ake yinsa ta zama kamar mujiya Cikin mutane.
Haka ma bangaran Anty Amarya ita Kadai kamar mayya ta gaji da kiran wayoyin su Jidda sun ki Daga kiranta Har ta A"i taki Daukan wayanta ballatana taji wani Hali sakina ke ciki ta rasa ina zata saka kanta taji Dadi har Sabeeha bata nan sun tafi da ita.
Hajiya Uwani kuma kafin Safe har ta Rame saboda tashin Hankali sannan tayi ta kiran Batula bata samu ba tana so ta Sanar da ita komai fa ya Tsaya.
Alokacin Datake kiranta ita ta kama Hanyar Minna domin taje ta aiwatar da gudurin Uwani bata sani ba,Ajalinta ne yake kiranta.
Domin sun fita Tsafe ba Dadewa suka samu Mummunan Hatsari da yayi Sanadiyar rasa rayuwakan mutum Hudu Dake motar har da Batula aciki..!
Sai da Hajiya ta saka baki sannan su Ya Aisha suka Tafi da su Amina gidan su ya Jafar saboda su Shirya Sa"adatu kuma Mallan ya kira Jidda yace Sa"adatu ta Dawo gida ko batasan yau za"a Daura mata aure bane..?
Ba Dadewa suka Dawo ita da Sadiya fuska duk ta Kode saboda kuka gidan su ya Jafar suka wuce tunda chan zasu shirya kafin Daurin auran.
Anan ne su ya Aisha ke jin Labarin Sakina cikinta ya zube sannan tana chan ana mata karin jini bata san inda kanta yake ba.
Sadiya ke maida musu zencen tana kuka su ya Abida na Faman bata baki Amina kuma na tare da su Hanne ita yanzu tama Daina kukan Hamida ce sai Ahankali ita da Hanne suna ta faman bata Baki ammh Taki sakin jikinta gashi ana Daura aure za'a tafi Dasu mallam yace bamai Daga wannan auran.
Baba Mallam da Aba tun safe suka fita ba wanda yasan inda suka je sun dai yi mgana da Hajiya kafin su fita Sannan har yan bazanga da bakin gusai suka iso maza basu dawo ba sai wajen 12,da rabi na rana suka Dawo Shima Baki akayi daga maiduguri wani kawun su Hajiya sai D'ansa guda Daya wanda ko Hajiya bata san da zuwansu ba.
Ashe Labarin abunda mamanmu ta aika yaje kunnen su kawu Salisu matan sun kirasu sun Fada musu komai,Kawu Salisu sai Fada yake yi yanaCema Aba ya saki Balaraba taje duniyace Mallam ne ma ke basa bakin kan mganar Aba dai bai ce koma ba ai ko bai ce balaraba ta bar mai gida ba in Tana da kunya basai ma ta jira yace ba zata san inda Dare yayi mata.
Zuwa Lokacin Yan Daurin aure sun fara Zuwa Mutanen Yola ne suka fara zuwa da Mata guda biyu suka zo aka kai su Shashen Hajiya sai yan Zaria suma sun Iso da mace Daya.
Na gombe ne karshen isowa su kan maza ne kadai suka iso banda mace ko Daya.
Amaran nachan gidan ya Jafar an samu sun yi wanka sun saka wani Less din da Mallam ya Dinka musu mai Fari da Golden sai Hijabansu mai ruwan kasa Itama Amina ta shirya Cikin leshinta mai Tsada da ya Aisha ta Dinka mata iri daya da ita har da Yakaka sai dai ita Bubu tayi saboda Cikin jikinta kowa ka gani ba walwala ido Duk ya kumbura.
Su ya Zulaihat sun zo da Safe suka Hade dasu Hamida da Amina suna ta kuka dasu ya Jadwa suna ta basu Hakuri su kuma suna cema musu ba Laifinsu bane sai da ya Aisha tace zata Kira Hajiya sannan suka sarara.
Misalin karfe Daya da wani abu na Rana Kofar gidan mallam ya Cika ba matsaka Tsinke su ya Danmallam sai Lokacin suka iso Cikin shigarsu ta alfarma haka ma su Ya Jafar mallam ma da Sabuwar shadda da rawani haka ma Aba kowa dai yayi kokarin Boye abunda ke ransa har da su Nazeem kuwa.
Alokacin kuma Hajiya Uwani ta san da abunda ya faru da yar"uwarta Batula sai ta rude kuka kamar zata Haukace bata tsaya neman kowa ba ta Hada kayanta Ko Umaima bata Tsaya bi ta kanta ba,ta ma bar Shashen nata tana Shashen Hajiya ta shiga Cikin yan Biki ita kadai ce batasan me ya faru ba mutane sun yi yawa yasa har ta fito ta tari abun hawa ta hau zuwa Tasha ba wanda ya lura da ita ammh Nazeem ya ganta sai dai bai nuna ya ganta ba yana Tunanin abunda ya Dace da ita kenan ya Dauka ta neman ma kanta mafita ne kafin mallam ya koreta.
Anty Amarya kuma tana Shashenta ko kare bata kara gani ba,kaf Danginta suna asibiti wajen sakina su jidda kuma suna Tare da Sa"adatu domin cire mata Damuwar dake damunta duk da suma karfin Hali ne Mamanmu kuwa Sai da ta raina kanta Har Daki yan Gusai suka Bita suka mata tsofin Allah Tsine shiyasa ta kasa Fitowa Tayi kuka har ta bama uku Lada yan"uwanta sun Tsine mata kamar me sun ce ana Gama Biki yau gobe zasu koma sannan sun ga karfin Halinta Data iya Takowa gidan Sa"idu..
Ita kuma tana Tunanin ina Zata..?
Bata da inda zataje a karbeta Ta riga tayi ma rayuwarta mummunan Tabon da har Abada bazai goge ba.
Karfe Biyu aka Dauran auran su Hanne,Na Aba aka fara Daurawa da Hadiza Babbar Diyar kanwar Hajiya Yagana Datayi aure mijinta ya rasu bata kuma taba Haihuwa ba..!
Hadizan ma da ita aka zo Biki Suma kansu basu sani ba sai da aka Daura shi ya kawo kawun Hajiya Tun Daran Jiya mallam ya kirasa yamai bayani Tun Safe kuma suka Biyo Jirgi Daman a Bauchi yake da zama shi da iyalansa. !
Daurin auran daya bama kowa mamaki Hajiya kam Bakinta yaki rufuwa Mallam a koda yaushe Tunaninsa mai kyau ne
Daga nasa sai na Hamida sai na Sa"adatu na hanne ne na karshe Bayan an Daura auran aka shiga taya juna Murna ya jafar yayi mamaki Lokacin Daya ga wanda Hanne ta aura har ya bashi Hannu sukayi musabaha bai daina mamaki ba.
Har sai da shi yace mai""Ya jafar Allah ya Rubuta Amina ba matata bace..Hannatu ce matata..,!
Ya jafar ya jinjina kai aransa yana kara yima Allah kirari.
Su Danmallam suna cikin jama"a suna ta Faman gaisawa da mutane Bakinsa har Kunne shi da Aliyu,da Nazir nan kasan ransa Halin da Amina take Ciki yake so ya sani Sakina kuma bata gabansa bai san Halin Datake Ciki ba Sannan basu kirasa ba shima bai nemi kowa ba.
Suna cikin gaisawa da Mutanan ne ya Hango Amina suna tafe ita da Zafira Amina ta saka Hijabi mai Ruwan Sararin Samaniya kalan leshinta da Takalminta mai Saukakan Tudu tana Tafiya cikinta yana gaba da ita Saboda Girmansa har suka shige gidan mallam
Ayadda Danmallam yaga Fuskarta ta Kumbura ne yasa Hankalinsa ya tashi yaja Hannun Aliyu suka bi bayansu Baya son yaga Amina na cikin Damuwa,suna shiga kuma haraban gidan yan bazanga suka taresa ana ta gaisawa yasa basu samu karisa cikin gidan da wuri ba.
Amina kuma daman Ya Aisha ne tace Hajiya na kiranta, taso ta jira su taho dasu Hanne suna Sauya kaya yasa tace Zafira ta rakota su suna chan ko Mganar auran Aba din ma basu sani ba sai bayan tahowarta sannan Anty Fadila take fadamusu itama Mijinta ne ya kirata ya Fadamata.
Amina har ta shiga Shashen Hajiya ta zama abar kallo da Sha"awa suna shiga Falon cike da jama"a.
Da Hajiya suka ci karo da ta fito Daga Dakinta Taci gayunta itama bakinta Har kunne Amina suna gaisawa da yan Falon yawancin yan"uwan Hajiya ne taga dai ana nuna tw ita bata san me ya faru ba.
Yakaka ce Amina ta Hango zaune itama ta sha gayunta ta karisa suka gaisa Yakaka na fadin"wasu baki ne suka zo suna son ganinki..Hajiya ta saka aka kiraki..!
Hajiya ta kariso wajensu zatayi mgana kenan sai ga wata Farar mata gajera ta fito Daga Dakin Hajiya bayan ta wata mata ce itama suna yanayi sai da tana dan tsawo ita.
Hajiya na ganinsu ta juya tana Fadin"Yauwa Nenne ga ma Aminar nan ta kariso..!
Ta fada tana riko Hannun Amina har gaban matar da Amina ta kasa Dauke Ido a kanta.
Wacce aka kira da Nenne ta Rike Hannun Amina cikin Fara"arta take Fadin"Allahu akbar Rahina..Kinga Aminar Aminullahi..Allah ya rubuta Ba matar sa bace..Rabo ne rabo ne ya Haddasa abubuwan da sukayi ta Faruwa..!
Wacce aka kira da Rahina tabi Amina da kallo Kafin tace"Ba Shakka yau naga Amina..Aminar da kaf Danginmu ba wanda bai santa ba..Sannu Amina Allah ya raba Lafiya..!
Tafada tana kallonta sai Amina ta kasa mgana ta koma tana Binsu da kallo Hajiya tace"Bafa ta gane ku ba inaga sai kun mata bayani..!
Tafada tana Dariya.
Nenne ta kara rike Hannun Amina Tana Fadin"Amina baki gane ni ba ko..?
Ai nasan baki sanni a Fuska ba sai Muryata..Nice fa NENNE..Nennen Aminu fa..!
Sai alokacin Amina ta Gane ina ta san muryan Ido ta waro kafin tace"Nenne..!
Nenne na Dariya tace"Alkwarin Allah ya Cika Amina..Aminu da bai Sameki ba..Sai Allah ya kaddara yar"uwarki Hannatu ce RABONSA..!
sai amina ta kara zaro ido Cikin mamaki bata samun Damar mgana ba Ya Danmallam da ya Aliyu suka shigo Falon bayan su kuma ya Nazir ne yana Cema yan Falon Tawagan Angon Hannatu zasu shigo su gaida su.
Sai Amina ta juya suka Hada ido da ya Danmallam ya sakar mata ido ita bashi ma take kallo ba Wanda ya shigo ne cikin Farar shadda da babbar Riga shi da wasu maza su uku.
Su ya Danmallam suka basu waje su ka kariso tsakiyar Falon suka Duka suna gaida wadanda ke falon.
Kan Aminu na kasa ne Yaji Nenne na Fadin"Aminu yau dai naga AMINA..yau naga Amina..!
Take fada Hakoranta duka suna Waje..Atare Aminu da Danmallam suka Dago kansu.
Shi Danmallam Wanda aka kira da Aminu yake kallo shi kuma Aminu Nenne ya kallo sai kuma karaf suka Hada ido Hudu da Amina..
Mennarsa da rashinta yasa kadan ya Rage bai Haukaace ba itace agabansa ta Sauya har da Tsohon Ciki ma ajikinta..!
*Janafty**TFZB2028*
*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yada'ashi..Pay N500 via Jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan lambar 09069067488*
Aminu kallon Amina yake yi da wani mamaki a saman fuskarsa yana mamakin ganin sauyawarta da komai ma acikin shekaru biyu da wani abu daya shafe bai ganta ba abunda yasa ya kasa daina kallonta Katon Cikin Dake jikinta wannan ya kara tabbatar mai da gaske ya rasa Amina rashi na har Abada..!
Shi kuma Danmallan kallon Aminu yake da wani abu acikin ransa kamar almara sai yaji ransa na kuna da wani kishin Aminu acikin ransa in ya tuna abubuwan da suka faru sannan Abaya Amina taso Aminu shiyasa yaji wani Duhu ya mamayesa na ganin Aminu da irin kallon dayake bin Amina Dashi ko shi mallam bai tattauna dashi kan wanda Hannatu zata aura ba abunda a bazata yajisa.
Aliyu dake gefensa shima Aminun yake kallo saboda ai shima yasan Labarinsa sai da Dariya ta kusa kamashi yadda yaga Shehi yake kallon Aminu kamar zai shakeshi yana Faman sakin Huci Sama sama.
Aliyu ya raba ta gefen kunnensa yana Fadin"Cool Down mana Shehi..!
Hararansa yayi kafin yace"Ta ina naga Wani Cool down baka ga yarda yake ta kallemin mata bane..?.
Ko ba auran Hannatu a kansa bai san Noor ta Haramta garesa bane yake binta da kallon Daya wuce ka'ida..?
Aliya na Danne dariyan sa Lokaci Daya yana Fadin"Yi hakuri zai bari..Kallo Daya ne fa na Musulunci..!
Wani Kallo da yayi ma Aliyu sai da ya matsa yana Dariya lokaci Daya yana Fadin"Ana Asif..Shehin Amina..!
Kwafa Umar yayi bai kara mgana ba Amina yake satan kallo ransa yayi fari Daya ga bata kallon barayin Aminu yanzu sai ya karkata yana kallon Aminu sai yaga kansa na kasa suna mgana da wanda ke gefensa ajiyar rai yayi har yana Hararan Aminu ta gefen ido Aliyu na ankare dashi yana Dariya aransa yana Ayyana wani irin so Shehi ke yi ma Amina..?
Bai taba ganinsa ya nuna kishi kan abu ba sai ayau din nan.
Nenne kuma na rike da Hannuwan Amina Fara"arta taki gushewa sai Faman washe baki take yi har gaban su Aminu dake Durkushe shi da Nura da Abokin aikinsa Oscar duk da yanzu ya Daina waka ammh ana tare ba"a rabu ba.
Har gabansu takai Amina tana Fadin"Aminu kaga abunda nake fada maka ko..?
Na sha Fada maka Allah ya Boye wani abu Tsakaninka da Amina saboda irin son da kayi mata..Rabo ne..Wannan Rabon ne ya raba Tsakaninku sannan da kuma Kaddaran auran yar"uwanta Hannatu Allah mai iko Amina..Rahinatu kin ga Ikon Allah ko..?
Rahina ta jinjina kai kafin tace"Nagani Allah ya rabasu lafiya. !
Ta amsa da Ameen Aminu dai kansa na kasa ko Dagowa bai yi ba Amina na haka ta kasa sakewa sannan mamakin yadda al"amura suka juye basu barta ba.
Nenne tace"Ina mijin naki Amina..?
Ance Babban yaron Hajiya kike aure wanda ke zaune a madina ko..?
Kai kawai Amina ta iya Daga mata Cikin Fara"a Nenne tace"Yana ina..?
Ina so na gansa ne mu gaisa..?
Amina ta Dago kanta tana kallon Dannallam da yayi saurin Dauke kansa Dukkansu suka bi wajen da kallo har shi kanshi Amunun Daidai da karisowar Hajiya wajen Dazu ta bar Falon ne sai yanzu ta shigo Nenne na ganinta tace"Hajiya wancan ne Mijin Amina..?
Ta fada tana nuna barayin da su Danmallam suke Hajiya ta murmusa kafin Tace"Eh Shine..Danmallan ka kariso ku gaisa da Mahaifiyar Aminu wanda ya nemi Amina da farko Allah bai yi ba..!
Tafada tana kallon Danmallan din Daya Hade ransa kanar bai taba Dariya ba,Aminu kallo daya yayi mai ya Maida kansa kasa azuciyarsa yana jin wani Nauyi Har yau har gobe bai Daina son Amina ba ya sota da dukkan Zuciyarsa ne sai dai ganin Danmallam a matsayin wanda ta aura sai ya Sare domin ai ta samu babban Goro ne.
Sannan duk da bai taba ganinsa ba yasha jin Labarinsa wajen Amina ashe shine mallan ya aura mata..?
Hakane mganar Nanne Rabo ne..Sannan bawa bai isa ya kankare abunda Allah ya Tsara ba,Sannan matar Mutum ya tabbatar mishi da itace Kabarinsa.
Har su Danmallan suka kariso gaban Nenne bai iya Dago kansa ba yana jin Nura na mai mganar ga Mijin Amina wanda ya kasa sa nan bai ko Kara marmarin kallonsa ba.
Ita kuwa kallon Danmallam take Cikin Fara"arta kafin tace"Masha Allah..Sannun kaji Allah yayi albarka..Ashe Amina kuma rabonka ce..?
Aminu ya so Amina son da bai taba yima wata Diya mace ba..kaganshi nan Saboda rashin Amina Dakyar muka samo Aminu da Addu"o"i da Nasihu yakusa shekara yana jinyar Zuciyarsa Dakyar da sidin goshi muka samu ya Farfardo nasha Fadamai yayi Hakuri yayi takwalli Akwai tanadin da Allah yayi masa agaba haka kuwa akayi kwatsam sai ga Mallam ya Dira a yola wajen Alhaji Babba da mganar Ya bama Aminu auran Hannatu yarsa..Shima bai yi gaddama ba, ya amsa domin na Fadamai daman itace maatarsa Amina kawai Sanadi zata zame sa..Gashi kuma komai ya Faru yadda Allah ya Tsara..muna namu ne Allah na nashi..Allah ya baku zaman Lafiya dukkan ku..Ita kuma Amina Allah ya sauketa Lafiya yasa abokiyar arzikinkace..!
Gabadaya suka amsa mata da Ameen har da Aminu da su Nura sai ya Danmallan yaji Nenne ta Burgesa kansa na kasa ya amsa mata lokaci Daya yana fadin"Mungode Mama...Allah ya kara girma..!
Ta amsa da Ameen ita da Rahina Amina dai kanta na kasa tana Satar kallon Aminu sai taji ya bata Tsausayi Ashe har jinya yayi tayi bayan rabuwarsu..?
Ai ita kanta Shaida ne Aminu ya sota sai dai bata Taba Zaton abun har yakai haka ba nan da nan sai Idanuwanta suka kawo kwallah.
Jin yadda Nenne ke Fadama Hajiya wuyar da suka sha kafin Aminu ya manta da komai anan ne taji har ya bar Kano da waka gabadaya ya koma Yola yana cigaba da kasuwancinsa shekara daya da wani abu kenan an samu ya Dawo Cikin Hayyacinsa..!
Hajiya ta jinjina kai ita kanta Lamarin ya Dauremata kai da Farko da Mallam ya Sameta da mganar zai nemi iyayen Aminu kan mganar Hannatu shi fa har yanzu sai yake ganin kamar bai kyauta ma yaron nan ba sannan da gaske yake yi tun a wanchan Lokacin da yace zai bashi Hanne.
Hajiya bata iya yin gaddama da Shawaran mallam ba Sai dai tayi Fatan Inda Alheri Allah ya Tabbatar in babu kuma Allah ya watsar da al"amarin sannan Tunda taga mallam ya Dage sai ta bishi da Fatan Alheri tasan yana da Dalili Tunda bai taba Tallata ya"yansa ba wannan din ma Domin da Dalili ne.
Daman yana da Lambar Alhaji Babba tun wanchan zuwan da sukayi ya karbi Lambarsa basu taba mgana ba sai da Mallam din ya yanke shawaran zuwa chan yola suyi mgana sannan ya Kirasa suka Tattauna a kuma Satin Mallam yaje Yola shi da idi suka gana da Alhaji Babba ya kuma karbi mganar hannun bibbiyu sannan ya labartamai yadda suka sha Fama da Aminu mallam yaji Tsausayinsa sosai alokacin aka kira Aminu yazo jin Bukatar yasa bai yi gaddama ba. Ya Dauki hakan a matsayin nasa kaddaran kenan Mallam ya ga karamcin rikesa sukayi sai washegari suka juyo shi da Idi..
Sannan sun biyosa Daga baya akayi neman aure aka biya Sadaki da Lokaci bayan nan ne Aminu yazo suka gana da Hannatu kowannensu yayi mamakin ganin Dan"uwansa barin ma Hanne da tayi ta kuka tana tunanin me zata ce Amina..?
Shi kuma Aminu Kwatan kwacin Soyayyar da Amina keyi ma su Hannatu da wanda ke tsakaninsu yasa ya amince da auran Hanne Dari Bisa Dari.
Nenne bakinta har kunne take ta Godiya tana Fadin"Munga karamci Munga Kauna da kara..Allah yayi ma wannan zuru"ar albarka..!
Hajiya na amsa da Ameen aranta taji Dadi tasan Hanne bata fada hannun banza ba Nenne da zuru"arta masu karamci ne
Amina na chan tayi nisa cikin Tunani ashe har su ya Danmallam da su Aminun sun yi ma su Hajiya sallama sun Fice Daga Falon tana chan cikin Tunani bata ma sani ba sai da suka Fice ta waiga taga basu afalon sannan ta iya Sauke Nunfashi mai karfi Sulalewa tayi daga wajen Nenne ta koma kusa da Yakaka ta zauna suna Hira sama sama rabin Hankalinta na kan Dangin Hajiya yan maiduguri Dake ta shiga suna fita sannan suna kuma Rangada guda sai da Hajiya ta Tsawar tar musu sannan suka Daina ita Amina bata kawo komai aranta ba ta Dauka dai suna yi ne saboda Bikin su Hannatu.
Su Hanne take jira taji Dalilinsu na Boye mata Aminu
Showing 120001 words to 123000 words out of 146831 words
Haka ma bangaran Anty Amarya ita Kadai kamar mayya ta gaji da kiran wayoyin su Jidda sun ki Daga kiranta Har ta A"i taki Daukan wayanta ballatana taji wani Hali sakina ke ciki ta rasa ina zata saka kanta taji Dadi har Sabeeha bata nan sun tafi da ita.
Hajiya Uwani kuma kafin Safe har ta Rame saboda tashin Hankali sannan tayi ta kiran Batula bata samu ba tana so ta Sanar da ita komai fa ya Tsaya.
Alokacin Datake kiranta ita ta kama Hanyar Minna domin taje ta aiwatar da gudurin Uwani bata sani ba,Ajalinta ne yake kiranta.
Domin sun fita Tsafe ba Dadewa suka samu Mummunan Hatsari da yayi Sanadiyar rasa rayuwakan mutum Hudu Dake motar har da Batula aciki..!
Sai da Hajiya ta saka baki sannan su Ya Aisha suka Tafi da su Amina gidan su ya Jafar saboda su Shirya Sa"adatu kuma Mallan ya kira Jidda yace Sa"adatu ta Dawo gida ko batasan yau za"a Daura mata aure bane..?
Ba Dadewa suka Dawo ita da Sadiya fuska duk ta Kode saboda kuka gidan su ya Jafar suka wuce tunda chan zasu shirya kafin Daurin auran.
Anan ne su ya Aisha ke jin Labarin Sakina cikinta ya zube sannan tana chan ana mata karin jini bata san inda kanta yake ba.
Sadiya ke maida musu zencen tana kuka su ya Abida na Faman bata baki Amina kuma na tare da su Hanne ita yanzu tama Daina kukan Hamida ce sai Ahankali ita da Hanne suna ta faman bata Baki ammh Taki sakin jikinta gashi ana Daura aure za'a tafi Dasu mallam yace bamai Daga wannan auran.
Baba Mallam da Aba tun safe suka fita ba wanda yasan inda suka je sun dai yi mgana da Hajiya kafin su fita Sannan har yan bazanga da bakin gusai suka iso maza basu dawo ba sai wajen 12,da rabi na rana suka Dawo Shima Baki akayi daga maiduguri wani kawun su Hajiya sai D'ansa guda Daya wanda ko Hajiya bata san da zuwansu ba.
Ashe Labarin abunda mamanmu ta aika yaje kunnen su kawu Salisu matan sun kirasu sun Fada musu komai,Kawu Salisu sai Fada yake yi yanaCema Aba ya saki Balaraba taje duniyace Mallam ne ma ke basa bakin kan mganar Aba dai bai ce koma ba ai ko bai ce balaraba ta bar mai gida ba in Tana da kunya basai ma ta jira yace ba zata san inda Dare yayi mata.
Zuwa Lokacin Yan Daurin aure sun fara Zuwa Mutanen Yola ne suka fara zuwa da Mata guda biyu suka zo aka kai su Shashen Hajiya sai yan Zaria suma sun Iso da mace Daya.
Na gombe ne karshen isowa su kan maza ne kadai suka iso banda mace ko Daya.
Amaran nachan gidan ya Jafar an samu sun yi wanka sun saka wani Less din da Mallam ya Dinka musu mai Fari da Golden sai Hijabansu mai ruwan kasa Itama Amina ta shirya Cikin leshinta mai Tsada da ya Aisha ta Dinka mata iri daya da ita har da Yakaka sai dai ita Bubu tayi saboda Cikin jikinta kowa ka gani ba walwala ido Duk ya kumbura.
Su ya Zulaihat sun zo da Safe suka Hade dasu Hamida da Amina suna ta kuka dasu ya Jadwa suna ta basu Hakuri su kuma suna cema musu ba Laifinsu bane sai da ya Aisha tace zata Kira Hajiya sannan suka sarara.
Misalin karfe Daya da wani abu na Rana Kofar gidan mallam ya Cika ba matsaka Tsinke su ya Danmallam sai Lokacin suka iso Cikin shigarsu ta alfarma haka ma su Ya Jafar mallam ma da Sabuwar shadda da rawani haka ma Aba kowa dai yayi kokarin Boye abunda ke ransa har da su Nazeem kuwa.
Alokacin kuma Hajiya Uwani ta san da abunda ya faru da yar"uwarta Batula sai ta rude kuka kamar zata Haukace bata tsaya neman kowa ba ta Hada kayanta Ko Umaima bata Tsaya bi ta kanta ba,ta ma bar Shashen nata tana Shashen Hajiya ta shiga Cikin yan Biki ita kadai ce batasan me ya faru ba mutane sun yi yawa yasa har ta fito ta tari abun hawa ta hau zuwa Tasha ba wanda ya lura da ita ammh Nazeem ya ganta sai dai bai nuna ya ganta ba yana Tunanin abunda ya Dace da ita kenan ya Dauka ta neman ma kanta mafita ne kafin mallam ya koreta.
Anty Amarya kuma tana Shashenta ko kare bata kara gani ba,kaf Danginta suna asibiti wajen sakina su jidda kuma suna Tare da Sa"adatu domin cire mata Damuwar dake damunta duk da suma karfin Hali ne Mamanmu kuwa Sai da ta raina kanta Har Daki yan Gusai suka Bita suka mata tsofin Allah Tsine shiyasa ta kasa Fitowa Tayi kuka har ta bama uku Lada yan"uwanta sun Tsine mata kamar me sun ce ana Gama Biki yau gobe zasu koma sannan sun ga karfin Halinta Data iya Takowa gidan Sa"idu..
Ita kuma tana Tunanin ina Zata..?
Bata da inda zataje a karbeta Ta riga tayi ma rayuwarta mummunan Tabon da har Abada bazai goge ba.
Karfe Biyu aka Dauran auran su Hanne,Na Aba aka fara Daurawa da Hadiza Babbar Diyar kanwar Hajiya Yagana Datayi aure mijinta ya rasu bata kuma taba Haihuwa ba..!
Hadizan ma da ita aka zo Biki Suma kansu basu sani ba sai da aka Daura shi ya kawo kawun Hajiya Tun Daran Jiya mallam ya kirasa yamai bayani Tun Safe kuma suka Biyo Jirgi Daman a Bauchi yake da zama shi da iyalansa. !
Daurin auran daya bama kowa mamaki Hajiya kam Bakinta yaki rufuwa Mallam a koda yaushe Tunaninsa mai kyau ne
Daga nasa sai na Hamida sai na Sa"adatu na hanne ne na karshe Bayan an Daura auran aka shiga taya juna Murna ya jafar yayi mamaki Lokacin Daya ga wanda Hanne ta aura har ya bashi Hannu sukayi musabaha bai daina mamaki ba.
Har sai da shi yace mai""Ya jafar Allah ya Rubuta Amina ba matata bace..Hannatu ce matata..,!
Ya jafar ya jinjina kai aransa yana kara yima Allah kirari.
Su Danmallam suna cikin jama"a suna ta Faman gaisawa da mutane Bakinsa har Kunne shi da Aliyu,da Nazir nan kasan ransa Halin da Amina take Ciki yake so ya sani Sakina kuma bata gabansa bai san Halin Datake Ciki ba Sannan basu kirasa ba shima bai nemi kowa ba.
Suna cikin gaisawa da Mutanan ne ya Hango Amina suna tafe ita da Zafira Amina ta saka Hijabi mai Ruwan Sararin Samaniya kalan leshinta da Takalminta mai Saukakan Tudu tana Tafiya cikinta yana gaba da ita Saboda Girmansa har suka shige gidan mallam
Ayadda Danmallam yaga Fuskarta ta Kumbura ne yasa Hankalinsa ya tashi yaja Hannun Aliyu suka bi bayansu Baya son yaga Amina na cikin Damuwa,suna shiga kuma haraban gidan yan bazanga suka taresa ana ta gaisawa yasa basu samu karisa cikin gidan da wuri ba.
Amina kuma daman Ya Aisha ne tace Hajiya na kiranta, taso ta jira su taho dasu Hanne suna Sauya kaya yasa tace Zafira ta rakota su suna chan ko Mganar auran Aba din ma basu sani ba sai bayan tahowarta sannan Anty Fadila take fadamusu itama Mijinta ne ya kirata ya Fadamata.
Amina har ta shiga Shashen Hajiya ta zama abar kallo da Sha"awa suna shiga Falon cike da jama"a.
Da Hajiya suka ci karo da ta fito Daga Dakinta Taci gayunta itama bakinta Har kunne Amina suna gaisawa da yan Falon yawancin yan"uwan Hajiya ne taga dai ana nuna tw ita bata san me ya faru ba.
Yakaka ce Amina ta Hango zaune itama ta sha gayunta ta karisa suka gaisa Yakaka na fadin"wasu baki ne suka zo suna son ganinki..Hajiya ta saka aka kiraki..!
Hajiya ta kariso wajensu zatayi mgana kenan sai ga wata Farar mata gajera ta fito Daga Dakin Hajiya bayan ta wata mata ce itama suna yanayi sai da tana dan tsawo ita.
Hajiya na ganinsu ta juya tana Fadin"Yauwa Nenne ga ma Aminar nan ta kariso..!
Ta fada tana riko Hannun Amina har gaban matar da Amina ta kasa Dauke Ido a kanta.
Wacce aka kira da Nenne ta Rike Hannun Amina cikin Fara"arta take Fadin"Allahu akbar Rahina..Kinga Aminar Aminullahi..Allah ya rubuta Ba matar sa bace..Rabo ne rabo ne ya Haddasa abubuwan da sukayi ta Faruwa..!
Wacce aka kira da Rahina tabi Amina da kallo Kafin tace"Ba Shakka yau naga Amina..Aminar da kaf Danginmu ba wanda bai santa ba..Sannu Amina Allah ya raba Lafiya..!
Tafada tana kallonta sai Amina ta kasa mgana ta koma tana Binsu da kallo Hajiya tace"Bafa ta gane ku ba inaga sai kun mata bayani..!
Tafada tana Dariya.
Nenne ta kara rike Hannun Amina Tana Fadin"Amina baki gane ni ba ko..?
Ai nasan baki sanni a Fuska ba sai Muryata..Nice fa NENNE..Nennen Aminu fa..!
Sai alokacin Amina ta Gane ina ta san muryan Ido ta waro kafin tace"Nenne..!
Nenne na Dariya tace"Alkwarin Allah ya Cika Amina..Aminu da bai Sameki ba..Sai Allah ya kaddara yar"uwarki Hannatu ce RABONSA..!
sai amina ta kara zaro ido Cikin mamaki bata samun Damar mgana ba Ya Danmallam da ya Aliyu suka shigo Falon bayan su kuma ya Nazir ne yana Cema yan Falon Tawagan Angon Hannatu zasu shigo su gaida su.
Sai Amina ta juya suka Hada ido da ya Danmallam ya sakar mata ido ita bashi ma take kallo ba Wanda ya shigo ne cikin Farar shadda da babbar Riga shi da wasu maza su uku.
Su ya Danmallam suka basu waje su ka kariso tsakiyar Falon suka Duka suna gaida wadanda ke falon.
Kan Aminu na kasa ne Yaji Nenne na Fadin"Aminu yau dai naga AMINA..yau naga Amina..!
Take fada Hakoranta duka suna Waje..Atare Aminu da Danmallam suka Dago kansu.
Shi Danmallam Wanda aka kira da Aminu yake kallo shi kuma Aminu Nenne ya kallo sai kuma karaf suka Hada ido Hudu da Amina..
Mennarsa da rashinta yasa kadan ya Rage bai Haukaace ba itace agabansa ta Sauya har da Tsohon Ciki ma ajikinta..!
*Janafty**TFZB2028*
*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yada'ashi..Pay N500 via Jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan lambar 09069067488*
Aminu kallon Amina yake yi da wani mamaki a saman fuskarsa yana mamakin ganin sauyawarta da komai ma acikin shekaru biyu da wani abu daya shafe bai ganta ba abunda yasa ya kasa daina kallonta Katon Cikin Dake jikinta wannan ya kara tabbatar mai da gaske ya rasa Amina rashi na har Abada..!
Shi kuma Danmallan kallon Aminu yake da wani abu acikin ransa kamar almara sai yaji ransa na kuna da wani kishin Aminu acikin ransa in ya tuna abubuwan da suka faru sannan Abaya Amina taso Aminu shiyasa yaji wani Duhu ya mamayesa na ganin Aminu da irin kallon dayake bin Amina Dashi ko shi mallam bai tattauna dashi kan wanda Hannatu zata aura ba abunda a bazata yajisa.
Aliyu dake gefensa shima Aminun yake kallo saboda ai shima yasan Labarinsa sai da Dariya ta kusa kamashi yadda yaga Shehi yake kallon Aminu kamar zai shakeshi yana Faman sakin Huci Sama sama.
Aliyu ya raba ta gefen kunnensa yana Fadin"Cool Down mana Shehi..!
Hararansa yayi kafin yace"Ta ina naga Wani Cool down baka ga yarda yake ta kallemin mata bane..?.
Ko ba auran Hannatu a kansa bai san Noor ta Haramta garesa bane yake binta da kallon Daya wuce ka'ida..?
Aliya na Danne dariyan sa Lokaci Daya yana Fadin"Yi hakuri zai bari..Kallo Daya ne fa na Musulunci..!
Wani Kallo da yayi ma Aliyu sai da ya matsa yana Dariya lokaci Daya yana Fadin"Ana Asif..Shehin Amina..!
Kwafa Umar yayi bai kara mgana ba Amina yake satan kallo ransa yayi fari Daya ga bata kallon barayin Aminu yanzu sai ya karkata yana kallon Aminu sai yaga kansa na kasa suna mgana da wanda ke gefensa ajiyar rai yayi har yana Hararan Aminu ta gefen ido Aliyu na ankare dashi yana Dariya aransa yana Ayyana wani irin so Shehi ke yi ma Amina..?
Bai taba ganinsa ya nuna kishi kan abu ba sai ayau din nan.
Nenne kuma na rike da Hannuwan Amina Fara"arta taki gushewa sai Faman washe baki take yi har gaban su Aminu dake Durkushe shi da Nura da Abokin aikinsa Oscar duk da yanzu ya Daina waka ammh ana tare ba"a rabu ba.
Har gabansu takai Amina tana Fadin"Aminu kaga abunda nake fada maka ko..?
Na sha Fada maka Allah ya Boye wani abu Tsakaninka da Amina saboda irin son da kayi mata..Rabo ne..Wannan Rabon ne ya raba Tsakaninku sannan da kuma Kaddaran auran yar"uwanta Hannatu Allah mai iko Amina..Rahinatu kin ga Ikon Allah ko..?
Rahina ta jinjina kai kafin tace"Nagani Allah ya rabasu lafiya. !
Ta amsa da Ameen Aminu dai kansa na kasa ko Dagowa bai yi ba Amina na haka ta kasa sakewa sannan mamakin yadda al"amura suka juye basu barta ba.
Nenne tace"Ina mijin naki Amina..?
Ance Babban yaron Hajiya kike aure wanda ke zaune a madina ko..?
Kai kawai Amina ta iya Daga mata Cikin Fara"a Nenne tace"Yana ina..?
Ina so na gansa ne mu gaisa..?
Amina ta Dago kanta tana kallon Dannallam da yayi saurin Dauke kansa Dukkansu suka bi wajen da kallo har shi kanshi Amunun Daidai da karisowar Hajiya wajen Dazu ta bar Falon ne sai yanzu ta shigo Nenne na ganinta tace"Hajiya wancan ne Mijin Amina..?
Ta fada tana nuna barayin da su Danmallam suke Hajiya ta murmusa kafin Tace"Eh Shine..Danmallan ka kariso ku gaisa da Mahaifiyar Aminu wanda ya nemi Amina da farko Allah bai yi ba..!
Tafada tana kallon Danmallan din Daya Hade ransa kanar bai taba Dariya ba,Aminu kallo daya yayi mai ya Maida kansa kasa azuciyarsa yana jin wani Nauyi Har yau har gobe bai Daina son Amina ba ya sota da dukkan Zuciyarsa ne sai dai ganin Danmallam a matsayin wanda ta aura sai ya Sare domin ai ta samu babban Goro ne.
Sannan duk da bai taba ganinsa ba yasha jin Labarinsa wajen Amina ashe shine mallan ya aura mata..?
Hakane mganar Nanne Rabo ne..Sannan bawa bai isa ya kankare abunda Allah ya Tsara ba,Sannan matar Mutum ya tabbatar mishi da itace Kabarinsa.
Har su Danmallan suka kariso gaban Nenne bai iya Dago kansa ba yana jin Nura na mai mganar ga Mijin Amina wanda ya kasa sa nan bai ko Kara marmarin kallonsa ba.
Ita kuwa kallon Danmallam take Cikin Fara"arta kafin tace"Masha Allah..Sannun kaji Allah yayi albarka..Ashe Amina kuma rabonka ce..?
Aminu ya so Amina son da bai taba yima wata Diya mace ba..kaganshi nan Saboda rashin Amina Dakyar muka samo Aminu da Addu"o"i da Nasihu yakusa shekara yana jinyar Zuciyarsa Dakyar da sidin goshi muka samu ya Farfardo nasha Fadamai yayi Hakuri yayi takwalli Akwai tanadin da Allah yayi masa agaba haka kuwa akayi kwatsam sai ga Mallam ya Dira a yola wajen Alhaji Babba da mganar Ya bama Aminu auran Hannatu yarsa..Shima bai yi gaddama ba, ya amsa domin na Fadamai daman itace maatarsa Amina kawai Sanadi zata zame sa..Gashi kuma komai ya Faru yadda Allah ya Tsara..muna namu ne Allah na nashi..Allah ya baku zaman Lafiya dukkan ku..Ita kuma Amina Allah ya sauketa Lafiya yasa abokiyar arzikinkace..!
Gabadaya suka amsa mata da Ameen har da Aminu da su Nura sai ya Danmallan yaji Nenne ta Burgesa kansa na kasa ya amsa mata lokaci Daya yana fadin"Mungode Mama...Allah ya kara girma..!
Ta amsa da Ameen ita da Rahina Amina dai kanta na kasa tana Satar kallon Aminu sai taji ya bata Tsausayi Ashe har jinya yayi tayi bayan rabuwarsu..?
Ai ita kanta Shaida ne Aminu ya sota sai dai bata Taba Zaton abun har yakai haka ba nan da nan sai Idanuwanta suka kawo kwallah.
Jin yadda Nenne ke Fadama Hajiya wuyar da suka sha kafin Aminu ya manta da komai anan ne taji har ya bar Kano da waka gabadaya ya koma Yola yana cigaba da kasuwancinsa shekara daya da wani abu kenan an samu ya Dawo Cikin Hayyacinsa..!
Hajiya ta jinjina kai ita kanta Lamarin ya Dauremata kai da Farko da Mallam ya Sameta da mganar zai nemi iyayen Aminu kan mganar Hannatu shi fa har yanzu sai yake ganin kamar bai kyauta ma yaron nan ba sannan da gaske yake yi tun a wanchan Lokacin da yace zai bashi Hanne.
Hajiya bata iya yin gaddama da Shawaran mallam ba Sai dai tayi Fatan Inda Alheri Allah ya Tabbatar in babu kuma Allah ya watsar da al"amarin sannan Tunda taga mallam ya Dage sai ta bishi da Fatan Alheri tasan yana da Dalili Tunda bai taba Tallata ya"yansa ba wannan din ma Domin da Dalili ne.
Daman yana da Lambar Alhaji Babba tun wanchan zuwan da sukayi ya karbi Lambarsa basu taba mgana ba sai da Mallam din ya yanke shawaran zuwa chan yola suyi mgana sannan ya Kirasa suka Tattauna a kuma Satin Mallam yaje Yola shi da idi suka gana da Alhaji Babba ya kuma karbi mganar hannun bibbiyu sannan ya labartamai yadda suka sha Fama da Aminu mallam yaji Tsausayinsa sosai alokacin aka kira Aminu yazo jin Bukatar yasa bai yi gaddama ba. Ya Dauki hakan a matsayin nasa kaddaran kenan Mallam ya ga karamcin rikesa sukayi sai washegari suka juyo shi da Idi..
Sannan sun biyosa Daga baya akayi neman aure aka biya Sadaki da Lokaci bayan nan ne Aminu yazo suka gana da Hannatu kowannensu yayi mamakin ganin Dan"uwansa barin ma Hanne da tayi ta kuka tana tunanin me zata ce Amina..?
Shi kuma Aminu Kwatan kwacin Soyayyar da Amina keyi ma su Hannatu da wanda ke tsakaninsu yasa ya amince da auran Hanne Dari Bisa Dari.
Nenne bakinta har kunne take ta Godiya tana Fadin"Munga karamci Munga Kauna da kara..Allah yayi ma wannan zuru"ar albarka..!
Hajiya na amsa da Ameen aranta taji Dadi tasan Hanne bata fada hannun banza ba Nenne da zuru"arta masu karamci ne
Amina na chan tayi nisa cikin Tunani ashe har su ya Danmallam da su Aminun sun yi ma su Hajiya sallama sun Fice Daga Falon tana chan cikin Tunani bata ma sani ba sai da suka Fice ta waiga taga basu afalon sannan ta iya Sauke Nunfashi mai karfi Sulalewa tayi daga wajen Nenne ta koma kusa da Yakaka ta zauna suna Hira sama sama rabin Hankalinta na kan Dangin Hajiya yan maiduguri Dake ta shiga suna fita sannan suna kuma Rangada guda sai da Hajiya ta Tsawar tar musu sannan suka Daina ita Amina bata kawo komai aranta ba ta Dauka dai suna yi ne saboda Bikin su Hannatu.
Su Hanne take jira taji Dalilinsu na Boye mata Aminu
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41 Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49