ƙone ko tsinke ba'a fita da shi ba. Ana cikin wannan tashin hankalin ƴarta Hannatu ta dawo gida wai mijinta ya saketa. Gaba ɗaya Umma ta sake hargitsewa jiki ya koma ɗanye sharaf. Sai da aka kira Smart ana faɗa masa ne ya saka aka kaita asibiti. Satin ta ɗaya aka sallamonta. Gaba ɗaya Salim ya koma kamar zararre. Sai kuka yake yana jama Umma ALLAH ya isa akan itace ta ja masa. Ai dama nakan tudu ya faɗa duk bala'in data ƙulla akan Smart sai ya dawo kansu. Gashi nan kuwa. Ta cucesu ta zalunce su bazasu yafe ba. Ranar da matar Salim ta gudu da ƴaƴansa bayan ta saida gidan da shi ya kaɗai ya rage masa ai kaɗan ya rage a ɗaureshi a turu saboda tsabar zaucewa. Umma ta dinga kuka dan dama dai Salim ɗin ne abin tinƙahonta...........✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣2️⃣
.......A ɓangaren Garko family ma dai ALLAH ya bama Dada da Baba Garko lafiya har sun dawo gida Nigeria. Sai dai Dada ƙarfin hali kawai take. Gaba ɗaya ta zama wata shiru-shiru. Sai da kaga ta tasa hoton Maman Mawaddat da na Sultana gaba tana kuka. A yanzu Baba Garko kan zauna ya lallasheta da mata nasiha. Hakama amaryarta takan ƙyautata mata duk dan dai ta kwantar da hankalinta, haka ma ƴaƴanta basa gajiyawa wajen tattalinta saboda an tabbatar musu zuciyarta idan har ta buga shike nan kuma. Dan haka kowa baya wasa da al'amarinta. Lulu kanta ba'a barta a baya ba wajen lallashin Dadan. Dan tana kallonta tamkar Mawaddat ɗin ta ne data rasa. Akoda yaushe cikin yin video call suke da ita....
__________★
Shirye-shiryen bikin Maryam ya kankama sosai, dan takowane ɓangare shiri kawai akeyi. Ana saura sati guda ɗaurin aure Smart da iyalinsa suka iso gida Nigeria. Ƙasar da yay kewa. Tarba ya samu maiban mamaki da ga al'ummar ƙasar tasa da ƴan uwa da abokan arziƙi. Dan da ƙyar suka iya baro airport sai da taimakon jami'an tsaro. Yayinda ya samu rakkiyar masoya har gida. Anan ma ya samu yaran anguwa da iyaye suna jiransa. Sai ga Smart na hawaye dan farin ciki. Ya tabbatar da mutane rahama ne. Duk wanda yace maka yana sonka da ƙaunarka ya gama maka komai a rayuwa. (Ya ALLAH ka barmu da masoyanmu. Duk wanda ya somu dominka ya rabbi shima ka soshi shi da zuri'arsa baki ɗaya. ❤️❤️❤️😘 wannan nakune masoyan alkairi 🙏).
Anan ɗin ma dai da ƙyar ya samu suka shiga gida saboda yanayin Lulu. Dan cikinta yayi girma sosai wannan karon fiye dana AA. Ga kuma kullum cikin laulayi take dan tunda ya fara tsufa bata da wani ishashen lafiya. Duk da dama dai haka taketa fama tun da cikin ya shiga watanni biyar. Babu kunya yau kam Smart ya rungume Ammah da Abbah a gaban jama'ar gidansu. Ya kuma rungume ƙannensa su Mubarak da yasan suna matuƙar kaunarsa. Kannensa mata nata kawo masa gaisuwar girmamawa harma da wanda suka girmesa kamar wani sarki. Tunda Ummah ta leƙo sau ɗaya ta gansa bata sake maimaitawa ba, ɗaki ta shige tana sakin wani irin kuka mai ƙona zuciya. Smart ya koma kamar wani baƙin bature. Ko makaho ya laluba yasan kuɗi da jin daɗin rayuwa da ɗaukaka sun zauna sai dai fatan gamawa da rayuwa lafiya.
Shiko sanin bata da isashiyar lafiya har ɗaki yaje ya gaisheta tare da duk sauran matan Abba har aunty Amarya. Ita kanta Mama a ruɗe take, kawai dai tana ƙoƙarin dannewa ne kar ai mata irin kallon da akema Umma. Dan ƙamshin Smart kawai rikita zuciya yake. Saboda kowa ya gama sanin hankalin Ummah fa a tashe yake. Wasu a cikin yaranta har abun nata na basu kunya.
Bayan yaci ya sha daga girkin mahaifiyarsa data musu girki da kanta dan Lulu bata iya cin komai sai kunun gyaɗa. Shi kaɗai taima sha na hauka dan motsi kaɗan taji yunwa yanzu. AA na hannun iyayensa wannan ya ɗauka ya ba wancan haka aketayi. Yaron birgesu yake gashi fes kamar ka lashe, komai na ubansa bai bari ba. Zuwa yanzu ya ɗan fara magana sai dai ba gane abinda yake nufi akeyiba ma sosai. Kwanciya Lulu tayi danta hutama ranta. Yayinda su Ammah da Smart suka buɗe shafin hira dan Gwaggo Sa'adah na gidan da su aunty Bilkisu da Hawwah. Daga baya sai ga Abba shima ya shigo duk da su Smart ɗin sun je sun gaishesa...
Washe gari aka kawo lefen Maryam daga gidan su Ahamd. Lefe ne na nunama tsara dan an nuna dukiya kam babu ƙarya. Ƙwaƙwalwar Umman neman zautuwa takeyi. Dan kasa jurewa tai yau ma sai kulle kanta tai a ɗaki. Ga dangin Ammah dana Abba nata zuba mata habaici batare da sun duba cewa ƴar uwarsu bace ba. Anyi komai cike da girmama juna da mutuntawa dan suma sun bada tukuyci mai tsoka. Bayan wucewar ƴan kawo lefe Smart ya ɗauki Lulu da AA da Asma'u suka nufi gidan su Lulun. Daddy da su Amrah sunyi farin cikin ganinta, duk da kuwa jiya harda su a ƴan tarbarsu. Basu koma gida ba sai dare. Mommy ma taji daɗin ganinsu. Tana ta tsokanar AA. Hira sosai Smart suka sha da Daddy, dan anan suka yini sai bayan sallar azhar suka nufi gidan Uncle Yousuf. Anan ɗin ma dai hirar aka sha, samun su twins da sukai can yasa Smart da Lulu fahimtar akwai wani abu tsakanin Hussain da Asma'u. Hakan yama Lulu daɗi sosai ita da Smart. Basu bar nan ba sai bayan la'asar. Sun nufi gidan Baba garko inda suka ƙarasa yinin. Itama dai Dada harda kukanta dan ta fahimci dai waɗan nan ma'aurata kainuwa ne dashen ALLAH. Sannan FURAR DANƘO ne damasu ace za'asha farau-farau abune mai wahalar gaske. Jiki luɓus suka koma gida dan Lulu tayi laushi. Ammah taita ma Smart faɗan miyasa bai barta acan ba yaketa yawo da ita haka. Shi dai murmushi kawai yayi yana kallon Lulu dake masa gwalo ƙasa-ƙasa. Washe gari yana tare da Ahmad da Coach, acan ya yini sukasha hirarsu da ubangidansa. Bai dawo gidan ba sai dare dan har Malam na Yakasai yaje ya gaidar bai manta alkairi ba nan ma....
Al'amarin biki ya kankama sosai, Smart ya haɗama amarya gidan mijinta da kaya na kece raini da nunawa tsara. Yayinda aka fara events da aka shirya wanda ya kafa ya tsare ya hana Lulu zuwa ko ɗaya saboda yanayinta. Daga ƙarshe ma da yaga hayaniyar gidan na mata yawa sai ya dinga janyeta zuwa masaukinsa. Acan suke kwana sai da safe ya dawo da ita nan ta yini cikin danginsa. Lulu ta amsa suna matar babban Yaya. Dan komi aka buƙata bata jin ko ɗar zata fidda a jakarta ta bada batare da tabi takan mijinta ba. Sai wasu a ƴan uwa suka fara tsogumin ai ta kankane komai sai abinda taso take badawa. Tun anayin ƙus-ƙus har zancen ya fito fili yakai kunnen su Ammah. A take Ammah ta nuna ɓacin ranta akan hakan, yayinda Smart da shima ransa ya ɓaci ya basu amsa da ai kai da kaya duk mallakar wuyane. Shi kansa a ƙarƙashin say ɗin Lulun yake bama dukiyarsa ba. Ballema ko sisi bai bata ba duk abinda suka nema ta basun kuɗinta ne. Wannan zantukan nasa yasa jikunansu yin sanyi, dama dai cikin dangin Abba ne da ƴaƴan Mama da wasu ana Ummah masu gulmar. Sai aka koma ƴar sinne kawunan jin kunya.
Ana gobe ɗaurin aure akai dinner. Ita kaɗai Smart ya bari Lulu ta halarta. Shima kuma yaje. Dan tare sukaje tana gefensa riƙe da hannunta AA daya maƙale masa da ga hannun su Abdull ɗauke a kafaɗarsa. Sun isa a lokacin da kusan kowa ya gama zuwa. Dan har biki ya fara. Dan haka gaba ɗaya attention na mutane ya dawo kansu musamman yanda mc ke kwarzanta wanene Smart ɗin da matsayinsa a wajen ango Ahmad da ma Amarya Maryam. Nan fa dangin Ahmad ɗin masu ɗan jijji da kai irin na dangin miji suka shiga hankalinsu. Dan sun fahimci abinda sukeji basu yarda ba ashe gaskiya ne. Dan kamanin Smart da Maryam a bayyane suke. Nan fa ƴammata suka ruɗe da ganin matashin ɗan ƙwallon da duniya ke yayi mai ji da kuɗi. Sai dai Lulu dake fama da cikinta tana nane da abunta. Duk yarinyar data kama tana kallar mata miji kuwa zatasha harara. Shiko Smart nata ƙunshe dariya dan yana sane da matar tasa. Amarya da ango sunsha ƙyau har sun gaji, yayinda bakin Ahmad yaƙi rufuwa. Liƙi sosai daya ruɗa hall ɗin Lulu da Smart suka dinga zuba musu harda AA da Ahmad ya ɗaga sama yana sumbatarsa da faɗama mc cewar a sanar kowa ya sani wannan surukinsa ne. In sha ALLAH yanda suka taru anan bikin aurensu haka wataran zasu taru bikin auren AA da matar da zasu haifa masa. Wannan zance na Ahmad yasa kowa dariya a wajen tare da addu'ar ALLAH ya tabbatar da hakan. Ba'a tashi ba Smart ya ɗauki matarsa suka gudu dan taje ta huta saboda bata jimirin hayaniya yanzu....
Washe gari aka ɗaura auren Ahmad Rabi'u Ƙoƙi, da amaryarsa Maryam Mika'il Mawashi akan sadaki naira dubu ɗari biyat bayan sakkowa da ga massalacin juma'a. Ɗauri aure ne daya samu halartar manyan mutane a dalilin gidajen biyu. Tare da ɗunbin masoyan Smart da ga jihohi daban-daban. Anyi walima da yamma. Zuwa bayan isha'i aka shirya kai amarya ɗakinta. Yayinda kaf yayunta harda su Sadiq ƙanana suka taru a falon Abba domin mata nasiha. Tasha kuka sosai har muryarta na dishewa. Dan yayun nata sun mata nasiha mai ratsa zuciya. Bayan an kammala Smart da Salim da Zubair da Kamal suka sakata a danƙarereiyar motar da Smart ya siya mata suka kaita gidan mijinta da rakkiyar mata iyaye guda biyar kawai. Da zasu taho ne ta rungume Smart tana kuka da jera masa godiya. Murmushi yayi a hankali yana mai lumshe idanunsa kafin ya ɗagota a jikinsa. Fuskarta ya riƙe cikin hannayesa yana girgiza mata kai alamar tayi shiru. Daga haka ya shiga gaya mata daɗaɗan kalaman da saida ta saki murmushi. Sannan ya kamo hannun Ahmad ya saka masa nata a ciki ya ɗan bubbuga kafaɗarsa ya fice yana maida hawayen da suka cika masa ido shima. Smart na matuƙar so da ƙaunar ƴan uwansa matuƙa a rayuwa. Akwai shaƙuwa sosai a tsakaninsu duk da bawani sakewa yake da su ba. Dama sauran duk sun fita harma sun shiga mota. Yana zuwa shima ya shiga kawai suka wuce........✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣3️⃣
.......Washe garin da aka miƙa Maryam gidan miji Mawashi family suka tashi da tashin hankali biyu. Na farko shine gano Huwaila ɗauke da cikin shege na watanni biyar. Tashin hankalin bayyanar wannan ciki kuma yasa Ummah yanke jiki ta faɗi. Inda faɗuwar tata ta zama sanadin samun paralysis. Smart na masaukinsa yana barcin gajiya Lulu a jikinsa ya samu kira da ga Salim. Dole ya shirya ya nufo gidan da Lulu data dage bazai barta ita kaɗai ba. Sun sami gida a rikice. Ko Ummah ba'a ɗauka ba zuwa asibiti sai da yazo ya fara faɗa. Bayan ankai Ummah asibiti suka samu tabbacin ta samu shanyewar ɓarin jiki gida suka dawo da ita bisa shawarar doctor bayan anyi treatment ɗinta yanda ya kamata. Ummah dai an tafi, dan babu abinda ke motsi a ɓarinta na dama sai ido da kai. Amma daga wuyanta zuwa yatsanta ma ƙafa komai cak. Sai ɗayan ɓarin haggun kawai. Babu abinda take sai hawaye. Dan bakin ma idan tayi magana ba'aji sosai sai yawu ke fita babu ko ƙyawun gani.
Smart da Salim suka tsare Huwaila. Zata musu wani kwana-kwana tasha maruka a hannun Smart. Salim ya rufeta da duka da ƙyar aka tsaida shi saboda lalurar dake a jikinta. Wahalar da tasha yasata faɗin gaskiyar cewar saurayinta ne ya mata lokacin suna tare da Umma a gidan Kawu Jibirin, idan tace ta tafi makarantar islamiyya sai ya ɗauketa a hanya su tafi hotol ko ɗakin abokansa. Ran kowa ya ɓaci Abba harda hawaye yana jama Umma ALLAH ya isa da jin nadama bisa nadama akan aurenta. Dan bai tsira da komai ba sai baƙin ciki da tashin hankali tun daga ƙuruciya har zuwa yau. Garama yanzu da Smart ke ƙoƙarin dawo da su Salim a hayyacinsu. Dan a yanzu haka jira yake a kammala bikin nan ya gyarama Salim shagunansa da suka ƙone. Smart yasa an nemo wanda yayma Huwaila ciki tare da iyayensa. Da farko ya musa harda cewa shi baima taɓa ganin Huwaila ba, sai da Smart yay masa jan ido harda maruka biyu a gaban iyayensa babu ko kunyar idonsu sannan ya faɗi gaskiya, amma yace ai bashi kaɗai bane tana kaima wasu. Huwaila ta sanya kuka da rantsuwa da shi kaɗai take tarayya, hasalima shine ya fara saninta ɗiya mace, tana ma da shedar hakan. Ansha rikici sosai har sai da Huwaila ta kawo recording na wayar da suka dingayi da ta dinga ajiyewa sannan fa shegen yay laushi. Inda aka tsaida magana da zaran ta haihuwa za'a ɗaura musu aure. Sauran ƴamatan gidan kuma ya basu tabbacin nan da wata uku kowacce ta kawo mijin aure in ba hakaba shi zai zaɓo musu. Hakan ya saka iyayen jin kwanciyar hankali. Dan sai ga Mama sarkin ruɗiya yau na sakama Smart albarka. Saboda ba ƙaramin tayar mata da hankali batun cikin nan na Huwaila yay ba, dan itama tana da ɗaya a ɗakinta mai rawar kan tsiyar da giggiwa. Haka ta tasa ƴaƴanta gaba wanda basuyi aure ba tana roƙonsu ALLAH Annabi su taimaka mata su rike mutuncin kansu karsu kasheta tun lokacinta baiyi ba kamar yanda Huwaila ta zama sanadin Ummanta. Sun daiga yanda tarbiyyar ƴaƴan Ammah a gidan ta jawo musu alkairi.....
Samun lafawar ƙurar biki ta bama Smart nutsuwar fuskantar ƴan uwansa. Yayinda ya nutsu wajen nemawa ƴan uwansa maza da matan ma abinyi. Tare da zagaye dangin mahaifiyarsa dana mahaifinsa kaf yay musu alkairai masu tsoka da yaketa samun albarka shida zuri'arsa. Shine har dangin Mama dana Aunty Amarya, dan ita Umma danginta sune dangin Abba sai dai na ɓangaren mahaifiyarta. Gefe ɗaya kuma ya samu damar gina wasu manya-manyan mall guda biyu da kafa business daban-daban. Tare da yin amfani da ƙungiyar Lulu ya tallafama yara da ɗan yawa akan karatu. Masu shaye-shaye a ciki ya kaisu rihab. Dan Nadiya dake ta lallaɓa rayuwarta a yanzu tare da Ummita tsaye suke akan ƙungiyar. A cikin wannan halin bikin Ummita da Usman ya tashi suma. Haka Lulu taita ƙoƙari nan ma akayi komai da ita. Ta kuma bama Nadiya shawara akan ya kamata itama ta samu miji mai irin ciwonta suyi aure tunda yaron data haifa ya rasu. Ranar Nadiya tayi kuka sosai, tare jerama Lulu da Smart har ma da su Uncle Yousuf addu'oi. Dan yanzu ta koma gidansu a dalilin sanya baki da baba Garko yayi a zancen, babu kuma wanda take ganin mutunci da kima yanzu a duniya sama da Lulu da Smart. Amaryar Baba Garko ma ta shigo cikin tawagar masu kula da ƙungiya. Hakama Tajuddeen da a yanzu ya sakama kansa haƙuri game da al'amarin Lulu yana bada gudunmawa. Shima dai an saka bikinsa da ƙanwar amaryar mahaifinsa. Tunda ya lura yarinyar na masifar sonshi mahaifiyarsa da su Baba Garko suka bashi shawarar ya aureta kawai ya rufama kansa asiri, dan yanzu ba gida duka bane zai nema aure a bashi saboda tabon da mahaifinsu ya bar musu a cikin al'umma. Kowa ya zata Dada zataƙi. Sai gashi babu ko ja'in ja ta amince harda bada gudunmawar ta...
_______★
Hutun Smart ya ƙare zasu koma England sai dai Ammah tace bada Lulu ba. Dan a gida zata haihu wannan karon itama taga gatan da kowace ɗiya ke samu. Ba haka yaso ba dan haka ya dinga fushi. Ammah ko ta tattarashi ta watsar da faɗin yama fashe mana. Mawaddat ce dai babu inda zataje sai ta haihu tunda watan gobe ne haihuwar. Har kawo zancen AA zai shiga makaranta yayi amma Ammah tayi mirsisi da shi. Sai ma tace masa ya tafi da AA ɗin su zauna Lulu ce dai babu inda zataje. Babu yanda ya iya haka ya tattara rai a jagule ya tafi Lulu na faman masa dariya da gwalo. Dan ita farin ciki take da barinta a wajen Ammahn ta. Tana so da ƙaunar baiwar ALLAHr nan a rayuwar. Itama kuma Ammahn na nuna mata ƙauna mai tsayawa a rai. Idan ka gansu tamkar ba surukai ba. Wannan soyayyar tasu daga ALLAH ce kawai za'ace..
Bayan wucewar Smart babu jimawa aka ƙarasa masa ginin katafaren gidansa da mutane keta magana akansa duk da basu san kona wanene ba. Dan hatta Lulu bata sani ba. Ammah da Abbah da Ahmad da Coach sai Uncle Yousuf ne kawai suka san gidan na Smart ne. Kamar abinda Lulu ke jira kenan ta fara naƙuda. Hankalin su Ammah ya tashi dan cikin dare al'amarin ya tasar mata. Gashi Ammah ta fahimci Lulu nada masifar tsoro ga kuma ta da Naƙuda mai wahala. Dole suka wuce asibiti a daren nan bakunansu da addu'a. A wannan karon ma dai cs aka
Showing 285001 words to 288000 words out of 294165 words
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣2️⃣
.......A ɓangaren Garko family ma dai ALLAH ya bama Dada da Baba Garko lafiya har sun dawo gida Nigeria. Sai dai Dada ƙarfin hali kawai take. Gaba ɗaya ta zama wata shiru-shiru. Sai da kaga ta tasa hoton Maman Mawaddat da na Sultana gaba tana kuka. A yanzu Baba Garko kan zauna ya lallasheta da mata nasiha. Hakama amaryarta takan ƙyautata mata duk dan dai ta kwantar da hankalinta, haka ma ƴaƴanta basa gajiyawa wajen tattalinta saboda an tabbatar musu zuciyarta idan har ta buga shike nan kuma. Dan haka kowa baya wasa da al'amarinta. Lulu kanta ba'a barta a baya ba wajen lallashin Dadan. Dan tana kallonta tamkar Mawaddat ɗin ta ne data rasa. Akoda yaushe cikin yin video call suke da ita....
__________★
Shirye-shiryen bikin Maryam ya kankama sosai, dan takowane ɓangare shiri kawai akeyi. Ana saura sati guda ɗaurin aure Smart da iyalinsa suka iso gida Nigeria. Ƙasar da yay kewa. Tarba ya samu maiban mamaki da ga al'ummar ƙasar tasa da ƴan uwa da abokan arziƙi. Dan da ƙyar suka iya baro airport sai da taimakon jami'an tsaro. Yayinda ya samu rakkiyar masoya har gida. Anan ma ya samu yaran anguwa da iyaye suna jiransa. Sai ga Smart na hawaye dan farin ciki. Ya tabbatar da mutane rahama ne. Duk wanda yace maka yana sonka da ƙaunarka ya gama maka komai a rayuwa. (Ya ALLAH ka barmu da masoyanmu. Duk wanda ya somu dominka ya rabbi shima ka soshi shi da zuri'arsa baki ɗaya. ❤️❤️❤️😘 wannan nakune masoyan alkairi 🙏).
Anan ɗin ma dai da ƙyar ya samu suka shiga gida saboda yanayin Lulu. Dan cikinta yayi girma sosai wannan karon fiye dana AA. Ga kuma kullum cikin laulayi take dan tunda ya fara tsufa bata da wani ishashen lafiya. Duk da dama dai haka taketa fama tun da cikin ya shiga watanni biyar. Babu kunya yau kam Smart ya rungume Ammah da Abbah a gaban jama'ar gidansu. Ya kuma rungume ƙannensa su Mubarak da yasan suna matuƙar kaunarsa. Kannensa mata nata kawo masa gaisuwar girmamawa harma da wanda suka girmesa kamar wani sarki. Tunda Ummah ta leƙo sau ɗaya ta gansa bata sake maimaitawa ba, ɗaki ta shige tana sakin wani irin kuka mai ƙona zuciya. Smart ya koma kamar wani baƙin bature. Ko makaho ya laluba yasan kuɗi da jin daɗin rayuwa da ɗaukaka sun zauna sai dai fatan gamawa da rayuwa lafiya.
Shiko sanin bata da isashiyar lafiya har ɗaki yaje ya gaisheta tare da duk sauran matan Abba har aunty Amarya. Ita kanta Mama a ruɗe take, kawai dai tana ƙoƙarin dannewa ne kar ai mata irin kallon da akema Umma. Dan ƙamshin Smart kawai rikita zuciya yake. Saboda kowa ya gama sanin hankalin Ummah fa a tashe yake. Wasu a cikin yaranta har abun nata na basu kunya.
Bayan yaci ya sha daga girkin mahaifiyarsa data musu girki da kanta dan Lulu bata iya cin komai sai kunun gyaɗa. Shi kaɗai taima sha na hauka dan motsi kaɗan taji yunwa yanzu. AA na hannun iyayensa wannan ya ɗauka ya ba wancan haka aketayi. Yaron birgesu yake gashi fes kamar ka lashe, komai na ubansa bai bari ba. Zuwa yanzu ya ɗan fara magana sai dai ba gane abinda yake nufi akeyiba ma sosai. Kwanciya Lulu tayi danta hutama ranta. Yayinda su Ammah da Smart suka buɗe shafin hira dan Gwaggo Sa'adah na gidan da su aunty Bilkisu da Hawwah. Daga baya sai ga Abba shima ya shigo duk da su Smart ɗin sun je sun gaishesa...
Washe gari aka kawo lefen Maryam daga gidan su Ahamd. Lefe ne na nunama tsara dan an nuna dukiya kam babu ƙarya. Ƙwaƙwalwar Umman neman zautuwa takeyi. Dan kasa jurewa tai yau ma sai kulle kanta tai a ɗaki. Ga dangin Ammah dana Abba nata zuba mata habaici batare da sun duba cewa ƴar uwarsu bace ba. Anyi komai cike da girmama juna da mutuntawa dan suma sun bada tukuyci mai tsoka. Bayan wucewar ƴan kawo lefe Smart ya ɗauki Lulu da AA da Asma'u suka nufi gidan su Lulun. Daddy da su Amrah sunyi farin cikin ganinta, duk da kuwa jiya harda su a ƴan tarbarsu. Basu koma gida ba sai dare. Mommy ma taji daɗin ganinsu. Tana ta tsokanar AA. Hira sosai Smart suka sha da Daddy, dan anan suka yini sai bayan sallar azhar suka nufi gidan Uncle Yousuf. Anan ɗin ma dai hirar aka sha, samun su twins da sukai can yasa Smart da Lulu fahimtar akwai wani abu tsakanin Hussain da Asma'u. Hakan yama Lulu daɗi sosai ita da Smart. Basu bar nan ba sai bayan la'asar. Sun nufi gidan Baba garko inda suka ƙarasa yinin. Itama dai Dada harda kukanta dan ta fahimci dai waɗan nan ma'aurata kainuwa ne dashen ALLAH. Sannan FURAR DANƘO ne damasu ace za'asha farau-farau abune mai wahalar gaske. Jiki luɓus suka koma gida dan Lulu tayi laushi. Ammah taita ma Smart faɗan miyasa bai barta acan ba yaketa yawo da ita haka. Shi dai murmushi kawai yayi yana kallon Lulu dake masa gwalo ƙasa-ƙasa. Washe gari yana tare da Ahmad da Coach, acan ya yini sukasha hirarsu da ubangidansa. Bai dawo gidan ba sai dare dan har Malam na Yakasai yaje ya gaidar bai manta alkairi ba nan ma....
Al'amarin biki ya kankama sosai, Smart ya haɗama amarya gidan mijinta da kaya na kece raini da nunawa tsara. Yayinda aka fara events da aka shirya wanda ya kafa ya tsare ya hana Lulu zuwa ko ɗaya saboda yanayinta. Daga ƙarshe ma da yaga hayaniyar gidan na mata yawa sai ya dinga janyeta zuwa masaukinsa. Acan suke kwana sai da safe ya dawo da ita nan ta yini cikin danginsa. Lulu ta amsa suna matar babban Yaya. Dan komi aka buƙata bata jin ko ɗar zata fidda a jakarta ta bada batare da tabi takan mijinta ba. Sai wasu a ƴan uwa suka fara tsogumin ai ta kankane komai sai abinda taso take badawa. Tun anayin ƙus-ƙus har zancen ya fito fili yakai kunnen su Ammah. A take Ammah ta nuna ɓacin ranta akan hakan, yayinda Smart da shima ransa ya ɓaci ya basu amsa da ai kai da kaya duk mallakar wuyane. Shi kansa a ƙarƙashin say ɗin Lulun yake bama dukiyarsa ba. Ballema ko sisi bai bata ba duk abinda suka nema ta basun kuɗinta ne. Wannan zantukan nasa yasa jikunansu yin sanyi, dama dai cikin dangin Abba ne da ƴaƴan Mama da wasu ana Ummah masu gulmar. Sai aka koma ƴar sinne kawunan jin kunya.
Ana gobe ɗaurin aure akai dinner. Ita kaɗai Smart ya bari Lulu ta halarta. Shima kuma yaje. Dan tare sukaje tana gefensa riƙe da hannunta AA daya maƙale masa da ga hannun su Abdull ɗauke a kafaɗarsa. Sun isa a lokacin da kusan kowa ya gama zuwa. Dan har biki ya fara. Dan haka gaba ɗaya attention na mutane ya dawo kansu musamman yanda mc ke kwarzanta wanene Smart ɗin da matsayinsa a wajen ango Ahmad da ma Amarya Maryam. Nan fa dangin Ahmad ɗin masu ɗan jijji da kai irin na dangin miji suka shiga hankalinsu. Dan sun fahimci abinda sukeji basu yarda ba ashe gaskiya ne. Dan kamanin Smart da Maryam a bayyane suke. Nan fa ƴammata suka ruɗe da ganin matashin ɗan ƙwallon da duniya ke yayi mai ji da kuɗi. Sai dai Lulu dake fama da cikinta tana nane da abunta. Duk yarinyar data kama tana kallar mata miji kuwa zatasha harara. Shiko Smart nata ƙunshe dariya dan yana sane da matar tasa. Amarya da ango sunsha ƙyau har sun gaji, yayinda bakin Ahmad yaƙi rufuwa. Liƙi sosai daya ruɗa hall ɗin Lulu da Smart suka dinga zuba musu harda AA da Ahmad ya ɗaga sama yana sumbatarsa da faɗama mc cewar a sanar kowa ya sani wannan surukinsa ne. In sha ALLAH yanda suka taru anan bikin aurensu haka wataran zasu taru bikin auren AA da matar da zasu haifa masa. Wannan zance na Ahmad yasa kowa dariya a wajen tare da addu'ar ALLAH ya tabbatar da hakan. Ba'a tashi ba Smart ya ɗauki matarsa suka gudu dan taje ta huta saboda bata jimirin hayaniya yanzu....
Washe gari aka ɗaura auren Ahmad Rabi'u Ƙoƙi, da amaryarsa Maryam Mika'il Mawashi akan sadaki naira dubu ɗari biyat bayan sakkowa da ga massalacin juma'a. Ɗauri aure ne daya samu halartar manyan mutane a dalilin gidajen biyu. Tare da ɗunbin masoyan Smart da ga jihohi daban-daban. Anyi walima da yamma. Zuwa bayan isha'i aka shirya kai amarya ɗakinta. Yayinda kaf yayunta harda su Sadiq ƙanana suka taru a falon Abba domin mata nasiha. Tasha kuka sosai har muryarta na dishewa. Dan yayun nata sun mata nasiha mai ratsa zuciya. Bayan an kammala Smart da Salim da Zubair da Kamal suka sakata a danƙarereiyar motar da Smart ya siya mata suka kaita gidan mijinta da rakkiyar mata iyaye guda biyar kawai. Da zasu taho ne ta rungume Smart tana kuka da jera masa godiya. Murmushi yayi a hankali yana mai lumshe idanunsa kafin ya ɗagota a jikinsa. Fuskarta ya riƙe cikin hannayesa yana girgiza mata kai alamar tayi shiru. Daga haka ya shiga gaya mata daɗaɗan kalaman da saida ta saki murmushi. Sannan ya kamo hannun Ahmad ya saka masa nata a ciki ya ɗan bubbuga kafaɗarsa ya fice yana maida hawayen da suka cika masa ido shima. Smart na matuƙar so da ƙaunar ƴan uwansa matuƙa a rayuwa. Akwai shaƙuwa sosai a tsakaninsu duk da bawani sakewa yake da su ba. Dama sauran duk sun fita harma sun shiga mota. Yana zuwa shima ya shiga kawai suka wuce........✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣3️⃣
.......Washe garin da aka miƙa Maryam gidan miji Mawashi family suka tashi da tashin hankali biyu. Na farko shine gano Huwaila ɗauke da cikin shege na watanni biyar. Tashin hankalin bayyanar wannan ciki kuma yasa Ummah yanke jiki ta faɗi. Inda faɗuwar tata ta zama sanadin samun paralysis. Smart na masaukinsa yana barcin gajiya Lulu a jikinsa ya samu kira da ga Salim. Dole ya shirya ya nufo gidan da Lulu data dage bazai barta ita kaɗai ba. Sun sami gida a rikice. Ko Ummah ba'a ɗauka ba zuwa asibiti sai da yazo ya fara faɗa. Bayan ankai Ummah asibiti suka samu tabbacin ta samu shanyewar ɓarin jiki gida suka dawo da ita bisa shawarar doctor bayan anyi treatment ɗinta yanda ya kamata. Ummah dai an tafi, dan babu abinda ke motsi a ɓarinta na dama sai ido da kai. Amma daga wuyanta zuwa yatsanta ma ƙafa komai cak. Sai ɗayan ɓarin haggun kawai. Babu abinda take sai hawaye. Dan bakin ma idan tayi magana ba'aji sosai sai yawu ke fita babu ko ƙyawun gani.
Smart da Salim suka tsare Huwaila. Zata musu wani kwana-kwana tasha maruka a hannun Smart. Salim ya rufeta da duka da ƙyar aka tsaida shi saboda lalurar dake a jikinta. Wahalar da tasha yasata faɗin gaskiyar cewar saurayinta ne ya mata lokacin suna tare da Umma a gidan Kawu Jibirin, idan tace ta tafi makarantar islamiyya sai ya ɗauketa a hanya su tafi hotol ko ɗakin abokansa. Ran kowa ya ɓaci Abba harda hawaye yana jama Umma ALLAH ya isa da jin nadama bisa nadama akan aurenta. Dan bai tsira da komai ba sai baƙin ciki da tashin hankali tun daga ƙuruciya har zuwa yau. Garama yanzu da Smart ke ƙoƙarin dawo da su Salim a hayyacinsu. Dan a yanzu haka jira yake a kammala bikin nan ya gyarama Salim shagunansa da suka ƙone. Smart yasa an nemo wanda yayma Huwaila ciki tare da iyayensa. Da farko ya musa harda cewa shi baima taɓa ganin Huwaila ba, sai da Smart yay masa jan ido harda maruka biyu a gaban iyayensa babu ko kunyar idonsu sannan ya faɗi gaskiya, amma yace ai bashi kaɗai bane tana kaima wasu. Huwaila ta sanya kuka da rantsuwa da shi kaɗai take tarayya, hasalima shine ya fara saninta ɗiya mace, tana ma da shedar hakan. Ansha rikici sosai har sai da Huwaila ta kawo recording na wayar da suka dingayi da ta dinga ajiyewa sannan fa shegen yay laushi. Inda aka tsaida magana da zaran ta haihuwa za'a ɗaura musu aure. Sauran ƴamatan gidan kuma ya basu tabbacin nan da wata uku kowacce ta kawo mijin aure in ba hakaba shi zai zaɓo musu. Hakan ya saka iyayen jin kwanciyar hankali. Dan sai ga Mama sarkin ruɗiya yau na sakama Smart albarka. Saboda ba ƙaramin tayar mata da hankali batun cikin nan na Huwaila yay ba, dan itama tana da ɗaya a ɗakinta mai rawar kan tsiyar da giggiwa. Haka ta tasa ƴaƴanta gaba wanda basuyi aure ba tana roƙonsu ALLAH Annabi su taimaka mata su rike mutuncin kansu karsu kasheta tun lokacinta baiyi ba kamar yanda Huwaila ta zama sanadin Ummanta. Sun daiga yanda tarbiyyar ƴaƴan Ammah a gidan ta jawo musu alkairi.....
Samun lafawar ƙurar biki ta bama Smart nutsuwar fuskantar ƴan uwansa. Yayinda ya nutsu wajen nemawa ƴan uwansa maza da matan ma abinyi. Tare da zagaye dangin mahaifiyarsa dana mahaifinsa kaf yay musu alkairai masu tsoka da yaketa samun albarka shida zuri'arsa. Shine har dangin Mama dana Aunty Amarya, dan ita Umma danginta sune dangin Abba sai dai na ɓangaren mahaifiyarta. Gefe ɗaya kuma ya samu damar gina wasu manya-manyan mall guda biyu da kafa business daban-daban. Tare da yin amfani da ƙungiyar Lulu ya tallafama yara da ɗan yawa akan karatu. Masu shaye-shaye a ciki ya kaisu rihab. Dan Nadiya dake ta lallaɓa rayuwarta a yanzu tare da Ummita tsaye suke akan ƙungiyar. A cikin wannan halin bikin Ummita da Usman ya tashi suma. Haka Lulu taita ƙoƙari nan ma akayi komai da ita. Ta kuma bama Nadiya shawara akan ya kamata itama ta samu miji mai irin ciwonta suyi aure tunda yaron data haifa ya rasu. Ranar Nadiya tayi kuka sosai, tare jerama Lulu da Smart har ma da su Uncle Yousuf addu'oi. Dan yanzu ta koma gidansu a dalilin sanya baki da baba Garko yayi a zancen, babu kuma wanda take ganin mutunci da kima yanzu a duniya sama da Lulu da Smart. Amaryar Baba Garko ma ta shigo cikin tawagar masu kula da ƙungiya. Hakama Tajuddeen da a yanzu ya sakama kansa haƙuri game da al'amarin Lulu yana bada gudunmawa. Shima dai an saka bikinsa da ƙanwar amaryar mahaifinsa. Tunda ya lura yarinyar na masifar sonshi mahaifiyarsa da su Baba Garko suka bashi shawarar ya aureta kawai ya rufama kansa asiri, dan yanzu ba gida duka bane zai nema aure a bashi saboda tabon da mahaifinsu ya bar musu a cikin al'umma. Kowa ya zata Dada zataƙi. Sai gashi babu ko ja'in ja ta amince harda bada gudunmawar ta...
_______★
Hutun Smart ya ƙare zasu koma England sai dai Ammah tace bada Lulu ba. Dan a gida zata haihu wannan karon itama taga gatan da kowace ɗiya ke samu. Ba haka yaso ba dan haka ya dinga fushi. Ammah ko ta tattarashi ta watsar da faɗin yama fashe mana. Mawaddat ce dai babu inda zataje sai ta haihu tunda watan gobe ne haihuwar. Har kawo zancen AA zai shiga makaranta yayi amma Ammah tayi mirsisi da shi. Sai ma tace masa ya tafi da AA ɗin su zauna Lulu ce dai babu inda zataje. Babu yanda ya iya haka ya tattara rai a jagule ya tafi Lulu na faman masa dariya da gwalo. Dan ita farin ciki take da barinta a wajen Ammahn ta. Tana so da ƙaunar baiwar ALLAHr nan a rayuwar. Itama kuma Ammahn na nuna mata ƙauna mai tsayawa a rai. Idan ka gansu tamkar ba surukai ba. Wannan soyayyar tasu daga ALLAH ce kawai za'ace..
Bayan wucewar Smart babu jimawa aka ƙarasa masa ginin katafaren gidansa da mutane keta magana akansa duk da basu san kona wanene ba. Dan hatta Lulu bata sani ba. Ammah da Abbah da Ahmad da Coach sai Uncle Yousuf ne kawai suka san gidan na Smart ne. Kamar abinda Lulu ke jira kenan ta fara naƙuda. Hankalin su Ammah ya tashi dan cikin dare al'amarin ya tasar mata. Gashi Ammah ta fahimci Lulu nada masifar tsoro ga kuma ta da Naƙuda mai wahala. Dole suka wuce asibiti a daren nan bakunansu da addu'a. A wannan karon ma dai cs aka
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96 Chapter 97Chapter 98Chapter 99