kulawa da san danne damuwa Daddy ya ce, “Ina jinka mike faruwa Auta? Danni duk ka ɗaga min hankali da wannan yanayin naka wlhy.”
Numfashi mai ɗaci Uncle Yousuf yaja da gyara zamansa. Kai tsaye ya ce, “Akan Mawaddat ne.”
“Kuma dai Yousuf? To mi ta sake yi?”. Da ga jin a yanda Daddy yay tambayar kasan ransa a jagule yake. Amma sai Uncle Yousuf ɗin yay biris ya cigaba da faɗin, “Gaskiyar da muke buƙatar gani da ido ce na gani jiya a zahirance. Dan an maido min Mawaddat gida a buge tana warin kayan maye kamar ma harda giya”.
Tsurru Daddy yay yana kallon Uncle Yousuf, sai kuma cikin rawar murya kamar mai shirin yin kuka ya ce, “Yousuf dan ALLAH ka gayamin gaskiya, dan in har wani yazo ya faɗa maka nasan za'a iyama Mawaddat sharri kasanta da magauta. Na rasa mi yarinyar nan ta tsarema wani a rayuwa. Gashi ita bata damu da kowa ba amma ita an dam........”
Dakatar da shi Uncle Yousuf yay da faɗin, “Yaya! Kasan dai bazan ma Mawaddat ƙarya ba dan naci riba ko? Kuma ni babu wanda yazo ya faɗa min ni na gani da idanuna. Kuma gashi misawarka tasa na fahimci kai kanka baka san Mawaddat bata kwana gida ba ma. Hakan na nufin dama ba yau ta fara fitar dare ba batare da ka sani ba kuma baka taɓa maida hankali ko damuwa ba akan tabbatar da kowa na gida kafin ka kwanta. Yaya bansan yashe ka koma haka ba, shin dan ALLAH miya canjaka? Anya kuwa son Mawaddat kakeyi da gaske har cikin ranka? Wace irin bahaguwar rayuwace wannan mara fasali. Iyayenmu sun baku tarbiyya gwargwadon iyawarsu kai da Aunty Kareema. Sannan kuma kun bani dan gashi a yanzu ina cin ribarta matsayin nagartaccen mutum da ke banbance fari da baƙi koda a cikin rufewar idanu ne. Sannan sauran yaran ma suna samun irin tarbiyyar dana samu da ga gareku. Shin miyasa komai ya canja akan Mawaddat ne? Miyasa makahon so ya lulluɓe zuciyarka kake ɗorata akan abinda zata iya kaico da kai wataran da tunanin soyayya ce. Ban ce karka sota ba, amma ka dinga dubayya mana. Shin dole ne sai ka nuna mata ƙazamar soyayya zamu san kaso mahaifiyarta kamar haka itama? Ko sai ka mata makahon so zai sanarma duniya ita ɗin ƴar sonka ce da ta fito da ga jikin matar son ka?. Anya yaya ba alhakin Aunty Kareema bane kuwa ke bibiyarku akan Mawaddat kai da mahaifiyarta? Anya ba farkawa ya kamata kayi da ga nannauyan barcinka ba a wannan gaɓar kafin komai ya ƙarasa taɓarɓarewa mu rasa Mawaddat gaba ɗayanta”.
Sosai jikin Daddy ya ƙara yin sanyi, dan dama harga ALLAH ƙarfin hali kawai yake na son musawa uncle Yousuf ɗin tunda shima ya ga shigowarta gidan a ɗazun da safen batare da ita ko wani ya sani ba. Wannan damuwar ce ya tashi da ita, sai dai ya rasa ta yanda zai tunkari Mawaddat ɗin shine ya huce haushin akan Mubeen da Mommy. A hankali ya damƙo hanun Uncle Yousuf cikin nasa ya ƙanƙame da ƙarfi, so yake ko sau ɗaya yayi kuka akan wannan damuwar ta halin rayuwar da Mawaddat ta jefa kanta a ciki amma ya kasa. Sai dai idanunsa sunyi wani masifar kaɗawa da ja. Cikin rawar murya ya ce, “Nagode ɗan uwana. Nagode da ka kasance mai faɗa min gaskiya komai ɗacinta. Wlhy auta al'amarin Mawaddat shine mafi zama ƙololiwar damuwata a yanzu fiye da komai, dan hanani barci yake yi. Zan faɗa maka gaskiya ko jiya nasan fitar ta a gidan nan, kuma nabi bayanta, sai kuma na samu yaron nan driver da ka kawo shima ɗin yabi bayanta. Dan haka na laɓe a kangwon kusa da gidan data shiga a wajen har kunama ta harbeni jiyan. Ban damu da azabar kunamarba, ni dai burina yaron nan ya fito da ita a gidan lafiya. Cikin amincin UBANGIJI kuwa sai gashi ya fito da ita a mota, na fito zan sake biyosu duk da azabar harbin kunamar da nake ciki idona ya ganemin ɗan gidan tsohon gwamna M Atik Kumo zai shiga gidan shima. Na shiga tashin hankali matuƙa, sai dai ban tsayaba na biyo motar tata dan naga ina yaron nan zai kawota sai naga gidanka ya nufa da ita. Nutsuwar hakan dana samu ce ta sani komawa da baya can gidan ɗin dai na sake tsayawa a mota, abinda ya sake tadamin hankali Yousuf su Alhaji Baita na gani sun fito a gidan nan dai da Mawaddat ta shiga kusan ƙarfe ukun dare. Wlhy tsabar ruɗani bamma san kunamata ta sauka ba. Da ƙyar na iya sake maido kaina gida shine fa ko rintsawa banyi ba har akai sallar asuba, bayan na dawo massalaci naga shigowarta gidan nan”. Ya ƙare maganar hawayen da yaketa son su zubo na sauka a yanzu masu zafi. Sosai shima Uncle Yousuf ya shiga ruɗani da tashin hankali. Dan jin sunayen manyan mutane da duk wanda ka tambaya zai tabbatar maka ɗunbin ganin mutuncinsu da yake a cikin wannan labari na yayansa......
Daddy ne ya katsesa da faɗin, “Yousuf kaina ya kulle gaba ɗaya akan al'amurin nan, ka kawo mafita inba hakaba ina gab da kaiwa ƙasa akan lamarin Mawaddat”.
“Yaya mafita ɗaya muke da ita shine yi mata aure....”
“Aure Yousuf? To da wa? Kasan dai Mawaddat bata kula kowa. Kana dai ganin duk kurari da jan idon Baba (Alhaji Sufi Garko) yayi ya barta akan sanya ranarta da yaron Sulaiman data bijirewa. Har gargaɗin duk randa wani ya sake zuwa garesa domin santa zai aura masa ita koba amincewar ta da mu kammu yay mata amma bata ɗauki hakan da muhimmanci ba saboda bushewar zuciya. Yousuf na rasa da ga ina na kuskure akan Mawaddat. Shin nuna mata soyayya na nufin ba dai-dai ba kenan?”.
“Humm Yaya wannan harda laifinka kaima ka sani, ba'a hana iyaye su nunama ƴaƴansu soyayya ba, sai dai ba ƙazamar soyayya irin wadda kaima Mawaddat ba da har tazama jagoran hanata fahimtar minene addininta. Yaya kofa salla nagartacciya Mawaddat bata iya ba a wannan shekarun nata balle azo ga sauran al'amuran addini, hakan kuma duk kuskurenka ne da kasa barinta ta samu tarbiyya irinta uwa a wajen Aunty Kareema saboda son zuciyarka..... Amma dai mu ajiye abinda ya wuce mu kalla na yanzu. Yanzu dai bayan tabbatar da aure ne mafitarmu akan lamarin Mawaddat bani da wani idea kuma. Amma dai ka bani lokaci nayi nazari tukunna. Sannan dan ALLAH ka kwantar da hankalinka. Dan lamarin Mawaddat an baro shiri ne tun rani. Amma insha ALLAHU tsayayyen miji a gareta zai jagoranceta da sabuwar tarbiyyarsa irin wadda tun farko ya kamata ace ta samu da ga garemu. Addu'a ya kamata mu duƙufa mata musamman ma kai ɗin nan. Sannan mu dage da sadaka ALLAH ya shiryar mana da ita, ya kuma kawo mana mafita cikin sauƙi. Sannan ka ajiye batun su Alh. Baita ni da kaina zanyi bincike a kansu insha ALLAHU zan gano alaƙarta da su”.
“Shike nan Yousuf ALLAH yay maka albarka.”
“Amin yaya”.
Daddy ya sake nisawa a hankali da faɗin, “Sai dai kabi a hankali a duk wani bincikenka dan a wannan gaɓar da gaske inajin ƙanina, tsoro na gaske nakeji wlhy a wannan gaɓar. Miya kawo su Alh. Baita cikin rayuwar Mawaddat?”.
“Bana tunanin wani abu saɓanin wanda zuciyata ke kallo yaya. Kasan dai da yawan wasu manyan ƙasar nan sunata taka wata rawa cikin rayuwar lalacewar yaranmu batare da mun farga ba”.
“Nafika sanin hakan Yousuf. Sai dai al'amarin ya wuce a yanda kai kake kallonsa da hasashensa. Kai dai kamar yanda na faɗa maka inajin tsoro da gaske a yanzu tsoro nake ji irin wanda a baya babu shi a zuciyata.....”
“Yaya na kasa fahimtar mi kake nufi ka ruɗar dani fa, Miye ke baka tsiro ne wai?”.
Murmushi Daddy yayi mai nuna tsantsar damuwa a bayyane. Maimakon amsa sai ya dafa kafaɗar Uncle Yousuf tare da ɗan bubbugawa ya miƙe. “Tashi kaje office auta karka makara”.
Kallo Uncle Yousuf ya bisa da shi mai tsayawa a rai, sai zuciyarsa ke wani irin rawa dan shi kaɗai yasan mi yake iya hangowa game da ɗan uwan nasa, sai kawai shima yaji kamar ya fara jin tsoron. Tabbas akwai ɓoyayyen al'amari wanda ya kamata ace ya sani amma ta yaya? (Bincike akan alaƙar Mawaddat da su Hon. Babale Nakowa) kansa ya jinjina cikin gamsuwa da shawarar zuciyarsa. Dan haka shima ya miƙa ya fice. Da kallo yabi motar Yayansa dake ƙoƙarin ficewa a gidan. Numfashi ya sauke da ƙyar tare da nufar tashi motar shima.
★★★ ∆ ★★★
Smart kam tattara al'amarin Lulu yay ya wancalakar gefe domin fuskantar tasa mai muhimmanci. Gida ya nufa kai tsaye saboda kiran da Abba yay masa. Ya samu gidan da ƴar hayaniyar kasancewar zuwan Sa'id da wasu kawunansa uku. Cikin girmamawa ya gaishesu batare da ya kalla inda Sa'id ya ke gurfane ba kamar mai kuka. Ya maida hankalinsa ga Abba da Hawwah ke a kusa da ƙafafunsa kamar tana kuka itama.
“Abba gani”.
Ya faɗa cikin dakewarsa. Nisawa Abba yay da nuna Hawwah ya ce, “Kaine ka ɗakko Hauwa'u a gidanta?”.
“Eh tabbas nine Abba”.
“Me yasa?”.
Shiru ya ɗan yi kafin ya nisa. “Abba saboda ta kirani akan ga mahaifiyar mijinta na neman ƙonata da mangyaɗa. Banje gidan da nufin ɗakkota ba sai jin ba'asi na kuma sasanta kamar na baya da akai batare da kun sani ba. Sai dai na samu abin ya wuce yanda nake zatonsa shiyyasa na ɗakkota kafin a cutar da ita tunda mu bawai mun daina sonta bane ba. Ba kuma mun bashi bane dan mun gaji da ita a gidan nan kota gundiremu. Abba abubuwa da yawa sun faru akan auren Hawwah amma ina sasantawa a iya can batare da kai ko Ammah kun taɓa sani ba. Bama ku ba hatta da Aunty Bilkisu ban taɓa sanarmawa ba, kuma na gargaɗi Hawwah sanar ma kowa. Shiyyasa wannan karon na ɗakkota kuma bazata sake koma musu gida ba. Yaje ya auri wadda mahaifiyarsa ke son zama da ita haka nan dan ALLAH kowa ya huta.”........✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣7️⃣
.......“Humm akwai wahala sosai da bata da misali. Na ƙara jin ƙaunar mahaifiyata da jinjina mata wahalar da tai dani a dalilin wannan cikin. Ko abinci bana iya ci, da naci sai amai, ko wani abu na sha sai nayi amai. Gashi nan ko yanzu dana haihu magani ma ya gagareni sai dai allurai ake min dan in naga magani amai nake ji. Kunun gyaɗa ne kawai ya zama abincina kwana da yini. Gaba ɗaya dai abin babu sauƙi kawai dan ba'a iya misaltashi ma Aliyu. Balle naƙuda Hummm......”
Duk da a dunƙule ta bashi labarin ya fahimci dai ciki ya hanata shaye-shaye, sai kunun gyaɗa daya zamar mata abinci kawai. Cikin ƙara sanyaya murya da jin tausayinta da farin ciki ya ce, “Addu'ata dare da rana UBANGIJI ya tasirantar da itane atare da gudan jinina, ya ƙarasa min aikin dana fara kenan, sannan a kowane awa bayan awa yana tuna miki Abbiensa ne ta hanyar shan abinda yafi so fiye da komai.” yanda ya ƙare maganar da ƴar dariyar tsokana ya sata ɗan harararsa da taɓe baki, sai dai batasan hararar tata ba ta juye ne zuwa wani sassanyan kallon dake neman hargitsama Smart lissafi da hankali.
“Ita hararar nan tana son tada zaune tsaye ne fa. Zakuma ta iya takalo yaƙin ƙasa da ƙasa a taƙaice rigakafi yafi magani”. Ya faɗa a wani irin kasalance yana ƙasa-ƙasa da idanu. Ba fahimtar zancensa tai ba, amma salon da yay maganar da yanda yake wani narke idanu da murya ya sata janye jikinta a nasa cikin basarwa duk da saƙon nasa ya isa ga manyan mata fiye da yanda yay tsammani. Shima kawai sai ya basar cikin sauke ajiyar zuciya ya ce, “Yanzu miye shirinki akan suna gobe idan ALLAH ya kaimu?”.
Cikin mamaki ta ce, “Suna kuma? Da suwa za'ayi sunan to? Bayan naga idan za'ai suna a gida Nigeria taruwa dangi sukeyi da matan anguwa, in dai ban manta ba haka na gani a sunan Deen ɗin mu fa anyi, anan kuma mu yanzu wa garemu da zai zo?”.
“Mu mana, iya mu ɗin nan ma ai mun wadatar muyi suna bawai wajibi bane sai antarun kamar yanda kika gani a sunan Deen, in sha ALLAHU kuma za'a yanka masa rago kamar yanda ake yankama kowa. Ƙyautar da ban san da itaba ce ba fa a hannuna, taya bazan nuna godiyar ALLAH ba nikam. Sannan ni so nake daga nan mu wuce kawai basai kin koma Nigeria ba”.
“Hanyoyin nuna godiyar ALLAH ai suna da yawa ba sai ta hanyar yin taron suna ba. Sannan idan ban koma Nigeria ba ina kake son naje banda neman magana irin taka. Kuma ni nama faɗa maka na shirya cigaba da zama da kai ne? Auren contract akayi kuma ya ƙare it's ok”.
“Hakane kam, Alhamdullah suma waɗan can godiyar UBANGIJI ɗin duk na kamanta su, amma duk da haka dai ina son muyi shagalin suna. Kinga koda ƙannensa sun zo nan gaba suma shi bazaiga an musu ba'ai masa ba”. Ya ƙare maganar batare daya amsa maganartata ta ƙarshe ba.
Hakan ya bata haushi, dan haka a tunzire ta ce, “Miye wani ƙanne? Malam ka san abinda kake faɗa fa! Na gaya maka ni na gama auren nan”.
Dariya ta bashi ganin yanda tai maganar a gatsire, amma sai ya danne da ƙyar yay murmushi kawai da faɗin, “Naki tsarin kenan wannan ai”.
“Kamar ya nawa tsarin kenan?. Amma kasan dai ba haka akai da kai ba ko?”.
“Humm” yace kawai. Baice komai ba akan maganar tata yanzun ma, sai ma ya nuna mata ledojin da suka shigo da shi. “Kuyi haƙuri da waɗan nan babu yawa, sauran abinda ya dace duk na damƙashi a hannun Usman. Munyi magana da Daddy akan suna son a turaki Saudiya ki zauna a can na wani lokaci saboda Kawunki Sulaiman, dan bazai taɓa ƙyaleki ba zai cigaba da bibiyar al'amarin ku. Ke yaya kika gani?”.
“Ni babu inda zani, shi ɗin banza da zan cigaba da masa wasan ɓuya. Ko wannan ɗin ma da yaga yaci nasara saboda Dada ne wlhy, sannan ina kan sani na cigaba da biye masa bayan nasan manufarsa. Nayi hakkanne kawai domin sake tabbatar da shi ɗin waye. Amma har miye wani Sulaiman can”.
Murmushi yayi kaɗan, a zuciyarsa yana ayyana (ashe a wajen Daddy kika gado wannan taurin ran naki da kafiya) a zahiri kam sai ya nisa cikin ɗan cije lips ɗinsa ya ce, “Zamu iya tunanin shi ba abin tsoro bane ba, sai dai idan muka shagala da hakan zai mana illa a ƙanƙanin lokaci cikin salon duka ta inda bazamu taɓa iya sosawa ba balle mu rama. Mawaddat Kawunki ya wuce duk yanda kike tunani a kansa. Domin ya jima biye da rayuwarki tun kina ƙarama. Bana raba ɗayan biyu shine ya koya miki shaye-shaye. Kuma shine ya taɓa harar rayuwarki ta hanyar keta miki haddinki har kike firgita kika tsani maza....”
Da wani irin sauri ta kallesa, sai kuma jikinta ya fara tsuma. Dan danan annurin fuskarta ya ɓace gaba ɗaya. Cikin yanayin faɗa-faɗa ta ce, “Aliyu rayuwata ta baya ta zamar maka abar bibiyane ko mi?”.
“No ko ɗaya, mizai sa na bibiya bayan na gama fahimtar komai. Sannan Mawaddat nake so ba halayenta ba. Ruwana ne na maidata a irin halayyar da nafi buƙata kona barta da wanda na ganta a ciki. Mawaddat ki sani shure-shure baya hana mutuwa, duk yanda kike jin zaki iya ɓoye abinda ya faru a baya wataran zuciyarki bazata iya ɗauka ba. Kiyi haƙuri ba ina tilasta miki bane sai kin sanar min, kidai sani cigaba da riƙewar zai iya sake nakasaki akan shaye-shayen nan. Doctor ya jima da tabbatar da idan kika cigaba zaki cutu, sannan a yanzu ke ɗin Uwa ce Mawaddat, taya kike tunanin idan yaron mu ya taso yaji wannan ɗibi'ar koda a labari ne zaiyi farin ciki. Mahaifiyarki mutuniyar kirkice data shinfiɗama rayuwarta alkairai da dama da a yanzu sune ke bibiyarta da ke kanki har maƙiyanki da nata suka gagara cin galaba a kanki. Taya kike tunanin naki ɗiyan zasu samu irin wannan kariyar idan har baki zama uwa ta ƙwarai ba Mawaddat. Please ina so ki canja, canjawar taki kuma zata tabbatane kawai ta hanyar fidda abinda ke zuciyarki, dan shine yay miki nauyin da har kike jin abinda kike sha zai iya danne miki shi. Taya za'a gyara ɓarna da ɓarna banda wautarki......”
Wani irin kuka mai tsuma zuciyar da ta saki ne ya saka shi yin shiru, a hankali ya furzar da iska tare da miƙewa ya koma daf da ita, matsota yay ya saka a jikinsa ya rungume. Sai kawai ta sake sakin masa kuka da iya dukkan ƙarfinta da baƙin cikin dake cinkushe da zuciyarta da ƙwaƙwalwa. Bai sake mata magana ba ya barta tai kukan mai isarta dan haka zai rage mata nauyin zuciyar. Tako yi kukan
Showing 216001 words to 219000 words out of 294165 words
Numfashi mai ɗaci Uncle Yousuf yaja da gyara zamansa. Kai tsaye ya ce, “Akan Mawaddat ne.”
“Kuma dai Yousuf? To mi ta sake yi?”. Da ga jin a yanda Daddy yay tambayar kasan ransa a jagule yake. Amma sai Uncle Yousuf ɗin yay biris ya cigaba da faɗin, “Gaskiyar da muke buƙatar gani da ido ce na gani jiya a zahirance. Dan an maido min Mawaddat gida a buge tana warin kayan maye kamar ma harda giya”.
Tsurru Daddy yay yana kallon Uncle Yousuf, sai kuma cikin rawar murya kamar mai shirin yin kuka ya ce, “Yousuf dan ALLAH ka gayamin gaskiya, dan in har wani yazo ya faɗa maka nasan za'a iyama Mawaddat sharri kasanta da magauta. Na rasa mi yarinyar nan ta tsarema wani a rayuwa. Gashi ita bata damu da kowa ba amma ita an dam........”
Dakatar da shi Uncle Yousuf yay da faɗin, “Yaya! Kasan dai bazan ma Mawaddat ƙarya ba dan naci riba ko? Kuma ni babu wanda yazo ya faɗa min ni na gani da idanuna. Kuma gashi misawarka tasa na fahimci kai kanka baka san Mawaddat bata kwana gida ba ma. Hakan na nufin dama ba yau ta fara fitar dare ba batare da ka sani ba kuma baka taɓa maida hankali ko damuwa ba akan tabbatar da kowa na gida kafin ka kwanta. Yaya bansan yashe ka koma haka ba, shin dan ALLAH miya canjaka? Anya kuwa son Mawaddat kakeyi da gaske har cikin ranka? Wace irin bahaguwar rayuwace wannan mara fasali. Iyayenmu sun baku tarbiyya gwargwadon iyawarsu kai da Aunty Kareema. Sannan kuma kun bani dan gashi a yanzu ina cin ribarta matsayin nagartaccen mutum da ke banbance fari da baƙi koda a cikin rufewar idanu ne. Sannan sauran yaran ma suna samun irin tarbiyyar dana samu da ga gareku. Shin miyasa komai ya canja akan Mawaddat ne? Miyasa makahon so ya lulluɓe zuciyarka kake ɗorata akan abinda zata iya kaico da kai wataran da tunanin soyayya ce. Ban ce karka sota ba, amma ka dinga dubayya mana. Shin dole ne sai ka nuna mata ƙazamar soyayya zamu san kaso mahaifiyarta kamar haka itama? Ko sai ka mata makahon so zai sanarma duniya ita ɗin ƴar sonka ce da ta fito da ga jikin matar son ka?. Anya yaya ba alhakin Aunty Kareema bane kuwa ke bibiyarku akan Mawaddat kai da mahaifiyarta? Anya ba farkawa ya kamata kayi da ga nannauyan barcinka ba a wannan gaɓar kafin komai ya ƙarasa taɓarɓarewa mu rasa Mawaddat gaba ɗayanta”.
Sosai jikin Daddy ya ƙara yin sanyi, dan dama harga ALLAH ƙarfin hali kawai yake na son musawa uncle Yousuf ɗin tunda shima ya ga shigowarta gidan a ɗazun da safen batare da ita ko wani ya sani ba. Wannan damuwar ce ya tashi da ita, sai dai ya rasa ta yanda zai tunkari Mawaddat ɗin shine ya huce haushin akan Mubeen da Mommy. A hankali ya damƙo hanun Uncle Yousuf cikin nasa ya ƙanƙame da ƙarfi, so yake ko sau ɗaya yayi kuka akan wannan damuwar ta halin rayuwar da Mawaddat ta jefa kanta a ciki amma ya kasa. Sai dai idanunsa sunyi wani masifar kaɗawa da ja. Cikin rawar murya ya ce, “Nagode ɗan uwana. Nagode da ka kasance mai faɗa min gaskiya komai ɗacinta. Wlhy auta al'amarin Mawaddat shine mafi zama ƙololiwar damuwata a yanzu fiye da komai, dan hanani barci yake yi. Zan faɗa maka gaskiya ko jiya nasan fitar ta a gidan nan, kuma nabi bayanta, sai kuma na samu yaron nan driver da ka kawo shima ɗin yabi bayanta. Dan haka na laɓe a kangwon kusa da gidan data shiga a wajen har kunama ta harbeni jiyan. Ban damu da azabar kunamarba, ni dai burina yaron nan ya fito da ita a gidan lafiya. Cikin amincin UBANGIJI kuwa sai gashi ya fito da ita a mota, na fito zan sake biyosu duk da azabar harbin kunamar da nake ciki idona ya ganemin ɗan gidan tsohon gwamna M Atik Kumo zai shiga gidan shima. Na shiga tashin hankali matuƙa, sai dai ban tsayaba na biyo motar tata dan naga ina yaron nan zai kawota sai naga gidanka ya nufa da ita. Nutsuwar hakan dana samu ce ta sani komawa da baya can gidan ɗin dai na sake tsayawa a mota, abinda ya sake tadamin hankali Yousuf su Alhaji Baita na gani sun fito a gidan nan dai da Mawaddat ta shiga kusan ƙarfe ukun dare. Wlhy tsabar ruɗani bamma san kunamata ta sauka ba. Da ƙyar na iya sake maido kaina gida shine fa ko rintsawa banyi ba har akai sallar asuba, bayan na dawo massalaci naga shigowarta gidan nan”. Ya ƙare maganar hawayen da yaketa son su zubo na sauka a yanzu masu zafi. Sosai shima Uncle Yousuf ya shiga ruɗani da tashin hankali. Dan jin sunayen manyan mutane da duk wanda ka tambaya zai tabbatar maka ɗunbin ganin mutuncinsu da yake a cikin wannan labari na yayansa......
Daddy ne ya katsesa da faɗin, “Yousuf kaina ya kulle gaba ɗaya akan al'amurin nan, ka kawo mafita inba hakaba ina gab da kaiwa ƙasa akan lamarin Mawaddat”.
“Yaya mafita ɗaya muke da ita shine yi mata aure....”
“Aure Yousuf? To da wa? Kasan dai Mawaddat bata kula kowa. Kana dai ganin duk kurari da jan idon Baba (Alhaji Sufi Garko) yayi ya barta akan sanya ranarta da yaron Sulaiman data bijirewa. Har gargaɗin duk randa wani ya sake zuwa garesa domin santa zai aura masa ita koba amincewar ta da mu kammu yay mata amma bata ɗauki hakan da muhimmanci ba saboda bushewar zuciya. Yousuf na rasa da ga ina na kuskure akan Mawaddat. Shin nuna mata soyayya na nufin ba dai-dai ba kenan?”.
“Humm Yaya wannan harda laifinka kaima ka sani, ba'a hana iyaye su nunama ƴaƴansu soyayya ba, sai dai ba ƙazamar soyayya irin wadda kaima Mawaddat ba da har tazama jagoran hanata fahimtar minene addininta. Yaya kofa salla nagartacciya Mawaddat bata iya ba a wannan shekarun nata balle azo ga sauran al'amuran addini, hakan kuma duk kuskurenka ne da kasa barinta ta samu tarbiyya irinta uwa a wajen Aunty Kareema saboda son zuciyarka..... Amma dai mu ajiye abinda ya wuce mu kalla na yanzu. Yanzu dai bayan tabbatar da aure ne mafitarmu akan lamarin Mawaddat bani da wani idea kuma. Amma dai ka bani lokaci nayi nazari tukunna. Sannan dan ALLAH ka kwantar da hankalinka. Dan lamarin Mawaddat an baro shiri ne tun rani. Amma insha ALLAHU tsayayyen miji a gareta zai jagoranceta da sabuwar tarbiyyarsa irin wadda tun farko ya kamata ace ta samu da ga garemu. Addu'a ya kamata mu duƙufa mata musamman ma kai ɗin nan. Sannan mu dage da sadaka ALLAH ya shiryar mana da ita, ya kuma kawo mana mafita cikin sauƙi. Sannan ka ajiye batun su Alh. Baita ni da kaina zanyi bincike a kansu insha ALLAHU zan gano alaƙarta da su”.
“Shike nan Yousuf ALLAH yay maka albarka.”
“Amin yaya”.
Daddy ya sake nisawa a hankali da faɗin, “Sai dai kabi a hankali a duk wani bincikenka dan a wannan gaɓar da gaske inajin ƙanina, tsoro na gaske nakeji wlhy a wannan gaɓar. Miya kawo su Alh. Baita cikin rayuwar Mawaddat?”.
“Bana tunanin wani abu saɓanin wanda zuciyata ke kallo yaya. Kasan dai da yawan wasu manyan ƙasar nan sunata taka wata rawa cikin rayuwar lalacewar yaranmu batare da mun farga ba”.
“Nafika sanin hakan Yousuf. Sai dai al'amarin ya wuce a yanda kai kake kallonsa da hasashensa. Kai dai kamar yanda na faɗa maka inajin tsoro da gaske a yanzu tsoro nake ji irin wanda a baya babu shi a zuciyata.....”
“Yaya na kasa fahimtar mi kake nufi ka ruɗar dani fa, Miye ke baka tsiro ne wai?”.
Murmushi Daddy yayi mai nuna tsantsar damuwa a bayyane. Maimakon amsa sai ya dafa kafaɗar Uncle Yousuf tare da ɗan bubbugawa ya miƙe. “Tashi kaje office auta karka makara”.
Kallo Uncle Yousuf ya bisa da shi mai tsayawa a rai, sai zuciyarsa ke wani irin rawa dan shi kaɗai yasan mi yake iya hangowa game da ɗan uwan nasa, sai kawai shima yaji kamar ya fara jin tsoron. Tabbas akwai ɓoyayyen al'amari wanda ya kamata ace ya sani amma ta yaya? (Bincike akan alaƙar Mawaddat da su Hon. Babale Nakowa) kansa ya jinjina cikin gamsuwa da shawarar zuciyarsa. Dan haka shima ya miƙa ya fice. Da kallo yabi motar Yayansa dake ƙoƙarin ficewa a gidan. Numfashi ya sauke da ƙyar tare da nufar tashi motar shima.
★★★ ∆ ★★★
Smart kam tattara al'amarin Lulu yay ya wancalakar gefe domin fuskantar tasa mai muhimmanci. Gida ya nufa kai tsaye saboda kiran da Abba yay masa. Ya samu gidan da ƴar hayaniyar kasancewar zuwan Sa'id da wasu kawunansa uku. Cikin girmamawa ya gaishesu batare da ya kalla inda Sa'id ya ke gurfane ba kamar mai kuka. Ya maida hankalinsa ga Abba da Hawwah ke a kusa da ƙafafunsa kamar tana kuka itama.
“Abba gani”.
Ya faɗa cikin dakewarsa. Nisawa Abba yay da nuna Hawwah ya ce, “Kaine ka ɗakko Hauwa'u a gidanta?”.
“Eh tabbas nine Abba”.
“Me yasa?”.
Shiru ya ɗan yi kafin ya nisa. “Abba saboda ta kirani akan ga mahaifiyar mijinta na neman ƙonata da mangyaɗa. Banje gidan da nufin ɗakkota ba sai jin ba'asi na kuma sasanta kamar na baya da akai batare da kun sani ba. Sai dai na samu abin ya wuce yanda nake zatonsa shiyyasa na ɗakkota kafin a cutar da ita tunda mu bawai mun daina sonta bane ba. Ba kuma mun bashi bane dan mun gaji da ita a gidan nan kota gundiremu. Abba abubuwa da yawa sun faru akan auren Hawwah amma ina sasantawa a iya can batare da kai ko Ammah kun taɓa sani ba. Bama ku ba hatta da Aunty Bilkisu ban taɓa sanarmawa ba, kuma na gargaɗi Hawwah sanar ma kowa. Shiyyasa wannan karon na ɗakkota kuma bazata sake koma musu gida ba. Yaje ya auri wadda mahaifiyarsa ke son zama da ita haka nan dan ALLAH kowa ya huta.”........✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
VIP🔥💯
Zafin kai 3k
Furar danko 3k
Tabarmar kashi 3k
Bakon munafuki 3k
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣7️⃣
.......“Humm akwai wahala sosai da bata da misali. Na ƙara jin ƙaunar mahaifiyata da jinjina mata wahalar da tai dani a dalilin wannan cikin. Ko abinci bana iya ci, da naci sai amai, ko wani abu na sha sai nayi amai. Gashi nan ko yanzu dana haihu magani ma ya gagareni sai dai allurai ake min dan in naga magani amai nake ji. Kunun gyaɗa ne kawai ya zama abincina kwana da yini. Gaba ɗaya dai abin babu sauƙi kawai dan ba'a iya misaltashi ma Aliyu. Balle naƙuda Hummm......”
Duk da a dunƙule ta bashi labarin ya fahimci dai ciki ya hanata shaye-shaye, sai kunun gyaɗa daya zamar mata abinci kawai. Cikin ƙara sanyaya murya da jin tausayinta da farin ciki ya ce, “Addu'ata dare da rana UBANGIJI ya tasirantar da itane atare da gudan jinina, ya ƙarasa min aikin dana fara kenan, sannan a kowane awa bayan awa yana tuna miki Abbiensa ne ta hanyar shan abinda yafi so fiye da komai.” yanda ya ƙare maganar da ƴar dariyar tsokana ya sata ɗan harararsa da taɓe baki, sai dai batasan hararar tata ba ta juye ne zuwa wani sassanyan kallon dake neman hargitsama Smart lissafi da hankali.
“Ita hararar nan tana son tada zaune tsaye ne fa. Zakuma ta iya takalo yaƙin ƙasa da ƙasa a taƙaice rigakafi yafi magani”. Ya faɗa a wani irin kasalance yana ƙasa-ƙasa da idanu. Ba fahimtar zancensa tai ba, amma salon da yay maganar da yanda yake wani narke idanu da murya ya sata janye jikinta a nasa cikin basarwa duk da saƙon nasa ya isa ga manyan mata fiye da yanda yay tsammani. Shima kawai sai ya basar cikin sauke ajiyar zuciya ya ce, “Yanzu miye shirinki akan suna gobe idan ALLAH ya kaimu?”.
Cikin mamaki ta ce, “Suna kuma? Da suwa za'ayi sunan to? Bayan naga idan za'ai suna a gida Nigeria taruwa dangi sukeyi da matan anguwa, in dai ban manta ba haka na gani a sunan Deen ɗin mu fa anyi, anan kuma mu yanzu wa garemu da zai zo?”.
“Mu mana, iya mu ɗin nan ma ai mun wadatar muyi suna bawai wajibi bane sai antarun kamar yanda kika gani a sunan Deen, in sha ALLAHU kuma za'a yanka masa rago kamar yanda ake yankama kowa. Ƙyautar da ban san da itaba ce ba fa a hannuna, taya bazan nuna godiyar ALLAH ba nikam. Sannan ni so nake daga nan mu wuce kawai basai kin koma Nigeria ba”.
“Hanyoyin nuna godiyar ALLAH ai suna da yawa ba sai ta hanyar yin taron suna ba. Sannan idan ban koma Nigeria ba ina kake son naje banda neman magana irin taka. Kuma ni nama faɗa maka na shirya cigaba da zama da kai ne? Auren contract akayi kuma ya ƙare it's ok”.
“Hakane kam, Alhamdullah suma waɗan can godiyar UBANGIJI ɗin duk na kamanta su, amma duk da haka dai ina son muyi shagalin suna. Kinga koda ƙannensa sun zo nan gaba suma shi bazaiga an musu ba'ai masa ba”. Ya ƙare maganar batare daya amsa maganartata ta ƙarshe ba.
Hakan ya bata haushi, dan haka a tunzire ta ce, “Miye wani ƙanne? Malam ka san abinda kake faɗa fa! Na gaya maka ni na gama auren nan”.
Dariya ta bashi ganin yanda tai maganar a gatsire, amma sai ya danne da ƙyar yay murmushi kawai da faɗin, “Naki tsarin kenan wannan ai”.
“Kamar ya nawa tsarin kenan?. Amma kasan dai ba haka akai da kai ba ko?”.
“Humm” yace kawai. Baice komai ba akan maganar tata yanzun ma, sai ma ya nuna mata ledojin da suka shigo da shi. “Kuyi haƙuri da waɗan nan babu yawa, sauran abinda ya dace duk na damƙashi a hannun Usman. Munyi magana da Daddy akan suna son a turaki Saudiya ki zauna a can na wani lokaci saboda Kawunki Sulaiman, dan bazai taɓa ƙyaleki ba zai cigaba da bibiyar al'amarin ku. Ke yaya kika gani?”.
“Ni babu inda zani, shi ɗin banza da zan cigaba da masa wasan ɓuya. Ko wannan ɗin ma da yaga yaci nasara saboda Dada ne wlhy, sannan ina kan sani na cigaba da biye masa bayan nasan manufarsa. Nayi hakkanne kawai domin sake tabbatar da shi ɗin waye. Amma har miye wani Sulaiman can”.
Murmushi yayi kaɗan, a zuciyarsa yana ayyana (ashe a wajen Daddy kika gado wannan taurin ran naki da kafiya) a zahiri kam sai ya nisa cikin ɗan cije lips ɗinsa ya ce, “Zamu iya tunanin shi ba abin tsoro bane ba, sai dai idan muka shagala da hakan zai mana illa a ƙanƙanin lokaci cikin salon duka ta inda bazamu taɓa iya sosawa ba balle mu rama. Mawaddat Kawunki ya wuce duk yanda kike tunani a kansa. Domin ya jima biye da rayuwarki tun kina ƙarama. Bana raba ɗayan biyu shine ya koya miki shaye-shaye. Kuma shine ya taɓa harar rayuwarki ta hanyar keta miki haddinki har kike firgita kika tsani maza....”
Da wani irin sauri ta kallesa, sai kuma jikinta ya fara tsuma. Dan danan annurin fuskarta ya ɓace gaba ɗaya. Cikin yanayin faɗa-faɗa ta ce, “Aliyu rayuwata ta baya ta zamar maka abar bibiyane ko mi?”.
“No ko ɗaya, mizai sa na bibiya bayan na gama fahimtar komai. Sannan Mawaddat nake so ba halayenta ba. Ruwana ne na maidata a irin halayyar da nafi buƙata kona barta da wanda na ganta a ciki. Mawaddat ki sani shure-shure baya hana mutuwa, duk yanda kike jin zaki iya ɓoye abinda ya faru a baya wataran zuciyarki bazata iya ɗauka ba. Kiyi haƙuri ba ina tilasta miki bane sai kin sanar min, kidai sani cigaba da riƙewar zai iya sake nakasaki akan shaye-shayen nan. Doctor ya jima da tabbatar da idan kika cigaba zaki cutu, sannan a yanzu ke ɗin Uwa ce Mawaddat, taya kike tunanin idan yaron mu ya taso yaji wannan ɗibi'ar koda a labari ne zaiyi farin ciki. Mahaifiyarki mutuniyar kirkice data shinfiɗama rayuwarta alkairai da dama da a yanzu sune ke bibiyarta da ke kanki har maƙiyanki da nata suka gagara cin galaba a kanki. Taya kike tunanin naki ɗiyan zasu samu irin wannan kariyar idan har baki zama uwa ta ƙwarai ba Mawaddat. Please ina so ki canja, canjawar taki kuma zata tabbatane kawai ta hanyar fidda abinda ke zuciyarki, dan shine yay miki nauyin da har kike jin abinda kike sha zai iya danne miki shi. Taya za'a gyara ɓarna da ɓarna banda wautarki......”
Wani irin kuka mai tsuma zuciyar da ta saki ne ya saka shi yin shiru, a hankali ya furzar da iska tare da miƙewa ya koma daf da ita, matsota yay ya saka a jikinsa ya rungume. Sai kawai ta sake sakin masa kuka da iya dukkan ƙarfinta da baƙin cikin dake cinkushe da zuciyarta da ƙwaƙwalwa. Bai sake mata magana ba ya barta tai kukan mai isarta dan haka zai rage mata nauyin zuciyar. Tako yi kukan
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73 Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99