kuwa kana fatan gamawa da duniya lafiya Dad. Ace iyayenka ne abokan gabarka. In dai dan ni kakeyi toka ajiye dan nikam dai na haƙura da Mawaddat koda ace sonta zai zamar min ajalina. Duk ƴan uwanka gasu nan har wanda basa ƙasar kai kaɗai ne ka fita zakka a cikinsu saboda son zuciya. Idan ta mutu sai kazo zaman gaisuwa ai” ya faɗa yana yanke kiran wani irin kuka mai cin rai na kufce masa...

*_★UK★_*

    .....A dalilin wayar Tajuddeen da mahaifinsa su Lulu suka san halin da ake ciki. Domin suna tsaka da ganin zaman meeting ɗin Alh. Sulaiman da abokansa ta direct camara ɗin su. Hankalin Lulu ya tashi matuƙa, dan koma minene ya faru Dada ba abar yardawarta bace ba. Kuka ta fara cikin tashin hankali ta shiga neman layin ƴan uwa. Da kyar ta samu Uncle Amin ya ɗaga. Cikin kuka take faɗin yanzu nan Dada na'a irin wannan halin amma babu wanda ya faɗa mata. Lallashinta Uncle Amin ɗin ya farayi akan ta kwantar da hankalinta tai mata addu'a daga inda take. Amma ina Lulu taƙi saurarensa. Shima Smart ɗin ta matuƙar tayar masa da hankali, dole ya saya mata ticket dan bazai juri ganinta a haka ba. Sai dai ita kaɗai zata taho banda AA. Ta barsa wajen Iya Tabawa da aunty Bilkisu da har yanzu bata kammala ganin likita ba duk da tana a gida lokaci-lokaci dai take zuwa ana dubata asibitin........✍️



_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥



*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲




  🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗



           𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻


𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣7️⃣




.......Uncle Yousuf da kansa yaje ɗaukar Lulu airport. Da ga airport ɗin kuma asibiti suka wuce kai tsaye. Ba ƙaramin girgiza zuciyarta tayi da ganin kowa da kowa na asibitin ba. Ashe ƴan Saudiyya ma har sun ƙaraso. Kasa haƙuri tai sai da ta leƙa Dada ta window. Dan an hana kowa shiga wajenta Baba Garko ne kawai ya shiga bayan likitoci sun sami kanta da ga aman jinin da take yi. Kuka sosai Lulu keyi da ya sake ɗaga hankalin duk wanda ke a wajen. Uncle Taheer Auta ne ya kama hannunta suka bar wajen, da ga gefe ya zaunar da ita yana lallashinta akan ta daina kuka addu'a Dada ke buƙata a yanzu. A hakama an samu kanta ba kamar da safe ba. Wannan ɗan lalashin da autan Dadan ya mata ne ya ɗan saka mata nutsuwa kaɗan ta rage kukan da take yi. Lokacin da zasu wuce gida tace ita a barta anan zata kwana. Hajiya Turai mahaifiyar Tajuddeen ce tai ƙarfin halin cemata, “A'a Mawaddat kema kulawar kike buƙata ai a wannan halin da kike ciki. Ga tafiya mai nisa kinyo”. Da yawan ahalin wannan family sun san ALLAH ya bama Hajiya Turai baiwar gane ciki koda ƙarami ne, dan haka kowa ya fahimci abinda take nufi akan Lulu ballema duk mai lura yaga Lulu yasan tana da ciki saboda illahirin halittun jikinta sun nuna hakan duk da kuwa akwai jin daɗi da samun kwanciyar hankali. Abinda bata sani ba hatta Iya Tabawa ta jima da fahimtar tana da ciki, tayi gum da bakinta ne kawai har ya bayyana kansa. Ita kanta aunty Bilkisu cikin kokwanto take magana ce kawai batayi ba. Amma har so tai ta tseguntama Ammah da ga baya kuma dai tai shiru dai. Lulu dai ba fahimtar Hajiya Turai tayi ba, sai dai babu yanda zatai ta yarda ta bisu. Kasancewar motar Hajiya Turai ɗin ta shiga sai kawai ta wuce da ita can gidansu (Gidan Alh Sulaiman kenan).

        Alh. Sulaiman da tun wayarsa da Tajuddeen ransa ke'a ɓace yana zaune labarin zuwan Lulu Nigeria ya sameshi. Baida niyyar zuwa asibitin duk da baƙaƙen maganganun da ɗan cikin nasa ya faɗa masa sun kartar masa zuciya amma jin abar farautarsa a kusa da shi ya sashi niyyar zuwa. Sai dai bai baro Companyn nashi ba sai dare sosai saboda bada ƙafa. Sun riga sun gama shirya yanda zasu sace Lulu shida yaransa. Dan haka kai tsaye asibitin ya nufo. Sai dai ya samu kowa ya tafi sai ƙanwar Baba Garko kaɗai da ke tare da Dada. Inna Sadiya nada labarin komai na tsakanin Sulaiman da iyayen nasa, dan haka ta kallesa sheƙeƙe ta watsar, gaisuwar tasa ma sama-sama ta amsa masa. Duk yanda yaso jin wani abu daga gareta bata kulashi ba. Dole ya kama gabansa yana jan tagwayen ƙwafa da jin kamar ya make banza ya wuce. Yana fitowa yay kiran yaronsa Malami. Ya sanar masa su rabu zuwa gidan Daddy da Uncle Yousuf dan Lulu bata asibitin. Sun amsa masa da girmamawa, duk da sun san tsaron dake zagaye da gidajen daya faɗa ɗin, daga haka ya wuce gidansa shima. Koda ya iso bai nema matarsa ba kamar yanda itama ba shiga sabgarsa takeba a yanzun, dan tace zaman ƴaƴanta kawai takeyi ita kam dan ya gama fita mata a rai kasancewar amaryarsa ta sanar mata komai. Dan bayan dawowarta ƴaƴanta mata yayun Tajuddeen da ita sunje gidan su amaryar tasa domin lallashinta itama ta dawo ta nuna musu ai itakam tabar gidan nan har abada. Da suka matsa ne taja Hajiya Turai gefe ta sanar mata komai tare da nuna mata video ɗin nan. Hankalinta ya tashi matuƙa, dan itace ma ta bata shawarar ta kaima su Baba Garko videon inba haka ba mijin nasu zaibi duk wata hanya ya kwacesa a hanunta. Ba ƙaramin ruɗani Hajiya Turai ta shiga ba a week ɗin da ya gabata, da ƙyar ta iya tausar zuciyarta ko yaranta bata sanarmawa ba har yanzu.
        Zuwa cikin dare jikin Lulu ya ɗume da zazzaɓi, kasancewar kwana biyun nan haka take fama sai bata damu ba. Ta dai sha magani ta kwanta duk da tana jin kewar mijinta ta taushi zuciyarta, sai gabannin asuba zazzaɓin ya saketa. Tana idar da salla kasa haƙuri tayi ta ɗora layinta na Nigeria akan waya. Smart ta fara kira. Bugu ɗaya ya ɗaga mata. A tare suka sauke nannauyan numfashi. Kafin a hankali ya fara furta, “Kin san ko yanda kika bar zuciyata cikin barazana da tashin hankali Baby luv. Tunda kika sauka nake jiran kiranki amma shiru har na fara jin nauyin yawan kiran da nakema Daddy da Uncle Yousuf.”
        “Kayi haƙuri”.
  Ta furta a hankali. Ajiyar zuciya ya sake saukewa da faɗin, “Ya zanyi, na haƙura. Ina dai fatan babu wata matsala ko? Dan wlhy gaba ɗaya na kasa nutsuwa duk da nasan wawan baiyi zaton kina gidansa ba”.
    Murmushi Lulu tayi har yana iya jiyo sautinsa. Cikin ƙara tausasa harshe ta ce, “Bayan ka bashi ƙafa taya zai iya gano ka. Dolene na bama wanda ya saka maka suna Smart ƙyauta gaskiya. Mutum yana nemana ruwa a jallo amma ka turoni gidansa na kwana kuma. Sannan kada ka manta kawuna ne kake cema wawa”.
         Ƙaramar dariya yayi shima. Ya ce, “ALLAH sarki masu kawu yi sorry. Sannan banda wata mafita sai hakan ai. Dan nasan bazai taɓa kawoma ransa zaki zo gidansa ki kwana ba. Yanzu dai sai kiyi taka tsan-tsan kuma.”
     “In sha ALLAHU mijina. Jiya gaba ɗaya kewarka ta hanani isashen barci”.
               “Uhm kamar da gaske. Ni ban san daɗin baki. Ina Aliyu yaga wannan matsayin. Ke dai kawai kice tsoro ya hanaki barci kina a gidan dodoki”.
          “Oh hakama zakace ko? Shikenan ai zan rama. Bazan ma dawo ba sai bayan wata tara kama kanka”.
     Dariya sosai yakeyi da faɗin, “Haba Baby luv ki tausayamin mana. Ni kaina kin ganni nan yanzu haka nama kasa kwanciyar sai lissafi nake da kallon hotunanki kawai. Na gayyato Baban Ammah ya tayani kwana ya addabeni da ɓuruntu.”
          Cikin dariya ta ce, “Kai miya kaika wannan gangancin siyen gida a sama.”
      “To yana iya kewar Mamansa ta isheni ne. Ni da ƙyar ma idan zan iya haƙuri ban taho Nigeria ɗin nan ba”.
   Idanu ta waro sosai kamar tana gabansa. Ta ce, “Are you serious zaka iya barin wannan kwallon ka taho Nigeria?”.
        “Humm yarinyar nan kina wasa da Aliyu ko? Zan baki mamaki”.
    “A'a A'a nagode basai ka bani ba. Ai nasan zaka aika wlhy yi zamanka na yafe. Nima ba jimawa zanyiba ai. Yanzu dai ina son naje naga Ammah yaya za'ayi?”.
    “Kefa rigimarki yawa gareta Mrs Mawashi. Keda ake ɓoyonki ina kuma zaki je yawo?”.
            “Zuwa wajen uwata ne yawo. To nidai kasan yanda zakai dani gaskiya”. Ta faɗa cikin shagwaɓa har yana iya jiyo sautin yanda take buga ƙafa ƙasa.
       “Kirufamin asiri Baby luv nayi barcina lafiya, kinga dai na sakama raina haƙuri tunda kika taho ko kuka banyi ba”.
    Sosai Lulu take dariya. Ta ce, “Kuka fa?”.
“Eh mana, na dai zama kalar tausayine kawai ko wanka yau ma bazanyiba. To in nayi wazan mawa baƙya kusa”.
Dariya ta sake ƙyalƙyalewa da shi. Smart ɗinta kenan Zuma ga zaƙi ga harbi. Duk wanda kake buƙata za'a sayar maka akan farashin da ya dace. Sun jima suna hirarsu kafin ta tashi tayi shirin zuwa asibiti. Dan bazata iya sake komawa barci ba....

      ★Yaran Alh. Sulaiman nacan sun kasa sun tsare a tituna jiran fitowar Lulu da ga gidansu ko gidan Uncle Yousuf. Anan ko su har sun fice gidan Alh. Sulaiman sai fitar motar matarsa ya jiyo. Ƙwafa yayi dan yayi alwashin koya mata hankali itama dan yasan ita ke zuga masa yara suna mai rashin mutunci. Ranar matan sun masa akan dawowarta gidan. Jiya kuma Tajuddeen ya masa akan Dada. Bai damu da fitar tata ba dan yasan asibiti ta wuce. A asibiti sun samu jikin Dada yau dai Alhmdllh, da sauƙi irin na malam bahaushe da ake faɗi. Amma dai har yanzu bata gane komai, sai ambaton sunan Sulaiman da take a hankali hawaye na ziraro mata. Duk wanda ya shiga dubata sai ya fito da mamakin yanda ta damu da al'amarin yayan nasu Sulaiman haka, bayan rashin mutuncin da yake zuba musu salo-salo. Sai da ta koma barci ne Baba Garko ya ce iyayen su sameshi gaba ɗaya a gida. Ganin haka sai itama Lulu tai kiran Smart kawai akan zuwa wajen Ammah. Sai da yay ɗan jimmm sannan ya amsa mata da “Naga dai kin matsa da ganin Ammahn nan, ɗan bani 10minut haka”.
       Baki ta murguɗa masa tamkar tana gabansa....


      *_GARKO HOUSE_*

     Ƴaƴansa ne gaba ɗaya. Alh. Sulaiman da wanda suka rasu biyu mahaifiyar Lulu da Sultana ne kawai babu. Sunyi kusan zaman mintuna huɗu kafin ya fito. Bayan yakai zaune suka sake gaishe da mahaifin nasu. Da kai ya amsa musu yana gyara zama dan zuciyarsa sam babu daɗi. Sai da ya gama ƙare musu kallo ɗaya bayan ɗaya kafin yay gyaran muryar da ta sakasu sake maida hankalinsu garesa.
       “Na taraku anan ne a dalilin abinda yay sanadin kwanciyar mahaifiyarku asibiti duk da ni har yanzu ban san minene ba shiyyasa na buƙaci ganinku mu gani tare dan zata iya yiwuwa nima na tsinta kaina a yanayin da yafi nata ma...” cikin tashin hankali da ruɗani duk suke kallonsa. Bai damu ba ya cigaba da faɗin, “Nasan wasunku sun san rikicin dake tsakanin ɗan uwanku da matansa wasu basu sani ba. A watannin da suka gabata rikicin da bamu san tushensa ba ya ɓarke a tsakanin Sulaiman da matansa su dukansu har suka wuce gida. Sai daga baya uwar ƴaƴansa ta dawo amaryar da al'amarin yafi tsamari a kanta taƙi ta koma. Na barsu ne naga iya inda abin nasu zai kai sai kuma gashi jiya ta samemu anan gida. Flash drive ta kawo mana ta tace shine sanadin rikicin nasu. Da ga haka batai mana wani ƙarin bayani ba ta tafi. Bayan wucewartan ne mahaifiyarku tazo ta ɗauki Flash ɗin ta wuce da shi sai mai aikinta ta isarmin da saƙon gata can ta faɗi babu rai. Duk abinda zai saka mahaifiyarku a wannan mummunan yanayin bazai kasance mai sauƙi ba. Shiyyasa tun jiya na kasa dubawa ni kaɗai na zaɓi mu duba tare da ku”. Ya ƙare maganar yana jawo tab ɗin Dada da har yanzu flash ɗin ke a jiki. kusa da shi duk yay musu nunin su dawo. Haka suka zauna wasu kusa da shi a ƙasa wasu a kujera. Babu wanda zuciyarsa bata kaɗa ba a lokacin da fuskar marigayiya Mawaddat ta bayyana. Kafin sukai karshen videon babu wanda jikinsa baya rawa a cikinsu, ga hawaye duk ya cika musu idanu. Auta da yafi kowa shaƙuwa da Sultana a gidan baima san sanda ya fashe da kuka ba tamkar ƙaramin yaro. Kasa jurewa Baba Garko yayi ya miƙe jikinsa na karkarwa. Sai dai dole sukai saurin riƙosa saboda hajijiya dake neman zubar da shi a ƙasa, shima sai kawai ya fashe da kuka. Kukan mahaifin nasu ya sake tayar musu da hankali. Suma duk suka fara sharar hawaye..........✍️


_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥



*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲




  🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗



           𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻


𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣8️⃣




.........Kiran Smart ya saka Lulu tashi ta koma gefe. Kafin ma tace wani abu ya furta, “Akwai matsala fa Baby luv. Dan Kawunki ya baza yaransa sosai nemanki. Fitarki a asibin nan ma inaga sai da jami'an tsaro”.
        Murmushi Lulu tai har yana iya jiyo sautinsa. Ta wawwaiga gefenta, tabbatar da babu kowa a kusa da ita cikin sake ƙasa da murya ta ce, “Karka damu zan tafi yanzu. Ka turo min address na wajen kawai kai dai”.
    “Kin san mi kike faɗa kuwa. Taya zaki fita a gaɓar da wannan mara imanin ke nemanki ruwa a jallo. Ayanzu haka asibitin yake shirin tahowa dan ya samu tabbacin kina a ciki. Ga Uncle Yousuf nan zuwa shi da Daddy ma”.
             “Ka kwantar da hankalinka zamu wuce plan E ne yanzu a kansa”.
      “What! Plan E fa?. No no no Mawaddat. Bakya ganin halin da tsohuwar nan take ciki. Mu rushe plan E ma kwata-kwata bashi da amfani”.
      “Shiko keda amfani musamman a wannan gaɓar Mr A. Dan babu abinda ya rage mana kuwa sai plan E ɗin. Dada ta riga taga video, shine ma dalilin kasancewar ta a wannan halin. A yanzu haka Grandpa da Uncles suna zaman meeting kuma nasan duk a kansa ne. So kaga abinda ya rage kawai mu ƙarasa sauran aikin. Dan haka yanzu zan saki....”
       Da sauri ya ce, “Maw....” kafin ya ma ƙarasa sunan nata ta yanke wayar. Dan zuciyarta gaba ɗaya ta riga da ta gama kaiwa bango. Duk kiran da yake mata bata ɗaga ba. Cikin abinda baifi mintuna biyar ba ta gama sakin videon a ɓoyayyun shafukan data ɗauki tsawon lokaci tana raino da tara followers. Shafi ne da dama yake taka rawar gani akan harkar fyaɗe da shaye-shaye. Ta ginashi tun lokacin da su Dada suka saceta. Zuwa yanzu shafukan nada ɗunbin mabiya saboda abubuwan da ake posting a cikinsu. Sunasa kuma guda ɗaya ne a instegram, twitter, facebook, TikTok, da website. Sunan wanda ta saka, da abinda ta rubuta a saman video ɗin yasa cikin ƙanƙanin lokaci ya samu makallata masu ɗunbin yawa, kafin kace mi an fara shearing ɗinsa. 
     Yaron Alh. Sulaiman da suka kafa suka tsare a bakin asibiti na jiran fitowar Lulu ne ya fara cin karo da video ɗin, shima wani abokinsa ne ya tura masa yana tambayar ya duba wannan ba ogansa bane. Wani ihun tashin hankali ya fasa batare da ya farga ba. Har takai wanda ke ɗan wuwwucewa ta wajen suna kallonsa. Jiki na rawa ya shige mota. Kira ya dannama Alh. Sulaiman dake tsaka da yin online meeting shima a mota dan yana hanyarsa ta tahowa asibitin ya samu kira da ga Lagos. Sun buƙaci ya ajiye koma mi yake yi zasuyi online meeting na gaggawa. Hakan ya sashi samu waje yay parking hankali a tashe. Suna tsaka da tattaunawar akan batun kayansu ne dai kiran malami ya shigo masa. Bai yi niyar ɗagawa ba sai da yaga kira na biyar na sake shigo masa kuma duk da ga malamin ne. Yasan baya masa irin wannan kiran mafarautan, dan haka zuciyarsa ta bashi lallai akwai matsala. Dole yay excusing kansa ya ɗaga kiran.
       “Oga ka duba na tura maka saƙo ta WhatsApp. Wlhy akwai matsala. Babbar matsala ma kuwa”.
    Ba ƙaramin faɗuwa gaban Alh. Sulaiman yayi ba. Babu shiri ya shiga WhatsApp ɗinsa. Ai kawai sai ga mutumin waya na neman suɓuce masa. Duk da shi ya ga video ɗin amma tashin hankalinsa anan a ina malami ya samesa shi kuma? Ko amaryarsa da flash ɗin ke'a wajensa ce ta tura masa? Kai ina. Rashin samun gamsashiyar amsa ya sashi kiran malami. Muryarsa har harɗewa take wajen tambayarsa a ina ya samu video ɗin. Malami da gaba ɗaya yake a ruɗe ya ce, “Oga bama ni ba, a kowace waya zaka iya samunsa a yanzu. Dan an sake shi ne a wasu shafukan sada zumunta da ke a manyan apps da mutanenmu suka bama amanna. A yanzu haka wani abokina ne ya tura min wannan bayan na turo maka nima na shiga bincike wlhy tako ina videos ɗin trending sukeyi.
Showing 276001 words to 279000 words out of 294165 words