Allah amma anan wattap kawai saboda haka ku bani had'in kai dan Allah naga canji a wannan karan ngd_
Chapter 20
______Sun d'auki kusan mintuna goma shabiyar a haka batare da d'ayan su ya yi 'kwa'k'kwaran motsi ba sai sautin bugun zuciyar Sadeeq dake sauka fat fat, Siddeeqah kuwa duk da akwai na'urar sanyin dake saka cikin motar sanyi saida ta jike da gumi sharkaf idanuwan ta sun dad'a fitowa waje, dago raunannun idanun sa yayi da suka koma launin gwauta saboda tsabar bacin rai ya sauke su akan na Siddeeqah, da sauri ta maida kanta kasa tana wasa da y'atsun hannun ta zuciyar sa ce take ingiza sa da ya shake mata wuya wata zuciyar kuma ta ce masa "Kul Sadeeq ka kashe gawar da ba taka ba, ka bud'e mata mota ta fita" haka kuwa akai yabi shawarar zuciyar da ta gar gad'e sa soboda haka ya bude mata murfin motar Siddeeqah naji ya bud'e tayi sauri ta bude murfin ta fito har tana neman dungurawa a kasa soboda yanayin Sadeeq d'in yayi mugun bata tsoro da sauri da sauri take tafiya jefa kafar ta kawai take batare da tasan inda take jefewa ta ba, ji tai ta ci karo da mutum a tsorace ta ja da baya ganin Sadeeq ne yabiyo ta d'ayar hanyar da ake iya haduwa da Wanda yabi ta gaban gida, yanda taga yanayin sa har yafi d'azun firgitar wa idanuwan sa sun kara yin jaa kamar Jan gauta, nufo ta ya fara yana d'an Murmushi yana shafa sajen sa, 'kafa mai naci ban baki ba gudu ta fara shima ya mara mata baya cikin ikon Allah saiga Momy a harabar gidan da alamar wani abu take ne ma saboda idanuwan ta a kasa suke, da gudu Siddeeqah taje bayan ta ta 'boye tana nishi "ke lafiyan ki kuwa daga ina haka kamar an koro ki?". Momy ta fad'a tana duban Siddeeqah Bata lura da Sadeeq ba, da hannu Siddeeqah ke nuna mata inda Sadeeq yake sai alokacin Momy ta dube sa, washe baki yai ya wayance yace ma Siddeeqah "ba dai kin ki bari na kama ki ba nima zan rama yarinya, waifa Momy ce mata nayi ta jirani mu taho tare shine ina gama faking ta rigani fitowa shine nabi bayan ta da ta hango ni sai tafara gudu nima shine na biye mata". Siddeeqah kamar sakarya haka ta saki baki da hanci tana kallon shi lallai ya iya tsara labari,
cikin gamsuwa da abinda ya fad'a Momy tace "ai da baka biye mata ba yarinya ce, amma gaskiya kun dade ko ka kaita wani gurin ne? Daddyn ku na ta kiran ka a waya baka dauka munyi tunanin ko ba lafiya ba hankali ya fara tashi".
"Wallahi lafiya lau Momy layi muka tarar a gurin saloon d'in, amma me ya fito dake naga kamar wani abu kike nema?".
"to babu damuwa, eh wallahi d'an kunnen Jiddah ne guda daya ya fad'i sanda suka dawo daga asbiti".
Tace "anan ya fad'i shine nace bari na duba ko zan gani".
"haba Momy ke da kanki ina sauran yaran gidan?".
"Suna ciki Khadija ta ce ta gaji zata shiga ta huta dan ko abincin rana bata ci ba, Umar kuma yana tare da Jiddah, Ummi kuma tun safe ban kuma ganin ta ba".
"Kibar neman haka Momy muje ciki ba rabon ta bane kawai sai asai mata wani".
"dama a cikin irin tsara bar da auntyn kaduna ta kawo musu ne alokacin da ta dawo daga India daham ne yanada tsada sosai yanzu ita kadai ce ba ta da".
"Momy ita ta jawa kanta".
Siddeeqah kamar ruwa ya cinye ta Momy ce ta kama hannun ta tace "muje ciki yau na girka abinda ki ka fi so a bincin gargajiya".
"dan Allah fa Momy?".
"zan miki 'karya ne?".
"a a Momy".
Ta fad'a tana rufe fuskan ta da tafin hannun ta ahaka suka karasa cikin gidan Siddeeqah na mamakin Sadeeq,
Yayin da shi kuma ya ji haushin ganin Momy a harabar gidan batare da ya ma Siddeeqah matsiyacin duka ba dan so yayi ya mata dukan ban kwana saboda ba lallai ya kuma haduwa da ita ba har sai ta dawo hutun makaranta, yanda bazata manta dashi ba
♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾
Kamar wacce tayi karya takai ta komo tarasa ina zata sa kanta dafa kafad'ar ta akai da han zari ta dago kanta ganin Lubancy ce Kawar ta yasa Zuby sauke ajiyar zuciya tace "kawata kin zo a dai dai dan dama yanzu nike shirin zuwa gidan ku wallahi ina cikin tashin hankali nasan babu Wanda zai fitar dani saike".
"haba ke kuwa kinada ni kike cewa kina cikin tashin hankali kin manta wace ni kin manta kirari na? Bari na na tuna miki".
"a a barshi ban manta ba kai na ne ya kulle na rasa mai yake min dadi, sai yanzu dana ganki na ji sauki a raina nasan ke a wurin ki ba komai bane soboda na shiga matsalar da tafi wannan kuma kin mini maganin ta".
"yauwa yar gari ashe baki manta da wace ce kike tare da ita ba".
Zuby tace "kawa ta mu zauna na baki labarin abinda ya sa na shiga cikin tashin hankali".
Saida Lubancy ta je ta bude karamin fridge din dake dakin ta dauko goran lemu sannan ta dawo ta zauna a bakin gado tace
"ina jinki".
"ina wannan gayen da nike baki labari Wanda na had'u dashi a Instagram kwanaki kin tuna shi?".
"Eh anyi haka na tuna to mai ya faru dashi ko shima an fad'a masa halin ki ne".
Lubancy ta fad'a haka tana duban kawar ta
"ko daya kawa ta nan take Zuby ta kwashe duk abinda ya faru ta fad'a ma Lubancy,
tsaki Lubancy taja kana tace "wallahi Zuby kina bani mamaki d'an karamin abu duk ki bi ki tada hankalin ki ba kin ce yana soki ba?".
"Eh yana sona na gani a cikin 'kwayar idanun sa".
"kuma kince yarinyar suna kama".
"wallahi suna masifar kama abinda ya bani haushi" da yace" min 'yar mai gadin su ce baki ga yarinyar ba kama da larabawa take yi".
Lubancy tace "dadi na dake gajen hakuri da kin bisa a yadda yace idan ma da wata a 'kasa zamuji daka baya, kince kina son sa kuma auren sa zakiyi kin tafka kuskure da kika ce masa karya yake saboda shine gaba dake, amma ko nan gaba ki kiyaye kisan kalar maganar da zaki dunga gaya masa, Zan san yadda zamu bullo wa lamarin, saboda nima yanzu tawa ce ta kawo ni tun jiya da muke chart kika fad'a min kin gama al'adar naji kamar nayi tsun tsuwa nazo saboda nayi missing d'in ki ".
"Kawata kenan wallahi bakida hakuri". Zuby ta fad'a tana zuge zif d'in rigar ta,
ita ko Lubancy dama doguwar riga ce ta zumbulo sai undies da ta saka nan take ita ma ta cire doguwar rigar tayi cilli da ita ta kamo Zuby suka 'karasa cire ma juna kaya,
sosai Lubancy ta rikice saboda Zuby Allah ya yi mata baiwar komai bata da makusa a halittar jikin ta shine ke rud'an maza
sakonni suka fara aika wa junan su sosai suke romance suna ihu. Babu inda basa tabawa a jikin junan su
Wa'iya zu billah lallai halin Zuby sai ita baza taso Sadeeq ya sani ba dan shi kamilar mace yake so ya aura,
ja musu 'kofar nayi ina takaicin rayuwar Zuby
♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾
Ina cin danbun ina side yatsun hannu na Ummi na hango tana sauko wa daga sama dinning din tazo ta zauna da alamar daga bacci ta tashi saboda yadda idanuwan ta sukayi, kallo na tayi tace "maiyar dambu sai kace kin samu wani abun dadin, ko naman kaza baki masa irin wannan santin, ni kuma wallahi na tsane sa dole nike ci nasan Daddy ne yasa Momy tayi dan shima yana son dambu".
Nace "yarinya da kinsan kalan dadin da nike ji alokacin da nike cin dambu da ko magana aka ce ki min bazaki ba saboda idan zan baki amsa a cikin santi zan baki yanzu dai bari na gama sai ki sake maimaita abinda kika fad'a".
Ummi tace "tab sai na tsaya har sai kin gama kamar yarinyar ki bani da wannan lokacin bari naje ko Indomie na dafa dan yau ba zanci danbun ba".
"ke dai kika sani idan za a shekara ana jera yin dambu babu abinda zai dame ni".
"uhm". Ummi ta fad'a ta nufi hanyar kitchen
Umar ne tafe rike da hannun Jiddah tana ta ciza lebe ahankali suka karaso gurin Umar yai sauri ya ja mata kujera tai saurin dakatar da shi da fad'in "Umar mai kake shirin yi haka to wallahi na daina had'a gurin zama da wannan 'yar kauyen muje falo idan ta gama sai nazo muci".
Kallon ta nayi na kwashe da dariya nace "da alamar har yanzu bakin ki bai mutu ba".
Umar na kalla nace "wai ka nuna mata madubi kuwa? na tabbatar da taga yadda nayi mata da ko suna na taji an ambata gaban ta ne zai fad'i dan Allah idan bata ga ni ba maza je ka d'auko saboda ina son ta san ruwa ba sa'an kwando bane".
"Aunty Siddeeqah dan Allah ku daina wallahi banajin dadin hakan ko kadan". Umar ya fad'a kamar zai rushe da kuka
ganin haka yasa nace "to shikenan kani na ya wuce amma kaja mata kunne kasan ni duk Wanda yai min kan kara na itace nake masa".
Umar yace
"Aunty Jiddah muje".
A masifan ce Jiddah ta kwace hannun ta fuuu ta wuce falo ta zauna tana kananun magan-ganun da ita kadai tasan mai take cewa
🤙 _Hy guys please don't forget to comment vote and follow me on Wattpad join my group on Telegram please please please_ 🥰
NI DA YAYA SADEEQ
˙·٠•●♥ بسم الله الرحمن الرحيم ♥●•٠·˙
Chapter 21
So sai Siddeeqah take dariya harda rike ciki, tana ayyana yadda zata gyara ma Jiddah zama dan wallahi ta daina daukar rainin hankali
Take Umar ya mara ma Jiddah baya yana ma-ma kin tsanar da suka ma juna kamar ba 'yan uwan juna ba
A zaune ya sami Jiddahn a kan kujera sai cika take tana batsewa tana ganin sa ta daure fuska tace "mai kazo yi wuce ka bani guri munafuki ni zaka raina ma hankali a gaba na za ka dunga yiwa waccan yar kyauyen magana? Har da ce mata aunty saboda munafurci na cin ka". Ta karasa maganar tana nuno masa inda nike
shi dai Umar bai ce mata komai ba sai ma-maki ma da ta kara bashi
Jin kamar ana hayaniya Momy ta fito da Alamar daga bacci ta tashi, a dai dai lokacin Ummi ta fito daga kitchen hannun ta dauke da plate din abin ci, kallon mu Momy ta shiga yi ido cikin ido daga karshe ta sauke su akan Jiddah tayi mata kallo irin na gar gadi, ba tare da tace mana komai ba ta koma ciki abin ta
Ummi kuwa zama tai a dinning din tana fadin "wash Allah na".
Kallon ta nayi nace "kefa raguwa ce daga dafa Indomie sai kizo kina wash kamar wacce tayi abin a zo a gani?".
"Bazaki gane bane". Ummi ta fada tana kai lomar Indomie
Shi kuwa Sadeeq tun sanda suka shigo ya haura sama soboda yana bukatar ya huta dan zubi ba karamin bata mishi rai tayi ba sosai yake ma-ma kin ta dan shi baya son rashin kunya musamman ma idan yasan ya girmi mutum to yana so a girma ma shi, a gogan hannun sa ya cire tare da lalu ba aljihun sa ya ciro wayar sa ya aje a kan madubi kana ya shiga cire kayan jikin sa, wannan ita ce dabi'ar Sadeeq a duk sanda zai shiga wanka sai ya fara cire kayan sa a bedroom sannan ya ke shiga bayi, to bayan ya shiga ya dauki kusan mintuna 43 a cikin bayin yana cuda jikin sa ya zuba wancan ya zuba wannan sai da yaji kam shin ya mishi yadda yake so, sannan ya fito daga cikin kwamin wankan ya zo gurin da tawul yake a rataye ya daura a kugun sa kana ya dauki karami ya shiga goge kansa daga haka ya fito a bayin
* * * * * * *
A ban garan su Zuby kuwa bayan sun gama fasikan cin su suka shiga wanka nan ma sai da suka bata mintoci suna kissing din juna kamar wasu mata da miji Zuby ta manta da wani Hallita mai suna Sadeeq saboda Lubancy ba baya ba wajen romance ta iya solon makirci da yaudara kala kala
Bayan sun fito daga wan kan ne suka shafa mayuka masu kam shi tare da fesa body sprea riga da wando Zuby ta dauko a cikin durowar ta kana ta duby Lubancy tace "sweety wani kalar kaya zan fiddo miki?".
"My love duk wanda kika dauko min zan sa". Lubancy ta fada cikin salo mai Jan hankali
To bayan sun gama shirya wa suka shiga fesa tura ruka masu sanyin kamshi gami da daukar hankalin wanda duk a ka gibta ta kusa dashi,
Hijabi suka zum bula har kasa tare da saka safa a kafar su ke idan ki ka gansu zaki rantse mutanen arziki ne
Falo suka fito inda suka tar da Mama zaune tana kallon BBC World news, ta maida gaba daya hankalin ta da nutsuwar ta akan TV
Kamshin tura-ran tilon diyar ta-ta a duniya ne ya dawo da ita ga barin kallon TV
kallon su tayi cikin sakin fuska tace "kar dai har zaki tafi?".
Mama ta fada tana duban Lubancy wacce ke tsaye tana dan Murmushin tace "Eh Mama zan tafi dama sako na kawo mata".
Kallon Zuby Mama tayi ta ce "iya rigima ina zuwa kuma? ko rakiya zaki mata".
"Eh mama". Zuby ta bata amsa a takai ce
To babu damuwa ki dawo Lafiya amma gaskiya yau kar ki dade kin San abban ki yana gari, motsi kadan yace "kina ina?". Sai dai nayi masa karyan kan ki na miki ciwo kina bacci kin ce kar a tashe ki har sai kin tashi, kiss Zuby ta manna ma Mama a goshi tana fadin "Allah ya bar min ke Mama na I love you". "Love you too". Mama ta fada tana dariya irin ta-su ta manya da yike ita ma irin gogag-gun iya yan nan ne, kuma ta san da duk wani abu da diyar ta-ta take aika wa asali ma ita ce ta sata akan hanyar
* * * * * * * *
To a bangaren Sadeeq kwance yake a kan make kyan gadon sa idon shi a rufe kamar mai bacci amma kuma ba bacci yake ba a duniyar tunani yake
Wayar sa ce ta shiga ringing amma be da niyar dauka har kiran ya katse saida a ka sake kira a koro na biyu ya bude raunan-nun idanun shi ya lalabi wayar ganin sunan Farooq na yawo akan screen d'in wayar ya danna picking kana ya kara a kunne
daga can ban-garen Farooq yace "kai bana son iya shege tun dazun nike kiran ka baka dauka ba, ba yan kasan haka kawai ba zan dunga kiran ka ba".
"Ina jin ka to". Sadeeq ya fad'a yana cin magani
Farooq ya kwashe da dariya yace "dan iska wannan ji da kan naka ba shi zai sa a dunga maka abinda ka ke so ba, ni dai kasan ba tsoran ka zan ji ba ko?".
Cikin jin haushin kalaman Farooq Sadeeq yace "malam ya i she ka haka ka fadi abinda ya kawo ka ina jin ka".
Farooq yace "akan maganar makarantar matar ka ne na gama magana da wannan abokin nawa da yake koyar wa a makarantar ya sama mata admission yace maganar aji sai idan an kaita sun mata interview zasu gane ajin daya dace da ita, saboda haka daga yau zuwa kowace rana zaku iya kaita dan har register yai mata ".
Shiru Farooq yayi ko Sadeeq din zai ce wani abu amma sai yaji a kasin haka,
Bayan wasu yan daki ku Sadeeq yace "ka gama?".
Cikin takai cin abokin nasa Farooq yace "dan iska insha Allah wannan yarinyar da ka ke rainawa sai ta zame maka ciwan ido, yana gama fad'ar haka ya kashe wayar sa
Aje wayar sadeeq yayi gami da daga kafada alamar ko in kula ya tabe baki a can cikin zuciyar sa yana jin dadin zai rabu da ala ka kai
NI DA YAYA SADEEQ
˙·٠•●♥ بسم الله الرحمن الرحيم ♥●•٠·˙
Chapter 22
To bayan fitar su Zuby gidan su Lubancy suka zarce dake wata unguwa amma unguwar ba ta masu kudi can bace, kuma ita Lubancy iyayan ta sun rasu tun tana yar karama, a gurin kawun ta take, kasance war sa namiji ba ko da yaushe yake gida ba shiya yasa Lubancy ta zama abar da ta zama yanzu duk da matar kawun na kokari amma sam Lubancy ta raina ta bata jin maganar ta, ganin Allah bai bata haihuwa ba kar ta cika matsawa ace dan bata son zafin yara bane shiyasa ma yanzu ta zuba mata idanu, in dai duniya ce wanda bai zo ba ma jiran shi take.
Duk da sun sami matar kawun a tsakar gida, haka su ka wuce ta ba tare da sunyi mata sallama ba, da shigar su dakin Lubancyn suka wuce suna wani shan kamshi.
A cikin zuciyar ta take musu adduar shiriya dan baza tayi musu mugun fata ba kuma Allah na gani tayi iya bakin kokarin ta dan ta san abin da suke aikata wa ba abin arziki bane, ta bar ma Allah saboda duk zagin da mutanen unguwa suke mata yana dawo wa kunne ta a cewar su "dan ba yarinyar ta bace shiyasa ta barta tana yin abin da ta ga dama". Amma ita ta san d'a a wannan zamanin ko kai ka haife shi sai kayi hakuri da shi.
* * * * * * * * *
To bayan sallar isha'i ne Daddy ya ce wa Momy "ta je ta kira masa yaran gidan zai yi magana dasu". Ba tare da tayi musu ba ta ce mai "to".
Falo ta fito in da ta kwalama Suwaiba mai aiki kira, nan take suwaiba ta zo tace "na'am". Momy tace "haura sama ki kira min yaran nan, ki tabbatar kin fada ma ko wacce su".
"To Hajiya".
Suwaiba ta fada kana ta
Showing 30001 words to 33000 words out of 51717 words
Chapter 20
______Sun d'auki kusan mintuna goma shabiyar a haka batare da d'ayan su ya yi 'kwa'k'kwaran motsi ba sai sautin bugun zuciyar Sadeeq dake sauka fat fat, Siddeeqah kuwa duk da akwai na'urar sanyin dake saka cikin motar sanyi saida ta jike da gumi sharkaf idanuwan ta sun dad'a fitowa waje, dago raunannun idanun sa yayi da suka koma launin gwauta saboda tsabar bacin rai ya sauke su akan na Siddeeqah, da sauri ta maida kanta kasa tana wasa da y'atsun hannun ta zuciyar sa ce take ingiza sa da ya shake mata wuya wata zuciyar kuma ta ce masa "Kul Sadeeq ka kashe gawar da ba taka ba, ka bud'e mata mota ta fita" haka kuwa akai yabi shawarar zuciyar da ta gar gad'e sa soboda haka ya bude mata murfin motar Siddeeqah naji ya bud'e tayi sauri ta bude murfin ta fito har tana neman dungurawa a kasa soboda yanayin Sadeeq d'in yayi mugun bata tsoro da sauri da sauri take tafiya jefa kafar ta kawai take batare da tasan inda take jefewa ta ba, ji tai ta ci karo da mutum a tsorace ta ja da baya ganin Sadeeq ne yabiyo ta d'ayar hanyar da ake iya haduwa da Wanda yabi ta gaban gida, yanda taga yanayin sa har yafi d'azun firgitar wa idanuwan sa sun kara yin jaa kamar Jan gauta, nufo ta ya fara yana d'an Murmushi yana shafa sajen sa, 'kafa mai naci ban baki ba gudu ta fara shima ya mara mata baya cikin ikon Allah saiga Momy a harabar gidan da alamar wani abu take ne ma saboda idanuwan ta a kasa suke, da gudu Siddeeqah taje bayan ta ta 'boye tana nishi "ke lafiyan ki kuwa daga ina haka kamar an koro ki?". Momy ta fad'a tana duban Siddeeqah Bata lura da Sadeeq ba, da hannu Siddeeqah ke nuna mata inda Sadeeq yake sai alokacin Momy ta dube sa, washe baki yai ya wayance yace ma Siddeeqah "ba dai kin ki bari na kama ki ba nima zan rama yarinya, waifa Momy ce mata nayi ta jirani mu taho tare shine ina gama faking ta rigani fitowa shine nabi bayan ta da ta hango ni sai tafara gudu nima shine na biye mata". Siddeeqah kamar sakarya haka ta saki baki da hanci tana kallon shi lallai ya iya tsara labari,
cikin gamsuwa da abinda ya fad'a Momy tace "ai da baka biye mata ba yarinya ce, amma gaskiya kun dade ko ka kaita wani gurin ne? Daddyn ku na ta kiran ka a waya baka dauka munyi tunanin ko ba lafiya ba hankali ya fara tashi".
"Wallahi lafiya lau Momy layi muka tarar a gurin saloon d'in, amma me ya fito dake naga kamar wani abu kike nema?".
"to babu damuwa, eh wallahi d'an kunnen Jiddah ne guda daya ya fad'i sanda suka dawo daga asbiti".
Tace "anan ya fad'i shine nace bari na duba ko zan gani".
"haba Momy ke da kanki ina sauran yaran gidan?".
"Suna ciki Khadija ta ce ta gaji zata shiga ta huta dan ko abincin rana bata ci ba, Umar kuma yana tare da Jiddah, Ummi kuma tun safe ban kuma ganin ta ba".
"Kibar neman haka Momy muje ciki ba rabon ta bane kawai sai asai mata wani".
"dama a cikin irin tsara bar da auntyn kaduna ta kawo musu ne alokacin da ta dawo daga India daham ne yanada tsada sosai yanzu ita kadai ce ba ta da".
"Momy ita ta jawa kanta".
Siddeeqah kamar ruwa ya cinye ta Momy ce ta kama hannun ta tace "muje ciki yau na girka abinda ki ka fi so a bincin gargajiya".
"dan Allah fa Momy?".
"zan miki 'karya ne?".
"a a Momy".
Ta fad'a tana rufe fuskan ta da tafin hannun ta ahaka suka karasa cikin gidan Siddeeqah na mamakin Sadeeq,
Yayin da shi kuma ya ji haushin ganin Momy a harabar gidan batare da ya ma Siddeeqah matsiyacin duka ba dan so yayi ya mata dukan ban kwana saboda ba lallai ya kuma haduwa da ita ba har sai ta dawo hutun makaranta, yanda bazata manta dashi ba
♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾
Kamar wacce tayi karya takai ta komo tarasa ina zata sa kanta dafa kafad'ar ta akai da han zari ta dago kanta ganin Lubancy ce Kawar ta yasa Zuby sauke ajiyar zuciya tace "kawata kin zo a dai dai dan dama yanzu nike shirin zuwa gidan ku wallahi ina cikin tashin hankali nasan babu Wanda zai fitar dani saike".
"haba ke kuwa kinada ni kike cewa kina cikin tashin hankali kin manta wace ni kin manta kirari na? Bari na na tuna miki".
"a a barshi ban manta ba kai na ne ya kulle na rasa mai yake min dadi, sai yanzu dana ganki na ji sauki a raina nasan ke a wurin ki ba komai bane soboda na shiga matsalar da tafi wannan kuma kin mini maganin ta".
"yauwa yar gari ashe baki manta da wace ce kike tare da ita ba".
Zuby tace "kawa ta mu zauna na baki labarin abinda ya sa na shiga cikin tashin hankali".
Saida Lubancy ta je ta bude karamin fridge din dake dakin ta dauko goran lemu sannan ta dawo ta zauna a bakin gado tace
"ina jinki".
"ina wannan gayen da nike baki labari Wanda na had'u dashi a Instagram kwanaki kin tuna shi?".
"Eh anyi haka na tuna to mai ya faru dashi ko shima an fad'a masa halin ki ne".
Lubancy ta fad'a haka tana duban kawar ta
"ko daya kawa ta nan take Zuby ta kwashe duk abinda ya faru ta fad'a ma Lubancy,
tsaki Lubancy taja kana tace "wallahi Zuby kina bani mamaki d'an karamin abu duk ki bi ki tada hankalin ki ba kin ce yana soki ba?".
"Eh yana sona na gani a cikin 'kwayar idanun sa".
"kuma kince yarinyar suna kama".
"wallahi suna masifar kama abinda ya bani haushi" da yace" min 'yar mai gadin su ce baki ga yarinyar ba kama da larabawa take yi".
Lubancy tace "dadi na dake gajen hakuri da kin bisa a yadda yace idan ma da wata a 'kasa zamuji daka baya, kince kina son sa kuma auren sa zakiyi kin tafka kuskure da kika ce masa karya yake saboda shine gaba dake, amma ko nan gaba ki kiyaye kisan kalar maganar da zaki dunga gaya masa, Zan san yadda zamu bullo wa lamarin, saboda nima yanzu tawa ce ta kawo ni tun jiya da muke chart kika fad'a min kin gama al'adar naji kamar nayi tsun tsuwa nazo saboda nayi missing d'in ki ".
"Kawata kenan wallahi bakida hakuri". Zuby ta fad'a tana zuge zif d'in rigar ta,
ita ko Lubancy dama doguwar riga ce ta zumbulo sai undies da ta saka nan take ita ma ta cire doguwar rigar tayi cilli da ita ta kamo Zuby suka 'karasa cire ma juna kaya,
sosai Lubancy ta rikice saboda Zuby Allah ya yi mata baiwar komai bata da makusa a halittar jikin ta shine ke rud'an maza
sakonni suka fara aika wa junan su sosai suke romance suna ihu. Babu inda basa tabawa a jikin junan su
Wa'iya zu billah lallai halin Zuby sai ita baza taso Sadeeq ya sani ba dan shi kamilar mace yake so ya aura,
ja musu 'kofar nayi ina takaicin rayuwar Zuby
♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾
Ina cin danbun ina side yatsun hannu na Ummi na hango tana sauko wa daga sama dinning din tazo ta zauna da alamar daga bacci ta tashi saboda yadda idanuwan ta sukayi, kallo na tayi tace "maiyar dambu sai kace kin samu wani abun dadin, ko naman kaza baki masa irin wannan santin, ni kuma wallahi na tsane sa dole nike ci nasan Daddy ne yasa Momy tayi dan shima yana son dambu".
Nace "yarinya da kinsan kalan dadin da nike ji alokacin da nike cin dambu da ko magana aka ce ki min bazaki ba saboda idan zan baki amsa a cikin santi zan baki yanzu dai bari na gama sai ki sake maimaita abinda kika fad'a".
Ummi tace "tab sai na tsaya har sai kin gama kamar yarinyar ki bani da wannan lokacin bari naje ko Indomie na dafa dan yau ba zanci danbun ba".
"ke dai kika sani idan za a shekara ana jera yin dambu babu abinda zai dame ni".
"uhm". Ummi ta fad'a ta nufi hanyar kitchen
Umar ne tafe rike da hannun Jiddah tana ta ciza lebe ahankali suka karaso gurin Umar yai sauri ya ja mata kujera tai saurin dakatar da shi da fad'in "Umar mai kake shirin yi haka to wallahi na daina had'a gurin zama da wannan 'yar kauyen muje falo idan ta gama sai nazo muci".
Kallon ta nayi na kwashe da dariya nace "da alamar har yanzu bakin ki bai mutu ba".
Umar na kalla nace "wai ka nuna mata madubi kuwa? na tabbatar da taga yadda nayi mata da ko suna na taji an ambata gaban ta ne zai fad'i dan Allah idan bata ga ni ba maza je ka d'auko saboda ina son ta san ruwa ba sa'an kwando bane".
"Aunty Siddeeqah dan Allah ku daina wallahi banajin dadin hakan ko kadan". Umar ya fad'a kamar zai rushe da kuka
ganin haka yasa nace "to shikenan kani na ya wuce amma kaja mata kunne kasan ni duk Wanda yai min kan kara na itace nake masa".
Umar yace
"Aunty Jiddah muje".
A masifan ce Jiddah ta kwace hannun ta fuuu ta wuce falo ta zauna tana kananun magan-ganun da ita kadai tasan mai take cewa
🤙 _Hy guys please don't forget to comment vote and follow me on Wattpad join my group on Telegram please please please_ 🥰
NI DA YAYA SADEEQ
˙·٠•●♥ بسم الله الرحمن الرحيم ♥●•٠·˙
Chapter 21
So sai Siddeeqah take dariya harda rike ciki, tana ayyana yadda zata gyara ma Jiddah zama dan wallahi ta daina daukar rainin hankali
Take Umar ya mara ma Jiddah baya yana ma-ma kin tsanar da suka ma juna kamar ba 'yan uwan juna ba
A zaune ya sami Jiddahn a kan kujera sai cika take tana batsewa tana ganin sa ta daure fuska tace "mai kazo yi wuce ka bani guri munafuki ni zaka raina ma hankali a gaba na za ka dunga yiwa waccan yar kyauyen magana? Har da ce mata aunty saboda munafurci na cin ka". Ta karasa maganar tana nuno masa inda nike
shi dai Umar bai ce mata komai ba sai ma-maki ma da ta kara bashi
Jin kamar ana hayaniya Momy ta fito da Alamar daga bacci ta tashi, a dai dai lokacin Ummi ta fito daga kitchen hannun ta dauke da plate din abin ci, kallon mu Momy ta shiga yi ido cikin ido daga karshe ta sauke su akan Jiddah tayi mata kallo irin na gar gadi, ba tare da tace mana komai ba ta koma ciki abin ta
Ummi kuwa zama tai a dinning din tana fadin "wash Allah na".
Kallon ta nayi nace "kefa raguwa ce daga dafa Indomie sai kizo kina wash kamar wacce tayi abin a zo a gani?".
"Bazaki gane bane". Ummi ta fada tana kai lomar Indomie
Shi kuwa Sadeeq tun sanda suka shigo ya haura sama soboda yana bukatar ya huta dan zubi ba karamin bata mishi rai tayi ba sosai yake ma-ma kin ta dan shi baya son rashin kunya musamman ma idan yasan ya girmi mutum to yana so a girma ma shi, a gogan hannun sa ya cire tare da lalu ba aljihun sa ya ciro wayar sa ya aje a kan madubi kana ya shiga cire kayan jikin sa, wannan ita ce dabi'ar Sadeeq a duk sanda zai shiga wanka sai ya fara cire kayan sa a bedroom sannan ya ke shiga bayi, to bayan ya shiga ya dauki kusan mintuna 43 a cikin bayin yana cuda jikin sa ya zuba wancan ya zuba wannan sai da yaji kam shin ya mishi yadda yake so, sannan ya fito daga cikin kwamin wankan ya zo gurin da tawul yake a rataye ya daura a kugun sa kana ya dauki karami ya shiga goge kansa daga haka ya fito a bayin
* * * * * * *
A ban garan su Zuby kuwa bayan sun gama fasikan cin su suka shiga wanka nan ma sai da suka bata mintoci suna kissing din juna kamar wasu mata da miji Zuby ta manta da wani Hallita mai suna Sadeeq saboda Lubancy ba baya ba wajen romance ta iya solon makirci da yaudara kala kala
Bayan sun fito daga wan kan ne suka shafa mayuka masu kam shi tare da fesa body sprea riga da wando Zuby ta dauko a cikin durowar ta kana ta duby Lubancy tace "sweety wani kalar kaya zan fiddo miki?".
"My love duk wanda kika dauko min zan sa". Lubancy ta fada cikin salo mai Jan hankali
To bayan sun gama shirya wa suka shiga fesa tura ruka masu sanyin kamshi gami da daukar hankalin wanda duk a ka gibta ta kusa dashi,
Hijabi suka zum bula har kasa tare da saka safa a kafar su ke idan ki ka gansu zaki rantse mutanen arziki ne
Falo suka fito inda suka tar da Mama zaune tana kallon BBC World news, ta maida gaba daya hankalin ta da nutsuwar ta akan TV
Kamshin tura-ran tilon diyar ta-ta a duniya ne ya dawo da ita ga barin kallon TV
kallon su tayi cikin sakin fuska tace "kar dai har zaki tafi?".
Mama ta fada tana duban Lubancy wacce ke tsaye tana dan Murmushin tace "Eh Mama zan tafi dama sako na kawo mata".
Kallon Zuby Mama tayi ta ce "iya rigima ina zuwa kuma? ko rakiya zaki mata".
"Eh mama". Zuby ta bata amsa a takai ce
To babu damuwa ki dawo Lafiya amma gaskiya yau kar ki dade kin San abban ki yana gari, motsi kadan yace "kina ina?". Sai dai nayi masa karyan kan ki na miki ciwo kina bacci kin ce kar a tashe ki har sai kin tashi, kiss Zuby ta manna ma Mama a goshi tana fadin "Allah ya bar min ke Mama na I love you". "Love you too". Mama ta fada tana dariya irin ta-su ta manya da yike ita ma irin gogag-gun iya yan nan ne, kuma ta san da duk wani abu da diyar ta-ta take aika wa asali ma ita ce ta sata akan hanyar
* * * * * * * *
To a bangaren Sadeeq kwance yake a kan make kyan gadon sa idon shi a rufe kamar mai bacci amma kuma ba bacci yake ba a duniyar tunani yake
Wayar sa ce ta shiga ringing amma be da niyar dauka har kiran ya katse saida a ka sake kira a koro na biyu ya bude raunan-nun idanun shi ya lalabi wayar ganin sunan Farooq na yawo akan screen d'in wayar ya danna picking kana ya kara a kunne
daga can ban-garen Farooq yace "kai bana son iya shege tun dazun nike kiran ka baka dauka ba, ba yan kasan haka kawai ba zan dunga kiran ka ba".
"Ina jin ka to". Sadeeq ya fad'a yana cin magani
Farooq ya kwashe da dariya yace "dan iska wannan ji da kan naka ba shi zai sa a dunga maka abinda ka ke so ba, ni dai kasan ba tsoran ka zan ji ba ko?".
Cikin jin haushin kalaman Farooq Sadeeq yace "malam ya i she ka haka ka fadi abinda ya kawo ka ina jin ka".
Farooq yace "akan maganar makarantar matar ka ne na gama magana da wannan abokin nawa da yake koyar wa a makarantar ya sama mata admission yace maganar aji sai idan an kaita sun mata interview zasu gane ajin daya dace da ita, saboda haka daga yau zuwa kowace rana zaku iya kaita dan har register yai mata ".
Shiru Farooq yayi ko Sadeeq din zai ce wani abu amma sai yaji a kasin haka,
Bayan wasu yan daki ku Sadeeq yace "ka gama?".
Cikin takai cin abokin nasa Farooq yace "dan iska insha Allah wannan yarinyar da ka ke rainawa sai ta zame maka ciwan ido, yana gama fad'ar haka ya kashe wayar sa
Aje wayar sadeeq yayi gami da daga kafada alamar ko in kula ya tabe baki a can cikin zuciyar sa yana jin dadin zai rabu da ala ka kai
NI DA YAYA SADEEQ
˙·٠•●♥ بسم الله الرحمن الرحيم ♥●•٠·˙
Chapter 22
To bayan fitar su Zuby gidan su Lubancy suka zarce dake wata unguwa amma unguwar ba ta masu kudi can bace, kuma ita Lubancy iyayan ta sun rasu tun tana yar karama, a gurin kawun ta take, kasance war sa namiji ba ko da yaushe yake gida ba shiya yasa Lubancy ta zama abar da ta zama yanzu duk da matar kawun na kokari amma sam Lubancy ta raina ta bata jin maganar ta, ganin Allah bai bata haihuwa ba kar ta cika matsawa ace dan bata son zafin yara bane shiyasa ma yanzu ta zuba mata idanu, in dai duniya ce wanda bai zo ba ma jiran shi take.
Duk da sun sami matar kawun a tsakar gida, haka su ka wuce ta ba tare da sunyi mata sallama ba, da shigar su dakin Lubancyn suka wuce suna wani shan kamshi.
A cikin zuciyar ta take musu adduar shiriya dan baza tayi musu mugun fata ba kuma Allah na gani tayi iya bakin kokarin ta dan ta san abin da suke aikata wa ba abin arziki bane, ta bar ma Allah saboda duk zagin da mutanen unguwa suke mata yana dawo wa kunne ta a cewar su "dan ba yarinyar ta bace shiyasa ta barta tana yin abin da ta ga dama". Amma ita ta san d'a a wannan zamanin ko kai ka haife shi sai kayi hakuri da shi.
* * * * * * * * *
To bayan sallar isha'i ne Daddy ya ce wa Momy "ta je ta kira masa yaran gidan zai yi magana dasu". Ba tare da tayi musu ba ta ce mai "to".
Falo ta fito in da ta kwalama Suwaiba mai aiki kira, nan take suwaiba ta zo tace "na'am". Momy tace "haura sama ki kira min yaran nan, ki tabbatar kin fada ma ko wacce su".
"To Hajiya".
Suwaiba ta fada kana ta
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11 Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18