matsayina na Uba a wajensa..Ina Fatan abubuwan da suka Faru su zama izna garemu da yan baya..Sannan ina Rokon Allah ya Tsaremu da zuru"armu gabadaya Daga Fadawa Halaka..!
Hajiya ta amsa da Ameen Ameen basu wani Dade suna mgana ba ta koma Shashenta ta bar mallam zai kwanta Saboda tun faruwar abun nan bai wani Cikin natsuwarsa abun ya tabasa sosai,Ita kanta sai a Hankali ta gama tsorata da Duniya da mutanen Cikinta Har ita kanta Nasara sai ahankali gidan gabadaya sai yayi kamar ba kowa,shuru kowa kumazaka gansa baya cikin Walwalarsa.
Hajiya bata yima Sarood mgana ba Illah ce mata tayi taje mallam na nemanta Sai da taje ne Mallam yayi mata Nasiha Daga karshe yace tayi Hakuri ta koma Gidan mijinta ta zauna kafin su tafi ta tabbarar mai da Insha Allahu zata koma sannan ya Sallameta Kai Tsaye kuma ya Kira Danmallam yace yazo yana nemansa Tun da yammah bai samu zuwa ba Sai Dare saboda Rigimar Amina wai sai yazo da ita bazata iya zama ita kadai ba yasan in yazo da ita sai ya shafada wajen Hajiya kamar yadda akayi Ranar shiyasa ya zauna ya lallabata Dakyar da Sharadin bazai Dade ba Sannan ta barsa ya fito.
Sai da suka Idar da Sallar Isha"i sannan Suka gana da mallam a Falonsa mallam bai nuna mai ya san wani abu ya tambayesa zaman me Saratu take bata koma gidansa ba..?
Sai ya karantamai yadda sukayi da ita Mallam yace"Wannan ba Hujja bane Umaru..ita macece kai kuma Namiji ne Shugaba..Kada ka manta adalci ne aikinka Tsakanin matanka..Kada ka bari Daya ta Rinjaye ka domin Ranar Lahira zaka tashi da Barayinka daya ne yana Rinjayan Daya. kada ka Duba wai Tare kuke achan duk wannan ba Hujja bace..Zaka raba musu kwana ne har Lokacin da zaka koma shine adalci..!
Danmallan kansa na kasa yana gyada kai bai ce komai ba Mallam ya Cigaba da fadin"Na kira ta na mata mgana saboda haka yanzu ka Dauki matarka ku tafi gidanku..Allah ya zaunar daku lafiya..!
Danmallam sai Lokacin ya Dago kansa yana Fadin"Naji Duka mganar ka mallam..Sai dai ina so kamin afuwa Zuwa gobe da zan cika Sati Daya awajen Amina sai na koma wajen Sarood din..!.
Mallam ya kallesa kafin yace"Shikenan daman na Tunasar Dakai ne..Itama akwai Hakkinta akanka Umaru kuma ina yi maka kwadayin Zama mutum adali Allah yayu muku albarka ya wajen ita mamar tawa..?
Fata dai ba wata Damuwa ko..?
Danmallam yace"Lafiya lau mallam..!
Daga haka shuru ya Biyo baya sai Danmallam din ne ya gyara zama yana Fadin"Mallam daman ina so nayi ma Hajiya mgana..Yakaka kakar mijin Aisha da bata koma ba tunda sun shaku da Aminar me zai hana ta koma chan Gidan Aminar su zauna tare..Ga Halin Datake ciki sannan in ina gidan Sarood bazan dinga Fargaba ba..!
Mallam acikin Ransa Hamdala yake yi Saboda yaga kaunar Mamar tasa a cikin Idanuwan Umar.
Kai Tsaye yace"Kayi Tunani mai kyau..Kada ka Damu zan yima Hajiyar mgana gobe sai ta saka Idi yakaita Yakaka akwai kirki da karamci Sosai shekaran jiya ta na nan har Dare muna ta hira da ita..!
Danmallam yayi godiyar har ya mike zai tafi Mallam ya saka Baki ya ka kirasa ya Dawo ya Durkusa a gabansa Mallam ya kallesa Kafin yace"Ya mganar Ka Da Sakina..?
Naji har yanzu baka ce komai ba..Sannan kana jin labarin Halin Datake ciki domin an ce ta kara rasa wannan cikin shima..Allah ya kyauta na gaba..!
Danmallam kansa na kasa yace"Mallam ni bansan komai ba tadai Kirani Sau biyu shekaran jiya ban Dauki kiranta ba..!
Mallam ya gyada kai kafin yace"Kaje kayi Tunani Umaru..Duk abunda ka yanke sai ka sanar dani..Ammh ina so ka Sani ka Bude zuciyarka Dakyau ka gani ko zaka bama Sakina Dama har ga Allah ina Tsausayinta domin Sharrin Marliya ne ya koma kanta Barin Ciki ga mace abun jin Zafi ne..Sannan abubuwa Dadama ba Laifinta bane..Kayi tunani kagani ko zaka iya yafe mata..Ban takura maka ba..Shawara ce Tsakanina Dakai..!
Danmallam kansa na kasa yace"Nagode Mallam Insha Allahu zan karbi mganarka..!
Daganan ya sakamai albarka sukayi sallama ya fito,Shashen Hajiya ya Shiga suka gaisa da yakaka da Hajiya nan yaga ma ya"yan Goggo Yagana sun zo wato yan"uwan Anty Hadiza sun kawo mata kayanta dake chsn da wasu Dake Dake daga mahaifiyarta Dazu da rana suka iso shiyasa bai Dade ba suna gaisawa yayi musu sallama ya fito a haraban gidan suka Hadu da Aba suka gaisa sun dan Taba Hira sama sama kafin ya shige motarsa ya bar gidan shi kuma Aba Falon mallam ya shiga.
Koda ya koma Amina ta cika kiris take jira tayi kuka,Allah ya tsaresa da Jidalinta shiyasa ya kasa gayamata Zai koma wajen Sarood har washegari Suka je asibiti da Duka Fayel dinta na Aaibitin datayi awo a Abuja wajen Dr.Ghali suka je inda ya Taba kaita Farko al"amarin.
Dr.Ghali nata mamakin wannan al"amarin Sha"awa suka basa har ya kasa Dauke ido Daga kansu ganin yadda Amina ke shagwaba Umar na Biye mata ya Dubata yace ba matsala Sai dai Jininta yayi Low sosai taci kayan ganye,Daga asibitin Da suka Dawo suka sake fita da kafa suka Zagayen anguwan saboda kafaduwan Amina su Saki suna Dawowa ba Dadewa sai ga Idi ya kawo Yakaka Murnan sai ya Dauke Hankalin Amina har ya sake wanka ya fita bata Damu ba.
Koda yaje abakin Hajiya Yaji abunda ya Faru da Maamanmu da Labarin yan"uwanta yau sun zo sun Dauketa tana Fadamai irin yadda Duniya ta juyama Mamanmu abaya har ga Allah bai wani Tsausaya mata ba,Aransa ma yasan Kadan ta fara gani
Da yammah ya Dauki Sarood suka koma gidansu batare daya Fadama Amina ba saboda bai son me zai ce mata Amina yadda take da kishi ya Tabbata in ya Biye mata sai ya shiga Wuta.
Ganin yanayin Sarood din itama tana Fama da Laulayin jiki yasa ya Zage ya taimaka mata suka gyara Gidan suka share ko"ina Girki kuma yace kada tayi ta kwanta ta Huta zai taho mata Dashi Daganan Gidan mallam ya koma sukayi sallar Isha"i sannan yayi musu sallama ya nufi gidan Amina ya Iskesu afalo ta baje suna ta Faman Hira da yakaka Sai Hankalinsa ya kwanta..
Yana shiga Daki ta Biyosa Lokacin yana ta Tunanin abunda zai ce mata tana shigowa tace mai bari tayi Fitsari ya Bita da kallo Tana tafiya Dakyar ta Shige Tiolet sai ya fita Falo ya samu Yakaka ya roketa tayi ma Amina bayani ya kasa Yakaka tace kada ya Damu yayi tafiyarsa zata fadamata Tsorin Jidalin Amina yake yi shiyasa Daganan bai koma Falon ba ya Fice Tana Fitowa taji karan Rufe get dinsa ta kalli Yakaka tana Fadin"Hubby ya Fita ne..?
Yakaka tace"Ya koma gidan Yar"uwanki chan zai kwana..!
Tafada tana Hade rai tasan Halin Amina gwara a mata Zafi Zafi
Amina taji dan Cikinta ya motsa da Sauri tace"bangane ba..?
Ina kenan..?
Yakaka tace"Mallam yace ya Dauki matarsa su koma gidansu wannan balarabiyar kinga ai tunda suka zo tana gidan mallam ke kuna ba kuma Tare da shi anan ba..?
Sai Amina ta koma ta Zauna akasan Cafet ta Rushe da kuka tana Fadin"Shine ko yagayamin..Ya kama Hanya ya tafi wajen wannan banzar matar tasa..?
Yakaka ta saki Baki kafin tace"Yau naga Tsiya..ke da zaki godema Allah miji na sonki Yan"uwansa kowa naji Dake..Ita wacce kike kishi akanta uban wa ma ya Damu da ita Labarci nan dai kinsan ba kowa ke jinsa ba..Bata da wani Sakewa kamar mujiya ki godema Allah bawan Allah nan na tafe rawan jiki akan ki ke bakya gani kina wani shanshanci ke kika sani..!
Yakaka ta karishe da juya mata baya tana cire naman Daya makale mata a Hakori da tsinke domin Amina ta bata na zamani tace ta rabata tayi da wanda ta sani Amina mganar Yakaka bai sa ta Daina kuka ba Domin wani Kishi ne ya Rufe mata ido har wani Duhu Duhu take gani sai da ta gaji da kanta ta Daina gani kuma Yakakar tayi mata banza ta cigaba da Harkokinta yasa ta tashi da Turtsetesn Cikinta ta koma Dakinta ta kwanta tana Sauke Numfashi Yakaka ta Bita da kallo kamar tayi Dariya

Har Washegari a kumbure tatashi Yakaka kala batace mata ba bayan gaisuwa Tana da garin kuni da Hajiya ta saka aka Dakata mata Yakaka ta Dama shi Sannan tayi musu Fanke bata jira Amina ba Data gama ta Dibar mata tana Tura Baki tace ta koshi Yakaka ta Kalleta kafin tatabe baki Tana Fadin"Ke kika sani..!
Daga haka ta koma Falo ta sha kununta ta ci fankenta ta koma ta kwanta chan wajen sha daya na Safe Danmallam ya shigo gidan anan Falo yaga Yakaka ya Durkusa ya gaisheta ta amsa Cikin Fara"a.
Kansa na kasa yace"Yakaka ina Mutuniyar taki na ganki ke kadai..?
Yakaka ta tabe baki tana Fadin"Waya sanin mata..?tun jiya da ka tafi na Fada mata ka tafi wajen balarabiyar nan take kuka sai da taga na mata banza ta Rarrafa ta koma Daki yau fa Da Fushin tatashi ko abun karin da nayi bata ci ba..Dakyar fa ta iya gaisheni Danmallam..!
Umar yayi mirmishi Daman yasan za"a rina Kansa ya sosa kafin yace"Bari na lallasota zamu zo Biko Yakaka..!
Yafada yana mikewa Yakaka ta mele Baki kafin tace"ai kada kuzo kana tashi Tafiya kafata kafarka sai ta Zauna ita kadai.!
Shidai yana yar Dariya ya shiga Bedroom din Amina ya isketa zaune da waya a kunnenta suna mgana da Hanne sai da ya zauna kusa da ita ya Fahimci da Hanne take mgana

Saboda ganinsa yasa taja Hiran taki karewa har tana cewa ta bata Aminu in yana kusa su gaisa yana kusa kuwa Hanne ta basa karo na Farko suka gaisa da Amina Danmallan yaji bazai iya ba suna cikin gaisawar ya karbe wayar ya Kasheta ta Kuramai ido Cikin Kishi kafin tace"Miye kuma na kashe min waya..?
Hararanta yayi kafin yace"Bansani ba..Baki ganni na shigo bane kike waya da wani kato..?
Amina zan saba miki fa..!
Shima ya mata jan ido daman jira take kawai sai ta saka kuka ta mike ta Fara jijjiga Jikinta tana Fadin"Dama kamin Fada mana..Kaje ka kwana da ita kazo kana min ihu akai..Tunda kamin Ciki ban da wani amfani awajenka..!
Kuka har da majina Baki ya Saki yana kallonta Jidalin Amina yanzu shi kawai ke Diban fire akansa ganin abun nata nayi gaba gaba yasa ya Mike ya rumgumota yana Fadin"Wayace miki baki da amfani a wajena..?
Amina har da wage baki wajen kuka ta kasa mgana kawai sai yayi mganinta ya Hade bakinsu waje Daya Dole ta natsu acikin kirjinsa Sai da ya Dauki Lokaci duk ya gama Shanye Hawayenta da majina sannan ya Dago Fuskarta yana Fadin"Ke ce abu mafi Daraja da kima awajena..Ina sonki AMINA..INA SONKI AMINENE..!
Ido ta Bude tana kallonsa ranta yayi Fari,Idonta ta ware mai kafin tace"La.Har da Aminene..?
Hancinta Yaja yana fadin"Sosai ma..Duk da Jidalin Datake min hakanan nake son kayana..!
Rumgumesa tayi Da Sauri tana Dariya tace"Ni ba ruwana..!
Yana jinta bai ce komai ba ya shiga wata Jahar kuma Duk da Nauyin Cikinta batamai gaddama ba Har sai da suka samu natsuwa sannan ta fara mai kukan bayanta ya kage shi kuma yana lallashinta haka ta kwanta yana ta Faman Matsa mata baayan da Kafafun nata bawan Allah.
Ita dai Yakaka tunda taji su shuru ta Shige Dakin Data sauka ta kwanta afili Ta Furta"Gulmammiya.. !
Ranar ma gidan Sarood ya kwana ko Sallama bai yi ma Amina ba Daga bari yazo taji shuru,Da Safe sai chan rana ya Dawo gidanta Harara kam da Turen Turen baki yashashi yana shiga da ita Daki kaji shuru shiyasa in tana ma Yakaka Jidalinta sai ta kalleta tace"Nama Lura ni kika raina..Meyasa shi baki mai..?
Yana zuwa kuka shige Daki sai naji shuru..!
Amina sai taji kumya ta rufe ido tana Fadin"Ai ina mai acikin Dakin..!
Yakaka ta mata Dakuwa tana Fadin"Raina min wayau..!
Amina ta fara Dariya Yakaka na Hararanta kafin tace"Allah ya shiryaki Amina..!
Ta amsa mata da Ameen haka suka cigaba da zamansu Lafiya Ranar dayake gidan Sarood ba sa sallaman arziki da Amina in kuma ya Dawo ya Dinga Fama da lallashi kenan ga Sarood din Cikim na bata wahala sai da ya kaita aaibiti komai taci sai amai Ga Jidalin Amina wlh baya kaunar ma ya Bata mata rai Tsoron kukanta yake ji.
Amina na cikin Farinciki da kwanciyar Hankali ta kara Kiba ta zama katuwa Danmallam ya siya mata Sabuwar waya samsumg Tana waya da duka yan"uwanta har su ya Zulfa bata yada su ba Tana kiransu susha Hira tun basa Sakin jiki har suka zo suka saki Tunda duka ya"yan yaya basu nuna musu kyama kan abunda Uwarsu ta aikata ba Jadwa ne ta Dauki Zafi itama Daga baya ta Saki arana kuwa ita dasu Hanne sa yi waya fin sau hudu Har sai da Danmallam ya musu Fada yace basu da Hankali ne nan fa ba gida bane..?
Su matan aure ne yanzu wani Shirmen dole sai sun barshi Baji sukayi ba aboye suna wayarsu barin ma in baya gidanta sai gashi yau Amina ke bama su Hanne wasu Shawarwarin sannan Fanin girki abunda ta iya ma basu iya ba Shiyasa har yau har gobe bazata manta da Hajiya da ya Aisha ba Duk tayi salla sai ta rokar musu Fatan gamawa da Duniya Lafiya.
Haihuwa dai shuru har EDD dinta ya wuce sai dai bata Damu ba Tunda Daman Before ne ko after har asibitin sun koma Dr.Ghali ya tabbatar musu da komai lafiya sai hankalinsu ya kwanta.
Bangaran Aba kuma komai Lafiya lau Anty Hadiza na kula dashi ta karbo Jawaad wajen Hajiya ya Dawo wajenta Abun yayi ma Aba Dadi tazo Ranar ta yinin ma Amina da Daddare Aba yazo ya Dauketa Dakyar ya shiga Gidan Amina yasa albarka Amina baki har Kunne saboda Murna Aba yazo Ruwa kadai ya sha ya saka albarka suka tafi Yakaka itama ta Bisu da saka albarka.
Bangaran mallam kuwa acikin Satin nan ya samu Lokaci Yaje Tsafe Idi ya Tukasa yayi ma yan"uwan Uwani Gaisuwan rasuwar Batula,Akwai mahaifiyarsu agidan da abokan zamanta Biyu bayan yayi musu gaisuwa nan ake fadamai Uwani na kwance ba Lafiya an je asibiti an yi Duk Gwaje gwaje an kasa gano abunda ke Damunta sai tace kirjinta da zuciyarta ke ciwo an ta neman Lambarsa afadamai ba'a samu ba..!
Sanda ya shiga inda Uwani take sai da ya kusa mata kuka tana kwance ta Zabge ta rame ta lalace Ba wannan kibar yau gata kwance ba kwalliya ba kayan kawa tana ganinsa ta fara kuka tana Fadin ya yafe mata.
Mallam ya jinjina kai yana kallonta kafin yace"Na yafe miki uwani..Saura ke da wanda ya Hallicceki..Sannan zan yi mgana da su Nazeem zasu zo su Dubaki..!
Daganan ya mike bayan ya ijiye mata Takardan daya rubuta mata Sakinta ya Fice ko bai Fadaa mata ba tasan ko na menene yasa ta Dinga kuka Tari ya Sarketa iyayanta yayi ma sallama da kudi 50k ya basu domin suna cikin yanayi don ma yaran maza na taimakawa.
Sai bayan fitarsa mahaifiyar uwani ta shiga Dakin ita ta karanta Sakin da mallam yayi ma Uwani Sai ta saka kuka tana fadin daman tasan za"a rina Domin zaman uwani bana Lafiya bane ba ya"yanta ba Dangin mijinta tasan wani abu ta aikata aranar Duka yan"uwan Uwani suka taru tana kuka tana Nadama ta basu labarin duk abunda ta aikata,Sun ji tsoron Duniya sannan sun yi Tir da ita har ta mahaifiyarta sai da tayi tir da ita tana kuka tana Fadin Batula ta rasu a Hanyar Shirka wannan wani irin tabewa ne sun fito daga babban gida ammh sun watsar da Tarbiyansu Tundaga ranar harta mahaifiyarta ta Daina bi ta kanta tana yashe Cikin Daki sai wanda yaga Allah yaga Annabi ne ma yake lekota yau ina ya"yan nata Datake yin komai Saboda su..?
Sun gujeta saboda mugun Halinta sannan ba mallam din ya Saketa ballatana ta hango cikar Burinta gata kwance ba Lafiya tana girban abunda ta Shuka kaiconta tayi kuka kamar ranta zai fita bamai lallashinta

Aranar da mallam ya Dawo Daga Tsafe ya Kira Anty Amarya Har Shashensa ya bata takardan Sakinta Ko da bata karanta tasan Dalili ta Fadi gabansa tana kukan ya yafe mata ya kalleta yace"Na yafe miki marliya..Yanzu Tsakaninki da Ubangijij ne..!
Daga haka ya shige ya barta nan tana kuka kukan nadama da rashin Madafa.
Bata zauna ba Kayanta ta Hada ta Rufe Shashen ta bama su Lami key din tace su kaima Hajiya ta Fice Daga Gidan tana kuka yau ina Burin nata..? Ta biye ma rudin zuciya ta karre a Tutar babu Tana kuka ta isa tasha ta samu Motar Dutse lokacin data isa Gidansu sai da tayi nadama.
Yan"uwanta basu karbeta ba haka suka gana mata tir da kaico har da uwar data Haifeta sai da ta juya mata baya ba yadda zasu yi su koreta ne ammh Kashi ya fita Daraja abinci sai dai yan aiki su bata tayi kuka tayi nadama Lokacin da bai da amfani ta Kira wayoyin su Sadiya ba wacce take Sauraranta.
Sakina kuma tana Gidan A"i ita ta Dauketa tana kula da ita bayan an sallamosu Daga asibiti Dayake nan kusa take aure Ranar da Anty Amarya Taje sai da ta raina kanta Har Marin ta sai da kanwarta A"i tayi abaya yadda suke jin mganarta Saboda auran Babban mutum kamar mallam..agaban idonta Sakina tana kuka tace itace ta cuceta ta rabata da auranta da kuma Halin Datake Ciki gashi sanadiyar barin cikin data dinga yi mahaifarta ta samu rauni Har ta fara Dagargajewa yanzu haka an cire mata mahaifa ita da Haihuwa har Abada ta Tsaneta bata son ganinta
Anty Amarya na kuka tana rokonsu gafara suka Tarkatota waje bayan A"i ta saka megadi ya sakar mata karnuka su suka kadata har waje nan bakin get din gidan ta durkushe tana wani irin kuka mai Cin rai kukan Nadama da nasani.

*******

EDD din Amina har ya tsallake da wajen Sati uku Bata haihu ba Sannan Cikinta ya fita wata na Tara har ya shiga goma sai kuma hankula suka fara tashi ita kanta Aminar ta kosa ta Haihu Cikin ya mata girma ya koma yana Rinjayanta.
Danmallam duk ya Damu ya koma yana matukar jin Tsausayinta Hajiya ta bada Shawaran su koma asibiti haka kuwa akayi da ita suka koma wajen Dr.ghali da Amina shi kanshi yanayin Daya ganta yasa yace zai sanya mata ruwan naguda ya gani.
Allah Sarki Duk mai imani sai ya Tsausayama Amina
Showing 129001 words to 132000 words out of 146831 words