kamar wasa ta Yafito Hamida tana Fadin"Hamida kinga ikon Allah ko..?
Amina an shiga kwaryan manya..!
An zama uwa..!
Amina na dariya batace musu komai ba Hamida tace"Sai a rage jidali Tunda an zama uwa ko Aminene..?
Amina tace"To Allah yasa ya ragun kunsan ba yin kaina bane..!
Suka Hada Baki wajen fadin"To yin waye..?
Sai da tayi Fari sannan tace"Na Allah ne..!
Dariya Hanne tayi ta Daka mata Duka abaya Amina ta sosa wajen tana Fadin"Lala sai na fadama Hubby na..!
Dariya suka kwashe mata suna Fadin su Hubby an jiki..!
Tun Safe Amina tayi wanka ita da yaran suka fara shiga suna fita suna fita gadonta kuma cike da kayan suna yan"uwanta sun mata kara ba wacce tazo Hannun Rabbana Aba ma da Turamansa da kayan yara Mallam ma kaya sai wanda ya gani Amina ba abunda zatace ma yan"uwanta da iyayanta sai godiya domin sun mata komai aduniya wajen ganin sun ingata rayuwarta.
Ya Danmallam bai zo gidan ba Ranar suna Saboda mutane sun dai yi waya da Safe da wayar Sarood daman ai nan ta kwana tare dasu ya Abida,wajen azahar sai ga su ya Aisha da kololin abinci kala kala lemuka daman da ruwa tun jiya aka Sauke su nan da nan aka fara Cin abinci Daman tuni kowa yayi wanka ya Shirya kansa Yakaka da Safe gidan Baba mallam ta koma tace bazata iya ba ta bar ma su Abida gidan su shakata..
Abun da ya bama Amina mamaki Sai ga Sa"adatu da ya Sadiya har da ya Jidda sun zo mata suna abun Sai da ya bata mamaki ammh bata nuna ba ta Saki Fuska suma sauran yan"uwa suka karbesu hannu Biyu da suna Dari Dari Daga baya suka shige Cikin yan"uwana ana ta Hiran masu Ciki su ya Abida da su ya Zeenatu har ya Zulaihat duk ciki garesu su ya Ikram kam yama tsufa tana ta fama dashi Chan da yammah sai ga su mariya da Samira yan makarantar Haddarsu Amina baki ta rike tana kallonsu tace"Su Mariya ne da su Samira. !
Suna dariya Mariya tace"Wlh mune su Amina..!
Sai dukkansu sukayi Dariya Hamida ta Fadama mariya Dayake suna Chart ai sukace sai sunzo sun ga Amina da abunda ta haifa aiko sun sha kallo Amina ta zama zara aciikin wata Duk inda tabi ita ake kallo ta zama abun Sha"awa kuma duka taron Saboda itane nan suka Hade dasu Hamida suna ta Hiran baya da irin abubuwan da suka faru Lokacin suna makaranta Har Sa"adatu ta shige Cikinsu
Dayake abun na malamai ne ba Kida ba wani Hayaniya ko Hotuna ta wayoyinsu suka taru yan"uwa suna ta Daukan kansu ya Danmallam kuma yayi walima achan masallacin Baba mallan anyi wa"azi sannan an ci an sha an raka yara da addu"a da Fatan Allah ya rayasu.
Aliyu na Tare dashi a matsayinsa na Amini sai su ya jafar da suka Dawo Daga wajen aiki da yammancin ranar tunda matan suna chan gidan Amina sai suka Sauke gajiyarsu Shashen Mallam nan sukaci abinci suka cigaba da Hira.
Aliya kuwa sai haba haba take da Amina abu kadan tace Amina kaza amina na yankwanata sai da Hanne ta mata mgana Amina ta mata wani kallo kafin tace"Ke ni fa na tsani Cusa kai..Ni ba kawartace ta kama kanta..!
Hanne tace"Kodai yaya ne ki mata uzuru ai don ke tazo.!
Amina ta bangaje Hanne tana Fadin"Naji..!
Hanne ta Bita da kallo Baki Bude akwai Hallayan Amina da Har Abada bazata iya sauyasu ba ance Hali ai Zanen Dutse ne.
Su mamaki ma ta basu da suka ga suna mgana da Sarood Cikin Harshen Labarci wayar Sarood din DanMallam ya Kira yace ta kaima Amina saboda ya yi ta Kiran wayanta bata Dauka ba Shiyasa ta kawo ma Amina ta karba sukayi mganar yace ina ta Jefar da wayarta tace bata sani ba suna cikin kaya mganar komawarsu asibiti yayi bayan yace mata sun yi mgana da Hajiya in sukaje kawai za"ayi ma yaran kaciya ne su Huta Amina tace ba Matsala Duk yadda suka yanke har ya bata Aliyu ya kara mata barka Sannan sukayi sallama ta fita Falo ta Nemo Sarood ta bata wayarta..
Hamida ce sai da tayi mgana ta kalli Amina sanda ta shigo Tana Fadin"Lalle Matar ya Danmallan kece kika kware da Labarci haka sai yarata kuke ke da yar Balarabiyar kishiyarki..!
Amina ta harareta Saboda su Sa"adatu na wajen yasa batayi mgana ba ammh ina ita ina wani Sakin jiki da Sarood ai kishiya sunanta Kishiya duk da tana da Kirki ammh dai kowa yayi ta kansa abunda ya faru agidansu ai Ishara ne ga masu sakarma Kishiya Ragamar gidansa da ya"yansu duk da ba Duka aka taru aka zama Daya ba akwai nagari acikin na banzan ammh Dai na banzan su sukafi yawa.
Sai dare ya Danmallam suka zo da Aliyu da su ya Jafar suka Dauki yaran su ya Aisha na fadin ayi ma yaran alkunya Danmallam yace kul..Da Mallam da Aba za"a dinga kiran su sune alkunyansu Daganan sai suka ja bakinsu sukayi Shuru ranar dai gidan Amina ya Cika da Baki duk nan suka kwana Ya Danmallan kuma da Abokinsa Dakin su Nazeem suka kwana..
Washegari wasu har sun yi shirin komawa irin su ya Zulaihat Sai ga Sakon mallam zai yi mgana dasu Dukkansu anjuma sai tafiya ta fasu kowacce ta Share waje ta zauna aka cigaba Da Hira Saboda an Haadu ba"a son Rabuwa da juna...gidan Amina aka kawo kan ragunan da aka gyara suka Dafa suka ci sannan Naman kuma achan su Mamata suka soya sai da aka musu nasu tunda dagachan aka Rabasa yadda kowa zai shaida harta Aba da Baba mallam an yi musu kullin su na Nama Anty Hadiza kuma ita tayi Yajin jego,zuwa yammah duk sun gama gyara ma Amina gidanta Yakaka ta Dawo ita tayi ma ma Amina wankan yammah ko kafin mangariba duk sun watse sun koma gidan Baba Mallam har su Hanne Amina da Farko Har da sa Rigiman ita ma sai taje Yakaka tace da Danyen Jegon ne zata fara yawo Dole ta Hakura ta koma tana ta Faman gunguni.
Achan gidan ya Danmallam kuwa Ana Idar da Sallar Isha"i mallam ya Hada Taron daya ce za"ayi Sannan har da su ya Nazeem da Uzairu sun iso aranar dukkansu mallam ya kira su yace yana som ganinsu gabadayansu suna Falon mallam illah banda Amina da ya Akila da bata samu zuwa ba sai ya Jadwa.
Ammh harda su ya Danmallan suna wajen,Aliyu dai sun tafi dazu da yammh shi da Aliya,Sai su ya Jafar da ya Nasir ya Nazir shima bashi wajen Tunda bai samu zuwa ba sai Aba sai Jawaad har Anty Hadiza da su mamata mallam yace su shigo Tunda Tunatarwa ne ya kamata suna wajen..
Nasir ne ya Bude taron da addu"an sannan Mallam ya fara jawabinsa da Farko Yayi musu wa"azin riko da Zumuncu da yadda zasu Hada kansu waje Daya su zama Dangi Daya kamar yadda yake fata sannan ya gangaro kan wa"azi kan shirka da azaban da Allah yayi tanadinsa domin masu Hadashi da wasu,Tunda ya fara mgana suka Fahimci inda ya Dosa sai jikin kowa yayi sanyi bai fito ya Fada musu Sakin daya shiga Tsakaninsa da Uwani da Marliya ba ballatana ta Bangaran Aba yadai gyara Zama ne ya Fara karanta musu muhimmancin Uwa ga ya"yanta sannan da irin yadda Annabi ya Fadi Darajan uwa.
Mallam ya kallesu Daya bayan Daya kafin ya Cigaba da Fadin"Ita uwa tana Daraja da kima..Annabi ya ambaci abi uwa sau uku kafin yace abi uba kunga ko ta haka kadai ya isa kusan Tasirin uwa..Sannan duk lalacewar Uwa uwace..Domin ta Dauki Ciki na Tsawon Wata Tara ta sha wahala kafin ta Haifi abunda ke Cikinta ga azaban Radadin Naguda wanda aka Fadama cewa acikin Azaban mutuwa ne aka Dibosa kadan..Kuma dukkanku kusan mutuwa tana zafi da azaba Saboda Alokacin da Annabi Sallallahu Alaihi wasallam zai bar Duniya Sai da ya ce Lalle mutuwa tana da zafi tana azaba da magagi Annabi ma kenan wanda ya kasance Shugaba ne na Hallitun Duniya ya Dandana azaban mutuwa ballata mu bayi da kowa kowan ba..?
To acikin wannan azabar ne aka Dandana ma uwa wajen Haihuwa bayan ta haihu kuma ta fara Wahalan shayarwa da Reno walwalun duniya akanta suka kare taki ci taki sha Duk domin ta inganta rayuwarka Sannan ta Jajirce wajen tarbiya bata barci Saboda ganin ta inganta Rayuwarka komai lalace uwa komai nata kan ya"yanta ne,kuma komai zata aikata mai kyau ko mara kyau ne to bazata Fara Duba kanta ba sai ta Duba ya"yanta ku Saki ranku ku Bude zuciyarku..Ku sani Cewa Uwa ta wuce wasa komai ta Zama awannan Duniyan bai kamata ta Fuskanci Tsagwamma da Kyama awajen ya"yan data Haifa bq ..Ko kuwa kowa zai gujesu bai kamata ku ya"yansu ku juya musu baya. !

Mallam ya Karishe Fada yana nazarinsu ganin yadda Gabadaya Jikinsu yayi sanyi ne yasa ya Cigaba da Fadin"Komai kuka samu anan Duniya baku isa ku biya kwayan Zarra na wahalan da iyayanku sukayi akan ku ba..Sannan kada ku manta Kisaar da wani cikin Sahabai yace ya Dauki mahaifiyarsa a saman kafadansa yayi dawafi da ita shin ko ya Biyata wahalansa da tayi akansa..?.
Annabi ya shaida masa cewa ko Kwayan Zarra bai biyata ba kun ga kenan Allah ne kadai yasan Alherin Uwa ga abunta ta Haifa..Da wannan Tunasar da nayi muku nake Fatan zaku Hankalrta..Uwani da Marliya da Balaraba sun aikata Laifi mai muni ammh kuma ga wajen Ubangiji abu ne mai Sauki in suka Rokesa zai iya yafe musu sannan muma mu sani afuwa da yafiya abu ne mai kyau tunda muma muna kuskure sannan Allah Gafurin Rahimun ne yana yi mana Gafara a duk sanda muka aikata Laifi yana mana afuwa koda Laifin mu yakai Cikin Duniyar nan ne to meyasa mu bazamu yi musu afuwa ba .?
Sai mu barsu su ji da Laifinsu Tsakaninsu da Ubangijinsu,Sannan ku sani aibata su ko gayamusu mummunar kalma bai Dace ba..Ku Sausauuta kalamanku kan iyayanku Domin Fadin mummuna mgana akansu Tamkar ja da hukuncin Allah ne Tunda shi ya Kaddari komai Daya Faru..Daga karshe ina Umartanku Gobe kuje ku Duba iyayanku mata sannan ku Musu kalamai mai Dadi Daga karshe ku yi afuwa ga laifikansu ko Wani Nauyin Zai ragu daga garesu..!

Gabadaya Falon baka jin komai sai Shesshekan kukan su ya Zulaihat Hamida ma sai kuka take jikinta Duk yayi sanyi,Saboda tasan ta aikata kuskure ta yi ta yabama mamanmu manganganu Allah ta Tuba dukkansu haka Suke fada aransu sannan Jikinsu Duk yayi sanyi da Nasihan mallam bayan nan ma Hajiya ta Dora da nata kafin su tashi sai da suka Tabbatar ma da mallan cewa komai ya wuce sannan zasu bi Umarninsa..
Haka taron nan ya tashi kowa jiki ba Dadi alamu nasihan mallam ta Shigi Kowa sannan Hatta Aba yaji Nauyin Zuciyarsa ta Ragu yana Tunanin zai iya yafe ma Mamammu har ya Jafar ma yaji aransa ya yafe mata shi da su ya Jawahir aransu sukaji sun yafe ma Mamanmu tun balle ma da su mamata ke Labarin Halin da mamanmu ke Ciki nan da suka ji Tsausayinta bayan sun Furta sun yafe mata.
Washegari Mota guda sukayi su ya Zulaihat zuwa Gusai har da Ya Jawahir da ya Jalela sukace zasu ce sai ya Sadiya da Jidda da Sa"adatu suka Dauki Hanyar Dutse sai Ya Nazeem da Nazifa da ya Uzairu sai Umaima suka Dauki Hanyar Tsafe sun yi waya da Shamsu zai samesu achan..!
Dukkansu Halin da suka iske iyayan nasu ya Raunana ta su sun kara Tsorata da Duniya Mamanmu nata yafi muni Tana kwance Cikin kashi da Ftsari bata iya mgana abinci ma ko ambata rabi ke shiga Cikinta ba baki ba Ido haka su ya Zeenatu ke kuka kamar ransu zai fita har ta su ya Jawahir sun koka Mamanmu sai dai taji muryansu bata gani sai kuka tana Faman mika hannunta mai Lafiya.
Allah Sarki ya Zeenatu da ya Zulfa da ya Jawahir suka Zage suka gyara mamanmu suka Sauya mata kaya ya Jaleela ta bada shawaran su kaita asibitin Basu ji Haushin kowa ba Ganin yadda aka banzarta da mamanmu ka shuka alheri ma ya ka kare ballatana ka shuka Sharrin
General Hospital Gusai suka kaita Liktoci nata Fadan an bari Jikinta ya Saki agida Dayake akwai kudi nan da nan aka karbeta aka shiga da ita aka Fara bata Taimakon gaggawa su kuma suna gefe suna ta Faman sharan kwallah
Zuwa yammah ta Dan fara Dawowa Hayyacinta sai dai anan asibitin zasu riketa zasu rika yi mata gashin kashi sannan sun saka mata abun Fitsari ta kasanta sannan da Drip wanda zai taimaka ya Dawo mata da Ruwan jikinta Daya zaganye a kwance aranar dai basu samu daman Dawowa ba Sai washegari da Mamammu ta dan Fara mgana kadan kadan tana kuka tana Rokonsu gafara suka Rumgumeta suna kuka suna Fadin sun yafe mata Jaleela ce da Jawahir suka Dawo Gumel aranar saboda washegari zasu tafi  zulfa da Zahra suna chan sai Hamida sai washegari zata koma Zulaihat ma Dagachan ta koma Jigawa sun bar ya Zahra data tambayi Mijinta zatayi sati wajen mamanmu Alla barshi ya Zulaihat zata Dawo ta karbeta sai ita ta koma gida.
Achan Tsafe ma abun ba Dadi Haj.Uwani ciwo ya kusa cinyeta ta rame ta lalace kamar ba ita ba su ya Nazeem suma sunyi kuka Halin da suka iske mahaifiyarsu aciki suma basu ji Hauahin kowa ba domin Gaskiyan mallam ne a wannan gabar sai su ya"yanta suma sun yi kokarin kaita asibiti aka Fada musu ko sun je baza"a ga komai ba Yayanta ne yayi musu kwantance wani mai mganin gargajiya anan kauyen Tsafe nan suka kaita ya Dubata yace babu abunda zai mata Ciwonta kaikayi ne ya koma kanta Sai dai Kawai ya bata wani mganin da Zata rika sha kirjinta ya kwanta mata da Tarin dake Sarketa haka suka Dawo da ita gida suka tasata suna faman kuka tana Hawaye tana Nishi wajen rokonsu gafara suka riketa suna Fadin sun yafe mata Nazeem shi yaje yazo da Likita ya Dubata yayi mata alluran barci Saboda ta samu barci sai abakin kakarsu suka san Mallam ya Saketa to damam ai sun san haka zai faru sai dai sun jinjina ma mallam ba Tozarci Cikin Lamarinsa Mutum ne mai Dattako..!
Ganin yaranta sun Sauko sun nemeta yasa suma yan"uwanta suka Sauko Daman Hannunka bazai taba Rubewa ka yanke ka yarba Dole itace Dolensu,Nazeem da Uzairu kwana Biyu sukayi suka koma bayan sun bar ma Nazifi kudi sosai Dayake Nazeem ya Fara aiki Shamsu kuma Sai ranar da zasu tafi ya iso nan suka barsa,Umaima dai gata nan ne dai sai ahankali Ita kanta aljanun su taba kwakwalwarta yau lafiya gobe Hauka ne Nazifa ce aka bari tana kula da Hajiyan Uwanin wanda har taji Sauki Data ga ya"yanta sannan Danginta sun mata afuwa..!
Chan Dutse ma abun yayi muni Domin sun je sun iske Anty Amarya ta Fita Daga cikin Hayyacinta Domin Tsorata take yi acikin barcinta sai ta rika ganin Yaya tana fito mata Tun abun na karami har ya Girmama bata iya barci Sai abun ya taba kanta gabadaya ta Birkice yan"uwanta sun taimaka mata sun kaita asibiti Shashen mahaukata ana Dubata To Cikin wannan Halin suka isketa ta Rame ta lalace duk ta Firgice kamar ba Marliya yar kwalisa ba alokacin Duka yan"uwanta sun koma Tsausayinta harta Sakina da Anty A"i sun koma suna Tsausaya mata ganin Halin data koma ko da Rana ne ana Zaune sai ta mike tana Firgita da Ihu su ya Jidda suma sun koka matuka haka suka Rumgumeta suna kuka Tsausayin Mahaifiyarsu ya kamasu Nadama suka kamasu na yarda suka ki nemanta na tsawon Lokaci.
Sukaji aransu sun yafe mata har Abada anan suka Hadu da Sakina da ta Dawo nan da zama sai sabon kuka Tana Faman fada musu ta gaji da kiran Danmallam bai Dauka ba ta turamai sako ba adadi bai mata Reply ba in ya Saketa ne ya Fadamata sakina duk ta Rame gwanin ban Tsausayi..
Nan Sa"adatu ke fadamata daga wajen sunan Amina suke yara sun ci sunan Aba da Mallam sannan Sarood ma Cikinta har ya fito Sakina sai kuka Nadama da tsoron Rayuwa na kara shiganta har hotunan yaran ta gani Aliya ta Turo mata ita yanzu ta gama ganin rayuwa wani kishi baya gabanta ta sanu ta san makomarta kawai irin yadda Anty Amarya ta koma ya isa mai Hankali ishara..!
Sa"adatu ce ta fara komawa gombe Daga baya kuma ya Jidda,Ya Sadiya na nan Dutse ita tunda sunzo ne ita da Mijinta Tana Cigaba da kula da Anty Amarya..!
Mallam yaji Dadi da yaran suka kirasa sukace sun je sun Duba iyayan nasu ya Dinga saka musu albarka sanna yaji ba Dadi da labarin halin da suka samu su Marliya abun dai sai Addu"an da Fatan gamawa da Duniya Lafiya..!
Hajiya ma dataji Hankalinta sai ya tashi ta tambayi Izini Mallam bai hanata ba ya barta ita da Hajiya Nasara da Anty Hadiza suka tafi Gusai suka Duba Mamanmu a asibiti haka ta rike Hajiya tana kuka,Hajiya na Faman share mata hawaye tana Fadin ta Yafe mata har ta Hajiya Nasara Sai da Jikinta yayi sanyi,Sun iske Zulaihat na asibitin ita ke kula da ita,Basu jima ba suka gaisheta da kayan Dubiyansu Daganan suka Dawo Washegari kuma Tsafe sukaje suka Duba Hajiya Uwani..Hajiya Babba sai da tayi mata kuka tana kuka tana rokonta gafara ta yafe mata da ita da ya"yanta Hajiya tace bakomai Nazifa ta nan bata tafi ba,Sannan Umaima na nan jiki Sai ahankali kawai..
Basu jima ba sallah kawai sukayi suka juya Dagan suka je Dutse suka Duba Amarya Halin da suka ganta sai Allah Amarya hauka Tuburan sun isketa sai da aka Rirriketa,Sadiya ke nan tare da ita da Sakina Hajiya sai da ta Tausaya ma Sakina duk ta Bushe ta gaida Hajiya sai Sharan kwallah take Sai ta bama Hajiya Tsausayi har tayi alkawarin yima Danmallan mgana in suka koma..!
Koda suka koma Jikinta Duk a Sanyaye bata samu yima Danmallam mganar ba sun dai yi da Mallan shima ya jinjina ya kada kai yayi musu Fatan Dacewa mganar Sakina kuma yace tana Hannun mijinta abunda ya yanke shine Daidai.
Amina kuma ana chan ana ta Jego Yakaka sai da Allah ya sakamata ita ke kula
Showing 135001 words to 138000 words out of 146831 words