ya gaisheta cikin Ladabi ta amsa tana kallonsa cikin mamakin ganinsa da Safe haka sai dai bata Tsawaita mamakinta ba Sanin Aliyun yana zuwa gaida Hajiya da mallam Lokaci bayan Lokaci koda Danmallam din baya kasar
Shashen mallam ya koma yamai sallama zai koma domin nan ya fara shiga suka gaisa bai dai zauna bane ganinsa suna mgana da Aba yace bari ya shiga ciki ya gaida Hajiya Mallam bai kawo ma kansa shima wani abu ya kawo Aliyu ba sanin Yadda yake Darajasu Dalilin kawai suna iyayen Abokinsa Umar.
Sallama sukayi yana ta sakamai albarka da Fatan Allah ya kaisa gida Lafiya kiran Danmallam bai shigomai ba sai da ya bar Gumel ya dau hanyar Dutse Gefen titi ya samu yayi fakin sannan ya Daga kiran nasa Daga chan bangaran Danmallan yayi mai sallama kamar yadda kowa yasan shi da zarar ya Dauki waya da sallama itace Farko a bakinsa
Aliyu bai wani amsa sallamarsa ba yace"Shehi wai miye sirrin ne..?
Umar yace"Sirrin na mene..?
Aliyu yace"To gani nayi ka bi ka Rude kan karamar yarinya sa"ar yarka ta Fari kuma kwaila..kuma kazama ka tadani Tundaga Dutse zuwa gumel haka Hajiya ma ta Dinga mamakin wannan aikin naka..!
Umar ya Dafe kansa dagachan bangaran kafin yace"meyasa ka bari kuka Hadu da Hajiya..?
Aliyu yace"Dole kuwa mu hadu don Daga Falon mallam shashenta naje neman Amina ta tabbatar min da batanan suna makarantar Hadda..!
Umar yace"Kash..Da tace haka sai kayi Tahowarka ba sai ka fadamata Dalilin zuwanka ba..!
Aliyu yayi wata Dariya kafin yace"Ai aikin gama ya riga ya gamu Shehi tuni na Rattafamata komai tace in munyi mgana Dakai na sanar maka ka kirata zaku yi mgana .!
Umar yayi shuru kafin yace"Kai dai baka da biyan Bukata duk ka bata komai ni fa kunyarta nake ji shiyasa ban kirata ba ita da mallam..!
Aliyu yace"Oho zakace haka mana Tunda na gama Biya ma Bukata akwai ai watarana ba agama ba..!
Umar yace"Naji bakomai dai nagode zan kirata yanzu..!
Aliyu yace"Ni fa baka Fadamin sirrin ba..!
Umar yace"Wani sirrin kenan..?
Aliyu na Dariya yace"Sirrin abunda ya susuta ka kan Aminatu mana..!
Umar ya saki karamin Tsaki kafin yace"bansani ba..!
Aliyu ya saka Dariya kafin yace"To to..Nagano Sirrin ma..Shiyasa jiya daka kirani bakace min wannan kazamar yarinyar ba kai Tsaye ka kira sunanta Tabbas yanzu ta tashi Daga kazama kwaila ta koma Sweet Amina..Ko Honey ce..?
Umar ya tsaki again kafin yace"Kai fa Dan iska ne..!
Daga haka ya Datse kiran Aliyu yabi wayarsa da kallo yana Dariya sosai in ya Tuna sanda aka aurama Umar Amina yana ta fada yar cikinsa ne ina zai kaita sai gashi kaji sa shuru ya shiga komar yara ya kasa sukuni.
Duk da yayi matukar mamakin yadda Komai ya faru Tsakanin Amina da Shehi sai dai bai Tsananta ba Sanin Tsakanin miji da mata sai Allah ammh Shehi ya bani a wajensa ya Dinga Tsokanarsa kenan.
Yana Mirmishin ya Tada motarsa ya bi hanya yana kara Dariyan Abokin nasa yana kuma Fatan yasa Amina ta mai mugun kamun da sai ya raina kansa.!
Bayan Tafiyar Aliyu Hajiya tayi ta Tunanin me yasa Danmallan ke son mgana da Amina haka da har ya kasa Hakuri..? Bata samu amsar ta ba sai tayi Tunanin kila yana so yaji Lafiyanta ne sannan ya tambayeta ko tana Bukatar wani abu daganan ta watsar da Tunanin ta koma Bedroom dinta tana gyarawa ba Dadewa ta samu kira Daga Danmallam bayan ta Dauka sumgaisa kamar yadda suka Saba sai kuma yayi Shuru yana jin kunyar yayi mata mgana ta san Halinsa Tunda ita ta Haifesa.
Yasa ta gyara Zama tana fadin"Dazu Aliyu abokin ka yazo..akan kai ka aikosa ya kawo ma Amina waya zaku yi mgana ko.?
Dakyar ya iya amsa ma Hajiya gani yake kamar zata Fahimci abunda ya Faru Tsakaninsa da Aminar.
Cikin Dattakonta ta cigaba da fadin"To nace yayi tafiyarsa Sabgoginsa ka taso mutum Tunda ga nisan Duniya Danmallam..! Ai sai ka Kirani muyi mgana ko ba Haka ba.?
Kai tsaye yace mata"Kiyi hakuri Hajiya..
Cikin Ladabinsa bata Damu ba tace"Ni ba laifi kamin ba..gani nayi ka basa wahala..Daman ina ta so na kira ka nayi maka bayanin Dalilin Dayasa ban bana Amina wayar nan ba duk da ni nace ka siya mata mgana mukayi da mallam ya nuna min Rike waya ga Amina yayi sauri sannan Duba da har yanzu akwai kuruciya a tare da ita..hakan zai Dauke Hankalinta har ya Taba karatunta da muke Fata ta Samu,ya nuna min na bari sai zuwa gaba in kazo ka tafi da itan sai ka siya mata wayar Lokacin tana gabanka zaka kula da Motsinta yanzu kuma ya nuna min gaskiya a"a shiyasa kaji Shuru ban bata wayar ba tana nan na ijiyeta..!
Cikin gamsuwa da mganar ta yace"Hakane Hajiya..!
Hajiya tace"To kaji yadda mukayi da mallam da Dalilin dayasa kaji shuru..Sannan yace in kana son jin Lafiyarta ne ka kirani ko mallam din sai in ta na nan sai abata ku gaisa..!
Danmallam yace"Shikenan Hajiya Allah ya kara girma..!
Hajiya ta amsa da Ameen kafin tace"suna Hadda ammah ina ga bazasu Dade ba in sun Dawo zan kiraka sai na Hadaku..!
Cikin Ladabinsa ya shiga Fadin"Allah yasa agama Lafiya Hajiya Allah ya kara Nisan kwana..!
Ta amsa da Ameen suka rabu bayan ta Tambayi Iyalansa da ayyukansa.
To sun ma gama wayar ba Dadewa wajen azahar sai ga su Aminan sun Dawo suna ta Murna an basu Hutun Sati ukun Dadinsu Daya gobe zasu fara Exam din second Semister a makarantar boko satin daya gabata Gabadaya Revision sukayi.
Amina ke fadin Dama islamiya ma ta bata da Hutu ai da sun ji Dadi.
Ba"a basu Sakamakon su ba sai Sun dawo Hutu sannan.
Anan Shashen Hajiya sukayi sallah Sukaci abinci Hajiya na ciki bata san Amina da Hamida sun koma gida ba Tana zuci zucin ta Kirata sai ta Kira Danmallam din ta Hadasu ko da ta Fito sai Hanne kawai ta gani a Falo ita ke Fada mata Su Amina sun tafi gida kai Tsaye tace Hanne taje ta kira mata Aminar.
Hanne ta mike ta saka Hijabi ta tafi tana zuwa ta iske su acikin Dakinsu har Amina ta kwanta bata ga mamanmu ba tana cikin Dakinta ta kwanta in ji Hamida jawaad ke ta wasa da Karamar kwallo a Tsakar gidan.
Da Farko Amina Dataji Hanne na Tashinta kin tashi tayi sai da tace mata Hajiya ke kiranta sannan ta Mike tana fadin"Kice Wlh Hanne..!
Hanne ta mike tana fadin"Au nace ma Wlh..!?
To ki zauna kin ga tafiyata..!
Amina ta mike tana fadin"Tsayani Hanne mu je..Fatana Allah yasa ba gida zata saka Idi ya kaini ba..!
Hamida da Hanne suka kalli juna kafin Hanne tace"To in chan din ne fa..? Ai kince gidan mijinki ne..!
Amina na saka Hijabi batayi mgana ba sai da ta gama sakawa sannan ta Dago Tana fadin"Ni yaushe na Fada..?
Allah ya isa na, wuta bal bal in ban Fada ba..!
Hamida na Dariya tace"Daman chan Allah ai ya ishi kowa Amina..!
Harara ta balla musu kafin ta bangaje Hamida ta wuce fuu hamida da Hanne suka.bita da kallo Hanne tace"Kamar an kara mata bala"i wlh bayan auran nan..!
Hamida tace"Kowa ma haka yake fadi..ya danmallam zai yi mganinta bari su koma Madina ki gani nan ta raina achan Ubanwa zata mawa .!
Hanne na Dariya tace aifa Daganan ta bi bayan Amina zuwa gidansu.
Koda Taje Amina da Hajiya na kuryan Daki Hanne na shiga Hajiya Data Kira Danmallam bai Dauka ba ta kalli Hanne ta nuna mata kofa Tana fadin"Jirata afalo..!
Hanne ta Tura baki kafin ta fita Amina ta Fakaici idon Hajiya tayi ma Hanne gwalo ita azatonta wani abun Dadi Hajiya zata bata sai da wayar Hajiya ta shiga kidan larabawa taga Hajiyqn ta Dauka ta mika mata tana Fadin"Karbi Mijinki ke son mgana Dake..!
Ta fada Lokaci Daya tana Ficewa Daga Dakin Harda Rufo mata kofar Bedroom din Amina gabanta ya Fadi tabi wayar da kallo ga sunan Danmallan nan baro baro na kan Layi sai jikinta ya fara rawa aranta tace na shiga uku ni Amina Allah yasa ba wani Abu akace mai nayi ba..
Jikinta a sanyaye ta kara wayar kunne Daidai Lokacin da Sanyayyiyar Muryansa ta Doketa Cikin Sallama da Hausansa daya Cakude da Larabci.
Sai da ya kara maimaita Sallamar sannan ta amsa Bakin da jikinta na rawa Tun kafin ya gama rufe baki Tace"Ina yi..yini..!
Ajiyar zuciyar daya sauke har sai da ta jisa a kunnenta Dayaji muryanta sai yaji Salama da natsuwa Cikin Taushinsa yace"AMINA...!
sai taji kamar yafi kowa iya Fadar sunan nata jin yadda ya kirata ita bazata iya tuna ko yama taba kiran sunanta ba Haka ba, jin tayi shuru yasa ya kara cewa"Amina kina lafiya..?
Cikin Sanyin Jiki tace"Na"am..eh lafiya kalau..!"
"Ya jikin ki..? Ina fatan kin warke babu kuma inda ke miki ciwo..?
Ya fada kai Tsaye domin baya Fatan ace wani abu kuma ya tashi bayan Tafiyarsa kunya ta kama Amina ta Dukar da kanta kamar yana ganinta ta kasa mgana sai gabansa ya Fadi da Sauri yace"Ko da wata matsala ne..?
Da Sauri tace"A"a na warke..!
Afili ta Furta"Alhamdulillah..!
Kafin yace"Naji Dadin haka ina Fata kamar yadda kikamin alkawarin baki gayama kowa ba ko..?
Sai da ta gyadamai kai kafin tace"Eh ban fadama kowa ba..!
Cikin jin Dadi yace"Dakyau naji Dadin Haka..Ya karatu fata kina maida Hankali wajen karatu..?.
Da Sauri tace"Eh yau ma mun yi Hutun Hadda..Gobe ma zamu Fara Jarabawa a boko..!
Kai ya gyada kafin yace"Allah ya bada sa"a..ki rika maida hankali kinji ko..?
Ta gyada kai ya cigaba da Fadin"Sannan ban da wasa ban da Fada ban da gujeguje ke yanzu ba yarinya bace kin tashi Daga su Hamida ke matar aure ce ba Daya kike Dasu ba kina jina ko..?
Nan ma kai ta gyada mai yace"Baki da baki ne..!
Ba nace ki daina min mgana Da kai ba .!
Da Sauri tace"Naji insha Allahu..!
Ajiyar rai ya Sauke kafin yace"Kina Bukatar wani abu..?
Tace bakomai kai Tsaye yace"Ki rika gaida Sakina in kun hadu tana gaba Dake kinji ko..?
Amina ta Tura baki kafin tace"Ni fa in na ganta batamin mgana sai tayi ta Hararana har zagina ma tanayi..!
Cikin mamaki yace"Ita Sakinar..?
Amina tace"Eh shiyasa nafi son zaman nan fiye da chan sannan achan ina jin Tsoro da Daddare bana iya barci don Allah ka Fadama Hajiya ta rika barina ina kwana anan in ka Dawo sai na koma achan..!
Kawai sai ta sakamai kuka sai yaji Hankalinsa ya tashi meke Damun yarinyar nan ne Cikin Tausasa Murya yace"Naji ki daina kuka zan mata mgana..Daman baki daina Firgita cikin barci ba..?
Tace mai eh sai da yayi shuru kafin yace"Ki samu mallam yau da Daddare in ya natsu ki Fadamai abunda kike jin in zaki Firgita kin ji ko..?
Tace"Na Fadamai..?
Yace"Eh ki Fadamai sannan mganar Zagin ki da Sakina ke yi kada ki Fadama kowa har su Hajiya zan mata Fada insha Allahu zata Daina ke dai in kin koma gidan kun Hadu ki rika gaisheta saboda ko bakomai Tana gaba Dake kuma a islamiya an koya muku yin biyayya ga na gaba da ku ko ba Haka ba..?
Tace eh ya cigaba da fadin"To ki rika bata girmanta kin ji ko..?.
Ta amsa da toh bai Tsawaita mganar ba yace"Zan ce ma Jafar a Cefanan wannan watan ya siya miki Goldenmorn da Cornfkles Saboda Saukaka miki Wahala sai ki Rika sha in zaki tafi makaranta..!
Tace "To nagode..!
Ya amsa ta da Fadin"Kada ki damu komai kike Bukata kada ki tambayi Hajiya ko mallan ki yi ma Jafar mgana ko kuma ki Dauki wayar Hajiya ki kirani kinji ko..!
Nan ma tace mai da toh tagode Dagnan yace ta maida Hankali a karatunta ta amsa mai Daganan ya mata sallama ya kashe wayar.
Tabi Wayar da kallo Tana Tura baki wai ta rika gaida Sakina Tab wannan mara mutumcin ne zata gaisheta..
Shi kuwa sai da sukayi mgana yaji Hankalinsa ya kwanta har ya natsu ya Cigaba da Duba Takardun Dalibansa da sukayi gwaji.
Da suka gama wayar kunya ta Hana Anina fitowa sai da Hajiya ta Shigo Daukan abu ta ganta zaune tayi shuru tace"A a Mamah tunda kun gama wayar ki fito falo hanne na jiranki mana sai ki zauna ke kadai..!
Jin haka yasa ta mike ta mikama Hajiya wayar, ta karba ta Fice da Sauri Hajiya ta bita da kallo tana Mirmishi a Cikin aranta tana Fatan addu"an su Allah ne ya karba na amitar da Ruhin Amina da Danmallam waje daya.
Amina na fita Hanne ta taso tana Tambayanta da wa tayi waya Amina ta balla mata Harara kafin tace"Bansani ba..!
Hanne na Dariya tace"Nasani Ya Danmallam ne..ko..?
Amina ta mata wani kallo kafin tace"In ma shine sai na Fada miki..?
Sirrin miji da mata..!
Hanne ta saki Dariya kafin ta Ja Hijabinta tana fadin"Bari naje na gayama Hamida..Sabon Update..!
Amina tayi Tsaki kafin tace"Ai ke Hanne mijinki ya shiga uku..duk wanda ya aureki ya auran ma kansa sai kin hada Fada a Family din mijinki Saboda munafuncinki..!
Hanne bata bi ta kanta ba ta fice Amina tayi zamanta Falon Hajiya chan sai gasun dawo Tare Hamida sai kara maimaita abun da Hanne ta gayamata take yi Amina ta musu wani banzan kallo kafin tace"kusan dai ni yanzu ba Sa"arku bace ko..?
Igiya uku ne akaina..Taimaka muku ma nake yi ina yawo da yara. !
Hanne da Hamida suka saki baki ganin haka yasa ta Musu gwalo tatashi da gudu ta Fada Dakin su Hanne Tana Dariya suka mara mata baya suna fadin yau sai ta gayamusu su waye yara..?
Ranar dai anan suka wuni Shashen Hajiya suna abunda suka saba sai bayan sun dawo islamiya ne Hajiya ta saka aka maida Amina gida tana kunkuni Tana komai bata samu yima Baba mallam bayani ba sai washegari da suka dawo makaranta ta Fadamai ya Dade yana mamaki ya tambayeta yaushe ta fara tsorata tace tun tana karama ta dade mallam ya Dinga Fadin Sakacin mamanmu da Aba da Amina na Fama da wannan Laluran ammh bsu sani ba Hajiya ce ma ta Lallasheshi ya bar mganar da yace har Aba din sai ya kira da mamanmu ya musu Fada.
Shi ya Rubuta mata addu"o'i ya bata yace ta Rika karantawa Duk Dare in zata kwanta Tare da Sauran addu"an barcin da Annabi ya koyar damu.
Amina yadda Taga Mallam ya Dau abun ne yasa itama bata Dauka da wasa ba sannan Danmallam ma sun sake mgana da wayar Hajiya Data Fadamai yadda sukayi da mallam ya mata Fada kan ta Dage kada wasa ya Dauke mata Hankali ta rika kwanciya bata karanta su ba.
Shiyasa ta Dake bata kwanciya sai ta karanta sai gashi kuma Cikin ikon Allah tunda ta Dage sai ta samu Saukin Firgita din sai abunda ba"a rasa ba Danmallam har da mallam sun yi mgana Mallam nata fada yana Fadin da Haka Umaima ta Fara gashi nan suna so su taba mata kwakwalwa Dannallam yana so ya Fadama Mallam bayan haka ma yana Zargin akwai wani abu Tattare da Amina sai dai kuma bai da Hujjan hakan ammh yana so sai in ya kara Dawowa ya Zauna ya Fahimci matsalanta Domin Ranar da abun nan ya Faru tsakaninsu da Washegarin nan da Safe yaga tana wasu abubuwan da Dole tana da wani abu a Tattare da ita.
*******
Kwantashi ba wuya a wajen Allah su Amina har sun gama Jarabawarsu sun yi Hutu taso ta zauna anan tayi Hutunta Hajiya ta hanata sai ta Roki Baba mallan kan su Hanne su Bita ko Sati Daya su yi da Farko Hajiya ta Hana sai da Mallam ya saka baki Sannan ta amince suka Tattara suka koma chan da Niyar Sati Daya zasu yi Saboda islamiya basu yi Hutu ba.
Mamanmu bata Damu ba da akace Hamida zata je gidan Amina Domin alokacin tana Tsakar Cin Duniyarta ne Domin komai tace Aba ya bata baya Gaddama Kudi yake sakar mata bana wasa ba ta zama Tauraruwa a wajen sa Mamanmu ta samu Cikar Burinta Fiye ma da yadda take fata shiyasa ta manta da kowa da komai ko Anty Amarya ta kirata bata ma kaunar Hakan gani take tana neman Takura mata Shiyasa Amina ma bata gabanta Ta barta da Anty Amarya chan itace Zatayi mganinta ita yanzu Sa"idu ne agabanta yanzu shawaran komai sai yayi da ita sai abunda tace koda yace Jafar yace kaza ya kamata ko Hajiya sai tasan yadda tayi ta Kushe mganarsu ta sauya da nata Shiga kawai take tana fita Daga kayan alfarma kamar wata Yarinya sannan Malaminsu tana sakarmai kudi sosai Domin ta yaba da aikinsa
Anty Amarya kuma tana nan tana Jiran gawom Shanu domin ta yarda da aikin Malam ya sanar da ita Nasara tatace shiyasa bata Damu ba ta koma ta Zauna tana jiran tsammani kamar yadda ta basa duka yardanta Shiyasa ko Sakina ta kirata tana mata Korafi take mata Fadan bata da Hakuri aiki nawa suka basa kuma ya Biya musu Bukata..?
To wannan ma ta Zauna ta Jira komai zai zama Daidai da yardan Allah abunda basu sani ba Daga wannan Lokacin aikin ya kuskure musu sannan zasu cigaba da jiran majirata ne Jiran da zai kai su ga Ranar Nadamar su da Tonon asirin su..!
Ko Hutun da su hanne suka tafi Sakina kamar ta Haukace saboda Bala'i Amina Mahaukaciya take so ta maidata,gwara ma su Hanne suna dan jin mganarta banda Amina sai ta gama masifarta sun ba'ta mata Falo ko Kitchen Amina ta mata gwalo ko Ta mata Tsaki ta shige Daki abunta Sakina taci ji Yatsa kamar me..?
Kamar yadda yace a Cefanan watan nan an kawo su Goldemorn su Amina an samu banza ana ta Wadaka madara kuma da kayan Tea kafin Sati sun kare saboda yadda suke barnan sa basa da aiki sai dan sululu ko Wainar Fulawa gashi Sakina bata son kazanta su kuma in suna aiki a Kitchen din sai sun yi kaca kaca dashi in tayi mgana Hanne da Hanida kadai ke Sauraranta banda Amina da take maidata ma mahaukaciya.
Sakina abun ya isheta kullum sai ta Kira Danmallan ta kaimai karan Amina da kannensa shi har ma ya gaji Saboda bai isa ya kore su ba Amina Matarsa ce sannan su Hanne kannensa ne ko ba aure suna da Damar zama agidansa watarana da abun ya ishesa sai yace ta bama Amina wayar da an bata ya fara mata Fada sai ta saka kuka tace In ta gaishe da Sakina sai taki amsawa ta bita da Zagi sannan bata barin su suna shiga Kitchen sai tace suna mata kazanta Ayadda
Showing 36001 words to 39000 words out of 146831 words
Shashen mallam ya koma yamai sallama zai koma domin nan ya fara shiga suka gaisa bai dai zauna bane ganinsa suna mgana da Aba yace bari ya shiga ciki ya gaida Hajiya Mallam bai kawo ma kansa shima wani abu ya kawo Aliyu ba sanin Yadda yake Darajasu Dalilin kawai suna iyayen Abokinsa Umar.
Sallama sukayi yana ta sakamai albarka da Fatan Allah ya kaisa gida Lafiya kiran Danmallam bai shigomai ba sai da ya bar Gumel ya dau hanyar Dutse Gefen titi ya samu yayi fakin sannan ya Daga kiran nasa Daga chan bangaran Danmallan yayi mai sallama kamar yadda kowa yasan shi da zarar ya Dauki waya da sallama itace Farko a bakinsa
Aliyu bai wani amsa sallamarsa ba yace"Shehi wai miye sirrin ne..?
Umar yace"Sirrin na mene..?
Aliyu yace"To gani nayi ka bi ka Rude kan karamar yarinya sa"ar yarka ta Fari kuma kwaila..kuma kazama ka tadani Tundaga Dutse zuwa gumel haka Hajiya ma ta Dinga mamakin wannan aikin naka..!
Umar ya Dafe kansa dagachan bangaran kafin yace"meyasa ka bari kuka Hadu da Hajiya..?
Aliyu yace"Dole kuwa mu hadu don Daga Falon mallam shashenta naje neman Amina ta tabbatar min da batanan suna makarantar Hadda..!
Umar yace"Kash..Da tace haka sai kayi Tahowarka ba sai ka fadamata Dalilin zuwanka ba..!
Aliyu yayi wata Dariya kafin yace"Ai aikin gama ya riga ya gamu Shehi tuni na Rattafamata komai tace in munyi mgana Dakai na sanar maka ka kirata zaku yi mgana .!
Umar yayi shuru kafin yace"Kai dai baka da biyan Bukata duk ka bata komai ni fa kunyarta nake ji shiyasa ban kirata ba ita da mallam..!
Aliyu yace"Oho zakace haka mana Tunda na gama Biya ma Bukata akwai ai watarana ba agama ba..!
Umar yace"Naji bakomai dai nagode zan kirata yanzu..!
Aliyu yace"Ni fa baka Fadamin sirrin ba..!
Umar yace"Wani sirrin kenan..?
Aliyu na Dariya yace"Sirrin abunda ya susuta ka kan Aminatu mana..!
Umar ya saki karamin Tsaki kafin yace"bansani ba..!
Aliyu ya saka Dariya kafin yace"To to..Nagano Sirrin ma..Shiyasa jiya daka kirani bakace min wannan kazamar yarinyar ba kai Tsaye ka kira sunanta Tabbas yanzu ta tashi Daga kazama kwaila ta koma Sweet Amina..Ko Honey ce..?
Umar ya tsaki again kafin yace"Kai fa Dan iska ne..!
Daga haka ya Datse kiran Aliyu yabi wayarsa da kallo yana Dariya sosai in ya Tuna sanda aka aurama Umar Amina yana ta fada yar cikinsa ne ina zai kaita sai gashi kaji sa shuru ya shiga komar yara ya kasa sukuni.
Duk da yayi matukar mamakin yadda Komai ya faru Tsakanin Amina da Shehi sai dai bai Tsananta ba Sanin Tsakanin miji da mata sai Allah ammh Shehi ya bani a wajensa ya Dinga Tsokanarsa kenan.
Yana Mirmishin ya Tada motarsa ya bi hanya yana kara Dariyan Abokin nasa yana kuma Fatan yasa Amina ta mai mugun kamun da sai ya raina kansa.!
Bayan Tafiyar Aliyu Hajiya tayi ta Tunanin me yasa Danmallan ke son mgana da Amina haka da har ya kasa Hakuri..? Bata samu amsar ta ba sai tayi Tunanin kila yana so yaji Lafiyanta ne sannan ya tambayeta ko tana Bukatar wani abu daganan ta watsar da Tunanin ta koma Bedroom dinta tana gyarawa ba Dadewa ta samu kira Daga Danmallam bayan ta Dauka sumgaisa kamar yadda suka Saba sai kuma yayi Shuru yana jin kunyar yayi mata mgana ta san Halinsa Tunda ita ta Haifesa.
Yasa ta gyara Zama tana fadin"Dazu Aliyu abokin ka yazo..akan kai ka aikosa ya kawo ma Amina waya zaku yi mgana ko.?
Dakyar ya iya amsa ma Hajiya gani yake kamar zata Fahimci abunda ya Faru Tsakaninsa da Aminar.
Cikin Dattakonta ta cigaba da fadin"To nace yayi tafiyarsa Sabgoginsa ka taso mutum Tunda ga nisan Duniya Danmallam..! Ai sai ka Kirani muyi mgana ko ba Haka ba.?
Kai tsaye yace mata"Kiyi hakuri Hajiya..
Cikin Ladabinsa bata Damu ba tace"Ni ba laifi kamin ba..gani nayi ka basa wahala..Daman ina ta so na kira ka nayi maka bayanin Dalilin Dayasa ban bana Amina wayar nan ba duk da ni nace ka siya mata mgana mukayi da mallam ya nuna min Rike waya ga Amina yayi sauri sannan Duba da har yanzu akwai kuruciya a tare da ita..hakan zai Dauke Hankalinta har ya Taba karatunta da muke Fata ta Samu,ya nuna min na bari sai zuwa gaba in kazo ka tafi da itan sai ka siya mata wayar Lokacin tana gabanka zaka kula da Motsinta yanzu kuma ya nuna min gaskiya a"a shiyasa kaji Shuru ban bata wayar ba tana nan na ijiyeta..!
Cikin gamsuwa da mganar ta yace"Hakane Hajiya..!
Hajiya tace"To kaji yadda mukayi da mallam da Dalilin dayasa kaji shuru..Sannan yace in kana son jin Lafiyarta ne ka kirani ko mallam din sai in ta na nan sai abata ku gaisa..!
Danmallam yace"Shikenan Hajiya Allah ya kara girma..!
Hajiya ta amsa da Ameen kafin tace"suna Hadda ammah ina ga bazasu Dade ba in sun Dawo zan kiraka sai na Hadaku..!
Cikin Ladabinsa ya shiga Fadin"Allah yasa agama Lafiya Hajiya Allah ya kara Nisan kwana..!
Ta amsa da Ameen suka rabu bayan ta Tambayi Iyalansa da ayyukansa.
To sun ma gama wayar ba Dadewa wajen azahar sai ga su Aminan sun Dawo suna ta Murna an basu Hutun Sati ukun Dadinsu Daya gobe zasu fara Exam din second Semister a makarantar boko satin daya gabata Gabadaya Revision sukayi.
Amina ke fadin Dama islamiya ma ta bata da Hutu ai da sun ji Dadi.
Ba"a basu Sakamakon su ba sai Sun dawo Hutu sannan.
Anan Shashen Hajiya sukayi sallah Sukaci abinci Hajiya na ciki bata san Amina da Hamida sun koma gida ba Tana zuci zucin ta Kirata sai ta Kira Danmallam din ta Hadasu ko da ta Fito sai Hanne kawai ta gani a Falo ita ke Fada mata Su Amina sun tafi gida kai Tsaye tace Hanne taje ta kira mata Aminar.
Hanne ta mike ta saka Hijabi ta tafi tana zuwa ta iske su acikin Dakinsu har Amina ta kwanta bata ga mamanmu ba tana cikin Dakinta ta kwanta in ji Hamida jawaad ke ta wasa da Karamar kwallo a Tsakar gidan.
Da Farko Amina Dataji Hanne na Tashinta kin tashi tayi sai da tace mata Hajiya ke kiranta sannan ta Mike tana fadin"Kice Wlh Hanne..!
Hanne ta mike tana fadin"Au nace ma Wlh..!?
To ki zauna kin ga tafiyata..!
Amina ta mike tana fadin"Tsayani Hanne mu je..Fatana Allah yasa ba gida zata saka Idi ya kaini ba..!
Hamida da Hanne suka kalli juna kafin Hanne tace"To in chan din ne fa..? Ai kince gidan mijinki ne..!
Amina na saka Hijabi batayi mgana ba sai da ta gama sakawa sannan ta Dago Tana fadin"Ni yaushe na Fada..?
Allah ya isa na, wuta bal bal in ban Fada ba..!
Hamida na Dariya tace"Daman chan Allah ai ya ishi kowa Amina..!
Harara ta balla musu kafin ta bangaje Hamida ta wuce fuu hamida da Hanne suka.bita da kallo Hanne tace"Kamar an kara mata bala"i wlh bayan auran nan..!
Hamida tace"Kowa ma haka yake fadi..ya danmallam zai yi mganinta bari su koma Madina ki gani nan ta raina achan Ubanwa zata mawa .!
Hanne na Dariya tace aifa Daganan ta bi bayan Amina zuwa gidansu.
Koda Taje Amina da Hajiya na kuryan Daki Hanne na shiga Hajiya Data Kira Danmallam bai Dauka ba ta kalli Hanne ta nuna mata kofa Tana fadin"Jirata afalo..!
Hanne ta Tura baki kafin ta fita Amina ta Fakaici idon Hajiya tayi ma Hanne gwalo ita azatonta wani abun Dadi Hajiya zata bata sai da wayar Hajiya ta shiga kidan larabawa taga Hajiyqn ta Dauka ta mika mata tana Fadin"Karbi Mijinki ke son mgana Dake..!
Ta fada Lokaci Daya tana Ficewa Daga Dakin Harda Rufo mata kofar Bedroom din Amina gabanta ya Fadi tabi wayar da kallo ga sunan Danmallan nan baro baro na kan Layi sai jikinta ya fara rawa aranta tace na shiga uku ni Amina Allah yasa ba wani Abu akace mai nayi ba..
Jikinta a sanyaye ta kara wayar kunne Daidai Lokacin da Sanyayyiyar Muryansa ta Doketa Cikin Sallama da Hausansa daya Cakude da Larabci.
Sai da ya kara maimaita Sallamar sannan ta amsa Bakin da jikinta na rawa Tun kafin ya gama rufe baki Tace"Ina yi..yini..!
Ajiyar zuciyar daya sauke har sai da ta jisa a kunnenta Dayaji muryanta sai yaji Salama da natsuwa Cikin Taushinsa yace"AMINA...!
sai taji kamar yafi kowa iya Fadar sunan nata jin yadda ya kirata ita bazata iya tuna ko yama taba kiran sunanta ba Haka ba, jin tayi shuru yasa ya kara cewa"Amina kina lafiya..?
Cikin Sanyin Jiki tace"Na"am..eh lafiya kalau..!"
"Ya jikin ki..? Ina fatan kin warke babu kuma inda ke miki ciwo..?
Ya fada kai Tsaye domin baya Fatan ace wani abu kuma ya tashi bayan Tafiyarsa kunya ta kama Amina ta Dukar da kanta kamar yana ganinta ta kasa mgana sai gabansa ya Fadi da Sauri yace"Ko da wata matsala ne..?
Da Sauri tace"A"a na warke..!
Afili ta Furta"Alhamdulillah..!
Kafin yace"Naji Dadin haka ina Fata kamar yadda kikamin alkawarin baki gayama kowa ba ko..?
Sai da ta gyadamai kai kafin tace"Eh ban fadama kowa ba..!
Cikin jin Dadi yace"Dakyau naji Dadin Haka..Ya karatu fata kina maida Hankali wajen karatu..?.
Da Sauri tace"Eh yau ma mun yi Hutun Hadda..Gobe ma zamu Fara Jarabawa a boko..!
Kai ya gyada kafin yace"Allah ya bada sa"a..ki rika maida hankali kinji ko..?
Ta gyada kai ya cigaba da Fadin"Sannan ban da wasa ban da Fada ban da gujeguje ke yanzu ba yarinya bace kin tashi Daga su Hamida ke matar aure ce ba Daya kike Dasu ba kina jina ko..?
Nan ma kai ta gyada mai yace"Baki da baki ne..!
Ba nace ki daina min mgana Da kai ba .!
Da Sauri tace"Naji insha Allahu..!
Ajiyar rai ya Sauke kafin yace"Kina Bukatar wani abu..?
Tace bakomai kai Tsaye yace"Ki rika gaida Sakina in kun hadu tana gaba Dake kinji ko..?
Amina ta Tura baki kafin tace"Ni fa in na ganta batamin mgana sai tayi ta Hararana har zagina ma tanayi..!
Cikin mamaki yace"Ita Sakinar..?
Amina tace"Eh shiyasa nafi son zaman nan fiye da chan sannan achan ina jin Tsoro da Daddare bana iya barci don Allah ka Fadama Hajiya ta rika barina ina kwana anan in ka Dawo sai na koma achan..!
Kawai sai ta sakamai kuka sai yaji Hankalinsa ya tashi meke Damun yarinyar nan ne Cikin Tausasa Murya yace"Naji ki daina kuka zan mata mgana..Daman baki daina Firgita cikin barci ba..?
Tace mai eh sai da yayi shuru kafin yace"Ki samu mallam yau da Daddare in ya natsu ki Fadamai abunda kike jin in zaki Firgita kin ji ko..?
Tace"Na Fadamai..?
Yace"Eh ki Fadamai sannan mganar Zagin ki da Sakina ke yi kada ki Fadama kowa har su Hajiya zan mata Fada insha Allahu zata Daina ke dai in kin koma gidan kun Hadu ki rika gaisheta saboda ko bakomai Tana gaba Dake kuma a islamiya an koya muku yin biyayya ga na gaba da ku ko ba Haka ba..?
Tace eh ya cigaba da fadin"To ki rika bata girmanta kin ji ko..?.
Ta amsa da toh bai Tsawaita mganar ba yace"Zan ce ma Jafar a Cefanan wannan watan ya siya miki Goldenmorn da Cornfkles Saboda Saukaka miki Wahala sai ki Rika sha in zaki tafi makaranta..!
Tace "To nagode..!
Ya amsa ta da Fadin"Kada ki damu komai kike Bukata kada ki tambayi Hajiya ko mallan ki yi ma Jafar mgana ko kuma ki Dauki wayar Hajiya ki kirani kinji ko..!
Nan ma tace mai da toh tagode Dagnan yace ta maida Hankali a karatunta ta amsa mai Daganan ya mata sallama ya kashe wayar.
Tabi Wayar da kallo Tana Tura baki wai ta rika gaida Sakina Tab wannan mara mutumcin ne zata gaisheta..
Shi kuwa sai da sukayi mgana yaji Hankalinsa ya kwanta har ya natsu ya Cigaba da Duba Takardun Dalibansa da sukayi gwaji.
Da suka gama wayar kunya ta Hana Anina fitowa sai da Hajiya ta Shigo Daukan abu ta ganta zaune tayi shuru tace"A a Mamah tunda kun gama wayar ki fito falo hanne na jiranki mana sai ki zauna ke kadai..!
Jin haka yasa ta mike ta mikama Hajiya wayar, ta karba ta Fice da Sauri Hajiya ta bita da kallo tana Mirmishi a Cikin aranta tana Fatan addu"an su Allah ne ya karba na amitar da Ruhin Amina da Danmallam waje daya.
Amina na fita Hanne ta taso tana Tambayanta da wa tayi waya Amina ta balla mata Harara kafin tace"Bansani ba..!
Hanne na Dariya tace"Nasani Ya Danmallam ne..ko..?
Amina ta mata wani kallo kafin tace"In ma shine sai na Fada miki..?
Sirrin miji da mata..!
Hanne ta saki Dariya kafin ta Ja Hijabinta tana fadin"Bari naje na gayama Hamida..Sabon Update..!
Amina tayi Tsaki kafin tace"Ai ke Hanne mijinki ya shiga uku..duk wanda ya aureki ya auran ma kansa sai kin hada Fada a Family din mijinki Saboda munafuncinki..!
Hanne bata bi ta kanta ba ta fice Amina tayi zamanta Falon Hajiya chan sai gasun dawo Tare Hamida sai kara maimaita abun da Hanne ta gayamata take yi Amina ta musu wani banzan kallo kafin tace"kusan dai ni yanzu ba Sa"arku bace ko..?
Igiya uku ne akaina..Taimaka muku ma nake yi ina yawo da yara. !
Hanne da Hamida suka saki baki ganin haka yasa ta Musu gwalo tatashi da gudu ta Fada Dakin su Hanne Tana Dariya suka mara mata baya suna fadin yau sai ta gayamusu su waye yara..?
Ranar dai anan suka wuni Shashen Hajiya suna abunda suka saba sai bayan sun dawo islamiya ne Hajiya ta saka aka maida Amina gida tana kunkuni Tana komai bata samu yima Baba mallam bayani ba sai washegari da suka dawo makaranta ta Fadamai ya Dade yana mamaki ya tambayeta yaushe ta fara tsorata tace tun tana karama ta dade mallam ya Dinga Fadin Sakacin mamanmu da Aba da Amina na Fama da wannan Laluran ammh bsu sani ba Hajiya ce ma ta Lallasheshi ya bar mganar da yace har Aba din sai ya kira da mamanmu ya musu Fada.
Shi ya Rubuta mata addu"o'i ya bata yace ta Rika karantawa Duk Dare in zata kwanta Tare da Sauran addu"an barcin da Annabi ya koyar damu.
Amina yadda Taga Mallam ya Dau abun ne yasa itama bata Dauka da wasa ba sannan Danmallam ma sun sake mgana da wayar Hajiya Data Fadamai yadda sukayi da mallam ya mata Fada kan ta Dage kada wasa ya Dauke mata Hankali ta rika kwanciya bata karanta su ba.
Shiyasa ta Dake bata kwanciya sai ta karanta sai gashi kuma Cikin ikon Allah tunda ta Dage sai ta samu Saukin Firgita din sai abunda ba"a rasa ba Danmallam har da mallam sun yi mgana Mallam nata fada yana Fadin da Haka Umaima ta Fara gashi nan suna so su taba mata kwakwalwa Dannallam yana so ya Fadama Mallam bayan haka ma yana Zargin akwai wani abu Tattare da Amina sai dai kuma bai da Hujjan hakan ammh yana so sai in ya kara Dawowa ya Zauna ya Fahimci matsalanta Domin Ranar da abun nan ya Faru tsakaninsu da Washegarin nan da Safe yaga tana wasu abubuwan da Dole tana da wani abu a Tattare da ita.
*******
Kwantashi ba wuya a wajen Allah su Amina har sun gama Jarabawarsu sun yi Hutu taso ta zauna anan tayi Hutunta Hajiya ta hanata sai ta Roki Baba mallan kan su Hanne su Bita ko Sati Daya su yi da Farko Hajiya ta Hana sai da Mallam ya saka baki Sannan ta amince suka Tattara suka koma chan da Niyar Sati Daya zasu yi Saboda islamiya basu yi Hutu ba.
Mamanmu bata Damu ba da akace Hamida zata je gidan Amina Domin alokacin tana Tsakar Cin Duniyarta ne Domin komai tace Aba ya bata baya Gaddama Kudi yake sakar mata bana wasa ba ta zama Tauraruwa a wajen sa Mamanmu ta samu Cikar Burinta Fiye ma da yadda take fata shiyasa ta manta da kowa da komai ko Anty Amarya ta kirata bata ma kaunar Hakan gani take tana neman Takura mata Shiyasa Amina ma bata gabanta Ta barta da Anty Amarya chan itace Zatayi mganinta ita yanzu Sa"idu ne agabanta yanzu shawaran komai sai yayi da ita sai abunda tace koda yace Jafar yace kaza ya kamata ko Hajiya sai tasan yadda tayi ta Kushe mganarsu ta sauya da nata Shiga kawai take tana fita Daga kayan alfarma kamar wata Yarinya sannan Malaminsu tana sakarmai kudi sosai Domin ta yaba da aikinsa
Anty Amarya kuma tana nan tana Jiran gawom Shanu domin ta yarda da aikin Malam ya sanar da ita Nasara tatace shiyasa bata Damu ba ta koma ta Zauna tana jiran tsammani kamar yadda ta basa duka yardanta Shiyasa ko Sakina ta kirata tana mata Korafi take mata Fadan bata da Hakuri aiki nawa suka basa kuma ya Biya musu Bukata..?
To wannan ma ta Zauna ta Jira komai zai zama Daidai da yardan Allah abunda basu sani ba Daga wannan Lokacin aikin ya kuskure musu sannan zasu cigaba da jiran majirata ne Jiran da zai kai su ga Ranar Nadamar su da Tonon asirin su..!
Ko Hutun da su hanne suka tafi Sakina kamar ta Haukace saboda Bala'i Amina Mahaukaciya take so ta maidata,gwara ma su Hanne suna dan jin mganarta banda Amina sai ta gama masifarta sun ba'ta mata Falo ko Kitchen Amina ta mata gwalo ko Ta mata Tsaki ta shige Daki abunta Sakina taci ji Yatsa kamar me..?
Kamar yadda yace a Cefanan watan nan an kawo su Goldemorn su Amina an samu banza ana ta Wadaka madara kuma da kayan Tea kafin Sati sun kare saboda yadda suke barnan sa basa da aiki sai dan sululu ko Wainar Fulawa gashi Sakina bata son kazanta su kuma in suna aiki a Kitchen din sai sun yi kaca kaca dashi in tayi mgana Hanne da Hanida kadai ke Sauraranta banda Amina da take maidata ma mahaukaciya.
Sakina abun ya isheta kullum sai ta Kira Danmallan ta kaimai karan Amina da kannensa shi har ma ya gaji Saboda bai isa ya kore su ba Amina Matarsa ce sannan su Hanne kannensa ne ko ba aure suna da Damar zama agidansa watarana da abun ya ishesa sai yace ta bama Amina wayar da an bata ya fara mata Fada sai ta saka kuka tace In ta gaishe da Sakina sai taki amsawa ta bita da Zagi sannan bata barin su suna shiga Kitchen sai tace suna mata kazanta Ayadda
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13 Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49