da Amina da yaranta sun koma asibiti an yi ma yaran Shayi na pampers har sun warke,Yaran sun yi Kiba sun yi Bulbul Saboda Amina Nononta mai kyau ne sannan Danmallan kullum sai yazo ya Dubasu Safe da yammah kwana ne yake yi Wajen Sarood Amina bata dai nuna Damuwarta ne ammh fa abun na cin Ranta,Don ma Yakaka na mata Fada sannan ta Dage da kokarin gyara Amina kamar yadda tayi alkawari hakama Anty Hadiza ba"a barta abaya ba Tana kokarin gyara Diyar tata.
Hajiya na Shirin samun Danmallam da mganar Sakina sai gashi yazo yana mata mganar Sarood zata koma Madina sun koma makaranta shi zai jira in Amina ta gama wankan jego su tafi Tare Hajiya batace komai ba tace Allah ya Tsare daganan ne tamai mganar Sakina sai ya nuna mata Sakon Datake Turamai na ban hakuri
Harda mganar cire mata mahaifa da akayi Hajiya jikinta ya karayin sanyi da Rayuwar nan ta kalli Danmallam cikin wani yanayi tace"Kayi hakuri Danmallam in har baka saketa ba kaje ka Daukota ka maidata gida..Na tabbata ta ga Ishara ga abubuwan da suka faru. !
Danmallam yace"Ban saketa ba Hajiya..Sai dai ina tsoron na Sake Dawo da ita ta batamin zama na..Ta Rikitamin gidana Hajiya. !
Hajiya tace"Bazatayi haka ba..Insha Allahu..!
Kai ya kada kafin yace"Shikenan insha Allahu in na gama chukun Chukun Tafiyar Sarood zan je na Taho da ita .!
Hajiya tace"Allah ya bada iko..Sannan ina so in kun sun samu Lokaci kai da su Nasir da Jafaru kuje ku Duba su Uwani da Marliya suna cikin wani Hali.
Bai yi gaddama ba ya amsa mata Domin sunyi mganar dasu Jafar zasu je su Dubasu ciwo ya kore komai ko don Darajan zaman tare da kuma ya"yan da suka Haifa.
Danmallam ba yi gigin Fadama Amina zai Dawo da Sakina ba asatin aka sama ma Sarood Visa ya kawota sukayi sallama da Amina yana zaune yana kallon Amina da mamakin yadda yaji labarci na Fita abakinta Kanar wacce ta zauna a madina bai Taba Sanin ta iya ba ballatana yayi Zaton tana ji..
Ta bama Sarood Atamfa da Su Turare da Sabulai Saboda ta mata kokari Sannan ta Dauki su Aba da suka yi Wayau ta Rumgumesu har Yakaka sai Yabon Sarood take yi,Haka ta Rumgume Amina suka rabu kan sai sun zo tunda Danmallan yace tare zasu Taho da Amina ita Aminar bata ma san mganar ba.
Daganan gidan mallan ya kaita tayi musu sallama Hajiya ta bata Turaren Wuta tace ta kaima Mami Sara.
Washegari ya kaita kano Jirgin yammah Tabi zuwa Jidda dare yayi mai ya kwana a Hotel da Safe ya Dawo.
Lokacin Amina saura kwana Uku tagama wanka Danmallan nata musu Shirin komawa Madina Hajiya tayi mai bakam sai da Amina tayi arba"in yayi mganar Tafiya Hajiya tace sai ta Zaga yan"uwanta ransa ya baci sai dai bai nuna ba gashi yana son kebewa da matarsa an hanasa da gangan Yakaka ke Tsare waje in ya shigo bata so basu gama gyara ba ya bata musu saboda ta Lura ita kanta Aminar Ja'ira ce..!
Kwana Biyu da arba"in dinta suka fara yawo ta fara zuwa Hadeja wajen goggo Jumai ta kai musu Yaran ta gani ta saka albarka suka kwana Daya ita da Yakaka Idi yakai su bayan sun Dawo Washegari suka tafi gusau wajen kwanansu Hudu,Har asibiti taje ta Duba Mamanmu Halin Data ganta sai da taji ta manta da komai ta yafe mata Ya Jamela ta rakata Mamanmu na Hawaye Amina ta Dora mata su Aba Ajikinta haka take son tayi mgana ba hali Hannunta mai Lafiya ta saka ta Dafa kansu tana hawaye ya Zeenatu suka samu a wajenta tana kula da ita raba raba suke da junansu.
Amina ta yawata Dangin Aba kusfa kusfa Har kwana sai da tayi agidansu Zafira,suka sha Hira Yakaka kuma ta Shige Cikin Dangi kamar yar gida Ta zama yar gidan baba mallam yanzu.
Ranar da suka Dawo gidan mallam suka kwana washegari suka tafi Dutse Gabadayansu har ya Danmallam da Su Ya jafar da Hajiya ta koma suka Duba Anty Amarya data koma bata mgana sai kuka duk ta Firgice wani Lokacin in abun ya tashi sai an Daureta Amina da su ya Jafar sun kara jin Tsoron Duniya Sadiya ta nan tare da ita Sannan sunga Sakina Amina tayi mamaki Sakina har da karban su Aba duk ta rame sai Amina taji ta bata Tsausayi basu Dade ba Daga Dutse Tsafe suka wuce chan din ma sai ahankali Hajiya uwani dai ba wani Cigaba tayi ta rokonsu Danmallan da Amina Gafara Allah yasa ita da Bakinma sai dai Ciwo duk yaci Jikinta Nazifa ta koma sai Yan"uwan Hajiya uwani ke kula da ita itama har Su Aba aka Doramata kan jikinta tana kallonsu tana Kuka.
Da zasu Dawo suka Dauko Umaima suka Dawo da ita,Umarnin mallam ne
Washegari kuma su ya Danmallam suka je gusai suka Duba mamanmu Suma kansu jikinsu yayi sanyi Tana kuka ba baki tana mika musu Hannu Tana neman gafara sukace sun yafe mata Duniya da Lahira sun bama Zeenatu kudade kafin su kamo Hanyar gida suna Hirar yadda Allah ke nuna ishara da izina tun a Duniya.
Amina taso taje gidajen yan"uwanta Mata Mallam ya hana yace ta shirya tabi mijinta alokacin Sai Hajiya ta hana tace sai dai yaje ya Dawo ,sai ya tafi da ita Lokacinn yaran sun kara wayau bazai Daukesu tana Danyen Jego ya Hau jirgi da ita.
Sannan kuma zatayi Jarabawaarta ta Fita alkawari tayi kuma sai ta cika.
Mallam sai yama kasa mgana Daga baya yaso ya nuna ma Hajiya bata isa ba sai dai data mai bayani sai ya gane gwara Amina tatafi da Tarkadunta sannan yaran su kara Wayau shi ya Lallashi Danmallam da bai da tacewa Hajiya ai tagama dashi.
Ya samu Amina yana mata magiyan taje tace ma Hajiya ita zata Bisa su tafi Amina tace bazata iya ba sai yayi Fushi batare da sanin kowa ba ya Nema ma kansa Visa shi da Sakina Sai ana Saura kwana Biyu Tafiyarsu yaje ya Daukota Sakina sai da tayi kuka har ta cire rai da auranta da Umar ganin san da suka zo ko fuska bai Sakin mata baHakama yan"uwanta nata jin Dadi,Gidan mallam ya fara kaita Hajiya da mallam suka Taru suka mata Nasiha mallam kanshi yaji Dadi yadda Umar ya zama mai Afuwa
Sai alokacin yake shaida musu jibi zasu koma Madina shi da ita Hajiya tasan don Turama Amina Haushi yayi sai bata nuna mai ba kuma bai Fadama Amina zai koma ba Dauke mata kafa yayi ana gobe Tafiyar yazo yaga yaransa ita tana barci sai da Safe Yakaka ke Fadamata,Bata san ya tafi ba Sai da sukayi waya da ya Aisha take Fadamata Ya Danmallam ya tafi da Sakina itama Hajiya ke Fadamata Ranar Amina wuni tayi kuka Yakaka na lallashinra abun fa da Ciwo aiko bai Fadamata komai ba ya Fadamata Zai Dawo da Sakina ammh Duk Sai dai Taji Daga sama itama sai ta Zuciya ta Cigaba da kula da kanta da ya"yanta.
An biya mata Jarabawar ta a Unity dinsu da an fara zata fara zuwa sannan Huce Takaicin abunda Danmallam yayi musu Hajiya ta saka Baki mallam ya barta sukaje Abuja suka kwana Biyu ita da Yakaka dagachan har da ya Aisha suka Dumguma sai Zaria wajen Hamida suka kwana Daya gidanta suka kwana Gidan ya Zulfa suna ta murna da ina suka saka da yan"uwansu sun je har kaduna gidan Abida sun je kano gidan ya Jidda Lagos ne da parthercourt yayi nisa basu je ba Amina ta taka yola Wajen Hanne sai gata agidan Aminu Taga Nenne Dangi kuwa sai zuwa ganin Aminan Aminu ake yi yara kam sun sha Dauka shi kanshi Aminun ya kasa sukunu ya siyo wannan ya siyo wanchan,Amina sai yi ma Hanne Tsiya take ganin ta da Ciki.
Kwanansu Biyu suka Dawo Gida suka Sauke Gajiya..
Danmallam bai nemeta ba itama kishi da Haushin Abunda yayi mata ta yi biris dashi,Shi ma Yayi zuciya ransa ya baci da abunda tayi mai sannan kuma bayan ya tafi bata nemesa ba abakin Mallam yaji Tafiye Tafiyen da Amina tayi ko izininsa ba"a nema bai Taba Jin Haushi in Hajiya ta yanke Hukunci kan matansa ba sai kan Amina ya Lura tafi son Ma Amina da kowa komai take so shi take yi..
Amina Taurin kanta bai barta ba,Tana nan dashi shiyasa ta nuna ma Danmallam kalanta Har Yakaka taji Haushinsa Sai dai tayi ta lallashin Amima kada ta Damu sai ya Nemesu.
Ana cikin haka suka fara WAEC ta Dinka sabbin kayan makaranta ta fara zuwa Ranar datake da paper yakaka take barin ma yaran Agidan mallam in ta Dawo sai ta biyo sai yammah su koma gida Domin yakaka bazata iya Ronon yaran ita kadai ba gasu sun fara girma da kiba suna samun kulawa sosai..
Tana kokarin ya kice Takaicin Danmallan aranta taurin kanta yasa bata ko nemesa ba shima yaki nementa Amina tasan yaushe zai nemeta yanan chan wajen Guzumanyen matansa ita kuma tana nan tana mai renon ya"ya..!
Zai gane shayi ruwa ne da Aminene yake zencen..!
*Godiyata ta musamman ga iyayena guda biyu da sune silar tsayuwa kan kafafuna da nayi ayau din nan Alhaji Umar Muhammad mailoki da Malama Hadiza Muhammad Ba"are,Baba, mama ina matukar godiya da jajircewan ku akaina Ina godiya da Goyon bayanku ina godiya ga Allah da kuka kasance iyaye nagari a wajenmu Allah ya saka muku da Alheri ya muku Tukwaici da gidan Aljannah Firdausi Ameen Ina matukar son ku Babanmu da Hajiya mama tamu Allah ya kara muku nisan kwana da kwanciyar Hankali Ababen Alhafarinmu..*
*Janafty**TFZB2031*
*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yada'ashi..Pay N500 via Jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan lambar 09069067488*
Shifa Namiji duk inda yake sai ya nuna kansa barin ma in yana da mace fiye da Daya,Sannan su fa abunda muke kallonsa abun kunya a wajensu Daidai ne kuma mai kyau ne sannan in zaki shekara kina kyautatamusu Rana Daya in kika karkace sai ya manta baya ya Dora miki laifin duk Duniya akanki sannan ba kasafai suke Fahintarmu yadda Ubangiji Ya bamu ikon mu fahimcesu ba.
To kamar haka ya faru Tsakanin Danmallan da Amina ko yaya ne so yake ya nuna mata ba ita kadai garesa ba in bata bishi ba ai ya tafi da Sakina Sannan yayi hakane domin ya kure Hakurinta yana ganin kamar in ya tafin zata nemesa ta basaa hakuri sai kuma yaga akasin haka ya fahimci Tana da Taurin kai da kafiya domin shima Daurayewa yake da bai nemeta ba shi adole sai ta nemesa ta basa Hakuri sannan su sai su daidaita ammh Ina Sai ya Fahimci Amina tayi nisan da batajin kira.
Wajen watansa Biyu da Tafiya ko Flashing bai taba mata ba, itama haka Sai dai ya Kira Hajiya ko mallam yaji Lafiyansu wani Lokacin ma suna gidan in Amina ta tafi Jarabawarta koda wasa bai bari kowa ya Fahimci akwai baraka Tsakaninsa da Amina ba ballatana ita data share batunsa Sai dai Yakaka Datake zaune da ita ta Fahimci Tsakanin ma"aurata basa mgana Dole wani abu na faruwa.
Amina sun gama WEAC dinsu Cikin Nasara suna jiran Ta gaba lokaci Daya tana kula da ya"yanta sai kuma alokacin Danmallam ya gaji da Jiran Amina ta Kirasa su sansanta shi ya Sauke Girman ya Kirata taki Dauka Har sai da ya jera mata wajen sati yana Kiranta Tana gani bata taba Dauka ba sai abun ya kara bashi mamaki gashi dai anan hankalinsa yana kwance ne saboda Sakina tayi Laushi Sosai kamar ba ita ba,ga Sarood Daman bata da Hayaniya Cikinta ya shiga watansa na bakwai kusan duka ayyukan Sakina ta Dauketa mata ita ke yi tace Sarood din ta Huta duk yadda yake jin Haushin Sakina Sai da ya Tsausayamata da aka cire mata Mahaifa,duk son ta Haihu Allah ya nuna mata nasa ikon Da Farko bai Sakar mata ba sai daga bayaa shima din ba Sosai ba kadahan kadahan dai kada ya shiga Hakkinta sannan ya Duba Nasihan mallam da Hajiya ammh Daidai da rana Daya bai taba mantawa da Amina ba yana Madina ne ammh gabadaya ransa da Tunaninsa na Nageria wajen Amina da ya"yansa yaso ya jure sai ya kasa ammh Sai gashi yana kiranta bata Daga wayarsa.
Daya Dameta sai ta Fara Dagawa ammh yayi sallaman Duniyan nan tayi mai bakan sai da yayi ta jin kananun kukan su Aba na yara tun yana ganin Lamarin nata wasa har ya Fahimci abun nata yayi nisa,Ita kuwa yadda Danmallan ya kunsa mata Bakinciki ya raina mata wayau ne ta Dauki alkwarin sai ya gane bai da wayau sai yasan ya wulakantata Shiyasa ko da yazo yana kiranta Daga baya bata Taba bashi Dama ba Tayi alkwarin sai ta rama Fiye da yadda yayi mata sannan ta koyamai Darasin da har Abada bazai kara gigin mai da ita mara amfani a wajensa ba !
Yakaka Tasan basa mgana da Mijinta ammh bata taba mata mgana ba Sai Ranar Aba na wajenta mallan ne ke wajen Amina tana basa Nono,ta kawo mata shi kenan ta iske waya gefen Amina ta saka ta speaker Muryan Danmallan Tar yana mgana sai magiyan kiran sunan Amina yake yi tayi kamar bata ji ba, Hankalinta ma na kan bama Mallam Nono kamar yana Kiran Dutse..!
Fadi yake yi "Noor don Allah ba don Halina ba kiyi mgana..!
Amina haba Amina..Haba Amina da Allah fa nake hadaki..Nasan kina jina..!
Kiyi mgana saiki fadamin Laifina i Promise you zan baki Hakuri..!
Kinji Amaryata..!
Amina tayi wani Dariyan rainin Hankali har sai da yaji aranta tace su Amarya an ji jiki ai baka san ni Amarya bace sau na nuna maka matsayina..!
Yakaka na bakin kofa baki ta saki Tana Bin Amina da kallo Har Danmallam ya gaji da magiya ya Datse kiran Sannan ta kariso Dakin koda Amina ta ganta bata Damu da taji ko bata ji ba yadda ta yi nisan nan Mallam ko Hajiya ne kadai zasu saukar da ita Su kuma tana da Tabbacin ya Danmallam bazai bari su sani ba..!
Mallam ta karba ta miko mata Aba Amina ta karbeshi tana bata rai tace"Ni wlh na fara gajiya yaran nan duk sun gama tsotseni na fara yamushewa..!.
Tafada tana wani Tura mai Nonon a baki ruwan nonon ya kawo yaran ya Shake ya fara Tari Yakaka tayi Saurin Ijiye mallam Kan gadon Amina ta karbesa ta Daga sa sama tana shafa Bayansa Cikin Lallashi Lokaci Daya Tana Hararan Amina data kauda kanta Gefe kamar bata ganta ba..!
Cikin Ikon Allah aka samu yayi barci ta Lallaba ta kwantar dashi gefen Dan"uwansa sannan ta Dawo kan Amina tana Fadin"Ashe zama na Dake bamai amfani bane Amina..?.
Ina ga gwara nayi tafiyata sai ki zauna ki yi yadda kika ga Dama..!
Yakaka ta fada Cikin bacin rai ta Juya da Niyyar Tafiya Amina ta mike ta Riko Hannunta tana Fadin"Haba yakaka me kuma ya faru..?
Yakaka ta juyo tana Hararanta tace"tambaya ta ma kike me ya faru ko..?
Ai kina Sane Mijinki ya kiraki kin Dauka kina ji yana mgana kin yi banza Dashi Sannan kina bama yaro nan Nono kina mai mugunta kina so ki kashe ya"yanki ne..?
Kada ma kiyi Tunanin domin kun samu matsala da Babansu kike jin Haushin su yaro ina ruwansa..?
Sannan ki Sani yaki dan zamba ne Amina kuma abunda Hakuri bai baka ba Wlh Tsiya bazai taba baka shi ba. !
Kawai sai Amina ta saka kuka ta sanya Tafukan Hannayenta ta rufe Fuskarta dashi tana wani irin kuka mai cin rai Kukan Daya Dade yana Damunta aranta sannan Hade yake da Kishi da Takaicin D'a Namiji.
Yakaka sai Tsausayinta ya kamata ta Jawota jikinta ta rumgumeta tana Buga bayanta alamun Lallashi.
Amina sai ta Bude muryanta tana kuka sosai har da Shessheka.
Yakaka na Dafa bayanta Lokaci Daya Tana Fadin"Kidaina kuka Amina. bari kada yaranki su tashi su ga kina kuka. !
Gefen gado ta zaunar da ita tana Share mata Hawaye Amina ta Dago Tana kallon yakaka Lokaci Daya tace"Yakaka meye laifina da ya Danmallam zai min wannan wulakancin..?
Yakaka tace"Me ya faru ne..?
Amina tace"Kan mganar komawarmu Madina tare ne Lokacin da zai koma ai kinsan dani zai tafi Daga baya sai Hajiya ta hana tace sai nayi jarabawa Sannan yara sun yi kwari ko..?
Yakaka tace"Eh anyi hakan..!
Amina na sharan kwallah ta Cigaba da Fadin"To shine fa yazo ya sameni wai sai naje na samu Hajiya nace ni zan Bisa..Ina aka taba yin hakan yakaka..?
Tsakanina ga Allah fa Hajiya matsayin uwa take gareni tana da kimar da zata yanke Hukunci kan abunda ya Shafeni nayi shuru da Bakina Saboda bazata taba aikata abunda zai zama Cuta gareni ba..!
Yakaka tace"Kwarai Amina..Daga ke har Danmallam din Hajiya ta isa ta Zartar da komai akan abunda ya Shafe ku batare da kun Daga ido kun kalleta ba..!
Amina na kuka tace"To shine fa Dalili Saboda nace mai ni bazan iya zuwa nayi ma Hajiya musu ba..Hajiya tamkar uwa take gareni tamin abunda ko Uwata Data Haifeni sai haka Tayaya zata ce ga abunda ya kamata kuma na bata kunya..?
Na fadamai bazan iya ba shima yayi hakuri nan da wata Biyar komai ya Daidaita sai in na koma chan ba Jeka ka Dawo shine yayi fushi Yakaka ya tafi ya Dauko Sakina fa ya tafi da ita yakaka Wlh kin ji rantsuwan musulmai bansan ya tafi ba ko sallama bai mim ba ballata nasan da Sakina zai koma in ya gayamin zan Hanasa ne ai matarsa ce Tare na gansu..Ammh sai yaki Darajani ya saka Kafa ya tafi ya manta Dani Ko waya bai tabamin ba sai acikin kwanakin nan duk wani abun na yaran nan ko kayan abinci sai dai su ya Jafar su kawo ni bai taba mgana Dani ba..Sai yanzu ya san Dani..?.
Yakaka ina Laifina domin naki Sauraransa don Allah..!
Amina ta karishe Fada Cikin kuka Yakaka ta jinjina kai kafin tace"Gaskiya Umaru bai kyauta ba..Nima da Hajiya ta Fadamin da Sakina ya tafi sai da naji ba Dadi to ganin baki min mganar ba yasa nima ban miki ba..!
Amina na jan majina tace"Yakaka ki Duba mganar nan ina Laifina aciki..?
Yakaka tace"Baki da Laifi Amina ai Hajiya tana gaba da Umar bama ke ba..Sannan abunda babba ya Hango ai yaro
Showing 138001 words to 141000 words out of 146831 words
Hajiya na Shirin samun Danmallam da mganar Sakina sai gashi yazo yana mata mganar Sarood zata koma Madina sun koma makaranta shi zai jira in Amina ta gama wankan jego su tafi Tare Hajiya batace komai ba tace Allah ya Tsare daganan ne tamai mganar Sakina sai ya nuna mata Sakon Datake Turamai na ban hakuri
Harda mganar cire mata mahaifa da akayi Hajiya jikinta ya karayin sanyi da Rayuwar nan ta kalli Danmallam cikin wani yanayi tace"Kayi hakuri Danmallam in har baka saketa ba kaje ka Daukota ka maidata gida..Na tabbata ta ga Ishara ga abubuwan da suka faru. !
Danmallam yace"Ban saketa ba Hajiya..Sai dai ina tsoron na Sake Dawo da ita ta batamin zama na..Ta Rikitamin gidana Hajiya. !
Hajiya tace"Bazatayi haka ba..Insha Allahu..!
Kai ya kada kafin yace"Shikenan insha Allahu in na gama chukun Chukun Tafiyar Sarood zan je na Taho da ita .!
Hajiya tace"Allah ya bada iko..Sannan ina so in kun sun samu Lokaci kai da su Nasir da Jafaru kuje ku Duba su Uwani da Marliya suna cikin wani Hali.
Bai yi gaddama ba ya amsa mata Domin sunyi mganar dasu Jafar zasu je su Dubasu ciwo ya kore komai ko don Darajan zaman tare da kuma ya"yan da suka Haifa.
Danmallam ba yi gigin Fadama Amina zai Dawo da Sakina ba asatin aka sama ma Sarood Visa ya kawota sukayi sallama da Amina yana zaune yana kallon Amina da mamakin yadda yaji labarci na Fita abakinta Kanar wacce ta zauna a madina bai Taba Sanin ta iya ba ballatana yayi Zaton tana ji..
Ta bama Sarood Atamfa da Su Turare da Sabulai Saboda ta mata kokari Sannan ta Dauki su Aba da suka yi Wayau ta Rumgumesu har Yakaka sai Yabon Sarood take yi,Haka ta Rumgume Amina suka rabu kan sai sun zo tunda Danmallan yace tare zasu Taho da Amina ita Aminar bata ma san mganar ba.
Daganan gidan mallan ya kaita tayi musu sallama Hajiya ta bata Turaren Wuta tace ta kaima Mami Sara.
Washegari ya kaita kano Jirgin yammah Tabi zuwa Jidda dare yayi mai ya kwana a Hotel da Safe ya Dawo.
Lokacin Amina saura kwana Uku tagama wanka Danmallan nata musu Shirin komawa Madina Hajiya tayi mai bakam sai da Amina tayi arba"in yayi mganar Tafiya Hajiya tace sai ta Zaga yan"uwanta ransa ya baci sai dai bai nuna ba gashi yana son kebewa da matarsa an hanasa da gangan Yakaka ke Tsare waje in ya shigo bata so basu gama gyara ba ya bata musu saboda ta Lura ita kanta Aminar Ja'ira ce..!
Kwana Biyu da arba"in dinta suka fara yawo ta fara zuwa Hadeja wajen goggo Jumai ta kai musu Yaran ta gani ta saka albarka suka kwana Daya ita da Yakaka Idi yakai su bayan sun Dawo Washegari suka tafi gusau wajen kwanansu Hudu,Har asibiti taje ta Duba Mamanmu Halin Data ganta sai da taji ta manta da komai ta yafe mata Ya Jamela ta rakata Mamanmu na Hawaye Amina ta Dora mata su Aba Ajikinta haka take son tayi mgana ba hali Hannunta mai Lafiya ta saka ta Dafa kansu tana hawaye ya Zeenatu suka samu a wajenta tana kula da ita raba raba suke da junansu.
Amina ta yawata Dangin Aba kusfa kusfa Har kwana sai da tayi agidansu Zafira,suka sha Hira Yakaka kuma ta Shige Cikin Dangi kamar yar gida Ta zama yar gidan baba mallam yanzu.
Ranar da suka Dawo gidan mallam suka kwana washegari suka tafi Dutse Gabadayansu har ya Danmallam da Su Ya jafar da Hajiya ta koma suka Duba Anty Amarya data koma bata mgana sai kuka duk ta Firgice wani Lokacin in abun ya tashi sai an Daureta Amina da su ya Jafar sun kara jin Tsoron Duniya Sadiya ta nan tare da ita Sannan sunga Sakina Amina tayi mamaki Sakina har da karban su Aba duk ta rame sai Amina taji ta bata Tsausayi basu Dade ba Daga Dutse Tsafe suka wuce chan din ma sai ahankali Hajiya uwani dai ba wani Cigaba tayi ta rokonsu Danmallan da Amina Gafara Allah yasa ita da Bakinma sai dai Ciwo duk yaci Jikinta Nazifa ta koma sai Yan"uwan Hajiya uwani ke kula da ita itama har Su Aba aka Doramata kan jikinta tana kallonsu tana Kuka.
Da zasu Dawo suka Dauko Umaima suka Dawo da ita,Umarnin mallam ne
Washegari kuma su ya Danmallam suka je gusai suka Duba mamanmu Suma kansu jikinsu yayi sanyi Tana kuka ba baki tana mika musu Hannu Tana neman gafara sukace sun yafe mata Duniya da Lahira sun bama Zeenatu kudade kafin su kamo Hanyar gida suna Hirar yadda Allah ke nuna ishara da izina tun a Duniya.
Amina taso taje gidajen yan"uwanta Mata Mallam ya hana yace ta shirya tabi mijinta alokacin Sai Hajiya ta hana tace sai dai yaje ya Dawo ,sai ya tafi da ita Lokacinn yaran sun kara wayau bazai Daukesu tana Danyen Jego ya Hau jirgi da ita.
Sannan kuma zatayi Jarabawaarta ta Fita alkawari tayi kuma sai ta cika.
Mallam sai yama kasa mgana Daga baya yaso ya nuna ma Hajiya bata isa ba sai dai data mai bayani sai ya gane gwara Amina tatafi da Tarkadunta sannan yaran su kara Wayau shi ya Lallashi Danmallam da bai da tacewa Hajiya ai tagama dashi.
Ya samu Amina yana mata magiyan taje tace ma Hajiya ita zata Bisa su tafi Amina tace bazata iya ba sai yayi Fushi batare da sanin kowa ba ya Nema ma kansa Visa shi da Sakina Sai ana Saura kwana Biyu Tafiyarsu yaje ya Daukota Sakina sai da tayi kuka har ta cire rai da auranta da Umar ganin san da suka zo ko fuska bai Sakin mata baHakama yan"uwanta nata jin Dadi,Gidan mallam ya fara kaita Hajiya da mallam suka Taru suka mata Nasiha mallam kanshi yaji Dadi yadda Umar ya zama mai Afuwa
Sai alokacin yake shaida musu jibi zasu koma Madina shi da ita Hajiya tasan don Turama Amina Haushi yayi sai bata nuna mai ba kuma bai Fadama Amina zai koma ba Dauke mata kafa yayi ana gobe Tafiyar yazo yaga yaransa ita tana barci sai da Safe Yakaka ke Fadamata,Bata san ya tafi ba Sai da sukayi waya da ya Aisha take Fadamata Ya Danmallam ya tafi da Sakina itama Hajiya ke Fadamata Ranar Amina wuni tayi kuka Yakaka na lallashinra abun fa da Ciwo aiko bai Fadamata komai ba ya Fadamata Zai Dawo da Sakina ammh Duk Sai dai Taji Daga sama itama sai ta Zuciya ta Cigaba da kula da kanta da ya"yanta.
An biya mata Jarabawar ta a Unity dinsu da an fara zata fara zuwa sannan Huce Takaicin abunda Danmallam yayi musu Hajiya ta saka Baki mallam ya barta sukaje Abuja suka kwana Biyu ita da Yakaka dagachan har da ya Aisha suka Dumguma sai Zaria wajen Hamida suka kwana Daya gidanta suka kwana Gidan ya Zulfa suna ta murna da ina suka saka da yan"uwansu sun je har kaduna gidan Abida sun je kano gidan ya Jidda Lagos ne da parthercourt yayi nisa basu je ba Amina ta taka yola Wajen Hanne sai gata agidan Aminu Taga Nenne Dangi kuwa sai zuwa ganin Aminan Aminu ake yi yara kam sun sha Dauka shi kanshi Aminun ya kasa sukunu ya siyo wannan ya siyo wanchan,Amina sai yi ma Hanne Tsiya take ganin ta da Ciki.
Kwanansu Biyu suka Dawo Gida suka Sauke Gajiya..
Danmallam bai nemeta ba itama kishi da Haushin Abunda yayi mata ta yi biris dashi,Shi ma Yayi zuciya ransa ya baci da abunda tayi mai sannan kuma bayan ya tafi bata nemesa ba abakin Mallam yaji Tafiye Tafiyen da Amina tayi ko izininsa ba"a nema bai Taba Jin Haushi in Hajiya ta yanke Hukunci kan matansa ba sai kan Amina ya Lura tafi son Ma Amina da kowa komai take so shi take yi..
Amina Taurin kanta bai barta ba,Tana nan dashi shiyasa ta nuna ma Danmallam kalanta Har Yakaka taji Haushinsa Sai dai tayi ta lallashin Amima kada ta Damu sai ya Nemesu.
Ana cikin haka suka fara WAEC ta Dinka sabbin kayan makaranta ta fara zuwa Ranar datake da paper yakaka take barin ma yaran Agidan mallam in ta Dawo sai ta biyo sai yammah su koma gida Domin yakaka bazata iya Ronon yaran ita kadai ba gasu sun fara girma da kiba suna samun kulawa sosai..
Tana kokarin ya kice Takaicin Danmallan aranta taurin kanta yasa bata ko nemesa ba shima yaki nementa Amina tasan yaushe zai nemeta yanan chan wajen Guzumanyen matansa ita kuma tana nan tana mai renon ya"ya..!
Zai gane shayi ruwa ne da Aminene yake zencen..!
*Godiyata ta musamman ga iyayena guda biyu da sune silar tsayuwa kan kafafuna da nayi ayau din nan Alhaji Umar Muhammad mailoki da Malama Hadiza Muhammad Ba"are,Baba, mama ina matukar godiya da jajircewan ku akaina Ina godiya da Goyon bayanku ina godiya ga Allah da kuka kasance iyaye nagari a wajenmu Allah ya saka muku da Alheri ya muku Tukwaici da gidan Aljannah Firdausi Ameen Ina matukar son ku Babanmu da Hajiya mama tamu Allah ya kara muku nisan kwana da kwanciyar Hankali Ababen Alhafarinmu..*
*Janafty**TFZB2031*
*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yada'ashi..Pay N500 via Jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan lambar 09069067488*
Shifa Namiji duk inda yake sai ya nuna kansa barin ma in yana da mace fiye da Daya,Sannan su fa abunda muke kallonsa abun kunya a wajensu Daidai ne kuma mai kyau ne sannan in zaki shekara kina kyautatamusu Rana Daya in kika karkace sai ya manta baya ya Dora miki laifin duk Duniya akanki sannan ba kasafai suke Fahintarmu yadda Ubangiji Ya bamu ikon mu fahimcesu ba.
To kamar haka ya faru Tsakanin Danmallan da Amina ko yaya ne so yake ya nuna mata ba ita kadai garesa ba in bata bishi ba ai ya tafi da Sakina Sannan yayi hakane domin ya kure Hakurinta yana ganin kamar in ya tafin zata nemesa ta basaa hakuri sai kuma yaga akasin haka ya fahimci Tana da Taurin kai da kafiya domin shima Daurayewa yake da bai nemeta ba shi adole sai ta nemesa ta basa Hakuri sannan su sai su daidaita ammh Ina Sai ya Fahimci Amina tayi nisan da batajin kira.
Wajen watansa Biyu da Tafiya ko Flashing bai taba mata ba, itama haka Sai dai ya Kira Hajiya ko mallam yaji Lafiyansu wani Lokacin ma suna gidan in Amina ta tafi Jarabawarta koda wasa bai bari kowa ya Fahimci akwai baraka Tsakaninsa da Amina ba ballatana ita data share batunsa Sai dai Yakaka Datake zaune da ita ta Fahimci Tsakanin ma"aurata basa mgana Dole wani abu na faruwa.
Amina sun gama WEAC dinsu Cikin Nasara suna jiran Ta gaba lokaci Daya tana kula da ya"yanta sai kuma alokacin Danmallam ya gaji da Jiran Amina ta Kirasa su sansanta shi ya Sauke Girman ya Kirata taki Dauka Har sai da ya jera mata wajen sati yana Kiranta Tana gani bata taba Dauka ba sai abun ya kara bashi mamaki gashi dai anan hankalinsa yana kwance ne saboda Sakina tayi Laushi Sosai kamar ba ita ba,ga Sarood Daman bata da Hayaniya Cikinta ya shiga watansa na bakwai kusan duka ayyukan Sakina ta Dauketa mata ita ke yi tace Sarood din ta Huta duk yadda yake jin Haushin Sakina Sai da ya Tsausayamata da aka cire mata Mahaifa,duk son ta Haihu Allah ya nuna mata nasa ikon Da Farko bai Sakar mata ba sai daga bayaa shima din ba Sosai ba kadahan kadahan dai kada ya shiga Hakkinta sannan ya Duba Nasihan mallam da Hajiya ammh Daidai da rana Daya bai taba mantawa da Amina ba yana Madina ne ammh gabadaya ransa da Tunaninsa na Nageria wajen Amina da ya"yansa yaso ya jure sai ya kasa ammh Sai gashi yana kiranta bata Daga wayarsa.
Daya Dameta sai ta Fara Dagawa ammh yayi sallaman Duniyan nan tayi mai bakan sai da yayi ta jin kananun kukan su Aba na yara tun yana ganin Lamarin nata wasa har ya Fahimci abun nata yayi nisa,Ita kuwa yadda Danmallan ya kunsa mata Bakinciki ya raina mata wayau ne ta Dauki alkwarin sai ya gane bai da wayau sai yasan ya wulakantata Shiyasa ko da yazo yana kiranta Daga baya bata Taba bashi Dama ba Tayi alkwarin sai ta rama Fiye da yadda yayi mata sannan ta koyamai Darasin da har Abada bazai kara gigin mai da ita mara amfani a wajensa ba !
Yakaka Tasan basa mgana da Mijinta ammh bata taba mata mgana ba Sai Ranar Aba na wajenta mallan ne ke wajen Amina tana basa Nono,ta kawo mata shi kenan ta iske waya gefen Amina ta saka ta speaker Muryan Danmallan Tar yana mgana sai magiyan kiran sunan Amina yake yi tayi kamar bata ji ba, Hankalinta ma na kan bama Mallam Nono kamar yana Kiran Dutse..!
Fadi yake yi "Noor don Allah ba don Halina ba kiyi mgana..!
Amina haba Amina..Haba Amina da Allah fa nake hadaki..Nasan kina jina..!
Kiyi mgana saiki fadamin Laifina i Promise you zan baki Hakuri..!
Kinji Amaryata..!
Amina tayi wani Dariyan rainin Hankali har sai da yaji aranta tace su Amarya an ji jiki ai baka san ni Amarya bace sau na nuna maka matsayina..!
Yakaka na bakin kofa baki ta saki Tana Bin Amina da kallo Har Danmallam ya gaji da magiya ya Datse kiran Sannan ta kariso Dakin koda Amina ta ganta bata Damu da taji ko bata ji ba yadda ta yi nisan nan Mallam ko Hajiya ne kadai zasu saukar da ita Su kuma tana da Tabbacin ya Danmallam bazai bari su sani ba..!
Mallam ta karba ta miko mata Aba Amina ta karbeshi tana bata rai tace"Ni wlh na fara gajiya yaran nan duk sun gama tsotseni na fara yamushewa..!.
Tafada tana wani Tura mai Nonon a baki ruwan nonon ya kawo yaran ya Shake ya fara Tari Yakaka tayi Saurin Ijiye mallam Kan gadon Amina ta karbesa ta Daga sa sama tana shafa Bayansa Cikin Lallashi Lokaci Daya Tana Hararan Amina data kauda kanta Gefe kamar bata ganta ba..!
Cikin Ikon Allah aka samu yayi barci ta Lallaba ta kwantar dashi gefen Dan"uwansa sannan ta Dawo kan Amina tana Fadin"Ashe zama na Dake bamai amfani bane Amina..?.
Ina ga gwara nayi tafiyata sai ki zauna ki yi yadda kika ga Dama..!
Yakaka ta fada Cikin bacin rai ta Juya da Niyyar Tafiya Amina ta mike ta Riko Hannunta tana Fadin"Haba yakaka me kuma ya faru..?
Yakaka ta juyo tana Hararanta tace"tambaya ta ma kike me ya faru ko..?
Ai kina Sane Mijinki ya kiraki kin Dauka kina ji yana mgana kin yi banza Dashi Sannan kina bama yaro nan Nono kina mai mugunta kina so ki kashe ya"yanki ne..?
Kada ma kiyi Tunanin domin kun samu matsala da Babansu kike jin Haushin su yaro ina ruwansa..?
Sannan ki Sani yaki dan zamba ne Amina kuma abunda Hakuri bai baka ba Wlh Tsiya bazai taba baka shi ba. !
Kawai sai Amina ta saka kuka ta sanya Tafukan Hannayenta ta rufe Fuskarta dashi tana wani irin kuka mai cin rai Kukan Daya Dade yana Damunta aranta sannan Hade yake da Kishi da Takaicin D'a Namiji.
Yakaka sai Tsausayinta ya kamata ta Jawota jikinta ta rumgumeta tana Buga bayanta alamun Lallashi.
Amina sai ta Bude muryanta tana kuka sosai har da Shessheka.
Yakaka na Dafa bayanta Lokaci Daya Tana Fadin"Kidaina kuka Amina. bari kada yaranki su tashi su ga kina kuka. !
Gefen gado ta zaunar da ita tana Share mata Hawaye Amina ta Dago Tana kallon yakaka Lokaci Daya tace"Yakaka meye laifina da ya Danmallam zai min wannan wulakancin..?
Yakaka tace"Me ya faru ne..?
Amina tace"Kan mganar komawarmu Madina tare ne Lokacin da zai koma ai kinsan dani zai tafi Daga baya sai Hajiya ta hana tace sai nayi jarabawa Sannan yara sun yi kwari ko..?
Yakaka tace"Eh anyi hakan..!
Amina na sharan kwallah ta Cigaba da Fadin"To shine fa yazo ya sameni wai sai naje na samu Hajiya nace ni zan Bisa..Ina aka taba yin hakan yakaka..?
Tsakanina ga Allah fa Hajiya matsayin uwa take gareni tana da kimar da zata yanke Hukunci kan abunda ya Shafeni nayi shuru da Bakina Saboda bazata taba aikata abunda zai zama Cuta gareni ba..!
Yakaka tace"Kwarai Amina..Daga ke har Danmallam din Hajiya ta isa ta Zartar da komai akan abunda ya Shafe ku batare da kun Daga ido kun kalleta ba..!
Amina na kuka tace"To shine fa Dalili Saboda nace mai ni bazan iya zuwa nayi ma Hajiya musu ba..Hajiya tamkar uwa take gareni tamin abunda ko Uwata Data Haifeni sai haka Tayaya zata ce ga abunda ya kamata kuma na bata kunya..?
Na fadamai bazan iya ba shima yayi hakuri nan da wata Biyar komai ya Daidaita sai in na koma chan ba Jeka ka Dawo shine yayi fushi Yakaka ya tafi ya Dauko Sakina fa ya tafi da ita yakaka Wlh kin ji rantsuwan musulmai bansan ya tafi ba ko sallama bai mim ba ballata nasan da Sakina zai koma in ya gayamin zan Hanasa ne ai matarsa ce Tare na gansu..Ammh sai yaki Darajani ya saka Kafa ya tafi ya manta Dani Ko waya bai tabamin ba sai acikin kwanakin nan duk wani abun na yaran nan ko kayan abinci sai dai su ya Jafar su kawo ni bai taba mgana Dani ba..Sai yanzu ya san Dani..?.
Yakaka ina Laifina domin naki Sauraransa don Allah..!
Amina ta karishe Fada Cikin kuka Yakaka ta jinjina kai kafin tace"Gaskiya Umaru bai kyauta ba..Nima da Hajiya ta Fadamin da Sakina ya tafi sai da naji ba Dadi to ganin baki min mganar ba yasa nima ban miki ba..!
Amina na jan majina tace"Yakaka ki Duba mganar nan ina Laifina aciki..?
Yakaka tace"Baki da Laifi Amina ai Hajiya tana gaba da Umar bama ke ba..Sannan abunda babba ya Hango ai yaro
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47 Chapter 48Chapter 49