jelly nasiha akan ta natsu, tare da kara mata haske a kan abubuwa.
Mu koma baya kaɗan, lokacin da daddyn Jelly ya ce su haura sama, time da Ommu take yi masu rashin mutunci, da suka shiga aunty ta kalli jini a jikin jelly hakan yasa ta saka jelly ta shiga toilet ta wanke jikinta ta bata sabon pant da kuma always ta saka, wannan dalilin yasa jelly ta fara kaunar Aunty, saboda kirkinta, bata share mutane. Bayan ta saka always ɗin Aunty ta kara bata doguwar rigarta ta sanya a jikin ta, wannan shine abin da ya faru bayan shigarsu ɗaki. MU KOMA IN DA MUKE A STORY.
Suna tsaka da hira aka sako waƙar bodyguard na Salman Khan a Tv, a ɗari Jelly ta miƙe tare da kure Volume na Tv ta fara tikar rawa.
Sai murmushi kowa yake yi yana kallonta, jawo hannun Rismha ta yi akan ta taso su yi, ai kuwa Rimsha bata ki ba suka shiga yin rawa a tare, sake jawo hannun Ayla ta yi, nan fa ita kuma Ayla ta saka kuka dan ba zata iya ba, jelly a tunaninta dan bata so ne yasa take kuka saboda idan baku mance ba halin jelly ɗin ce, idan bata son abu sai ta kama kuka, to tana tunanin kamar kowa ma haka ne, shiyasa sai ta kyale Ayla ɗin kawai suka cigaba da rawa da Rimsha, miƙewa ita ma Akila ta yi suka fara takawa a tare, da kaɗan da kaɗan Umaisha ma ta bi bayansu suka bar Aafia, Hanan da kuma Ayla sai Aunty, sun zuba masu idanu suna kallon yadda suke taka rawa kamar ba gobe, abin ba ƙaramin ƙayatarwa ya yi ba. HAPPINESS IS FREE.
A can waje kuma ana famar ɗaura aure.
After some minutes.
Bayan an ɗaura aure an dawo a palo suka sake ba je wa, Imran, Akil ba wanda ya tuna da Ammie zata karɓi wannan aure ne ko ba zata karɓa ba, sannan idan baku mance ba, jelly tun kafin ta san waye Hajiya Umaiya ta nuna bata son ta, idan baku mance ba bakar muguwa munafuka take kiran Hajiya Umaiya, ya kuke tunanin wannan zama zata kasan ce? Anya Ammie zata karɓi Jelly kuwa?. Ko dai zata gasa jelly kamar yadda ta gasa Umaisha? Mu dai je zuwa.
Sai murna suke yi, duk fuskar wadda ka kalla a cikin palon nan zaka kalli tsantsan farinciki a tattare da shi.
A wanann halin su Nawid suka iso suka same su, shi da Umminsa da kuma Hajiya Batula.
Abin da ya faru a gida bayan komar Nawid da ya kawo wa Imran Jelly shine, da ya koma bai sami Abbo a gidan ba, abin ya ɗaure mashi kai, kwata kwata babu Abbo babu alamar sa, kuma ga kofar ɗakin a rufe kamar yadda ya rufe Abbo ɗin, shi ne da ya dawo ya buɗe kofar, to ta ina Abbo ya fita?.
Ransa cike da tunani tare da mamaki ya kwanta kawai, amma ya kasa yin barci har wayewan gari.
Da gari ya waye ne Ummi ta tambayi ina baby, sai ya ce tana gidansu Abokinsa, bai gaya mata me ya faru, me Abbo ya aikata ba, ya rufe abin shi kaɗai domin bai kawo a ransa cewa tsafi Abbo zai yi da jelly ba, ya yi tunanin raping ɗin ta kawai zai yi, shiyasa ya rufe maganar dan a cewarsa abin kunya ne ya faɗi hakan, ya rufawa mahaifinsa asiri.
Nan fa Ummi ta fara faɗa akan me zai ɗauki baby ya kaita wani waje, ita ba ta yarda ba sai dai su je gidansu abokin a tare, hakuri ya rinƙa bata akan bari ya je ya ɗauko babyn, ina ta ki yarda ta ce sai dai su tafi tare, haka kuwa akayi shine suka taho tare, shi kuma Abbo shiru ba labarinsa, Allah kaɗai ya san ina ya tafi, ita ma Ummi bata neme shi ba, saboda ana hidimar biki tasan ba zama yake yi a gidan ba.
STORY💖
Hannu Nawid ya miƙawa dukka mazan cikin palon, ɗaya bayan ɗaya suka gaisa, su kuma matan suka gaisa da baki, ya sha mamakin ganin jelly a jikin daddy, kamar zai magana sai kuma dai ya danne ya yi shiru, ita ma Ummi gaisawa suka yi da mutanen cikin Palon, ita kuma Hajiya Batula mamakin ganin su daddyn Jelly ya hana ta magana, shima daddyn ido kawai ya bita da shi dan bai san me zai ce mata ba, Abbi ne kawai ya ce "Batula dama kin san hanyar gidana? Kin san in da nake shine baki taɓa zuwa ba?".
Shiru ta yi ta kasa magana, abubuwan da suka faru a baya ne kawai suka fara dawo mata a cikin ƙwaƙwalwarta. Hannu Abbi ya sa ya nuna mata sofa akan ta zauna, ba musu ta zauna gaba ɗaya palon suka yi shiru.
Ummi ne ta katse masu shirun da cewa "Baby kin san shine da kika zauna a jikinsa?" Ta yi maganar tana kallon daddy da jelly ke a jikinsa, Jelly kam ko kallon in da take ma bata yi ba, domin bata sansu ba.
Imran ne ya ce "Ummi babanta ne ai". A razane suka miƙe a tare ita da Nawid, kallon juna suka yi kafin su sake kallon Imran ɗin. Abbi ne ya ce masu su zauna sai ayi magana a nutse, ba musu suka zauna, Imran Abbi ya fara tambaya akan me ya faru a ina kanwar Hadiza wato
Showing 312001 words to 315000 words out of 344390 words
Sakin Jelly daddy ya yi yana faɗin "Rimsha ku je sama wajen Hanan ko, babyn daddy ta shi ku je ko?".
To suka amsa da shi, da kyar Ayla ta miƙe, da sauri Aunty ta zo ta dafa mata suka wuce sama, domin ita ma Aunty bata son tsayawa a wajen dan bata ma son jin hayaniyar tasu.
Dawo da kallonsa a kanta daddy ya yi tare da ɗaure fuska nan yau shima ransa ya yi mugun ɓaci, yau karo na biyu kenan da take cin mutuncin su a gaban ƴaƴansu to gaskiyar Imran ne yana da kyau su taka mata birki domin iskancin nata ya fara wuce misali.
"Hadiza ina ganin mutunci ki ne nima dan saboda Irfan, yaron kirki, Allah ya rufa mishi asiri ba ke kika raine shi ba, wlh nasan da ke kika ba su tarbiya ƴaran nan da sai sun zama kannen sheɗanu, yanzu ke ba abin kunya bane ma ki ɗauko kafar ki da sunan wai kin dawo gidan nan? Wlh ta bakin Imran kin yi babbar sa'ar Akil aure ta sauya shi, ba dan haka ba ko yaya suke da Irfan sai ya dalla maki mari, idan ma baki yi sa'a ba sai kin wuce gadon asibiti, yanzu tsabar rashin kunya ƴaƴan yaya babban ne talakawa? Ke kin sani a gaba ɗaya cikin mu a tsabar kuɗi dai daga Hosain sai Yaya babba wato Abban su Imran, ko dai dama baki san su Imran ƴaƴan yaya babba bane? To idan baki sani ba yanzu ki sani Akil kawai zai iya sayan Familynku baki ɗaya, sannan bugu da kari ƴaƴan Umaiya ce wadda ta ma fi yaya babba kuɗi, kuma ke kin sani ko ada baya da yaya ki ka kwaci kanki a hannun Umaiya? To ki sani barewa ba zata yi gudu ɗan ta ya yi rarrafe ba, tun wuri ki fita har karmu idan ba haka ba zaki yi dana sani, yadda ki ka san Umaiya a da to yanzu Akil ne photo copyn ta, shiyasa ki ka ji munce maki kin ciri tuta tun da har Akil ya iya danne zuciya ya kyaleki!!!".
Cikin sauri Ommu ta ce "Yanzu kenan Umaisha ɗan gidan Yaya babban ta aura?".
Ba wanda ya tanka mata a cikinsu, cikin zumuɗi ta ce "Kai amma Alhadulillah da ya kasance ba ƴaƴan Matsiyata ƴar cikina ta aura ba, kai abin ya min daɗi". Tana gama magana ta juyawa ta nufi sama, sai daɗi take ji.
Girgiza kai daddy ya yi tare da komawa ya zauna a saman sofa, shima Abbi zama ya yi a saman sofa yana mamakin hali irin na Aunty, Baiwar Allah mace mai sanin Yakamata, bata son hayaniya, mafi yawancin mata suna son su ga ana ci wa kishiyarsu mutunci amma ban da Aunty, da zarar sun fara faɗa zata wuce ɗakinta dan ma kada ta ga abin da yake faruwa, bata son hayaniya kuma bata son abin haushi, tana da zuciya mai kyau sosai, har cikin ransa yau Abbi ya ji wani irin mugun daɗi abin da Aunty ta aikata, ta san abin da take yi.
Shi kuma Imran sama ya haura domin ya je ya kira su jelly.
Jim kaɗan sai ga Ommu ta fito riƙe da wayarta ta canza shiga zuwa doguwar riga, da alama ya fasa fitan kenan.
Kusa da Abbi ta zo ta tsaya tare da miƙa mashi wayarta tana faɗin "Saka Mani number Umaisha ko kuma na mijinta a nan bari na kira shi ya kawo mani ita yanzun nan zan yi magana da ita".
Kallon daddyn Jelly Abbi ya yi, mamaki ya hana su magana, tun da ta dawo bata nemi yaran ba sai da ta ji Umaisha na auren Akil sannan ne zata ne me su dan ta ji ruwan kuɗi.
Sosai daddy yake addu'ar kada ta lalatawa yaran nan aurensu, dan yasan halinta sarai, zata iya kai Umaisha ta barota, kuma kun san tsakanin uwa da ƴa, sannan Ommu ba ruwanta da wai ƴar cikinta ce, idan bukatar ta ya biya shikenan ai.
Ƙin saka mata number Abbi ya yi, ya ce bashi da shi, ba dan ta so ba ta hakura ta koma sama tana tunanin yadda zata yi.
Tana komawa ba jimawa sai ga su Imran sun sauƙo kasa, jelly ta canza kaya zuwa doguwar riga ash color, shi kuma Imran yana manne da waya a kunne yana magana da Akil akan su zo gidan Abbi yanzu an gane Jelly.
Aunty na rungume da Ayla suka sauƙo kasa. Jikin daddy jelly ta je ta haye tana zuba mashi shagwaɓa akan tana kewarsa, da hannu ya yi wa Ayla alama akan ta zo ita ma, ba musu ta je dan dama bata taɓa yin musu da shi ba.
Ta gefen jikinsa ya jawota yana faɗin "Babyn daddy wannan ita ce Jelly" jin abin da daddy ya ce yasa Jelly ta yi saurin ɗago kai tana maimaita sunnan da daddy ya kira Ayla da shi.
Kamar wadda aka yi wa allura haka Jelly ta diro kasa ta yi zaman ƴan bori a tsakiyar carpet ɗin tare da fara wuwwurga kafafu a kasa tana ihu kamar ba lafiya ba, daddy ya san me take yi wa ihu, wato dan ya kira Ayla da babyn daddy shi ne take kuka, sunan babyn daddy sunan Jelly ɗin ne da yake kiranta da shi lokacin suna Kano.
Imran ne ya yi saurin marisowa wajenta tare da riƙota yana faɗin "Jelly menene?".
Cikin kuka ta ce "Yaya Imran daddy fa yanzu ya daina so na, kana ganin wata babyn ya samu". Babbar magana wai ɗan sanda ya ga gawar soja, dama shi daddy already yasan za'ayi hakan, yasan ba zata taɓa yarda da Ayla ba, shiyasa ya ce tana dawowa za'a ɗaura mata aure da Imran kowa ma ya huta.
Cikin sigar rarrashi Imran ya ce "Jelly wannan fa mummynki ce ba wai wata ba, mummy zaki ce mata".
Cak ta tsaya da kukan nata tare da ɗago idanu da sauri ta sauƙe akan Ayla ɗin. Kallon minti ɗaya ta yi mata kafin kuma ta kwashe da dariya kamar wata zautatciya, daddy kam ko ajikinsa dan ya san halin kayarsa, in dai jelly ce to fin hakan ma zata yi, sai ta sa ka ka yi tunanin ko kaine mahaukaci, wlh tsab jelly zata sanya ka fara tunanin anya kana lafiya kuwa? Anya kai ba mahaukaci bane kuwa?.
Shi kuwa Imran da yake har yanzu yana da sauran karatu akanta sai ya ce "Jelly lafiya kike dariya kuma?" Kara sautin dariyar tata ta yi har da rike ciki, kamar ba ita ba ce mai yin kuka yanzun nan.
Sai da ta yi dariyarta mai isarta sannan ta ce "Amma yaya Imran a sanina dai kafin mu zo nan lafiya lou kake, ya akayi kuma yanzu ka canza kamar mara lafiya?" Ɗan kallon kansa ya yi dan ko zai ga abin da ta gani a tattare da shi da ta ce mashi ba shi da lafiya.
Shikam daddy a zuciyarsa cewa ya yi kaɗan ka gani Imran ba dai jelly ba, wata rana sai ta sanya ka tuɓe wando a cikin jama'a, Abbi kuwa ban da murmushi ba abin da yake yi, ita kuwa Aunty yau ta ga duniya a wajen jelly, ta ga abin mamaki, Rimsha kam ko a jikinta, Hanan ce ma ta ɗan tsorata da ganin abin da jellyn take yi.
"Jelly wai me yake faruwa ne?" Cewar Imran, cikin dariya ta ce "Yaya Imran wannan ƴar karamar yarinyar da bata wuce na kamata na haɗiyeta na kora ruwa bace mummyna? Wai ka manta mummyna ta rasu ne? To idan ka manta na tuna maka, mummyna bata nan wannan kuma ai ko mai....." Bata karasa ba ta ja birki sakamakon karewa fuskar Ayla kallo da take yi.
Zubur ta miƙe tana faɗin "Ya na kalli tana kama da mumnyn kuma?" Da yake ta san fuskar mumnynta a hoto, da sauri ta koma jikin daddy tana tambayarsa ya akayi take kama da mummynta kuma.
Daddy bai san time ɗin da ya ce mata "kanwar mummyn ki ce ai". Imran yana ƙoƙarin gaya mata ita ce matar daddy, daddy ya yi saurin dakatar da shi domin kuwa yasan a yanzu dai jelly ba zata taɓa yarda da Ayla matarsa ba, for now dai a barta a kanwar mummyn kawai zai fi, sai ta kara hankali idan ta je gidan mijinta, idan ba haka ba yanzu zata yi masu karamin hauka.
Suna a haka wayar Imran ta fara kara, hannu yasa a aljihun nasa ya ciro wayar, Nawid ne yake kiransa, picking ya yi tare da manna wayar a kunnensa.
Maganar minti 5 suka yi, sannan Imran ya ce sai kun zo, daga nan suka yi sallama, hakan kuma ya yi daidai da danno hancin motar Akil cikin gidan.
Zama Imran ya koma ya yi a saman sofa, ita kuma Jelly tuni ta rungumi Ayla sun fara hira a matsayin kanwar mummynta, dama ta jima tana cewa daddy ya kai ta wajen ƴan uwan mumnynta ko kuma ya kawo mata su gida ta gansu, amma kullun sai ya rinƙa ce mata zai yi zai yi amma bai taɓa yi ɗin ba, sai ga shi yau ta ga kanwar mummyn nata ai farinciki ba'a magana, har da rungumar Ayla ta yi suna ta hira.
A haka Akil ya shigo ya same su, tare da Akila, Umaisha da kuma A'afia suke tafe, duk ya haɗo kansu dan su zo su sake kulla zumunci.
Sai murna suke yi kamar me, daddy ne ya ce da Akila ta tashi ta je ta ɗauko mashi kuɗi a cikin drawer mirror a ɗakinsa ta kawo mashi, to ta amsa mashi da shi tare da miƙe wa da sauri ta nufi waje.
Tana shiga palon suka ci karo da Irfan zai fito, cikin sauri ta yi baya zata faɗi, yana ƙoƙarin riƙota ta kauce mashi ta faɗi kasa, bata son ya taɓa ta dan kada ɓoyayyen masoyi ya ɓata rai.
Yadda ta kauce mashin ba ƙaramin mamaki ta ba shi ba, amma kuma bai kawo komai a ransa ba ya duka yana son ɗagota tare da yi mata sannu, kin yarda ya ɗagota ta yi, nan ta ce mashi a'a ya bari zata tashi, bai damu ba dan shima dama ba wani son cika taɓa jikinta ya yi ba, dan tsaro.
Bayan ta miƙe suka gaisa ya tambayeta yaushe suka zo, nan ta gaya mashi yanzun nan kuma daddy ne ya aiketa su Imran suna palo, da Muryarsa ya ce to ta ɗauko saƙon daddyn sai su wuce zuwa cikin gidan tare, to ta amsa da shi sannan ta wuce zuwa bedroom ɗin na daddy tare da taimakonsa wajen nuna mata bedroom ɗin.
Kuɗi ta ɗauko mashi wadda a kalla zasu iya kai 500k, Irfan na tsaye har ta fito suka jera zuwa cikkn gida.
Kamar yadda ta barsu haka ta shigo ta same su, sai hira ake zubawa kamar ba gobe, miƙawa daddy kuɗin ta zo ta yi tana faɗin "ga shi nan bappa".
Karɓa daddy ya yi tare da miƙawa Abbi ya ce ga sadakin Jelly, a matsayinsa na waliyin Imran, yana neman alfarmar da a ɗaura auren nan yanzu, Allah sarki kuruci dangin hauka, jin hakan yasa jelly ta rungume shi tana dariya tana faɗin zata zama matar yaya Imran, zata zama matar yaya Imran, shi kuwa Imran kasa da kansa ya yi duk kunya ta rufe shi, nan take Akil da Irfan suka fara tsokanarsa, aunty ce ta ce da Jelly ta ta so ta zo su ɗan yi magana.
To jelly ta amsa da shi tare da tashi ta je, har ga Allah duk wanda ya zauna da Aunty dole zata shiga ransa domin tana da halayya masu kyau, kowa ya zo gidan ita yake so ba Ommu ba, tana da tarin masoya ciki kuma har da ƴaƴan Ommu ɗin, domin Irfan yana kaunarta sosai saboda kirkinta, haka su Aafia ma, suna sonta, kowa nata ne bata da mugunta ko kaɗan.
Miƙewa Abbi ya yi ya ce su je waje bari ya kira makwabtansa sai a ɗaura auren. A tare gaba ɗaya mazan suka fita, su kuma matan suka cigaba da hira Aunty tana yiwa Jelly nasiha akan ta natsu, tare da kara mata haske a kan abubuwa.
Mu koma baya kaɗan, lokacin da daddyn Jelly ya ce su haura sama, time da Ommu take yi masu rashin mutunci, da suka shiga aunty ta kalli jini a jikin jelly hakan yasa ta saka jelly ta shiga toilet ta wanke jikinta ta bata sabon pant da kuma always ta saka, wannan dalilin yasa jelly ta fara kaunar Aunty, saboda kirkinta, bata share mutane. Bayan ta saka always ɗin Aunty ta kara bata doguwar rigarta ta sanya a jikin ta, wannan shine abin da ya faru bayan shigarsu ɗaki. MU KOMA IN DA MUKE A STORY.
Suna tsaka da hira aka sako waƙar bodyguard na Salman Khan a Tv, a ɗari Jelly ta miƙe tare da kure Volume na Tv ta fara tikar rawa.
Sai murmushi kowa yake yi yana kallonta, jawo hannun Rismha ta yi akan ta taso su yi, ai kuwa Rimsha bata ki ba suka shiga yin rawa a tare, sake jawo hannun Ayla ta yi, nan fa ita kuma Ayla ta saka kuka dan ba zata iya ba, jelly a tunaninta dan bata so ne yasa take kuka saboda idan baku mance ba halin jelly ɗin ce, idan bata son abu sai ta kama kuka, to tana tunanin kamar kowa ma haka ne, shiyasa sai ta kyale Ayla ɗin kawai suka cigaba da rawa da Rimsha, miƙewa ita ma Akila ta yi suka fara takawa a tare, da kaɗan da kaɗan Umaisha ma ta bi bayansu suka bar Aafia, Hanan da kuma Ayla sai Aunty, sun zuba masu idanu suna kallon yadda suke taka rawa kamar ba gobe, abin ba ƙaramin ƙayatarwa ya yi ba. HAPPINESS IS FREE.
A can waje kuma ana famar ɗaura aure.
After some minutes.
Bayan an ɗaura aure an dawo a palo suka sake ba je wa, Imran, Akil ba wanda ya tuna da Ammie zata karɓi wannan aure ne ko ba zata karɓa ba, sannan idan baku mance ba, jelly tun kafin ta san waye Hajiya Umaiya ta nuna bata son ta, idan baku mance ba bakar muguwa munafuka take kiran Hajiya Umaiya, ya kuke tunanin wannan zama zata kasan ce? Anya Ammie zata karɓi Jelly kuwa?. Ko dai zata gasa jelly kamar yadda ta gasa Umaisha? Mu dai je zuwa.
Sai murna suke yi, duk fuskar wadda ka kalla a cikin palon nan zaka kalli tsantsan farinciki a tattare da shi.
A wanann halin su Nawid suka iso suka same su, shi da Umminsa da kuma Hajiya Batula.
Abin da ya faru a gida bayan komar Nawid da ya kawo wa Imran Jelly shine, da ya koma bai sami Abbo a gidan ba, abin ya ɗaure mashi kai, kwata kwata babu Abbo babu alamar sa, kuma ga kofar ɗakin a rufe kamar yadda ya rufe Abbo ɗin, shi ne da ya dawo ya buɗe kofar, to ta ina Abbo ya fita?.
Ransa cike da tunani tare da mamaki ya kwanta kawai, amma ya kasa yin barci har wayewan gari.
Da gari ya waye ne Ummi ta tambayi ina baby, sai ya ce tana gidansu Abokinsa, bai gaya mata me ya faru, me Abbo ya aikata ba, ya rufe abin shi kaɗai domin bai kawo a ransa cewa tsafi Abbo zai yi da jelly ba, ya yi tunanin raping ɗin ta kawai zai yi, shiyasa ya rufe maganar dan a cewarsa abin kunya ne ya faɗi hakan, ya rufawa mahaifinsa asiri.
Nan fa Ummi ta fara faɗa akan me zai ɗauki baby ya kaita wani waje, ita ba ta yarda ba sai dai su je gidansu abokin a tare, hakuri ya rinƙa bata akan bari ya je ya ɗauko babyn, ina ta ki yarda ta ce sai dai su tafi tare, haka kuwa akayi shine suka taho tare, shi kuma Abbo shiru ba labarinsa, Allah kaɗai ya san ina ya tafi, ita ma Ummi bata neme shi ba, saboda ana hidimar biki tasan ba zama yake yi a gidan ba.
STORY💖
Hannu Nawid ya miƙawa dukka mazan cikin palon, ɗaya bayan ɗaya suka gaisa, su kuma matan suka gaisa da baki, ya sha mamakin ganin jelly a jikin daddy, kamar zai magana sai kuma dai ya danne ya yi shiru, ita ma Ummi gaisawa suka yi da mutanen cikin Palon, ita kuma Hajiya Batula mamakin ganin su daddyn Jelly ya hana ta magana, shima daddyn ido kawai ya bita da shi dan bai san me zai ce mata ba, Abbi ne kawai ya ce "Batula dama kin san hanyar gidana? Kin san in da nake shine baki taɓa zuwa ba?".
Shiru ta yi ta kasa magana, abubuwan da suka faru a baya ne kawai suka fara dawo mata a cikin ƙwaƙwalwarta. Hannu Abbi ya sa ya nuna mata sofa akan ta zauna, ba musu ta zauna gaba ɗaya palon suka yi shiru.
Ummi ne ta katse masu shirun da cewa "Baby kin san shine da kika zauna a jikinsa?" Ta yi maganar tana kallon daddy da jelly ke a jikinsa, Jelly kam ko kallon in da take ma bata yi ba, domin bata sansu ba.
Imran ne ya ce "Ummi babanta ne ai". A razane suka miƙe a tare ita da Nawid, kallon juna suka yi kafin su sake kallon Imran ɗin. Abbi ne ya ce masu su zauna sai ayi magana a nutse, ba musu suka zauna, Imran Abbi ya fara tambaya akan me ya faru a ina kanwar Hadiza wato
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105 Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115