zaune a wajen tana tunani har su Kausar suka dawo ƙarfe 6:30pm daidai su ka shigo cikin gidan daga tallan kifi.
Da sauri Rimsha ta miƙe ta rungumo Ayla tana son faɗa mata cewa Malika aljana ce, sai kuma ta kasa, ga dai maganar a bakin ta, amma ta kasa faɗe. Haka ta hakura suka yi alwala dan lokacin sallar mangariba ya yi.
Sai bayan sun yi sallah mangariba da issha ne suka zauna a palo suna hira. Miƙe wa Rimsha ta yi ta shiga kitchen wajen Iya, dan taya ta girki.
Yau tuwon semo da miyar Egusi Iya da Rimsha suka yi. Sai karfe 9 na dare suka kammala girkin suka dawo palo suka baje, suka fara cin abinci, suna ci suna hira, ita kuma Kausar tana ci tana haɗa zufa, don ba ta magana kam sai dai kai loma.
Suna tsaka da cin abincin ne boda Jami'u da boda Kabiru suka dawo. Da gudu Kausar ta tashi ta nufe su, tana ta washe baki. Tsalle tayi ta haye jikin boda Jami'u, ɗaga ta ya yi sama kamar yar baby, duk wannan kiba na Kausar bai hana shi ya iya ɗaga ta ba, dan Jami'u irin mazan nan masu tsawo da ƙiba, ga shi da kiran karfi.
Ihu ne ya kaure a gidan, na karti wato boda Jamiyu da boda Kabiru, don ba su san kanwarsu kuma yar autarsu ta dawo ba. Shi boda Jamiyu ɗa ne ga yayan baban Kausar kuma shi yake son Kausar ɗin ma'ana saurayinta ke nan. Ihu suke kamar ba lafiya ba, wai a haka murna suke nunawa, miƙewa Iya ta yi ta fara taya su. Bayin Allah Rimsha da Ayla suna ganin ikon Allah iya ganin idonsu a kasar Yarabawa, wani lokaci ma har tunani suke anya Iya ba ta samu matsala a ƙwaƙwalwarta ba kuwa mata ce wani lokaci bata da setti ko kaɗan.
Haka suka yi ta ihun nuna murnarsu na wani lokaci kafin nan su tsagaita, Jami'u ya sauƙe Kausar kasa daga jikin sa, sai dariya suke.
Daga Jami'u har Kabiru sun yi shocked da ganin su Rimsha, sai kallon Rimsha suke, dan akwai wutar nepa, haske ya karaɗe palon gabaɗaya hakan ya sa suka samu daman ganin Ayla da Rimsha sosai.
Jami'u ya kasa hakuri har sai da ya tambayi daga ina Rimsha take, nan fa Kausar ta fara basu labarin irin wahalar da suka sha tun shigar su daular Mutuwa har fitowar su. Sosai su Jami'u suka tausaya musu. Hannu ya kai zai shafi kan Rimsha, cikin sauri ta ɗan ja baya, yar dariya ya yi kafin ya ce "As from today you are my sister, so kada ki damu, na san halin ku Hausawa baku son a rinƙa taɓaku sai ku rinƙa avoiding na mutane, kamar ba ku da gaskiya." cikin harshen Turanci ya yi maganar. Shiru Rimsha ta masa, dan ita gaba ɗaya ma haushi suka bata, jibi yadda yake wani rungume Kausar dan iskanci kuma yasan akwai aure a tsakanin su. A ɓangaren Ayla ma ba karamin haushin abin ta ji ba, wasu karti da su ba kyan gani, ga shi dukansu sun wani saka gajeren wando zuwa guiwa da riga mai karamin hannu.
Shi kam Kabiru sai kallon Rimsha yake ya kasa dai'na wa, haka shi ma Jamiyu, sai dai shi Jamiyu satar kallon ta yake dan kada Iya ko Kausar su gane yana kallon nata.
Yanzu su ma a nan gidan za su kwana, Rimsha da Ayla suka yi wa kansu tambayar a tare a cikin zuciyoyinsu kamar abin haɗin baki, sai dai kuma ba su da amsar tambayar tasu.
Haka suka zauna a palon tare da su Jami'u, Rimsha kamar za ta yi kuka dan haushin zama da karti, haka ita ma Ayla. Ita kuwa Kausar sai faman wage hakwara take tana dariya kamar wata yar fari, sai murna take, ta wani zauna kusa da Jami'u suna kallon Yoruba film, ita kuma Iya ta ɓige da barci kwance saman sofa.
Sai misalin 11 na dare sannan su Jami'u suka wuce ɗakin su, wanda ya kasance kusa da ɗakin Iya ne, duk dai cikin rufi ɗaya. Tsoro sosai Rimsha ta ji lokacin da taga cewa a nan gidan su Jami'u za su kwana, ga shi ta lura da irin kallon ta da suka rinƙa yi mata.
Haka cike da tsoro suma suka wuce na su ɗakin, bayan Kausar ta tashi Iya daga barci, Iya ce ta kulle kofar falon da key da kuma sakata, sannan ta wuce ɗakinta ita ma. Rimsha dai ta tsorata sosai, gani take kamar za su zo su kama ta, shiyasa da suka shiga ɗaki ta riga su hayewa gado, ta tafi can karshen gado ta kwanta ta manne da bango, Ayla ce ta kwanta kusa da ita, sai Kausar a karshen gadon
To Rimsha mu Sarkin tsoro sai dai mu ce Allah ya tsare, na yi nan sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu.
Sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu
[11/11, 8:52 PM] +234 906 579 6460: 💞💞TRIPLET'S💞💞
🌹🌹Episode 13-14🌹🌹
A ɓangaren Ummi kuwa ƙara zaro ido waje ta yi ta ce "Abbo mene ne ya sa ba ka son haɗin?" A takaice ya ce "Saboda tsintaciyar mage ce, ba mu san asalinta ba." Ayya Jelly baiwar Allah tana can duniyar kaza ba ta tare da su, ba ta san wainar da ake toyawa ba.
"A'a Abbon Nawid kada mu yi haka da kai, idan muka ce don ba ta da asali ba za mu ba ta ɗanmu ba, to waye kake tun nin zai aure ta? Mu da muka san komai ma mun ki yarda, to waye kake tunani zai so ta, kuma ma ai yanzu mun zama mu ne asalinta iyayenta komai nata." Ɗaure fuska sosai Abbo ya yi kamar da gaske yana son hana Nawid ne don baby ba ta da asali, alhalin kuma kansa yake gyarawa hanya, yana son ya rushe maganar Nawid ne don ya gina tasa, wannan ita ce cakwakiya.
"Ummin Nawid na gama magana, ɗana yaro ne mai asali, don haka ba zai auri wadda ba ta da asali ba." Ya kai karshen maganar tare da cire hannunsa daga abincin ya miƙe ya bar wajen, cike da ɓacin rai a zahiri, amma cikin ransa kuma farinciki kamar ya zuba ruwa a kasa ya sha.
Sosai Ummi ta ji babu daɗi, kuma ta kudure a ranta sai Nawid ya auri Jelly don ita ce zaɓinta, ba ta son Nawid da kowace mace fa ce Jelly, ko me zai faru sai dai ya faru, ɓera ya ɓarar da garin kyanwa. Nawid, Jelly zai aura. Rai a matukar ɓace ita ma ta miƙe ta nufi bedroom nata, yau ranta ya ɓaci sosai ba za ta je wajen Abbo ɗin ba, kwanciya ta yi a ɗakinta.
Shi ma Nawid ganin iyayen nasa sun tafi ya sa ya miƙe ya nufi ɗakinsa, ransa fes sai wani murmushi yake saki, Abbonsa ya rushe maganar aurensa da mahaukaciya a cewarsa. Ita kuwa Jelly sai faman cin naman kaza take, kwatakwata ma ba ta san me suke tattaunawa a kanta ba, tana dai jin zancen nasu sama sama haka yana bi ta gefen kunnenta.
Sai da ta cinye kaza guda tas, ko kaɗan ba ta rage ba, kamar wata mai aljanun cin nama. Bayan ta kammala sai ta miƙe ta wuce bedroom nata tana lashe baki kamar wata tsohuwar mayya. Tana shiga ta haye saman gadonta tana sauke ajiyar zuciya, yau ko kayan barci ba ta samu sawa ba, don da ma Ummi ke saka mata kayan barci yau kuma ran Ummi a ɓace yake.
Abbo da Ummi ransu a ɓace barci ya yi awon gaba da su, Nawid kuwa farinciki cike fal ransa ya yi barci. A gefen ita ma Jelly da yake ba ta san me aka kulla ba, sai ta yi barcinta cikin kwanciyar hankali.
A ɓangaren Umaisha kuma, bayan sun ɗan yi shiru na yan mintuna ne, Umaisha ta katse musu shirun da cewa, "Yaya Akil don Allah gobe ka ɗauko Aunty Afi ta zo ta mana kwana biyu ka ji?" Shafa kanta ya yi kafin ya ce "To, na ji kuma zan je na ɗauko ta." Wani daɗi Umaisha ta ji ya rufe ta, da ƙarfi ta matse shi a jikinta, tana murna. "Za ki ɓalla ni ko?" Ya tambaya yana tsare ta da ido, dariya cikin hawaye ta yi tana faɗin, "Kai yaya Akil ni na isa na ɓalla ka ne?" Shiru ya mata don shi ma ba mai son yawan Magana ba ne. Haka suka yi shiru, ta yi luf a jikinsa har barci ya ɗauke ta, shi kuma sai faman kallon fuskarta yake yi.
Mu koma wajen Rimsha.
Bayan sun gama girki ita da Iya, ta fito ta shige cikin bandaki ta sake yin wanka abinta, don Rimsha akwai ta da bala'i son tsafta sosai, ba ta son datti ko kaɗan.
Bayan ta yi wanka ta sake shiryawa cikin wata doguwar riga ta Kausar, ta fito falo, nan ta samu Kausar da Ayla suna cin abinci, amma kowa kwanonsa daban, ma'ana daban-daban Iya ta saka musu abincin. Kusa da su ta zo ta zauna, Ayla ce ta jawo wani kwano da ke rufe a gefen su ta miƙa mata tana faɗin, "Ga naki abincin." Karɓa ta yi ta fara ci tana jin daɗi yau ta iya yadda ake yin miyar Steew da shinkafa.
Suna tsaka da cin abincin ruwan sama mai karfin gaske ya ɓarke, babu hadari babu komai suka ji zubar ruwa kamar da bakin kwarya, mamaki ne ya kama Ayla. Cike da mamaki ta ce, "Da ma wai har yanzu lokacin damina muke ne?" Kausar na fama da kokarin gutsirar ganda ta ce, "E mana, ni ma dai abin ya ba ni mamaki, rabon da na ga ruwan sama yau wajen sati biyu kenan? Tun da muka shiga Daular Mutuwa, kuma da muka fito ma ba a yi ruwa ba har muka iso nan." Juyawa Ayla ta yi tana kokarin yi wa Rimsha magana, sai suka ga, Rimsha ta a jiye kwanon abinci ta miƙe da gudu ta yi waje.
Cikin sauri Ayla ta ajiye cokalin hannunta, ta miƙe ta bi bayanta, don a tunaninta wani abin ne Rimsha ta ji a waje, shi ne ta je leƙowa.
Rimsha na fitowa ta shige cikin ruwan saman nan, tana dariya tana juyi a ciki kamar kifi, mamaki ya hana Ayla magana, ta tsaya kawai daga bakin kofa ta zuba wa Rimsha ido. Ita kam Kausar da ma idan tana cin abinci ba ta taɓa yarda wani abu ya tayar da ita, ba ta tashi har sai ta kai aya a cin abincin da take, sai ta ga karshen kwano take samun nutsuwa, don haka yanzu ma ba ta taso ba, tana zaune tana cin abincinta kawai.
Wani nishaɗi Rimsha ke ji yana ratsata, sai juyi take cikin ruwan saman nan tana dariya, ga ruwan zuba yake sosai kamar da bakin kwarya, ga shi babu iska. Tun tana karama take bala'i son ruwa, ko lokacin da suke gida tare da daddy in dai ba cikin dare aka yi ruwan sama ba, in da rana ne sai ta shiga, tun daddy na hana ta har ya hakura ya dai'na.
"Rimsha kina son ruwan sanyin nan ya saki mura ko?" Daga bayanta ta ji wannan zazzakar murya mai kama da tata, a sukwane ta juya, Malika ce ke tsaye ita ma cikin ruwan tana ta murmushi dimple nata irin na Rimsha na lotsawa.
Yar dariya Rimsha ta yi kafin ta ce "Malika me kika zo yi a nan? Ko dai ke ma yar nan garin ce?" Matsowa kusa da ita Malika ta yi tana ta murmushi ta ce, "A'a ni ba yar nan ba ce, na zo wucewa ne na gan ki kina wasa cikin ruwa na ce bari na zo mu gaisa" Kara faɗaɗa murmushi Rimsha ta yi tana faɗin "Gaskiya kina da kirki sosai, ina godiya." "Duk kirki na ai ban kai ki ba Rimsha" Cewar Malika, shiru Rimsha ta yi tana tunanin wani kirki ita kuma ta yi da har Malika take ce wa tana da kirki.
"Rimsha ki fita a cikin ruwan nan fa, kada mura ta kama ki". Cewar Malika, ta yi maganar tana kara matsowa kusa da ita, "Malika to ai ke ma kin shiga cikin ruwan, ke ma ki fita kada mura ta kama ki".
Jan dogon hanchinta Malika ta yi, kafin ta ce, "Ni kam mura ba za ta kama ni ba, don asalina ma a ruwa nake rayuwa, ke dai ki fita". Rimsha za ta yi magana Ayla dake tsaye a bakin kofa ta cikin falo tana ganin ta ta ce, "Rimsha kan ki ɗaya kuwa?" Juyowa Rimsha ta yi ta kalle ta tana faɗin, "Ban gane kai na ɗaya ba, me na yi kuma?" Ta yi maganar tana zaro dara-daran idanunta alamar mamaki, "Da wa kike magana to?" Cewar Ayla.
A sukawane Rimsha ta sake dawo da kallon ta kan Malika dake tsaye ta goya hannu a kirjinta sai murmushi take tana kallon su, juyawa ta yi ta sake kallon Ayla. A ɗan tsorace ta ce, "Ayla ban gane da wa nake magana ba? Ni da Malika ce mana".
Ɗan sako kai waje Ayla ta yi ta leƙo da kyau ko za ta ga wani ko wata da ke magana da Rimsha, amma sai ta ga wayam ba kowa. A kule ta ce "Wace ce kuma Malika? A ina kuma take? Don ni ban ga kowa a nan ba." Zaro ido sosai Rimsha ta yi ta ɗan ja baya daga kusa da Malika, ta matsa tana faɗin, "Ga ta nan ki gan ta." Zaro ido Ayla ta yi da nufin ya yi tozali da wacce ake nuna mata din amma babu abin da ta gani.
"Ki daina wahalar mini da kanki Rimsha Ayla ba za ta gan ni ba". Cewar Malika, juyo da kallon ta kan Malika ta yi, kirjinta sai dukan uku-uku yake, ta tsorata sosai, taya za a yi a ce ita tana kallon Malika, amma Ayla ba ta kallon ta.
"Me yasa kike tunani Rimsha?" Malika ce ta katse mata tunanin da take da tambayar ta. Yar firgita ta yi kafin ta ce, "Dole zan yi tunani mana Malika." Tsare ta da ido irin nata Malika ta yi tana faɗin "To tunanin me kike yi?" Ayla dai ta ga ikon Allah, don ba ta ganin Malika sai dai ta ga Rimsha nata surutu ita kaɗai kuma abin mamaki ba ta iya jiyo me Rimsha ke faɗa, sai dai bakinta kawai take gani yana motsawa. Babban magana wannan shine ruɗani!
"Malika me yasa Ayla ba ta ganin ki?". Cewar Rimsha, ta yi maganar a matukar tsorace, "Kina son ta gan ni ne?" Malika ta tambaya tana sanya hannunta a saman tsakiyar kan Rimsha, don ta tare mata ruwan saman dake dukan tsakiyar maɗigarta, don ruwan zuba yake sosai kamar da bakin kwarya.
"Eh mana Malika yana da kyau ai kowa ma ya gan ki, bai kamata ki ɓuya ba sa ganin ki ba, ai sai su yi tunanin da aljana nake magana." girgiza kai Malika ta yi tana faɗin "Yaro, yaro ne, amma dai ke yarinya ce mai zuciyar manya, ki ce Ayla ta kalli cikin ɗaki". Kananun shekarun Rimsha ya hana ta gane in da Malika ta dosa, don haka sai ta juya ta ce, "Ayla ki kalli cikin ɗaki." Ayla kuma ta yi zaton wani abu Rimsha ke nuna mata a cikin ɗakin don haka sai ta juya, ta kai kallonta cikin ɗakin, kafin ta juyo Malika ta bayyana yadda kowa zai iya ganin ta
Ayla ganin babu komai a cikin ɗakin yasa ta juyo tana faɗin, "Rimsha me zan gani a cikin ɗakin? Don na juya ban ga komai... Ba ta ƙarasa maganar ba idon ta ya sauka a kan Malika, a zabure ta ce, "Wace wanna mai bala'in kama da ke ɗin kuma Rimsha?" Juyowa Rimsha ta yi tana kallon Ayla kafin ta yi magana, Ayla ta yanke jiki ta faɗi kasa sumammiya, a sukwane ta dawo da kallon ta kan Malika, sai ta ga wayam babu Malika a wajen, Malika ta tafi, cike da tsoro ta fara waigawa ko za ta ga Malika, amma babu ita babu alamarta, da gudu ta kwasa ta bar cikin ruwan ta nufi wajen Ayla, in da take kwance magashiyan a kasa.
Kanta ta yi ta fara jijjiga ta tana kiran sunanta, hakan ya yi sanadiyar jawo hankalin Iya da kuma Kausar. Da sauri suka karaso wajen a tare, iya tana faɗin "Lafiya Rimsha?" Ganin Ayla kwance magashiyan a kasa yasa Iya ta yi kanta tana kiran sunanta.
Ruwan saman dake zuba daga jikin Rimsha shi ya zubar wa Ayla a fuskarta zuwa wuya. Hakan yasa ta farfaɗo daga suman da ta yi.
Har suna haɗa baki wajen cewa "Ayla lafiya?" Shiru ta ɗan yi kafin ta ce, "Babu komai." Don ta mance komai, a zahirin gaskiya abin da ya sanya ta suma shi ne ta ga lokacin da Malika ta ɓace, kuma kafin ta ɓace sai da ta ɗora hannunta a kan Rimsha dana sakin cool murmushi sannan ta ɓace, lokacin ita kuma Rimsha tana kallon Ayla ɗin abin ya faru. Wannan shi yasa Ayla ta suma, da ta farfaɗo kuma ta kasa faɗa musu me ta gani yasa har ta suma. Haka ta miƙe sai tambayar ta suke amma ta ce ba ta sani ba, ita ba ta san komai ba, haka suka kyale ta, Iya da Kausar suka koma cikin gida tare da Ayla, ita kuma Rimsha tsayuwa ta yi a wajen tana tunanin ina Malika ta tafi lokacin guda haka, ko alamarta babu, sannan me ya sanya Ayla suma? Sosai ta shiga duniyar tunanin sai dai kuma babu wata amsa da ta samu.
A hankali ta sako kafarta ba ta daddara ba ta sake komawa cikin ruwan saman ta ci gaba da wankanta, don ita da ruwan sama ba a raba su. Sai juyi take, wannan bakin gashin nan nata rabi ya kwanto mata a fuskarta rabi kuma ya kwata har gadon bayanta, sai sheki yake gwanin ban sha'awa.
Ruwan saman ya kai awa ɗaya yana zuba kamar da bakin kwarya, haka Rimsha ta tsaya a cikin ruwan tana wanka har sai da ruwan ya ɗauke. Ba yadda Ayla
Showing 42001 words to 45000 words out of 344390 words
Da sauri Rimsha ta miƙe ta rungumo Ayla tana son faɗa mata cewa Malika aljana ce, sai kuma ta kasa, ga dai maganar a bakin ta, amma ta kasa faɗe. Haka ta hakura suka yi alwala dan lokacin sallar mangariba ya yi.
Sai bayan sun yi sallah mangariba da issha ne suka zauna a palo suna hira. Miƙe wa Rimsha ta yi ta shiga kitchen wajen Iya, dan taya ta girki.
Yau tuwon semo da miyar Egusi Iya da Rimsha suka yi. Sai karfe 9 na dare suka kammala girkin suka dawo palo suka baje, suka fara cin abinci, suna ci suna hira, ita kuma Kausar tana ci tana haɗa zufa, don ba ta magana kam sai dai kai loma.
Suna tsaka da cin abincin ne boda Jami'u da boda Kabiru suka dawo. Da gudu Kausar ta tashi ta nufe su, tana ta washe baki. Tsalle tayi ta haye jikin boda Jami'u, ɗaga ta ya yi sama kamar yar baby, duk wannan kiba na Kausar bai hana shi ya iya ɗaga ta ba, dan Jami'u irin mazan nan masu tsawo da ƙiba, ga shi da kiran karfi.
Ihu ne ya kaure a gidan, na karti wato boda Jamiyu da boda Kabiru, don ba su san kanwarsu kuma yar autarsu ta dawo ba. Shi boda Jamiyu ɗa ne ga yayan baban Kausar kuma shi yake son Kausar ɗin ma'ana saurayinta ke nan. Ihu suke kamar ba lafiya ba, wai a haka murna suke nunawa, miƙewa Iya ta yi ta fara taya su. Bayin Allah Rimsha da Ayla suna ganin ikon Allah iya ganin idonsu a kasar Yarabawa, wani lokaci ma har tunani suke anya Iya ba ta samu matsala a ƙwaƙwalwarta ba kuwa mata ce wani lokaci bata da setti ko kaɗan.
Haka suka yi ta ihun nuna murnarsu na wani lokaci kafin nan su tsagaita, Jami'u ya sauƙe Kausar kasa daga jikin sa, sai dariya suke.
Daga Jami'u har Kabiru sun yi shocked da ganin su Rimsha, sai kallon Rimsha suke, dan akwai wutar nepa, haske ya karaɗe palon gabaɗaya hakan ya sa suka samu daman ganin Ayla da Rimsha sosai.
Jami'u ya kasa hakuri har sai da ya tambayi daga ina Rimsha take, nan fa Kausar ta fara basu labarin irin wahalar da suka sha tun shigar su daular Mutuwa har fitowar su. Sosai su Jami'u suka tausaya musu. Hannu ya kai zai shafi kan Rimsha, cikin sauri ta ɗan ja baya, yar dariya ya yi kafin ya ce "As from today you are my sister, so kada ki damu, na san halin ku Hausawa baku son a rinƙa taɓaku sai ku rinƙa avoiding na mutane, kamar ba ku da gaskiya." cikin harshen Turanci ya yi maganar. Shiru Rimsha ta masa, dan ita gaba ɗaya ma haushi suka bata, jibi yadda yake wani rungume Kausar dan iskanci kuma yasan akwai aure a tsakanin su. A ɓangaren Ayla ma ba karamin haushin abin ta ji ba, wasu karti da su ba kyan gani, ga shi dukansu sun wani saka gajeren wando zuwa guiwa da riga mai karamin hannu.
Shi kam Kabiru sai kallon Rimsha yake ya kasa dai'na wa, haka shi ma Jamiyu, sai dai shi Jamiyu satar kallon ta yake dan kada Iya ko Kausar su gane yana kallon nata.
Yanzu su ma a nan gidan za su kwana, Rimsha da Ayla suka yi wa kansu tambayar a tare a cikin zuciyoyinsu kamar abin haɗin baki, sai dai kuma ba su da amsar tambayar tasu.
Haka suka zauna a palon tare da su Jami'u, Rimsha kamar za ta yi kuka dan haushin zama da karti, haka ita ma Ayla. Ita kuwa Kausar sai faman wage hakwara take tana dariya kamar wata yar fari, sai murna take, ta wani zauna kusa da Jami'u suna kallon Yoruba film, ita kuma Iya ta ɓige da barci kwance saman sofa.
Sai misalin 11 na dare sannan su Jami'u suka wuce ɗakin su, wanda ya kasance kusa da ɗakin Iya ne, duk dai cikin rufi ɗaya. Tsoro sosai Rimsha ta ji lokacin da taga cewa a nan gidan su Jami'u za su kwana, ga shi ta lura da irin kallon ta da suka rinƙa yi mata.
Haka cike da tsoro suma suka wuce na su ɗakin, bayan Kausar ta tashi Iya daga barci, Iya ce ta kulle kofar falon da key da kuma sakata, sannan ta wuce ɗakinta ita ma. Rimsha dai ta tsorata sosai, gani take kamar za su zo su kama ta, shiyasa da suka shiga ɗaki ta riga su hayewa gado, ta tafi can karshen gado ta kwanta ta manne da bango, Ayla ce ta kwanta kusa da ita, sai Kausar a karshen gadon
To Rimsha mu Sarkin tsoro sai dai mu ce Allah ya tsare, na yi nan sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu.
Sai mun haɗu gobe idan mai dukka ya kai mu
[11/11, 8:52 PM] +234 906 579 6460: 💞💞TRIPLET'S💞💞
🌹🌹Episode 13-14🌹🌹
A ɓangaren Ummi kuwa ƙara zaro ido waje ta yi ta ce "Abbo mene ne ya sa ba ka son haɗin?" A takaice ya ce "Saboda tsintaciyar mage ce, ba mu san asalinta ba." Ayya Jelly baiwar Allah tana can duniyar kaza ba ta tare da su, ba ta san wainar da ake toyawa ba.
"A'a Abbon Nawid kada mu yi haka da kai, idan muka ce don ba ta da asali ba za mu ba ta ɗanmu ba, to waye kake tun nin zai aure ta? Mu da muka san komai ma mun ki yarda, to waye kake tunani zai so ta, kuma ma ai yanzu mun zama mu ne asalinta iyayenta komai nata." Ɗaure fuska sosai Abbo ya yi kamar da gaske yana son hana Nawid ne don baby ba ta da asali, alhalin kuma kansa yake gyarawa hanya, yana son ya rushe maganar Nawid ne don ya gina tasa, wannan ita ce cakwakiya.
"Ummin Nawid na gama magana, ɗana yaro ne mai asali, don haka ba zai auri wadda ba ta da asali ba." Ya kai karshen maganar tare da cire hannunsa daga abincin ya miƙe ya bar wajen, cike da ɓacin rai a zahiri, amma cikin ransa kuma farinciki kamar ya zuba ruwa a kasa ya sha.
Sosai Ummi ta ji babu daɗi, kuma ta kudure a ranta sai Nawid ya auri Jelly don ita ce zaɓinta, ba ta son Nawid da kowace mace fa ce Jelly, ko me zai faru sai dai ya faru, ɓera ya ɓarar da garin kyanwa. Nawid, Jelly zai aura. Rai a matukar ɓace ita ma ta miƙe ta nufi bedroom nata, yau ranta ya ɓaci sosai ba za ta je wajen Abbo ɗin ba, kwanciya ta yi a ɗakinta.
Shi ma Nawid ganin iyayen nasa sun tafi ya sa ya miƙe ya nufi ɗakinsa, ransa fes sai wani murmushi yake saki, Abbonsa ya rushe maganar aurensa da mahaukaciya a cewarsa. Ita kuwa Jelly sai faman cin naman kaza take, kwatakwata ma ba ta san me suke tattaunawa a kanta ba, tana dai jin zancen nasu sama sama haka yana bi ta gefen kunnenta.
Sai da ta cinye kaza guda tas, ko kaɗan ba ta rage ba, kamar wata mai aljanun cin nama. Bayan ta kammala sai ta miƙe ta wuce bedroom nata tana lashe baki kamar wata tsohuwar mayya. Tana shiga ta haye saman gadonta tana sauke ajiyar zuciya, yau ko kayan barci ba ta samu sawa ba, don da ma Ummi ke saka mata kayan barci yau kuma ran Ummi a ɓace yake.
Abbo da Ummi ransu a ɓace barci ya yi awon gaba da su, Nawid kuwa farinciki cike fal ransa ya yi barci. A gefen ita ma Jelly da yake ba ta san me aka kulla ba, sai ta yi barcinta cikin kwanciyar hankali.
A ɓangaren Umaisha kuma, bayan sun ɗan yi shiru na yan mintuna ne, Umaisha ta katse musu shirun da cewa, "Yaya Akil don Allah gobe ka ɗauko Aunty Afi ta zo ta mana kwana biyu ka ji?" Shafa kanta ya yi kafin ya ce "To, na ji kuma zan je na ɗauko ta." Wani daɗi Umaisha ta ji ya rufe ta, da ƙarfi ta matse shi a jikinta, tana murna. "Za ki ɓalla ni ko?" Ya tambaya yana tsare ta da ido, dariya cikin hawaye ta yi tana faɗin, "Kai yaya Akil ni na isa na ɓalla ka ne?" Shiru ya mata don shi ma ba mai son yawan Magana ba ne. Haka suka yi shiru, ta yi luf a jikinsa har barci ya ɗauke ta, shi kuma sai faman kallon fuskarta yake yi.
Mu koma wajen Rimsha.
Bayan sun gama girki ita da Iya, ta fito ta shige cikin bandaki ta sake yin wanka abinta, don Rimsha akwai ta da bala'i son tsafta sosai, ba ta son datti ko kaɗan.
Bayan ta yi wanka ta sake shiryawa cikin wata doguwar riga ta Kausar, ta fito falo, nan ta samu Kausar da Ayla suna cin abinci, amma kowa kwanonsa daban, ma'ana daban-daban Iya ta saka musu abincin. Kusa da su ta zo ta zauna, Ayla ce ta jawo wani kwano da ke rufe a gefen su ta miƙa mata tana faɗin, "Ga naki abincin." Karɓa ta yi ta fara ci tana jin daɗi yau ta iya yadda ake yin miyar Steew da shinkafa.
Suna tsaka da cin abincin ruwan sama mai karfin gaske ya ɓarke, babu hadari babu komai suka ji zubar ruwa kamar da bakin kwarya, mamaki ne ya kama Ayla. Cike da mamaki ta ce, "Da ma wai har yanzu lokacin damina muke ne?" Kausar na fama da kokarin gutsirar ganda ta ce, "E mana, ni ma dai abin ya ba ni mamaki, rabon da na ga ruwan sama yau wajen sati biyu kenan? Tun da muka shiga Daular Mutuwa, kuma da muka fito ma ba a yi ruwa ba har muka iso nan." Juyawa Ayla ta yi tana kokarin yi wa Rimsha magana, sai suka ga, Rimsha ta a jiye kwanon abinci ta miƙe da gudu ta yi waje.
Cikin sauri Ayla ta ajiye cokalin hannunta, ta miƙe ta bi bayanta, don a tunaninta wani abin ne Rimsha ta ji a waje, shi ne ta je leƙowa.
Rimsha na fitowa ta shige cikin ruwan saman nan, tana dariya tana juyi a ciki kamar kifi, mamaki ya hana Ayla magana, ta tsaya kawai daga bakin kofa ta zuba wa Rimsha ido. Ita kam Kausar da ma idan tana cin abinci ba ta taɓa yarda wani abu ya tayar da ita, ba ta tashi har sai ta kai aya a cin abincin da take, sai ta ga karshen kwano take samun nutsuwa, don haka yanzu ma ba ta taso ba, tana zaune tana cin abincinta kawai.
Wani nishaɗi Rimsha ke ji yana ratsata, sai juyi take cikin ruwan saman nan tana dariya, ga ruwan zuba yake sosai kamar da bakin kwarya, ga shi babu iska. Tun tana karama take bala'i son ruwa, ko lokacin da suke gida tare da daddy in dai ba cikin dare aka yi ruwan sama ba, in da rana ne sai ta shiga, tun daddy na hana ta har ya hakura ya dai'na.
"Rimsha kina son ruwan sanyin nan ya saki mura ko?" Daga bayanta ta ji wannan zazzakar murya mai kama da tata, a sukwane ta juya, Malika ce ke tsaye ita ma cikin ruwan tana ta murmushi dimple nata irin na Rimsha na lotsawa.
Yar dariya Rimsha ta yi kafin ta ce "Malika me kika zo yi a nan? Ko dai ke ma yar nan garin ce?" Matsowa kusa da ita Malika ta yi tana ta murmushi ta ce, "A'a ni ba yar nan ba ce, na zo wucewa ne na gan ki kina wasa cikin ruwa na ce bari na zo mu gaisa" Kara faɗaɗa murmushi Rimsha ta yi tana faɗin "Gaskiya kina da kirki sosai, ina godiya." "Duk kirki na ai ban kai ki ba Rimsha" Cewar Malika, shiru Rimsha ta yi tana tunanin wani kirki ita kuma ta yi da har Malika take ce wa tana da kirki.
"Rimsha ki fita a cikin ruwan nan fa, kada mura ta kama ki". Cewar Malika, ta yi maganar tana kara matsowa kusa da ita, "Malika to ai ke ma kin shiga cikin ruwan, ke ma ki fita kada mura ta kama ki".
Jan dogon hanchinta Malika ta yi, kafin ta ce, "Ni kam mura ba za ta kama ni ba, don asalina ma a ruwa nake rayuwa, ke dai ki fita". Rimsha za ta yi magana Ayla dake tsaye a bakin kofa ta cikin falo tana ganin ta ta ce, "Rimsha kan ki ɗaya kuwa?" Juyowa Rimsha ta yi ta kalle ta tana faɗin, "Ban gane kai na ɗaya ba, me na yi kuma?" Ta yi maganar tana zaro dara-daran idanunta alamar mamaki, "Da wa kike magana to?" Cewar Ayla.
A sukawane Rimsha ta sake dawo da kallon ta kan Malika dake tsaye ta goya hannu a kirjinta sai murmushi take tana kallon su, juyawa ta yi ta sake kallon Ayla. A ɗan tsorace ta ce, "Ayla ban gane da wa nake magana ba? Ni da Malika ce mana".
Ɗan sako kai waje Ayla ta yi ta leƙo da kyau ko za ta ga wani ko wata da ke magana da Rimsha, amma sai ta ga wayam ba kowa. A kule ta ce "Wace ce kuma Malika? A ina kuma take? Don ni ban ga kowa a nan ba." Zaro ido sosai Rimsha ta yi ta ɗan ja baya daga kusa da Malika, ta matsa tana faɗin, "Ga ta nan ki gan ta." Zaro ido Ayla ta yi da nufin ya yi tozali da wacce ake nuna mata din amma babu abin da ta gani.
"Ki daina wahalar mini da kanki Rimsha Ayla ba za ta gan ni ba". Cewar Malika, juyo da kallon ta kan Malika ta yi, kirjinta sai dukan uku-uku yake, ta tsorata sosai, taya za a yi a ce ita tana kallon Malika, amma Ayla ba ta kallon ta.
"Me yasa kike tunani Rimsha?" Malika ce ta katse mata tunanin da take da tambayar ta. Yar firgita ta yi kafin ta ce, "Dole zan yi tunani mana Malika." Tsare ta da ido irin nata Malika ta yi tana faɗin "To tunanin me kike yi?" Ayla dai ta ga ikon Allah, don ba ta ganin Malika sai dai ta ga Rimsha nata surutu ita kaɗai kuma abin mamaki ba ta iya jiyo me Rimsha ke faɗa, sai dai bakinta kawai take gani yana motsawa. Babban magana wannan shine ruɗani!
"Malika me yasa Ayla ba ta ganin ki?". Cewar Rimsha, ta yi maganar a matukar tsorace, "Kina son ta gan ni ne?" Malika ta tambaya tana sanya hannunta a saman tsakiyar kan Rimsha, don ta tare mata ruwan saman dake dukan tsakiyar maɗigarta, don ruwan zuba yake sosai kamar da bakin kwarya.
"Eh mana Malika yana da kyau ai kowa ma ya gan ki, bai kamata ki ɓuya ba sa ganin ki ba, ai sai su yi tunanin da aljana nake magana." girgiza kai Malika ta yi tana faɗin "Yaro, yaro ne, amma dai ke yarinya ce mai zuciyar manya, ki ce Ayla ta kalli cikin ɗaki". Kananun shekarun Rimsha ya hana ta gane in da Malika ta dosa, don haka sai ta juya ta ce, "Ayla ki kalli cikin ɗaki." Ayla kuma ta yi zaton wani abu Rimsha ke nuna mata a cikin ɗakin don haka sai ta juya, ta kai kallonta cikin ɗakin, kafin ta juyo Malika ta bayyana yadda kowa zai iya ganin ta
Ayla ganin babu komai a cikin ɗakin yasa ta juyo tana faɗin, "Rimsha me zan gani a cikin ɗakin? Don na juya ban ga komai... Ba ta ƙarasa maganar ba idon ta ya sauka a kan Malika, a zabure ta ce, "Wace wanna mai bala'in kama da ke ɗin kuma Rimsha?" Juyowa Rimsha ta yi tana kallon Ayla kafin ta yi magana, Ayla ta yanke jiki ta faɗi kasa sumammiya, a sukwane ta dawo da kallon ta kan Malika, sai ta ga wayam babu Malika a wajen, Malika ta tafi, cike da tsoro ta fara waigawa ko za ta ga Malika, amma babu ita babu alamarta, da gudu ta kwasa ta bar cikin ruwan ta nufi wajen Ayla, in da take kwance magashiyan a kasa.
Kanta ta yi ta fara jijjiga ta tana kiran sunanta, hakan ya yi sanadiyar jawo hankalin Iya da kuma Kausar. Da sauri suka karaso wajen a tare, iya tana faɗin "Lafiya Rimsha?" Ganin Ayla kwance magashiyan a kasa yasa Iya ta yi kanta tana kiran sunanta.
Ruwan saman dake zuba daga jikin Rimsha shi ya zubar wa Ayla a fuskarta zuwa wuya. Hakan yasa ta farfaɗo daga suman da ta yi.
Har suna haɗa baki wajen cewa "Ayla lafiya?" Shiru ta ɗan yi kafin ta ce, "Babu komai." Don ta mance komai, a zahirin gaskiya abin da ya sanya ta suma shi ne ta ga lokacin da Malika ta ɓace, kuma kafin ta ɓace sai da ta ɗora hannunta a kan Rimsha dana sakin cool murmushi sannan ta ɓace, lokacin ita kuma Rimsha tana kallon Ayla ɗin abin ya faru. Wannan shi yasa Ayla ta suma, da ta farfaɗo kuma ta kasa faɗa musu me ta gani yasa har ta suma. Haka ta miƙe sai tambayar ta suke amma ta ce ba ta sani ba, ita ba ta san komai ba, haka suka kyale ta, Iya da Kausar suka koma cikin gida tare da Ayla, ita kuma Rimsha tsayuwa ta yi a wajen tana tunanin ina Malika ta tafi lokacin guda haka, ko alamarta babu, sannan me ya sanya Ayla suma? Sosai ta shiga duniyar tunanin sai dai kuma babu wata amsa da ta samu.
A hankali ta sako kafarta ba ta daddara ba ta sake komawa cikin ruwan saman ta ci gaba da wankanta, don ita da ruwan sama ba a raba su. Sai juyi take, wannan bakin gashin nan nata rabi ya kwanto mata a fuskarta rabi kuma ya kwata har gadon bayanta, sai sheki yake gwanin ban sha'awa.
Ruwan saman ya kai awa ɗaya yana zuba kamar da bakin kwarya, haka Rimsha ta tsaya a cikin ruwan tana wanka har sai da ruwan ya ɗauke. Ba yadda Ayla
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15 Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102Chapter 103Chapter 104Chapter 105Chapter 106Chapter 107Chapter 108Chapter 109Chapter 110Chapter 111Chapter 112Chapter 113Chapter 114Chapter 115