ta Dawo da Cikin Umaru ajikinta Batula..Sannan da kayan lefe dana Haihuwa kamar za'a Bude shago sannan ga Makullin gidan daya Siya mata Batula ni fa bama shi ya Dameni ba Batula Amina Tsohon Ciki gareta Haihuwa ko yau ko gobe..!
Batula Cikin tashin Hankali tace"Ciki kuma Uwani..?.
Wai Wata Amina..?
Haj.Uwani na faman kokuwa da yanayinta tace"Batula Amina dai da aka Aurama Umar ita ke da Ciki fa..!
Batula tace"garin yaya..!
Ta yaya hakan zai faru alhalin kince kin tabbata ta sha mganin Mama..?
Haj.Uwani ta Runtse ido sai Hawaye Cikin Rawan murya tace"Bansani ba Batula bansani ba..Hajiya ta shammaceni..Shammatan datamin illah har Abada..!
Batula tace"To yanzu menene mafita..!?
Haj.Uwa ta Share Hawayenta Tana Fadin"Bazan karaya ba..Karaya ba na wa bane Batula..Dole ne nayi Nasara Batula ko ta halin kaka ne..Saboda haka ki Tashi sammako gobe ki koma wajen Mama ki fadamata Halin da ake Ciki..Ina so kada Cikin nan ya fito Duniya..Ina so a kashe koma menene acikinta ta haifesa ba rai kada yazo Duniya da ransa..Naji Samun Cikin kuskure ne sannan Hajiya in tasan wata ai bata san wata ba..Zan nuna mata Ni Uwani Kwalbar Sharri ce ko na Fashe ina da Sauran mamora..!
Batula tace"Gobe goben nan zan yi sammako..Wannan Labarin ya Firgitani ammh Hajiyar nar Allah ya Tsine mata albarka..!
Haj.Uwani Cikin Huci tace"Nayi alkwarin sai na Tarwatsa Farincikin su..Sai na Lalata musu wannan jin Dadin na su..!
Daga haka ta Datse kiran tana Sakin Huci kamar zakayan,Ta juyo a Fusace Kawai sai taci karo da Hajiya Tsaye da waya a Hannunta tana kallon Hajiya uwani Cikin wani yanayi.
Haj Uwani gabanta ya fadi ta Zaro Ido Jiki na rawa tana kallon Hajiya wacce ta Daga mata wayar hannunta ta nuna mata Sai ga sunan MALLAM baro baro alaman kira yana tafiya minti Goma sha Biyar alamun tun fara mganarta da Batula..
Jikinta na rawa Gabanta na Faduwa Zufa na keto mata ta ko"ina kawai sai ta Duka kan gwiwoyinta Domin tagama sanin Hajiya tasan wannan Boyayiyar Fuskar nata.
Cikin Rawan murya ta hada Hannayenta tana Fadin"Dom Allah Hajiya ki Rufamin asiri sharrin Shedan ne..!
Hajiya tayi mirmishin Takaici kafin ta kada kai tace"Ni ban isa na rufa miki asiri ba Uwani..Asirinki Daman chan a bankade yake..Duk wanda yace Tukuyar wani bazata tafasa ba to nashi ko Dumi bazatayi ba..Ki Fito ki Fallasa kanki Uwani Domin asirinki ya gama Tonuwa kinga wannan wayar..!.To mallam ne akan layi tun Fara mganarki da kanwarki yaji komai ki jira sakamakon ki Uwani..!
Daga haka ta katse wayarta agaban Haj.Uwani Dake zufa ko"ina na jikinta na rawa ta juya ta koma Shashenta Haj.Uwani na Rarrafe tabi bayanta tana kiran sunanta Hajiya Cikin wani yanayi ko waige bata karayi ba.
Tana shigowa Falon nata ta iske su Abida nata shewa sun tasa Amina gaba da shakiyanci sannan sauran matan kuma suna ta kara Daga kaya.
Anty Amarya ta kallah Dake Tsaye ta kasa gaba ballatana baya Mamammu kawai take kallo Tana auna yadda Balaraba ta raina mata wayau Saboda rashin ta ido ta gagije ta koma Cikin su Mamata ana ta Daga kaya da ita babu Abunda ya shafeta ko Kaffara bazatayi ba Karya ne balaraba tace batasan Amina nada Ciki ba..?
Ita Zata rufe abai bai..?
Daman ai Tun tuni ta daina Hada hanya da ita saboda taga ta riga ta gama Taimaka mata ta samu Duniya shine zataci Amanarta ta juya mata baya..?
Wlh yadda tayi alkwarin indai nata Burin bai cika ba to gayyar sai ta watse.
Tana cikin wannan Tunanin ne kawai Taji Ihun Sakina da Sauri ta juya sai taga Sakina a kasa tana gunjin kuka su Aliya na riketa da Sauri Anty Amarya ta kariso da Sauri tana rike Sakina bata so tayi wani abun da Hankalin Mutane zai dawo kansu yasa Cikin Tsawa tace"Miye haka Sakina.?
Aliya da Sadiya ku kama min ita muje Bangarena .!
Tafada tana kokarin wucewa Sakina tayi kukan kura ta Fincike daga rikon su Sadiya ta dira gaban Anty Amarya Duk da yadda Cikinta ke murda mata Ammh ina idonta ne ya Rufe bata ganin kowa sai Hango Amina da Ciki da kuma Uban Dukiyan da Umar ya Laftama Amina.
Anty Amarya ta kauce ma Sakina tana Fadin"Miye haka..?muje bangarena Sakina..!
Tafada tana kama Hannunta ganin yadda Hankalin kowa ya koma kansu Sakina ta Fizge hannunta Tana kallon Anty Amarya da Jajayen idanuwanta Cikin karaji tace"Ba inda zamu. Anan zamu yita ta kare..!
Tafada Sai hawaye Anty Amarya tasan bata Cikin Hayyacinta yasa ta Fizge ta zasu bar Falon ammh sai Sakina ta Kwace hannunta ta Turke Anty Amarya tana Fadin"Kunya kike ji kada mutane su ji yadda kika Dade kina Rainamin wayau Anty..?
Tafada tana sakar mata manyan Idanuwanta, Anty Amarya ta Zaro Ido Tana Fadin"Sakina kina cikin Hayyacinki kuwa..?
Sakina ta Kwashe da wata Dariya kafin tace"Eh tabbas bana cikin Hayyacina..Daman ai na Haukace..kalli kazamar yarinyar nan da Ciki Haihuwa ko yau ko gobe..Ni kuma kalleni shekara ta nawa ina Wahala ban samu ba..!
Koda yaushe mganar ki kenan na kwantar da Hankali na ni kadai zan zana Mowa a wajen Umar da Danginsa..Hakan ne Mowa..?
Ki kalli abunda ke faruwa a Falon nan kowa ni yake ma kallon kaskasci wannan ne Mowar..?
Ko dai Bora na zama mara amfani..?
Ina alkawarin naki..?
Ashe duk karyace bazaki iya komai ba Daga ke har malaminki makaryata ne Babu abunda zaku iya tunda har Amina ta Samu Ciki da Umar baku sani ba..!
Ta karishe Fada Cikin gunjin kuka Lokaci Daya tana jijjiga kafadun Anty Amarya tana Cigaba da Fadin"Kin manta kin Fadamin auran Amina haka zai kare a banza..?
Kin manta kin Fadamin yadda aka Daurasa haka za"a kwance sa..?
Ashe duk karya ce..?
Ashe ni kika raina ma wayau Marliya..?
Ta karishe Fada Cikin Tsawa da Budewar Murya da ya Sandarar da kowa acikin Falon har da su Sadiya da Jidda da suka zaro ido sun kasa Fahimtar me ya faru Hajiya na gefe tana kallonsu tayi mirmishi takaici ta Harde Hannayenta saman kirji Tana kallon abunda ke faruwa.
sakina ta sulale kasa tana kuka Tana Fadin"kin cuceni kin sa na yarda da kowa sama Dake...Ashe karya kike Fadamin..Ashe bazaki iya ba..Bazaki iya ba..!
Tafada tana Saka fuskarta Cikin Tafukan Hannayenta tana wani irin kukan Bakinciki da kishi.
Anty Amarya tana kokarin Daidaita kanta kada su tona ma kansu asiri ta Duka Zata riko Sakina tana Fadin"Sakina Saurare n..!
"Kada ki kara Tabani malama..!
Sakina ta Katseta Cikin karaji da sai da Anty Amarya ta fadi kasa jidda da Sadiya suka karisa suka riketa Jidda Ta kalli Sakina Cikin bacin rai Tana Fadin"Sakina Lafiyan ki kuwa..?
Kada Zafin kishi ya saka ki rasa natsuwarki mana..!
Sakina ta Dago Jajayen idanuwanta Ta balla mata Harara kafin tayi mgana Anty Amarya tayi saurin kwace jikinta cikin nasu Jidda tana Fadin"Yau za"ayi walkiya kowa zai bayyana..Na rantse da Allah ni MADINA bazan karbi Faduwa ni kadai ba..Sai dai mu yi Faduwar Guzuma..!
Tafada Lokaci Daya tana neman Balaraba Dake falon sai kawai ta Tsince ta Sum sum zata fice tun da taga Abunda ke faruwa tsakanin Madina da Sakina ta fara kokarin Barin Falon Cikin Rawan jiki Anty Amarya na Hangenta ta Daka Tsalle ta Rikota tana Fadin"Ina zaki kuma..?
Munafuka..Ai sai ki Tsaya kiga yadda wasan zai kare ko DAYYABA..?
Tafada Cikin tsaananin Tashin Hankali Datake Ciki da Jajayen Idanuwanta.
Mamanmu ta fara kokarin kwace kanta Cikin Borin kunya tana Fadin"wata dayyaban kuma..?
Marliya kada Zafin kishin ganin Amina da Ciki yasa ki fara Hauka mana..
Ko kafin ta rufe Baki Anty Amarya ta Tsinketa da mari mai Lafiya sai da kowa afalon ya Zaro ido Cikin mamaki Mamanmu sai da ta Duke Anty Amarya ta Bita ta Chakumo Wuyan riganta cikin karaji take fadin"Zaki ga Hauka yanzu nan Don Kutumar Ubanki Dayyaba..!
Lokaci Daya ta Jawo ta Tsakiyar Falon kamar kayan wanki ya Zulfa ta tare Anty Amarya tana fadin"Meyasa kika mareta kuma kike janta haka..?
Anty Amarya ta balla mata Harara da Jajayen Idanuwanta tana Fadin"Matsa ki bani wuri..Ai ke Mamanmu kika sani Balaraba baki san Wacece DAYYABA..ba yau zaku san aihinin wacece Fuskar wannan azzaluman matar..!
Sai kowa ya saki Baki Amina na Zaune tayi Dariya jin Dadi sai Hawaye afili ta Furta"Komai yazo karshe..!
Hamida ta kalleta Cikin wani yanayi tana Fadin"Me..ya ke faruwa..?
Sai Amina ta kasa ce mata komai Tsausayi suke bata yau zasu yi kwanan bakinciki in suka gano wacece ainihin mamansu.
Anty Amarya ta yarfar da Mamanmu nan Tsakiyar Falon Hajiya Goggo Husai ta mike tana Fadin"Ke marliya meye haka kuke yi kamar wasu yara..?
Anty Amarya ta Cire Dankwalinta Taci Damara tana Zaran ido ta nuna mamanmu Dake kifta ido ta rasa mafita Tace"Wannan zaku tambaya Abunda ya faru..Domin tasan komai..Nima shi nake tambayanta yanzu..Dayyaba ni zaki munafunta..?
Ni zaki yaudara ki Ha"inceni..?
Wlh na yi Rantsuwan
ko kaffara bazan yi ba kinsan inda Amina take da Halin Datake Ciki gani kikayi Burinki ya Cika Kin KASHE YAYA..sannan kin Samu Sa"idu yadda kike Fata shine yasa kika juyamin baya..?
To wlh kin yi Kuskure Ni Madina Fitilar Sharri ce ko ba kalanzir sai na kai Safe yadda ta bare dani da Uban kowa sai ta bare yau..!
Tafada Cikin karaji da Ihu kamar wata Mahaukaciya Daidai Lokacin da su Mallam sukayi sallama suka shigo Falon bayan sa kaf Zaratan ya"yansa ne kama Daga ya Danmallam Nazir ,Nasir,Nazeem,Jafar Uzairu,Shamsu Akilu da zubairu, Da Aba Aliyu abokin ya danmallam atare suka bayyana acikin Falon sai kuma waje ya Dau shuru kallo ya koma wajensu mallam.
Hajiya na ganinsu ta murmusa kafin tace"Yauwa ku kariso..Yau abun dake Boye ne zai fito Fili..anyi walkiya za"a ga kowa sannan an Dade ana ruwa kasa na Shanyewa...!
Kai Tsaye ta maida kallonta kan Anty Amarya da ko ganin su mallam bata Damu ba Burinta kawai gayyar ta watse Cikin wata murya tace"Marliya naj kin Fadi wata mgana da sunan HADIZA..?
me kike so ki fada ne..?
Anty Amarya ta kalli Mamanmu wacce ta ke kallonta Cikin Zaro Ido Jikinta na rawa ta tuma gaban Madina ta rike kafarta tana fadin"Madina don girma Allah ki rufamin asiri..Wlh na Rantse da wanda raina ke hannunsa bansan komai kan cikin Amina ba..!
Anty Amarya ta saka kafa ta Ture Mamanmu ta fadi Gefe Cikin Taruwan Hawaye tace"Wlh baki isa ba Balaraba..Ai ke kwalba ce uwar Sharri..Qur"ani kadai zaki Fadamin na yarda Dake..!
Yadda Kasuwar ta bare dani ban ci Riba ba kema yau sai ta bare dake Dayyaba..!
Tafada Lokaci Daya ta maida kallonta kan su Hajiya tana fadin"Hajiya..Mallam Sa"idu ina ya"yan Yaya su Jadwa..?
Tafada tana Binsu da kallo Cikin son suji me take son Fada suka tsura mata ido Ta juya tana kallon Mamanmu dake kuka tana rokonta kada ta Fada ta juya mata baya ta kalli Idon Aba tace"Kunga wannan matar ba Matar kwarai bace..Shekarun data kwashe tana Zaune daku duk na Cutarwarce..Muguwa ce Azzaluma ni Duk Mugunta na ban taba Kisa ba..Ammh Kunga wannan..?
To Tayi kisan kai ta kashe rai Har Lahira..!
Aba Cikin rawan baki dana murya yace"Wa...ta Kashe..?
Kafin ta samu bakin mgana Daga bayansu sukaji wata murya Cikin Kuna tace
"YAYA TA KASHE ABA..!
Sai kallo ya koma inda akaji mganar sai ga Amina ta bayyana a Tsakiyar Falin gaban Anty Amarya da Mamanmu da ke tsuggune cikin Fitar hawaye Duka Biyu.
Gabadaya sai kowa yaji wani sanyin jiki Aba sai da ya Dafa ya Danmallam Dake gefensa saboda jirin Daya kwashesa Anty Amarya kuma Amina take kallo da Mamakin a ina tasan wannan mganar..?
Mamanmu kuma kasa kawai tayi Dakai yauma Tubular sara"i babu Tsima babu Dubara.
Ya jalela da su ya Jadwa suman Tsaye sukayi ya jafar ne ya iya takowa ya iso gaban Amina ganinta da Ciki ba shi ne agabansa ba mganar data Fada ne abun Damuwa..
Cikin Fitan Hayyaci ya kama jijjiga Kafadun Amina yana Fadin"Wata Yayar ne ta kashe..?
UMMANMU..?
Ya fada Cikin Tsawa Idanuwansa Jajir kawai sai Amina ta Fashe da kuka ta Fada Jikin ya jafar tana nuna Mamanmu Cikin wata murya tana Fadin"Itace ta kashe mana Uwa ya Jafar..Itace ta rabamu da Aba..Itace ta rabani da Uwata Shekaru goma da wani abu bansan Dadinta ba..
Itace ta maka asiri domin ka lalace sai abun ya Dawo kaina.
Itace ta hada kai da Anty Amarya ana Zaluntar ya Danmallam itace kuma suka ka Hada kai domin su ga bayan aurena da ya danmallan da alwashin har Abada bazan taba Haihuwa ba..
Ya jafar wlh wannan matar muguwace kuma azzaluma ce ta Dade tana Zaluntarmu bamu sani ba..itace ta kashe mana YaYA DA kunnena naji ta tana Fada..!
Ta karishe fada Numfashinta na Sarkewa,Ya Jafar ya riketa Cikin wani yanayi yanayin da baya fatan ya Bude ido yaga abunda ke faruwa da gaske ne.
Durkushewa Amina tayi kasa Jafar ya Bita ya Tallafeta,ya Danmallam ya kariso ya riketa yana Cire mata Hijabi Saboda ta samu iska tana ganinsa ta Damke hannunta Cikin rawan murya tana Fadin"itace..Ita ta kashe mana YAYA..!
Malam dake tsaye yace"innalillahi wa"inna ilaihirraju"un..!
Sai kowa afalon ya Dauka Saboda kowa ya rasa abun Fadi.
Mamanmu na wani irin gunjin kuka tace"Kaico na..Bansan akwai wannan ranar ba..Da ban aikata abunda na aikata ba..Don Allah ku yafemin..!
Gabadaya kallonta kawai ake yi Cikin Wani yanayi Aba kuma zaman dirshan yayi a kasan Cafet ya kasa mgana su ya Jadwa kuma suna dai Tsaye da karfin Imani.
Hajiya ce ta kalli mamanmu tana Fadin"Balaraba me Hadiza ta miki kika Kasheta kika raba ta da wannan Duniyar..?
Tafada cikin wani yanayin muryanta kamar zatayi kuka Ranar da
Danmallan yazo mata da wannan mganar bata gasgasta ba har yau tana cikin Tantaman balaraba zata iya Kasje Yaya sai yanzu da komai yake neman bayyana.
Mamanmu tana kuka kanta na kasa ta kasa Dago kanta saboda kunya balle ta kalli Ya"yanta da yayan yaya ga Aba ga kunya mutanen Dake falon Anty Amarya kuma na Tsaye ta shirya komai ayau Sakina ma duk suna gefe banda kuka babu abunda take yi.
Amina kuma Danmallam jikinsa ya Tarairayota ya azata yana ta faman mata fifita da Hijabinta Sakina na kallonsu tana jin kamar ta mutu saboda bakinciki.
Kan Mamanmu na kasa ta fara mgana.
"SOYAYYAR SA"IDU CE SILA..."
*Janafty**TFZB2025*
*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yada'ashi..Pay N500 via Jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan lambar 09069067488*
Su Mamanmu na tsakar gida suna ta Hidima akazo da labarin Hajiya tace suzo ga Amina ta dawo Mamanmu sai taji kamar bataji da kyau ba badai Amina ba,in ma Aminar ne bata taba Tunanin ganin abunda zataje ta gani ba Saboda mai Fadar bata Fadi cewa Amina da tsohon ciki ta dawo ba.
Ana fadin ga Amina ta dawo kowa da kowa ya zura Hijabi har da goggo Husai da su ya Jawahir domin sun yi kewar yar kanwar tasu tarr da mutanen Gusai,har da matan su ya jafar dake gidan tunda chan gidan su Abida suka bar ma gidan su suna nan ana ta aiki dasu.
Mamanmu ko Hijabi bata tsaya sawa ba,Zanin goyon Zulfa ne Dake kan igiya ta Rataya sai gidan Baba mallam itace kan gaba so take taga da gasken Aminar ne..?
Domin har alokacin gabanta bai Fadi ba bata sare ba ballatana ranta ya kawo mata yau ranar Tonon asiri ce.
Sai dai me suna shiga falon sai kallo ya koma kansu Mamanmu bata lura da ko su Anty Amarya ba ballatana Uban kayan lefem Dake zube a falon Hajiya Burinta kawai taga Amina domin ta gasgasta abunda aka Fadamata yasa tana shigowa ta Daga Murya tana Fadin"Ina Aminar da akace ta Dawo..?
Amina..!
Ta fada da dan karfi domin ita a zatonta karye ne ba wata Amina,Sai dai ga mamakinta wata ta gani kamar Amina ta mike tsaye Dakyar har Yakaka na Taimakamata ta mike Sai ga Cikinta ya bayyana Cikin Ido tana kallon Mamanmu cikin wani yanayin Da ta kasa Fassarashi tace"Ga ni nan Mamanmu..!
Tafada da wani Sauti na Rauni Sai taji bata ji kunyar cikin dake jikinta ba Ko Hannunta bata saka ta kare kamar yadda ta saba ba so take taga yadda Mamanmu zatayi in ta ganta da Ciki.
Aikuwa Mamanmu ido ta Zaro Jikinta ba inda baya rawa ido ta murza ta kara Murza,kamar yadda su Ya Jalela suka saki Baki suna kallon Amina sun ma kasa mgana.
Goggo Husai ce Cikin mamaki tace"Amina..!
Tafada tana takawa gabanta Amina sai taji kunya kanta na kasa tace"Ina yini goggo..!
Sai goggo Husai ta rike baki ta kara Leka Fuskar Amina kafin ta kalli Cikin jikinta ta rike Haba tace"Ikon Allah Zainabu duk yaushe haka ta faru ba Labari ina tunanin ko Sa'idu bai Tabamin zencen Amina ba Domin da Jadwa ta fadamin bata a gida dana masa mgana yace min kinsan inda take bai taba Fadamin Halin da yarinyar nan take ciki ba..!
Hajiya na Tsaye ta murmusa Kafin tace"Ai ko shi Sa"idun bai sani ba..Dagani sai mallan Sai mijinta kadai muka san da wannan cikin Husai..!
Gogggo Husai ta kara jinjina kai kafin tace"To ina tayi renon Cikin..?
Hajiya tace"Abuja..wajen Aisha na kaita..!
Goggo Husai sai ta samu waje ta Zauna tana Fadin"Ikon Allah..!
Saboda abun ya bata mamaki ne dayasa kalamanta suka kare,Mamanmu kuma kamar suman Tsaye tayi daga inda take ko motsi ta kasa kamar yadda Anty Amarya da Haj.Uwani suke Dansare a tsaye sun rasa ma wani Tunani zasu yi duk yaushe hakan ta faru..!?
Su ya Jawahir kuwa karisawa gaban Amina sukayi suna kiran sunanta sai ta amsa tana gaishesu har da su ya Zulfa ya Zahra suna ta kallon Amina mamaki yasa sun ma kasa mgana ya Zulaihat ne sai da ta Rumgume Amina tana fadin"Allah Sarki Aminene..Aminene ta kusa zama uwa. !
Amina batace komai ba kanta na kasa,nan da nan falon ya kwace me da Hayaniyar mata yan gusai suma suna ta Tofa albarkacin Bakinsu,yan"uwan Amina kallonta kawai suke yi kamar wata Hallita ya Jadwa Mirmishi take yi a kasan ranta Lokaci Daya Hawaye suka kawo idonta afili ta Furta"Yau ina Yaya take..?
naso tana raye taga yadda Amina ta koma..Yau Amina ce da Cikin Haihuwa Sannan uwa uba Amina tayi hankali ba mgana ba fada ba tsiwa ba kunkuni madallah da uwa irin Hajiya madallah da Uba irin Baba mallam..Sannan madallah da Gwarzom Miji irin Yaya Danmallan..!
Ya Jaleela ta share kwallah ta rike Amina tana fadin"Amina naji Dadin ganinki haka naji Dadi..!
Kawai sai ta Fashe da kuka itama Aminar daman kiris take jira sai kuka Yakaka ta riketa ta koma ta zauna tana Fadin"ku daina sakata kuka tana da Lalura sannan kusanta akwai Daman arhan kuka..!
Kamar an ce ta kara ne haka Amina ke kuka su Jaleela ma suna Tayata
Showing 105001 words to 108000 words out of 146831 words
Batula Cikin tashin Hankali tace"Ciki kuma Uwani..?.
Wai Wata Amina..?
Haj.Uwani na faman kokuwa da yanayinta tace"Batula Amina dai da aka Aurama Umar ita ke da Ciki fa..!
Batula tace"garin yaya..!
Ta yaya hakan zai faru alhalin kince kin tabbata ta sha mganin Mama..?
Haj.Uwani ta Runtse ido sai Hawaye Cikin Rawan murya tace"Bansani ba Batula bansani ba..Hajiya ta shammaceni..Shammatan datamin illah har Abada..!
Batula tace"To yanzu menene mafita..!?
Haj.Uwa ta Share Hawayenta Tana Fadin"Bazan karaya ba..Karaya ba na wa bane Batula..Dole ne nayi Nasara Batula ko ta halin kaka ne..Saboda haka ki Tashi sammako gobe ki koma wajen Mama ki fadamata Halin da ake Ciki..Ina so kada Cikin nan ya fito Duniya..Ina so a kashe koma menene acikinta ta haifesa ba rai kada yazo Duniya da ransa..Naji Samun Cikin kuskure ne sannan Hajiya in tasan wata ai bata san wata ba..Zan nuna mata Ni Uwani Kwalbar Sharri ce ko na Fashe ina da Sauran mamora..!
Batula tace"Gobe goben nan zan yi sammako..Wannan Labarin ya Firgitani ammh Hajiyar nar Allah ya Tsine mata albarka..!
Haj.Uwani Cikin Huci tace"Nayi alkwarin sai na Tarwatsa Farincikin su..Sai na Lalata musu wannan jin Dadin na su..!
Daga haka ta Datse kiran tana Sakin Huci kamar zakayan,Ta juyo a Fusace Kawai sai taci karo da Hajiya Tsaye da waya a Hannunta tana kallon Hajiya uwani Cikin wani yanayi.
Haj Uwani gabanta ya fadi ta Zaro Ido Jiki na rawa tana kallon Hajiya wacce ta Daga mata wayar hannunta ta nuna mata Sai ga sunan MALLAM baro baro alaman kira yana tafiya minti Goma sha Biyar alamun tun fara mganarta da Batula..
Jikinta na rawa Gabanta na Faduwa Zufa na keto mata ta ko"ina kawai sai ta Duka kan gwiwoyinta Domin tagama sanin Hajiya tasan wannan Boyayiyar Fuskar nata.
Cikin Rawan murya ta hada Hannayenta tana Fadin"Dom Allah Hajiya ki Rufamin asiri sharrin Shedan ne..!
Hajiya tayi mirmishin Takaici kafin ta kada kai tace"Ni ban isa na rufa miki asiri ba Uwani..Asirinki Daman chan a bankade yake..Duk wanda yace Tukuyar wani bazata tafasa ba to nashi ko Dumi bazatayi ba..Ki Fito ki Fallasa kanki Uwani Domin asirinki ya gama Tonuwa kinga wannan wayar..!.To mallam ne akan layi tun Fara mganarki da kanwarki yaji komai ki jira sakamakon ki Uwani..!
Daga haka ta katse wayarta agaban Haj.Uwani Dake zufa ko"ina na jikinta na rawa ta juya ta koma Shashenta Haj.Uwani na Rarrafe tabi bayanta tana kiran sunanta Hajiya Cikin wani yanayi ko waige bata karayi ba.
Tana shigowa Falon nata ta iske su Abida nata shewa sun tasa Amina gaba da shakiyanci sannan sauran matan kuma suna ta kara Daga kaya.
Anty Amarya ta kallah Dake Tsaye ta kasa gaba ballatana baya Mamammu kawai take kallo Tana auna yadda Balaraba ta raina mata wayau Saboda rashin ta ido ta gagije ta koma Cikin su Mamata ana ta Daga kaya da ita babu Abunda ya shafeta ko Kaffara bazatayi ba Karya ne balaraba tace batasan Amina nada Ciki ba..?
Ita Zata rufe abai bai..?
Daman ai Tun tuni ta daina Hada hanya da ita saboda taga ta riga ta gama Taimaka mata ta samu Duniya shine zataci Amanarta ta juya mata baya..?
Wlh yadda tayi alkwarin indai nata Burin bai cika ba to gayyar sai ta watse.
Tana cikin wannan Tunanin ne kawai Taji Ihun Sakina da Sauri ta juya sai taga Sakina a kasa tana gunjin kuka su Aliya na riketa da Sauri Anty Amarya ta kariso da Sauri tana rike Sakina bata so tayi wani abun da Hankalin Mutane zai dawo kansu yasa Cikin Tsawa tace"Miye haka Sakina.?
Aliya da Sadiya ku kama min ita muje Bangarena .!
Tafada tana kokarin wucewa Sakina tayi kukan kura ta Fincike daga rikon su Sadiya ta dira gaban Anty Amarya Duk da yadda Cikinta ke murda mata Ammh ina idonta ne ya Rufe bata ganin kowa sai Hango Amina da Ciki da kuma Uban Dukiyan da Umar ya Laftama Amina.
Anty Amarya ta kauce ma Sakina tana Fadin"Miye haka..?muje bangarena Sakina..!
Tafada tana kama Hannunta ganin yadda Hankalin kowa ya koma kansu Sakina ta Fizge hannunta Tana kallon Anty Amarya da Jajayen idanuwanta Cikin karaji tace"Ba inda zamu. Anan zamu yita ta kare..!
Tafada Sai hawaye Anty Amarya tasan bata Cikin Hayyacinta yasa ta Fizge ta zasu bar Falon ammh sai Sakina ta Kwace hannunta ta Turke Anty Amarya tana Fadin"Kunya kike ji kada mutane su ji yadda kika Dade kina Rainamin wayau Anty..?
Tafada tana sakar mata manyan Idanuwanta, Anty Amarya ta Zaro Ido Tana Fadin"Sakina kina cikin Hayyacinki kuwa..?
Sakina ta Kwashe da wata Dariya kafin tace"Eh tabbas bana cikin Hayyacina..Daman ai na Haukace..kalli kazamar yarinyar nan da Ciki Haihuwa ko yau ko gobe..Ni kuma kalleni shekara ta nawa ina Wahala ban samu ba..!
Koda yaushe mganar ki kenan na kwantar da Hankali na ni kadai zan zana Mowa a wajen Umar da Danginsa..Hakan ne Mowa..?
Ki kalli abunda ke faruwa a Falon nan kowa ni yake ma kallon kaskasci wannan ne Mowar..?
Ko dai Bora na zama mara amfani..?
Ina alkawarin naki..?
Ashe duk karyace bazaki iya komai ba Daga ke har malaminki makaryata ne Babu abunda zaku iya tunda har Amina ta Samu Ciki da Umar baku sani ba..!
Ta karishe Fada Cikin gunjin kuka Lokaci Daya tana jijjiga kafadun Anty Amarya tana Cigaba da Fadin"Kin manta kin Fadamin auran Amina haka zai kare a banza..?
Kin manta kin Fadamin yadda aka Daurasa haka za"a kwance sa..?
Ashe duk karya ce..?
Ashe ni kika raina ma wayau Marliya..?
Ta karishe Fada Cikin Tsawa da Budewar Murya da ya Sandarar da kowa acikin Falon har da su Sadiya da Jidda da suka zaro ido sun kasa Fahimtar me ya faru Hajiya na gefe tana kallonsu tayi mirmishi takaici ta Harde Hannayenta saman kirji Tana kallon abunda ke faruwa.
sakina ta sulale kasa tana kuka Tana Fadin"kin cuceni kin sa na yarda da kowa sama Dake...Ashe karya kike Fadamin..Ashe bazaki iya ba..Bazaki iya ba..!
Tafada tana Saka fuskarta Cikin Tafukan Hannayenta tana wani irin kukan Bakinciki da kishi.
Anty Amarya tana kokarin Daidaita kanta kada su tona ma kansu asiri ta Duka Zata riko Sakina tana Fadin"Sakina Saurare n..!
"Kada ki kara Tabani malama..!
Sakina ta Katseta Cikin karaji da sai da Anty Amarya ta fadi kasa jidda da Sadiya suka karisa suka riketa Jidda Ta kalli Sakina Cikin bacin rai Tana Fadin"Sakina Lafiyan ki kuwa..?
Kada Zafin kishi ya saka ki rasa natsuwarki mana..!
Sakina ta Dago Jajayen idanuwanta Ta balla mata Harara kafin tayi mgana Anty Amarya tayi saurin kwace jikinta cikin nasu Jidda tana Fadin"Yau za"ayi walkiya kowa zai bayyana..Na rantse da Allah ni MADINA bazan karbi Faduwa ni kadai ba..Sai dai mu yi Faduwar Guzuma..!
Tafada Lokaci Daya tana neman Balaraba Dake falon sai kawai ta Tsince ta Sum sum zata fice tun da taga Abunda ke faruwa tsakanin Madina da Sakina ta fara kokarin Barin Falon Cikin Rawan jiki Anty Amarya na Hangenta ta Daka Tsalle ta Rikota tana Fadin"Ina zaki kuma..?
Munafuka..Ai sai ki Tsaya kiga yadda wasan zai kare ko DAYYABA..?
Tafada Cikin tsaananin Tashin Hankali Datake Ciki da Jajayen Idanuwanta.
Mamanmu ta fara kokarin kwace kanta Cikin Borin kunya tana Fadin"wata dayyaban kuma..?
Marliya kada Zafin kishin ganin Amina da Ciki yasa ki fara Hauka mana..
Ko kafin ta rufe Baki Anty Amarya ta Tsinketa da mari mai Lafiya sai da kowa afalon ya Zaro ido Cikin mamaki Mamanmu sai da ta Duke Anty Amarya ta Bita ta Chakumo Wuyan riganta cikin karaji take fadin"Zaki ga Hauka yanzu nan Don Kutumar Ubanki Dayyaba..!
Lokaci Daya ta Jawo ta Tsakiyar Falon kamar kayan wanki ya Zulfa ta tare Anty Amarya tana fadin"Meyasa kika mareta kuma kike janta haka..?
Anty Amarya ta balla mata Harara da Jajayen Idanuwanta tana Fadin"Matsa ki bani wuri..Ai ke Mamanmu kika sani Balaraba baki san Wacece DAYYABA..ba yau zaku san aihinin wacece Fuskar wannan azzaluman matar..!
Sai kowa ya saki Baki Amina na Zaune tayi Dariya jin Dadi sai Hawaye afili ta Furta"Komai yazo karshe..!
Hamida ta kalleta Cikin wani yanayi tana Fadin"Me..ya ke faruwa..?
Sai Amina ta kasa ce mata komai Tsausayi suke bata yau zasu yi kwanan bakinciki in suka gano wacece ainihin mamansu.
Anty Amarya ta yarfar da Mamanmu nan Tsakiyar Falon Hajiya Goggo Husai ta mike tana Fadin"Ke marliya meye haka kuke yi kamar wasu yara..?
Anty Amarya ta Cire Dankwalinta Taci Damara tana Zaran ido ta nuna mamanmu Dake kifta ido ta rasa mafita Tace"Wannan zaku tambaya Abunda ya faru..Domin tasan komai..Nima shi nake tambayanta yanzu..Dayyaba ni zaki munafunta..?
Ni zaki yaudara ki Ha"inceni..?
Wlh na yi Rantsuwan
ko kaffara bazan yi ba kinsan inda Amina take da Halin Datake Ciki gani kikayi Burinki ya Cika Kin KASHE YAYA..sannan kin Samu Sa"idu yadda kike Fata shine yasa kika juyamin baya..?
To wlh kin yi Kuskure Ni Madina Fitilar Sharri ce ko ba kalanzir sai na kai Safe yadda ta bare dani da Uban kowa sai ta bare yau..!
Tafada Cikin karaji da Ihu kamar wata Mahaukaciya Daidai Lokacin da su Mallam sukayi sallama suka shigo Falon bayan sa kaf Zaratan ya"yansa ne kama Daga ya Danmallam Nazir ,Nasir,Nazeem,Jafar Uzairu,Shamsu Akilu da zubairu, Da Aba Aliyu abokin ya danmallam atare suka bayyana acikin Falon sai kuma waje ya Dau shuru kallo ya koma wajensu mallam.
Hajiya na ganinsu ta murmusa kafin tace"Yauwa ku kariso..Yau abun dake Boye ne zai fito Fili..anyi walkiya za"a ga kowa sannan an Dade ana ruwa kasa na Shanyewa...!
Kai Tsaye ta maida kallonta kan Anty Amarya da ko ganin su mallam bata Damu ba Burinta kawai gayyar ta watse Cikin wata murya tace"Marliya naj kin Fadi wata mgana da sunan HADIZA..?
me kike so ki fada ne..?
Anty Amarya ta kalli Mamanmu wacce ta ke kallonta Cikin Zaro Ido Jikinta na rawa ta tuma gaban Madina ta rike kafarta tana fadin"Madina don girma Allah ki rufamin asiri..Wlh na Rantse da wanda raina ke hannunsa bansan komai kan cikin Amina ba..!
Anty Amarya ta saka kafa ta Ture Mamanmu ta fadi Gefe Cikin Taruwan Hawaye tace"Wlh baki isa ba Balaraba..Ai ke kwalba ce uwar Sharri..Qur"ani kadai zaki Fadamin na yarda Dake..!
Yadda Kasuwar ta bare dani ban ci Riba ba kema yau sai ta bare dake Dayyaba..!
Tafada Lokaci Daya ta maida kallonta kan su Hajiya tana fadin"Hajiya..Mallam Sa"idu ina ya"yan Yaya su Jadwa..?
Tafada tana Binsu da kallo Cikin son suji me take son Fada suka tsura mata ido Ta juya tana kallon Mamanmu dake kuka tana rokonta kada ta Fada ta juya mata baya ta kalli Idon Aba tace"Kunga wannan matar ba Matar kwarai bace..Shekarun data kwashe tana Zaune daku duk na Cutarwarce..Muguwa ce Azzaluma ni Duk Mugunta na ban taba Kisa ba..Ammh Kunga wannan..?
To Tayi kisan kai ta kashe rai Har Lahira..!
Aba Cikin rawan baki dana murya yace"Wa...ta Kashe..?
Kafin ta samu bakin mgana Daga bayansu sukaji wata murya Cikin Kuna tace
"YAYA TA KASHE ABA..!
Sai kallo ya koma inda akaji mganar sai ga Amina ta bayyana a Tsakiyar Falin gaban Anty Amarya da Mamanmu da ke tsuggune cikin Fitar hawaye Duka Biyu.
Gabadaya sai kowa yaji wani sanyin jiki Aba sai da ya Dafa ya Danmallam Dake gefensa saboda jirin Daya kwashesa Anty Amarya kuma Amina take kallo da Mamakin a ina tasan wannan mganar..?
Mamanmu kuma kasa kawai tayi Dakai yauma Tubular sara"i babu Tsima babu Dubara.
Ya jalela da su ya Jadwa suman Tsaye sukayi ya jafar ne ya iya takowa ya iso gaban Amina ganinta da Ciki ba shi ne agabansa ba mganar data Fada ne abun Damuwa..
Cikin Fitan Hayyaci ya kama jijjiga Kafadun Amina yana Fadin"Wata Yayar ne ta kashe..?
UMMANMU..?
Ya fada Cikin Tsawa Idanuwansa Jajir kawai sai Amina ta Fashe da kuka ta Fada Jikin ya jafar tana nuna Mamanmu Cikin wata murya tana Fadin"Itace ta kashe mana Uwa ya Jafar..Itace ta rabamu da Aba..Itace ta rabani da Uwata Shekaru goma da wani abu bansan Dadinta ba..
Itace ta maka asiri domin ka lalace sai abun ya Dawo kaina.
Itace ta hada kai da Anty Amarya ana Zaluntar ya Danmallam itace kuma suka ka Hada kai domin su ga bayan aurena da ya danmallan da alwashin har Abada bazan taba Haihuwa ba..
Ya jafar wlh wannan matar muguwace kuma azzaluma ce ta Dade tana Zaluntarmu bamu sani ba..itace ta kashe mana YaYA DA kunnena naji ta tana Fada..!
Ta karishe fada Numfashinta na Sarkewa,Ya Jafar ya riketa Cikin wani yanayi yanayin da baya fatan ya Bude ido yaga abunda ke faruwa da gaske ne.
Durkushewa Amina tayi kasa Jafar ya Bita ya Tallafeta,ya Danmallam ya kariso ya riketa yana Cire mata Hijabi Saboda ta samu iska tana ganinsa ta Damke hannunta Cikin rawan murya tana Fadin"itace..Ita ta kashe mana YAYA..!
Malam dake tsaye yace"innalillahi wa"inna ilaihirraju"un..!
Sai kowa afalon ya Dauka Saboda kowa ya rasa abun Fadi.
Mamanmu na wani irin gunjin kuka tace"Kaico na..Bansan akwai wannan ranar ba..Da ban aikata abunda na aikata ba..Don Allah ku yafemin..!
Gabadaya kallonta kawai ake yi Cikin Wani yanayi Aba kuma zaman dirshan yayi a kasan Cafet ya kasa mgana su ya Jadwa kuma suna dai Tsaye da karfin Imani.
Hajiya ce ta kalli mamanmu tana Fadin"Balaraba me Hadiza ta miki kika Kasheta kika raba ta da wannan Duniyar..?
Tafada cikin wani yanayin muryanta kamar zatayi kuka Ranar da
Danmallan yazo mata da wannan mganar bata gasgasta ba har yau tana cikin Tantaman balaraba zata iya Kasje Yaya sai yanzu da komai yake neman bayyana.
Mamanmu tana kuka kanta na kasa ta kasa Dago kanta saboda kunya balle ta kalli Ya"yanta da yayan yaya ga Aba ga kunya mutanen Dake falon Anty Amarya kuma na Tsaye ta shirya komai ayau Sakina ma duk suna gefe banda kuka babu abunda take yi.
Amina kuma Danmallam jikinsa ya Tarairayota ya azata yana ta faman mata fifita da Hijabinta Sakina na kallonsu tana jin kamar ta mutu saboda bakinciki.
Kan Mamanmu na kasa ta fara mgana.
"SOYAYYAR SA"IDU CE SILA..."
*Janafty**TFZB2025*
*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yada'ashi..Pay N500 via Jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan lambar 09069067488*
Su Mamanmu na tsakar gida suna ta Hidima akazo da labarin Hajiya tace suzo ga Amina ta dawo Mamanmu sai taji kamar bataji da kyau ba badai Amina ba,in ma Aminar ne bata taba Tunanin ganin abunda zataje ta gani ba Saboda mai Fadar bata Fadi cewa Amina da tsohon ciki ta dawo ba.
Ana fadin ga Amina ta dawo kowa da kowa ya zura Hijabi har da goggo Husai da su ya Jawahir domin sun yi kewar yar kanwar tasu tarr da mutanen Gusai,har da matan su ya jafar dake gidan tunda chan gidan su Abida suka bar ma gidan su suna nan ana ta aiki dasu.
Mamanmu ko Hijabi bata tsaya sawa ba,Zanin goyon Zulfa ne Dake kan igiya ta Rataya sai gidan Baba mallam itace kan gaba so take taga da gasken Aminar ne..?
Domin har alokacin gabanta bai Fadi ba bata sare ba ballatana ranta ya kawo mata yau ranar Tonon asiri ce.
Sai dai me suna shiga falon sai kallo ya koma kansu Mamanmu bata lura da ko su Anty Amarya ba ballatana Uban kayan lefem Dake zube a falon Hajiya Burinta kawai taga Amina domin ta gasgasta abunda aka Fadamata yasa tana shigowa ta Daga Murya tana Fadin"Ina Aminar da akace ta Dawo..?
Amina..!
Ta fada da dan karfi domin ita a zatonta karye ne ba wata Amina,Sai dai ga mamakinta wata ta gani kamar Amina ta mike tsaye Dakyar har Yakaka na Taimakamata ta mike Sai ga Cikinta ya bayyana Cikin Ido tana kallon Mamanmu cikin wani yanayin Da ta kasa Fassarashi tace"Ga ni nan Mamanmu..!
Tafada da wani Sauti na Rauni Sai taji bata ji kunyar cikin dake jikinta ba Ko Hannunta bata saka ta kare kamar yadda ta saba ba so take taga yadda Mamanmu zatayi in ta ganta da Ciki.
Aikuwa Mamanmu ido ta Zaro Jikinta ba inda baya rawa ido ta murza ta kara Murza,kamar yadda su Ya Jalela suka saki Baki suna kallon Amina sun ma kasa mgana.
Goggo Husai ce Cikin mamaki tace"Amina..!
Tafada tana takawa gabanta Amina sai taji kunya kanta na kasa tace"Ina yini goggo..!
Sai goggo Husai ta rike baki ta kara Leka Fuskar Amina kafin ta kalli Cikin jikinta ta rike Haba tace"Ikon Allah Zainabu duk yaushe haka ta faru ba Labari ina tunanin ko Sa'idu bai Tabamin zencen Amina ba Domin da Jadwa ta fadamin bata a gida dana masa mgana yace min kinsan inda take bai taba Fadamin Halin da yarinyar nan take ciki ba..!
Hajiya na Tsaye ta murmusa Kafin tace"Ai ko shi Sa"idun bai sani ba..Dagani sai mallan Sai mijinta kadai muka san da wannan cikin Husai..!
Gogggo Husai ta kara jinjina kai kafin tace"To ina tayi renon Cikin..?
Hajiya tace"Abuja..wajen Aisha na kaita..!
Goggo Husai sai ta samu waje ta Zauna tana Fadin"Ikon Allah..!
Saboda abun ya bata mamaki ne dayasa kalamanta suka kare,Mamanmu kuma kamar suman Tsaye tayi daga inda take ko motsi ta kasa kamar yadda Anty Amarya da Haj.Uwani suke Dansare a tsaye sun rasa ma wani Tunani zasu yi duk yaushe hakan ta faru..!?
Su ya Jawahir kuwa karisawa gaban Amina sukayi suna kiran sunanta sai ta amsa tana gaishesu har da su ya Zulfa ya Zahra suna ta kallon Amina mamaki yasa sun ma kasa mgana ya Zulaihat ne sai da ta Rumgume Amina tana fadin"Allah Sarki Aminene..Aminene ta kusa zama uwa. !
Amina batace komai ba kanta na kasa,nan da nan falon ya kwace me da Hayaniyar mata yan gusai suma suna ta Tofa albarkacin Bakinsu,yan"uwan Amina kallonta kawai suke yi kamar wata Hallita ya Jadwa Mirmishi take yi a kasan ranta Lokaci Daya Hawaye suka kawo idonta afili ta Furta"Yau ina Yaya take..?
naso tana raye taga yadda Amina ta koma..Yau Amina ce da Cikin Haihuwa Sannan uwa uba Amina tayi hankali ba mgana ba fada ba tsiwa ba kunkuni madallah da uwa irin Hajiya madallah da Uba irin Baba mallam..Sannan madallah da Gwarzom Miji irin Yaya Danmallan..!
Ya Jaleela ta share kwallah ta rike Amina tana fadin"Amina naji Dadin ganinki haka naji Dadi..!
Kawai sai ta Fashe da kuka itama Aminar daman kiris take jira sai kuka Yakaka ta riketa ta koma ta zauna tana Fadin"ku daina sakata kuka tana da Lalura sannan kusanta akwai Daman arhan kuka..!
Kamar an ce ta kara ne haka Amina ke kuka su Jaleela ma suna Tayata
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36 Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49