“Abu mai wahala kenan, dan ta yanke alaƙarmu, tare da gargaɗin nisantar ta. Nasan halinta kuma sarai idan ta faɗi abu har cikin ranta ne. Abu ne mai matuƙar wahala Lulu ta sake kallona balle har na shiga jikinta”.
“Zamu iya amfani da wata ai, amma ya zama ke zakina controlling nata”. Cewar Asim.
Kai Nadiya ta jinjina da faɗin, “Wai babbar magana. Na fahimci bakusan wacece Lulu ba. Kubar ganinta haka batajin magana tasan mitakeyi. Sannan koni kaina nasha wahala kafin mu fara abota gaskiya, dan bata da saurin sakewa da mutane, sannan ba kowa ke iya haƙuri da halin Lulu ba”.
“Karki damu inhar aka jajirce wannan ba komai bane ba. Sannan kema fa akan aikin nan zakija manda. Dan a yanzu haka zamu sauke miki miliyan ɗaya kafin ma aikin ya fara”.
Sosai Nadiya ta zaro ido waje, ranta fal farin ciki ta ce, “Yanzu yaya kuke so ayi?”.
Kallon juna sukai da murmushi, kafin Asim ya miƙa mata card da faɗin, “Ki samemu a wannan address ɗin zuwa anjima”.
“Wannan yafi komai sauƙi”.
Ta faɗa tana amsar card ɗin........
_______________★
Kwanaki uku kenan da fara fitar Lulu aiki, kullum kuma Smart ke kaita office da safe sannan shima ya koma gidan yay shirin tashi fitar a Napep. Idan ko fita ta kamata a yinin mai Napep ɗin nan da bata san da shi ba na biye da ita. Duk kuma inda ta saka ƙafa ana sanar masa. A lissafinsa dai babu wani abu dake faruwa, dan ranar farko ta sayi bread wanda bai san a tsakkiyarsa aka saka mata kayan shaye-shayen ta ba, kamar yanda takeyi sai zata kwanta tasha hakan tayi, shiyyasa bai gane komai ba sai ya ɗauka kawai gajiyar aikin data koma ce tunda tayi ƴar zirga-zirga. Washe gari dai yaga ta tashi a tsayenta bakamar kwana biyu datai wani sukuku ba. Rana ta biyu ma sai da tai amfani da dabarun nasu ta amsa, hakama jiya. Yau cikon kwana na uku yaso ya ɗan fara tsarguwa, amma dai baice komai ba. Yana son mata tambaya akan zuwa gidan su Sa'id sai kuma dai yay shiru. Sai kuma gashi a yau yana tare da Coach kira ya sameshi da ga Ammah wai yazo da sauri idan yana kusa. Ya Isa gidan da tunani kala-kala sai ya ɓige da samun mahaifiyar Sa'id da wasu ƴan uwanta maza uku dan dangin mahaifinsa sun rantse bazasu zo ba, ita data ɓata taje ta gyara sun dai zo na farko. Ba Smart kaɗai ba kowa ma na gidan nan yau mamakin jin maman Sa'id wai sunzo bada haƙuri ne da neman afuwar Hawwah dan ALLAH tai haƙuri ta koma yake. Smart yace shifa ƴar uwarsa bazata koma wannan gida ba, anyi kenan takardar saki kawai yake buƙata Sa'id ya kawo, dan suna sonta baza'a kashe musu yarinya ba. Sosai Maman Sa'id ke faman magiya akan wancan ma daya faru tsautsayi ne da munafuncin munafukai, amma yanzu ta gane gaskiya. Ankai ruwa rana matuƙa kafin Smart ya haƙura zata koman amma ba wannan gidan ba. Da sauri Mama tace ta yarda, Hawwah ta zaɓi duk inda take so a gidajensu a gyara mata. Wannan abu yaba kowa mamaki, Umma na son magana tana tsoron ta tanka Maman Sa'id tai mata bankaɗa tunda taji tana shaguɓe akan munafukai, ba kowa kuma ne mai zuwa ɓata Ammah da Hawwah a wajenta ba sai ita dama. Bayan wucewarsu kowa ya shiga mamaki, Abba ya tsare Smart akan miya ma maman Sa'id ɗin har tai irin wannan sakkowar lokaci ɗaya. Ya tabbatar musu bashi bane, dan shi target ɗinsa akan jiran dawowar mahaifin Sa'id ne ai. Yana son kawo Lulu a ransa wani gefe na zuciyarsa na musa masa. Amma dai duk da haka bayan ya koma gida da daddare sai da ya kasa haƙuri yay mata tambaya. Dariya kawai tayi taƙi faɗa masa komai, hakan ya tabbatar masa itace kenan tayi koma miye. Sai kawai ya zuba mata ido yana jin wani abu mai girma na ƙara ratsashi a kanta. Jin kaifin idanunsa a kanta ya sata dakatawa da ga abinda take a system ta ɗago, harararsa tai da faɗin, “Malam wannan kallon fa? Ni fa bana son kallo”. Ta ƙare maganar da murguɗa baki. Murmushi ya saki mai sanyi batare da ya janye idanun ba, sai ya samu kansa da furta, “Kullum sake mamaye komai da komai kike yi”. Bata fahimci ina ya dosa ba, sai dai yanda yay maganar a ƙasan maƙoshi da tausasa fitar sautin matuƙa ya sata tsayawa kallonsa, “Lafiya kake kuwa? Kodai kaima ka fara ban sani ba?”.
“Na fara mi?”.
“A hawa network mana”.
Ƙaramar dariya yay yana girgiza kansa. “Tom maybe na fara amma nawa ba irin naki bane gaskiya. Kema fata nake ki daina wannan ai ki dawo wannan irin nawan”.
Nan ɗin ma dai ba fahimtar tai ba, dan haka ma ta taɓe baki da miƙewa tana faɗin, “Ai kai kam wani lokacin kamar mai aljanu. Dolene na sanarma Ammah ta fara maka addu'ar su ko ka kwaso a drivern cin ba'a sani ba”. Daga haka ta wuce bedroom ta barshi yana murmushi.........✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 8️⃣1️⃣
.........Washe gari gidansu ya wuce bayan ya sauketa, anan ne yake samun Abba da Ammah da batun shifa yana zargin Mawaddat ce tayi koma miye. Dan an sanar masa taje gidan a ranar monday. Mamaki sukaitayi suma da tunanin to mita faɗa ma maman Sa'id da har ta risina haka da sauri. A gefe kuma ƙaunar yarinyar na sake shigar musu zukata. Kamar yanda akace sati ɗaya cikin satin Hawwah ta fara shirin komawa sabon gidanta danƙarere. Hankalin Umma ya sake tashi, da bin ƙwanƙwanto ta gano Lulu ce tamayi koma miye har komai ya dai-daita. Hankali a tashe ta nufi gidan Hajiya Naqiba ƙawarta. Acan suka baje faifain zagin Ammah da bata san sunayi ba da Ƴaƴanta suna neman mafita dan abubuwa fa nata faman kufce musu a hannu, sai dai gaba ɗaya hankalinsu da mugayen ƙudirinsu sun tattara ne ga Lulu yanzu. Dan sun fahimci shigowarta gidan abubuwa da yawa ke neman taɓarɓarewa. Duk da su basu fahimci cewar asirin jikin Smart ma ya gama warwarewa gaba ɗaya ba. Ga aikin Malam na-zuru yaƙi yiwuwa, dan kayan Lulu da Smart dai sun gagara ɗakkuwa. Hajiya Naqiba ce cikin dogon tunani ta ce, “Aminiya anya bazamu canja taku ba?”.
“Kamarya? Fito kimun dalla-dalla, kin san bana son kwana-kwana fa”.
“Ina nufin ba asiri bane kaɗai yanzu ya kamata musa gaba dole mu haɗa da makirci da kissa. Kamar dai yanda nai akan shegun yaran can na baƙar dagar tawa.”
“In dai wannan ne ai mun jima munayi Aminiya, yanzu ko ita akan wannan shegiyar da zata koma Hawwah ai kinga sai da muka haɗa da makirci waccan shegiyar da bamu san mitaje tayi ba ta ɓata mana komai.”
“Kwantar da hankalinki karki damu, murnarsu zata koma ciki ne. Yanzu mu fara kai wannan baƙuwar hauren ƙasa tukunna dai. Dan wannan ƴar iskar amaryar da aka jajubo muku na fahimci da ƙarfinta tazo, gashi yarinyar nada ilimi fiye da tunaninki kuma goyon turai, ga kuɗi a gida, kuɗi a mota, kuɗi a Office, kuɗi a banki. Idan mukai sake fa komai zai koma wanwarne, ni ko da kishiya da yaƴanta su ji daɗin duniya ko komawa sama dani gara ace kowa ya mutu a ƙasar, ke ama busa ƙaho”.
Dariya Umma tayi da faɗin, “Hajjaju ke bala'i ce ai, shiyyasa nake sake tausayin Matar gidan nan naki. Yanzu ke miye shawararki?”.
“Dole ne muyi bincike akan yarinyar mu samo wanda zamu shiga jikinsa nata mu mata rugu-rugu”.
“Tab babbar magana ta yaya kenan? Bayan kin san daga wane gida ta fito, gate ɗin gidan su ma taɓa shi ba masifa bane balle shiga gidan”.
“Kwantar min da hankalinki. Akwai matar nan mai min ƙunshi ranar ana labarin dukiyar da aka zubar a auren ita yarinyar da aka kai gidanku take cewa ai ita taga zahiri dan itace kema matar Alhaji Garko ƙunshi shekaru kusan shidda kenan, shiyyasa tasan abubuwa da yawa a gidan nan ko shagalin bikin nan duk akan idonsu akai komai. Ita kanta taci rabonta dan tayi ƙunshi sosai a gidan, sai dai ta fahimci kamar matar Alhaji Garko bata son auren fin ƙarfinta akayi, yarinyar da ɗan uwanta aka saka mata biki lokaci guda ta birkice wai sai yaron gidanku”.
“Kai haba da gaske wai? Anya ba asiri suka mata ba ma kuwa”.
“Wlhy haka tace, babu abinda Hafsatu bazata iyaba wlhy, wama ya sani. Shiyyasa nake ganin ya kamata muje gidan Alhaji Garko mu kunnowa Hafsatu wutar da zata ƙoneta ƙurmus har ƴaƴan nata a wannan karon. Ba suna murna sun samu ɗiyar biloniya ba. Zasuci ubansu ne”.
Dariya suka kwashe da ita suna tafawa......
_____________★★
Kwanaki sun ƙara shiɗawa, dan a lissafin Lulu dai next week ne rabuwarsu da Smart. A week ɗin daya wuce ya kaita gidansu da gidan Uncle Yousuf, daga nan ta samu ƙafar zuwa duk bayan kwana biyu haka idan ta fita aiki takan leƙasu duk da dai daga Daddy har Uncle Yousuf ɗin ma dai sunyi tafiya basa ƙasar ma. A ranta a duk sanda ta ƙiyasta tana jin farin cikin komawarta free dan ta fara jin ƙosawa da tsakurarsa musamman ta saka hijjabi da tafi cimata zuciya da rai fiye da komai. Sai dai wani sashe na zuciyar tata na mata kamar babu daɗi musamman idan ta tuna Ammah da ƴan uwansa. Takan faɗa dogon nazari akan hakan, amma idan taje duba jikin kakanta Alhaji Garko da har yanzu dai babu lafiya suna ma shirin fita da shi ƙasar ne duk da yana turjewa sai da Dada taita mata fanfo da zugeta. Wani lokacin Lulun kan nutsu ta saurareta, wani lokacin kuma tace “Kai Dada dan ALLAH wai miye matsalarki da Aliyu ne? Miyay miki?”. Dadan kan zazzageta wani lokacin ko balbaleta da faɗa dan masifaffiyar mata ce. Wannan faɗan da take takura mata da shi yasa kwana biyu Lulu bataje gidan ba, sai dai tai kira a waya taji yaya jikinsa. Hakan sai ya fara damun Dada, dan a ganinta wani asirin Smart ya sake tafkawa Lulu...
A ranar Juma'a da Lulu ke cika kwanaki uku rabonta da zuwa gidan Smart ya wuce Legos, Maryam da Asma'u aka kawo mata su tayata kwana, sai Mubarak da zaizo da dare, sai su Afrah suma da taje da kanta ta ɗebo. Nan fa shafta ta buɗe. Wucewar su Maryam ya ƙara zafar Umma, tai shiri ta nufi gidan aminiyarta Hajiya Naqiba rai ɓace. Bayan ta gama labarta mata Hajiya Naqiba tace tashi muje yau ayita ta ƙare. Sun je gidan mai ƙunshi da tace zatai musu rakkiya. Daga can suka tafi gidan Alhaji Garko. Sosai Umma ta sake girgiza da dukiyar waɗan nan mutane, nan fa zuciyarta ta ƙara ƙaimi wajen ƙulle-ƙulle na ganin auren Smart da Lulu ya gundile. Sunyi zama fin na awa ɗaya kafin hamshaƙiyar tsohuwa mai ji da kuɗi da hutu ta fito cikin isa da izzarta. Ai sai su Umma sukai saƙale suna kallon ikon ALLAH, dan Dada ta tsufa sosai kawai dai abinka da jin daɗi ne. Cikin girmamawa suka gaisheta tana amsa musu da ƙyar a yamutse. Mai ƙunshi ta mata bayani duk da dama ta fara sanar matan. Amma tsohuwar nan saita dubi su Umma a watse cike da isa ta ce, “Ku tabbatar duk abinda zai fito bakinki bazai zama wuƙar yankaku ba, dan bana son munafunci ni da kuke gani na anan”.
Muryar Umma na rawa ta ce, “Wlhy Hajiya a duk abinda mukazo miki da shi nan babu munafunci. Yaron nan asiri yayma ƴarku. Idan kuma baki yarda ba kisa malamai su bincika muku zaki fahimci gaskiyarmu. Amma kuyi da sauri dan yanzu haka yayi tafiya wai Niger da abokinsa kin san kuma yanda suka iya asiri bana raba ɗayan biyu wani bala'in zai sake haɗo muku (😂 Niger akacema su Umma Smart ya tafi raka Ahmad sayen shanu).
Mai ƙunshi da yake itama makirar mace ce tana kuma son sake samun fada a wajen Hajiya Dada sai ta sake taƙarƙarewa tana taya su Umma. Harda cewa zata raka Dada wajen wani malami a duba musu ɗan uwanta ne a Zuru yake. Amma batai maganar hakan ba sai da su Umma suka fito bayan an sallamesu. Hankalin Dada ya tashi, dan haka ta sallami su Umma tace mai ƙunshi tazo ta sameta gobe idan ALLAH ya kaimu bayan an wuce da Alhaji Garko dan zasuyi gaba ƙasar London ita sai nan da sati ɗaya zatabi bayansu. Cike da farin ciki su Umma suka fito da ƙyautar naira dubu ɗari kowa hansin-hansin. Mai ƙunshi kuwa ma basu san mi aka bata ba. Ta kumace dole su cire mata kasonta a ciki dan bazata rakosu a banza ba. Da ƙyar suka bata goma-goma suna ƙunƙuni. Tace oho dai shegu ai ni kunzo min da hanyar samun kuɗi, naci a wajenku, naci a wajenta, naci a wajen malamin da kukace aje.
Washe garin asabar aka wuce da Alhaji Sufi Garko ƙasar London dan likitoci anan gida Nigeria sun tabbatar poising ɗinsa akayi. Ba'a fahimci hakan ba kuma sai a tsakanin kwana biyun nan da gubar ta bayyana kanta, dan sun bashi wadda bata bayyana kanta da wuri har sai tayima jiki illa ne. Duk da wannan tashin hankalin da ake ciki hankalin Dada nakan Lulu da itama dai yau tazo gidan har da su Asma'u da su Afrah. Sai dai taƙi yarda ko sau ɗaya su zauna da Dada har sanda ambulance ta ɗauki Baba itama sai taja ƴan rakkiyarta suka bisu har airport. Basu baro ba sai da jirgin da za'a ɗauke sa a ciki shi kaɗai sai yaransa maza biyu ƙannen Alh Sulaiman da zasuyi gaba ya tashi. Kowa ya bisu da addu'a kafin yaje. Suna baro airport ɗin jirgin da ya ɗakko Tajuddeen da Alhaji Sulaiman (Tsule🤣) ya sauka shi kuma. Ya samu sauƙi sosai koma muce a zahiri ya warke, sai dai a zuciya kam babu abinda ya ragu na soyayyar da yakema Lulu. Ya samu kwanciyar hankali da nutsuwar zuciyane kawai bisa alƙawarin da mahaifinsa yay masa na sai ya mallaka masa Mawaddat ya kwantar da hankalinsa. Wannan dalili ne ya sashi jin ƙwarin gwiwar biyosa suka dawo. Manyan aminansa na yanzu duk da dama can aminan nasa ne matsaloli suka rabasu Alhaji Baita, Hon. Nakowa. Da Hon. Misau ne sukaje tarbarsu. Dan kaf Family na Garko babu wanda yasan da dawowar tasu a yau.......✍️
(🤔Tofa! Alhaji Sufi Garko ya tafi jiyya a dalilin poising nashi da akace anyi. Alhaji Sulaiman Sufi Garko ya dawo tare da ɗansa Tajuddeen Sulaiman Sufi Garko daya tashi a jiyyar soyayya babu wani damuwa tattare da al'amarin su. Anya kuwa babu wani abu a ƙasa? Humm kumu dai je zuwa to🚴).
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 8️⃣2️⃣
.......Dada tayi tunanin Lulu zata sake dawowa gidan, amma bayan duk ƴan rakkiyar Baba sun dawo sai gashi babu ita, sai ma sanar mata da akai ta wuce gidan ta. Hakan ya sake girgiza Dada ta kuma tabbatar da eh lallai da alamar ƙamshin gaskiya a zancen mutanen nan asiri yaron nan yay ma jikarta. A take ta dannama Fulera mai ƙunshi kira, batare dako amsa gaisuwar ta ba tace ta sameta yanzun. Fulera ido a kuɗi tuni tai tsalle tayo waje da ga gidan su, dan dama dai zawarci take kusan shekara tara kenan. Cikin ƙanƙanin lokaci sai gata a Garko house. Ta sami Hajiya Dada tare da mai aikinta dake mata irin waɗan nan ayyukan na sirri, dan Dada tunda jajayen sawu ƴan hannun bin malamai ne kam. Cikin gurfana Fulera ta miƙa gaisuwa, Dada ta amsa cike da isa. Babu wani jan lokaci ta sanar musu abinda take son a mata. Zasuje wajen mutumin da tace mata a Zuru ita da mai aikinta. Ba haka Fulera taso ba, amma dai babu damar musu dan haka ta amsa da to. Mota Dada ta bada akaisu tare da kuɗin amma sai ta damƙawa mai aikin nata. Nan ma Fulera taji zafi, ta dai danne, damar fara fita data samu kafin mai aikin Dada ta kimtso ta samu ta dannama Hajiya Naqiba kira ta sanar mata komai. Dariya Hajiya Naqiba tai da faɗin, “Kai tsohuwar nan mayyace akwai shegen wayo. Barta ai inta san wata bata san wata ba. Kwantar da hankalinki bari na kirashi kafin ku isa.”
Haka kuwa akai hajiya Naqiba tai kiran malam na-zuru, duk yanda suke so haka ta tsara masa, shima da yake shegen kansa ne yace karta damu. Abinka da lafiyayyar mota basu sha wahala ba, dan bayan azhar kaɗan suka isa zuru saboda gudu na masifa da drivern yayi. Malam na-zuru da yake yasan da zuwansu kafin ma su faɗi abinda ya kawosu ya shiga zayyane musu wai ai ya gani ne a cikin aikinsa. Tuni mai aikin Dada ta ruɗe ta danna mata kira, nan ma fa sukai magana da malam Na-zuru ya sake fanfa Dada da kalolin sharri wa Smart dangane da auren Lulu, harda cewa ai asiri Smart ɗin yay musu dan yaga kuɗi. A yanzu haka ma yana Niger yaje anyo masa wani babban ƙulli, zaita kwantar musu da kai ya nuna shi na ALLAH ne sai anan gaba kaɗan zai bayyana halayyarsa da mugun nufinsa. Tsaf Dada tahau ta zauna saboda tayi imani da malaman tsubbu matuƙa gaya. Malam na-zuru ya haɗa musu kayayyaki
Showing 147001 words to 150000 words out of 294165 words
“Nami kuma kenan?”.
“Akan ƙawar taki dai, dan bazan iya haƙura ba.”
“Abu mai wahala kenan, dan ta yanke alaƙarmu, tare da gargaɗin nisantar ta. Nasan halinta kuma sarai idan ta faɗi abu har cikin ranta ne. Abu ne mai matuƙar wahala Lulu ta sake kallona balle har na shiga jikinta”.
“Zamu iya amfani da wata ai, amma ya zama ke zakina controlling nata”. Cewar Asim.
Kai Nadiya ta jinjina da faɗin, “Wai babbar magana. Na fahimci bakusan wacece Lulu ba. Kubar ganinta haka batajin magana tasan mitakeyi. Sannan koni kaina nasha wahala kafin mu fara abota gaskiya, dan bata da saurin sakewa da mutane, sannan ba kowa ke iya haƙuri da halin Lulu ba”.
“Karki damu inhar aka jajirce wannan ba komai bane ba. Sannan kema fa akan aikin nan zakija manda. Dan a yanzu haka zamu sauke miki miliyan ɗaya kafin ma aikin ya fara”.
Sosai Nadiya ta zaro ido waje, ranta fal farin ciki ta ce, “Yanzu yaya kuke so ayi?”.
Kallon juna sukai da murmushi, kafin Asim ya miƙa mata card da faɗin, “Ki samemu a wannan address ɗin zuwa anjima”.
“Wannan yafi komai sauƙi”.
Ta faɗa tana amsar card ɗin........
_______________★
Kwanaki uku kenan da fara fitar Lulu aiki, kullum kuma Smart ke kaita office da safe sannan shima ya koma gidan yay shirin tashi fitar a Napep. Idan ko fita ta kamata a yinin mai Napep ɗin nan da bata san da shi ba na biye da ita. Duk kuma inda ta saka ƙafa ana sanar masa. A lissafinsa dai babu wani abu dake faruwa, dan ranar farko ta sayi bread wanda bai san a tsakkiyarsa aka saka mata kayan shaye-shayen ta ba, kamar yanda takeyi sai zata kwanta tasha hakan tayi, shiyyasa bai gane komai ba sai ya ɗauka kawai gajiyar aikin data koma ce tunda tayi ƴar zirga-zirga. Washe gari dai yaga ta tashi a tsayenta bakamar kwana biyu datai wani sukuku ba. Rana ta biyu ma sai da tai amfani da dabarun nasu ta amsa, hakama jiya. Yau cikon kwana na uku yaso ya ɗan fara tsarguwa, amma dai baice komai ba. Yana son mata tambaya akan zuwa gidan su Sa'id sai kuma dai yay shiru. Sai kuma gashi a yau yana tare da Coach kira ya sameshi da ga Ammah wai yazo da sauri idan yana kusa. Ya Isa gidan da tunani kala-kala sai ya ɓige da samun mahaifiyar Sa'id da wasu ƴan uwanta maza uku dan dangin mahaifinsa sun rantse bazasu zo ba, ita data ɓata taje ta gyara sun dai zo na farko. Ba Smart kaɗai ba kowa ma na gidan nan yau mamakin jin maman Sa'id wai sunzo bada haƙuri ne da neman afuwar Hawwah dan ALLAH tai haƙuri ta koma yake. Smart yace shifa ƴar uwarsa bazata koma wannan gida ba, anyi kenan takardar saki kawai yake buƙata Sa'id ya kawo, dan suna sonta baza'a kashe musu yarinya ba. Sosai Maman Sa'id ke faman magiya akan wancan ma daya faru tsautsayi ne da munafuncin munafukai, amma yanzu ta gane gaskiya. Ankai ruwa rana matuƙa kafin Smart ya haƙura zata koman amma ba wannan gidan ba. Da sauri Mama tace ta yarda, Hawwah ta zaɓi duk inda take so a gidajensu a gyara mata. Wannan abu yaba kowa mamaki, Umma na son magana tana tsoron ta tanka Maman Sa'id tai mata bankaɗa tunda taji tana shaguɓe akan munafukai, ba kowa kuma ne mai zuwa ɓata Ammah da Hawwah a wajenta ba sai ita dama. Bayan wucewarsu kowa ya shiga mamaki, Abba ya tsare Smart akan miya ma maman Sa'id ɗin har tai irin wannan sakkowar lokaci ɗaya. Ya tabbatar musu bashi bane, dan shi target ɗinsa akan jiran dawowar mahaifin Sa'id ne ai. Yana son kawo Lulu a ransa wani gefe na zuciyarsa na musa masa. Amma dai duk da haka bayan ya koma gida da daddare sai da ya kasa haƙuri yay mata tambaya. Dariya kawai tayi taƙi faɗa masa komai, hakan ya tabbatar masa itace kenan tayi koma miye. Sai kawai ya zuba mata ido yana jin wani abu mai girma na ƙara ratsashi a kanta. Jin kaifin idanunsa a kanta ya sata dakatawa da ga abinda take a system ta ɗago, harararsa tai da faɗin, “Malam wannan kallon fa? Ni fa bana son kallo”. Ta ƙare maganar da murguɗa baki. Murmushi ya saki mai sanyi batare da ya janye idanun ba, sai ya samu kansa da furta, “Kullum sake mamaye komai da komai kike yi”. Bata fahimci ina ya dosa ba, sai dai yanda yay maganar a ƙasan maƙoshi da tausasa fitar sautin matuƙa ya sata tsayawa kallonsa, “Lafiya kake kuwa? Kodai kaima ka fara ban sani ba?”.
“Na fara mi?”.
“A hawa network mana”.
Ƙaramar dariya yay yana girgiza kansa. “Tom maybe na fara amma nawa ba irin naki bane gaskiya. Kema fata nake ki daina wannan ai ki dawo wannan irin nawan”.
Nan ɗin ma dai ba fahimtar tai ba, dan haka ma ta taɓe baki da miƙewa tana faɗin, “Ai kai kam wani lokacin kamar mai aljanu. Dolene na sanarma Ammah ta fara maka addu'ar su ko ka kwaso a drivern cin ba'a sani ba”. Daga haka ta wuce bedroom ta barshi yana murmushi.........✍️
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 8️⃣1️⃣
.........Washe gari gidansu ya wuce bayan ya sauketa, anan ne yake samun Abba da Ammah da batun shifa yana zargin Mawaddat ce tayi koma miye. Dan an sanar masa taje gidan a ranar monday. Mamaki sukaitayi suma da tunanin to mita faɗa ma maman Sa'id da har ta risina haka da sauri. A gefe kuma ƙaunar yarinyar na sake shigar musu zukata. Kamar yanda akace sati ɗaya cikin satin Hawwah ta fara shirin komawa sabon gidanta danƙarere. Hankalin Umma ya sake tashi, da bin ƙwanƙwanto ta gano Lulu ce tamayi koma miye har komai ya dai-daita. Hankali a tashe ta nufi gidan Hajiya Naqiba ƙawarta. Acan suka baje faifain zagin Ammah da bata san sunayi ba da Ƴaƴanta suna neman mafita dan abubuwa fa nata faman kufce musu a hannu, sai dai gaba ɗaya hankalinsu da mugayen ƙudirinsu sun tattara ne ga Lulu yanzu. Dan sun fahimci shigowarta gidan abubuwa da yawa ke neman taɓarɓarewa. Duk da su basu fahimci cewar asirin jikin Smart ma ya gama warwarewa gaba ɗaya ba. Ga aikin Malam na-zuru yaƙi yiwuwa, dan kayan Lulu da Smart dai sun gagara ɗakkuwa. Hajiya Naqiba ce cikin dogon tunani ta ce, “Aminiya anya bazamu canja taku ba?”.
“Kamarya? Fito kimun dalla-dalla, kin san bana son kwana-kwana fa”.
“Ina nufin ba asiri bane kaɗai yanzu ya kamata musa gaba dole mu haɗa da makirci da kissa. Kamar dai yanda nai akan shegun yaran can na baƙar dagar tawa.”
“In dai wannan ne ai mun jima munayi Aminiya, yanzu ko ita akan wannan shegiyar da zata koma Hawwah ai kinga sai da muka haɗa da makirci waccan shegiyar da bamu san mitaje tayi ba ta ɓata mana komai.”
“Kwantar da hankalinki karki damu, murnarsu zata koma ciki ne. Yanzu mu fara kai wannan baƙuwar hauren ƙasa tukunna dai. Dan wannan ƴar iskar amaryar da aka jajubo muku na fahimci da ƙarfinta tazo, gashi yarinyar nada ilimi fiye da tunaninki kuma goyon turai, ga kuɗi a gida, kuɗi a mota, kuɗi a Office, kuɗi a banki. Idan mukai sake fa komai zai koma wanwarne, ni ko da kishiya da yaƴanta su ji daɗin duniya ko komawa sama dani gara ace kowa ya mutu a ƙasar, ke ama busa ƙaho”.
Dariya Umma tayi da faɗin, “Hajjaju ke bala'i ce ai, shiyyasa nake sake tausayin Matar gidan nan naki. Yanzu ke miye shawararki?”.
“Dole ne muyi bincike akan yarinyar mu samo wanda zamu shiga jikinsa nata mu mata rugu-rugu”.
“Tab babbar magana ta yaya kenan? Bayan kin san daga wane gida ta fito, gate ɗin gidan su ma taɓa shi ba masifa bane balle shiga gidan”.
“Kwantar min da hankalinki. Akwai matar nan mai min ƙunshi ranar ana labarin dukiyar da aka zubar a auren ita yarinyar da aka kai gidanku take cewa ai ita taga zahiri dan itace kema matar Alhaji Garko ƙunshi shekaru kusan shidda kenan, shiyyasa tasan abubuwa da yawa a gidan nan ko shagalin bikin nan duk akan idonsu akai komai. Ita kanta taci rabonta dan tayi ƙunshi sosai a gidan, sai dai ta fahimci kamar matar Alhaji Garko bata son auren fin ƙarfinta akayi, yarinyar da ɗan uwanta aka saka mata biki lokaci guda ta birkice wai sai yaron gidanku”.
“Kai haba da gaske wai? Anya ba asiri suka mata ba ma kuwa”.
“Wlhy haka tace, babu abinda Hafsatu bazata iyaba wlhy, wama ya sani. Shiyyasa nake ganin ya kamata muje gidan Alhaji Garko mu kunnowa Hafsatu wutar da zata ƙoneta ƙurmus har ƴaƴan nata a wannan karon. Ba suna murna sun samu ɗiyar biloniya ba. Zasuci ubansu ne”.
Dariya suka kwashe da ita suna tafawa......
_____________★★
Kwanaki sun ƙara shiɗawa, dan a lissafin Lulu dai next week ne rabuwarsu da Smart. A week ɗin daya wuce ya kaita gidansu da gidan Uncle Yousuf, daga nan ta samu ƙafar zuwa duk bayan kwana biyu haka idan ta fita aiki takan leƙasu duk da dai daga Daddy har Uncle Yousuf ɗin ma dai sunyi tafiya basa ƙasar ma. A ranta a duk sanda ta ƙiyasta tana jin farin cikin komawarta free dan ta fara jin ƙosawa da tsakurarsa musamman ta saka hijjabi da tafi cimata zuciya da rai fiye da komai. Sai dai wani sashe na zuciyar tata na mata kamar babu daɗi musamman idan ta tuna Ammah da ƴan uwansa. Takan faɗa dogon nazari akan hakan, amma idan taje duba jikin kakanta Alhaji Garko da har yanzu dai babu lafiya suna ma shirin fita da shi ƙasar ne duk da yana turjewa sai da Dada taita mata fanfo da zugeta. Wani lokacin Lulun kan nutsu ta saurareta, wani lokacin kuma tace “Kai Dada dan ALLAH wai miye matsalarki da Aliyu ne? Miyay miki?”. Dadan kan zazzageta wani lokacin ko balbaleta da faɗa dan masifaffiyar mata ce. Wannan faɗan da take takura mata da shi yasa kwana biyu Lulu bataje gidan ba, sai dai tai kira a waya taji yaya jikinsa. Hakan sai ya fara damun Dada, dan a ganinta wani asirin Smart ya sake tafkawa Lulu...
A ranar Juma'a da Lulu ke cika kwanaki uku rabonta da zuwa gidan Smart ya wuce Legos, Maryam da Asma'u aka kawo mata su tayata kwana, sai Mubarak da zaizo da dare, sai su Afrah suma da taje da kanta ta ɗebo. Nan fa shafta ta buɗe. Wucewar su Maryam ya ƙara zafar Umma, tai shiri ta nufi gidan aminiyarta Hajiya Naqiba rai ɓace. Bayan ta gama labarta mata Hajiya Naqiba tace tashi muje yau ayita ta ƙare. Sun je gidan mai ƙunshi da tace zatai musu rakkiya. Daga can suka tafi gidan Alhaji Garko. Sosai Umma ta sake girgiza da dukiyar waɗan nan mutane, nan fa zuciyarta ta ƙara ƙaimi wajen ƙulle-ƙulle na ganin auren Smart da Lulu ya gundile. Sunyi zama fin na awa ɗaya kafin hamshaƙiyar tsohuwa mai ji da kuɗi da hutu ta fito cikin isa da izzarta. Ai sai su Umma sukai saƙale suna kallon ikon ALLAH, dan Dada ta tsufa sosai kawai dai abinka da jin daɗi ne. Cikin girmamawa suka gaisheta tana amsa musu da ƙyar a yamutse. Mai ƙunshi ta mata bayani duk da dama ta fara sanar matan. Amma tsohuwar nan saita dubi su Umma a watse cike da isa ta ce, “Ku tabbatar duk abinda zai fito bakinki bazai zama wuƙar yankaku ba, dan bana son munafunci ni da kuke gani na anan”.
Muryar Umma na rawa ta ce, “Wlhy Hajiya a duk abinda mukazo miki da shi nan babu munafunci. Yaron nan asiri yayma ƴarku. Idan kuma baki yarda ba kisa malamai su bincika muku zaki fahimci gaskiyarmu. Amma kuyi da sauri dan yanzu haka yayi tafiya wai Niger da abokinsa kin san kuma yanda suka iya asiri bana raba ɗayan biyu wani bala'in zai sake haɗo muku (😂 Niger akacema su Umma Smart ya tafi raka Ahmad sayen shanu).
Mai ƙunshi da yake itama makirar mace ce tana kuma son sake samun fada a wajen Hajiya Dada sai ta sake taƙarƙarewa tana taya su Umma. Harda cewa zata raka Dada wajen wani malami a duba musu ɗan uwanta ne a Zuru yake. Amma batai maganar hakan ba sai da su Umma suka fito bayan an sallamesu. Hankalin Dada ya tashi, dan haka ta sallami su Umma tace mai ƙunshi tazo ta sameta gobe idan ALLAH ya kaimu bayan an wuce da Alhaji Garko dan zasuyi gaba ƙasar London ita sai nan da sati ɗaya zatabi bayansu. Cike da farin ciki su Umma suka fito da ƙyautar naira dubu ɗari kowa hansin-hansin. Mai ƙunshi kuwa ma basu san mi aka bata ba. Ta kumace dole su cire mata kasonta a ciki dan bazata rakosu a banza ba. Da ƙyar suka bata goma-goma suna ƙunƙuni. Tace oho dai shegu ai ni kunzo min da hanyar samun kuɗi, naci a wajenku, naci a wajenta, naci a wajen malamin da kukace aje.
Washe garin asabar aka wuce da Alhaji Sufi Garko ƙasar London dan likitoci anan gida Nigeria sun tabbatar poising ɗinsa akayi. Ba'a fahimci hakan ba kuma sai a tsakanin kwana biyun nan da gubar ta bayyana kanta, dan sun bashi wadda bata bayyana kanta da wuri har sai tayima jiki illa ne. Duk da wannan tashin hankalin da ake ciki hankalin Dada nakan Lulu da itama dai yau tazo gidan har da su Asma'u da su Afrah. Sai dai taƙi yarda ko sau ɗaya su zauna da Dada har sanda ambulance ta ɗauki Baba itama sai taja ƴan rakkiyarta suka bisu har airport. Basu baro ba sai da jirgin da za'a ɗauke sa a ciki shi kaɗai sai yaransa maza biyu ƙannen Alh Sulaiman da zasuyi gaba ya tashi. Kowa ya bisu da addu'a kafin yaje. Suna baro airport ɗin jirgin da ya ɗakko Tajuddeen da Alhaji Sulaiman (Tsule🤣) ya sauka shi kuma. Ya samu sauƙi sosai koma muce a zahiri ya warke, sai dai a zuciya kam babu abinda ya ragu na soyayyar da yakema Lulu. Ya samu kwanciyar hankali da nutsuwar zuciyane kawai bisa alƙawarin da mahaifinsa yay masa na sai ya mallaka masa Mawaddat ya kwantar da hankalinsa. Wannan dalili ne ya sashi jin ƙwarin gwiwar biyosa suka dawo. Manyan aminansa na yanzu duk da dama can aminan nasa ne matsaloli suka rabasu Alhaji Baita, Hon. Nakowa. Da Hon. Misau ne sukaje tarbarsu. Dan kaf Family na Garko babu wanda yasan da dawowar tasu a yau.......✍️
(🤔Tofa! Alhaji Sufi Garko ya tafi jiyya a dalilin poising nashi da akace anyi. Alhaji Sulaiman Sufi Garko ya dawo tare da ɗansa Tajuddeen Sulaiman Sufi Garko daya tashi a jiyyar soyayya babu wani damuwa tattare da al'amarin su. Anya kuwa babu wani abu a ƙasa? Humm kumu dai je zuwa to🚴).
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 8️⃣2️⃣
.......Dada tayi tunanin Lulu zata sake dawowa gidan, amma bayan duk ƴan rakkiyar Baba sun dawo sai gashi babu ita, sai ma sanar mata da akai ta wuce gidan ta. Hakan ya sake girgiza Dada ta kuma tabbatar da eh lallai da alamar ƙamshin gaskiya a zancen mutanen nan asiri yaron nan yay ma jikarta. A take ta dannama Fulera mai ƙunshi kira, batare dako amsa gaisuwar ta ba tace ta sameta yanzun. Fulera ido a kuɗi tuni tai tsalle tayo waje da ga gidan su, dan dama dai zawarci take kusan shekara tara kenan. Cikin ƙanƙanin lokaci sai gata a Garko house. Ta sami Hajiya Dada tare da mai aikinta dake mata irin waɗan nan ayyukan na sirri, dan Dada tunda jajayen sawu ƴan hannun bin malamai ne kam. Cikin gurfana Fulera ta miƙa gaisuwa, Dada ta amsa cike da isa. Babu wani jan lokaci ta sanar musu abinda take son a mata. Zasuje wajen mutumin da tace mata a Zuru ita da mai aikinta. Ba haka Fulera taso ba, amma dai babu damar musu dan haka ta amsa da to. Mota Dada ta bada akaisu tare da kuɗin amma sai ta damƙawa mai aikin nata. Nan ma Fulera taji zafi, ta dai danne, damar fara fita data samu kafin mai aikin Dada ta kimtso ta samu ta dannama Hajiya Naqiba kira ta sanar mata komai. Dariya Hajiya Naqiba tai da faɗin, “Kai tsohuwar nan mayyace akwai shegen wayo. Barta ai inta san wata bata san wata ba. Kwantar da hankalinki bari na kirashi kafin ku isa.”
Haka kuwa akai hajiya Naqiba tai kiran malam na-zuru, duk yanda suke so haka ta tsara masa, shima da yake shegen kansa ne yace karta damu. Abinka da lafiyayyar mota basu sha wahala ba, dan bayan azhar kaɗan suka isa zuru saboda gudu na masifa da drivern yayi. Malam na-zuru da yake yasan da zuwansu kafin ma su faɗi abinda ya kawosu ya shiga zayyane musu wai ai ya gani ne a cikin aikinsa. Tuni mai aikin Dada ta ruɗe ta danna mata kira, nan ma fa sukai magana da malam Na-zuru ya sake fanfa Dada da kalolin sharri wa Smart dangane da auren Lulu, harda cewa ai asiri Smart ɗin yay musu dan yaga kuɗi. A yanzu haka ma yana Niger yaje anyo masa wani babban ƙulli, zaita kwantar musu da kai ya nuna shi na ALLAH ne sai anan gaba kaɗan zai bayyana halayyarsa da mugun nufinsa. Tsaf Dada tahau ta zauna saboda tayi imani da malaman tsubbu matuƙa gaya. Malam na-zuru ya haɗa musu kayayyaki
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50 Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99